Citation: Karofi, I.A., Ado. A. and Lawal, M. (2024). Tarken Tubalan Gina Jigon Gargaɗi a Waƙar ‘Korona Biros’ ta Abdullahi Abubakar Lamiɗo. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 280-288. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.034.
TARKEN TUBALAN
GINA JIGON GARGAƊI
A WAƘAR
‘KORONA BIROS’ TA ABDULLAHI ABUBAKAR LAMIƊO
Isah Abubakar
Karofi
Sashen Nazarin
Harshen Hausa,
Kwalejin Ilimi ta
Isa Kaita, Dutsinma, Katsina
Abdulrahman Ado
Sashen Harsunan
Nijeriya,
Jami’ar Umaru Musa
Yar’adua, Katsina
Muntari Lawa
Department of
English
Isa Kaita College
of Education, Dutsinma, Katsina
Tsakure
Rubutacciyar waƙa saƙo ne
wanda aka gina shi a kan tsari mai ƙa’ida
ta baiti, ɗango, kari,
amsa-amo da rerawa da daidaita kalmomi da zaɓen
su da amfani da su cikin sigogin da ba lalle ne haka suke a maganar baka ba.
Don haka, marubuta waƙoƙin Hausa na tsara waƙoƙinsu domin su isar da saƙonninsu
a kan fannoni daban-daban ta hanyar amfani da wasu tubala waɗanda za su taimaka masu
wajen cim ma saƙon da suke son isarwa ga jama’a. Wannan takarda ta fito da yadda Abdullahi Abubakar
Lamiɗo ya yi amfani da
wasu tubala wajen tsara saƙon da waƙarsa take son isarwa ga masu karatu. An yi amfani da salon
nazari wajen fitar da wasu tubala guda shida waɗanda
suka gina babban jigon waƙar na gargaɗi.An
gudanar da wannan bincike bisa manufar bayyana wa masu nazari wasu tubalan da
mawaƙan
Hausa sukan yi amfani da su domin gina waƙoƙinsu domin cim ma manufofinsu na yin waƙoƙin. An
bi hanyoyi biyu kawai a wajen gudanar da wannan binciken, wato hanyar karantawa
daga wasu rubutattun bayanai da suka danganci rubutaccen adabi da kuma hira da
aka yi da wasu masana a kan rubutaccen adabi. An ɗora
wannan bincike a kan ‘Ra’in Gudummuwar Adabi’. Sakamakon binciken ya nuna cewa,
ana iya yin amfani da tubalan nazarin waƙoƙin Hausa, waɗanda wasu masana nazarin waƙoƙin
Hausa suka samar, domin yin nazarin kowace irin waƙa ta Hausa, don bayyana
manufar waƙoƙin
Hausa, waɗanda
marubuta waƙoƙin
Hausa suke rubutawa.
Fitilun Kalmomi: Tarke,
Tubalai, Jigo, Gargaɗi,
Waƙar
Korona Biros, Abdullahi Abubakar Lamiɗo
Gabatarwa
A wannan bincike, an yi nazarin
yadda wani marubucin waƙoƙin Hausa, watoAbdullahi Abubakar
Lamiɗo ya rubuta waƙarsa a kan annobar “Korona
Biros.” A cikin waƙar, an yi
nazarin yadda ya yi amfani da wasu tubalan nazarin waƙoƙi, waɗanda shi marubucin ya yi amfani
da su ya gina waƙarsa a
bisa jigon gargaɗi.
2.0 Sharar Fage
Jigon gargaɗi
wani babban jigo ne da marubuta waƙoƙin Hausa suke gina waƙoƙinsu da shi, domin fitar da manufofin da
suka sanya aka rubuta waƙar.
Cutar Korona biros kuwa, wata muguwar annoba ce da ta faro daga gabashin duniya
a hankali-a-hankali ta watsu tamkar wutar daji zuwa sassan duniya gabas da
yamma, kudu da arewa(Bala da Imam, 2020:100).
Cutar ba ta
bar manyan garuruwa ba ballantana ƙananan garuruwa waɗanda ƙarancin kula da lafiya ya yi masu zaman dirshan. Wannan
takarda ta yi duba ne a kan jigon gargaɗi a waƙar Korona biros wadda Abdullahi Abubakar Lamiɗo
ya rubuta a yayin da cutar Korona ta zaman wa duniya babban ƙalubale ta fuskar magancewa. Malam Abdullahi ya yi amfani
da ƙananan jigogi cike da kalmomi na hikima
masu ɗauke da zantuka ko saƙonni wajen ƙulla gargaɗi a
kan illar cutar Korona Biros kamar yadda ya kira ta a waƙarsa. Tubulan ko ƙananan
jigogi sun ba marubucin damar ƙara wa waƙar tsawo da armashi ga masu karantawa.
3.0 Manufar Bincike
An gudanar da wannan bincike
bisa manufar bayyana wasu tubalan nazari da wasu masana suka samar domin yin
nazarin rubutattun waƙoƙi a Hausa.
Haka kuma, ana son a bayyana
ire-iren wasu daga cikin tubula koƙananan jigogin nazarin waƙoƙin da
Abdullahi ya yi amfani da su wajen gina kalmomin gargaɗi a
cikin waƙarsa ta Korona Biros.
Bayan nan, ana son a kuma
bayyana yadda Malam Abdullahi ya yi amfani da waɗannan
tubala wajen gina waƙarsa ta
gargaɗi a kan annobar Korona Biros.
4.0 Hanyoyin Gudanar da Bincike
An bi hanyoyi guda biyu wajen
gudanar da wannan bincike. Da farko, an bi hanyar karantawa daga wasu
rubutattun bayanai, waɗanda suka haɗa da bugaggun littattafai da kundayen bincike da mujallu da
wasu takardu da aka gabatar a wasu tarurrukan ƙara wa juna sani.
Hanya ta biyu kuwa, ita ce ta
yin hira da wasu mutane da aka gana da su. A nan, an yi hira da ɗaya daga cikin editocin littafin wato Khalid Imam, wanda aka
samu wasu bayanai da aka sanya a cikin wannan bincike. Haka kuma, an yi hira da
wasu masana rubutaccen adabin Hausa. A wajensu aka samu wasu bayanai na tubalan
nazarin waƙoƙin baka da kuma wasu ƙananan jigogin da suke ɗauke da ire-iren waɗannan tubala.
5.0 Hanyar Ɗora Aiki
An ɗora
wannan takarda bisa ‘Mazhabar Rubutacciyar Waƙar
Baka’. Wannan ra’i ne wanda ya fi mayar
da hankali ne ga tattaro ra’ayoyin manazarta kan hanyar nazarin rubutacciyar waƙar Hausa. Masanin da ya assasa wanna ra’i shi ne Farfesa Abdulƙadir Ɗangambo a shekara ta 1975 har ya
rubuta littafi mai suna Gadon Feɗe Waƙa. A
kuma 1981 ya fito da Ɗaurayar
Gadon Feɗe Waƙa da kuma Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa
(Sabon tsari) a shekarar ta 2007. Masanin ya assasa wannan ra’in domin samar da
hanyar nazarin rubutacciyar waƙa na
bai-ɗaya karɓaɓɓe ga kowane mai nazari. Daga cikin magoya bayan
wannan ra’i akwai; Abdullahi Bayero Yahya da Isa Mukhtar da Aminu Lawal Auta da
Halima Abdulƙadir Ɗangambo da Ɗahiru Abdulƙadir da Mustapha Shu’aibu da sauransu (Gusau, 2015:21-22).
Da
yake takardar tana magana ne a kan tubalan da suka gina jigon gargaɗi na
waƙar ‘Korona Biros’ ta yi daidai da yadda Mazhabar
Rubutacciyar Waƙar Baka ta bayyana yadda ƙananan jigogi irin su faɗakarwa da gargaɗi da jan hankali da wa’azi da nasiha da sauransu a
matsayin tubalan da suke haɗuwa su tayar da babban a rubutacciyar waƙar baka. Waɗannnan tubala da Mazhabar ta zo da su an yi amfani
da su wajen cim ma burin takardar.
6.0 Bayanin
Diddigin Waƙa
Bayanin
diddigin waƙa ya danganci sanin salsalar waƙa da bayanin yadda aka sami waƙar domin tarke ko nazarinta. Haka kuma, a tabbatar da
shekarar da aka yi wannan waƙa (Yahya,
2014, sh.129).
Wannan waƙa an wallafa ta a shekarar 2020 a cikin littafin Corona Blues (A Bilingual Anthology
of Poetry), wanda Ismail Bala da Khalid Imam suka yi wa edita. Lambar fejin
waƙar 122 zuwa 125. Waƙar ‘yar ƙwar huɗu ce mai baiti talatin da huɗu
(34).
Abubakar Abdullahi Lamiɗo an haife shi a garin Gombe kamar yaddaya nuna a cikin waƙar a baiti na 34.
6.1 Bayanin Tubalan Gina Jigo
Tubalan
ginin turke ko jigo wasu maganganu ne da aka bi aka ƙuƙƙulla waƙa da su don ta ƙara
tsawo, amma ba su ne babbar manufar waƙar
ba (Gusau, 2003 sh. 30).
Jigo kamar
yadda Auta (2017, sh. 139) ya bayyana shi, da muhimmin saƙo ko manufar da mawallafi yake son isarwa ga jama’a. Wato
abin da waƙa ta ƙunsa dangane da manufa. Ya ƙara da cewa a cikin waƙoƙi akan sami
wani baiti da mawallafi yakan faɗi ƙwayar
jigonsa. Wato saƙon waƙar, sannan ya yi amfani da jawabin jigo da za su taimaka
masa ya tayar da wannan ƙwayar
jigon. Domin gane jigon waƙa, ana iya
bin ta a taƙaice baiti bayan baiti ana taƙaita abin da mawallafi ya faɗa
ba tare da yi wa waƙar sharhi
ba.
Kowace waƙa tana ginuwa ne a kan jigo ko saƙo, abin da ya karkasu zuwa babban jigo da ƙaramin jigo ko turke da tubalai waɗanda
da su ne ake gina kowane jigon waƙa (Yahya,
2015 sh.10).
6.3 Wasu Tubalan Gina Jigon Gargaɗi a
Waƙar
C.N.H.N. (2006:159) ya bayyana ma’anar gargaɗi
da
“Jan
hankali ko yin kashedi ko horo”.
Dangane da
abin da masana suka bayyana a kan ma’anar gargaɗi
kuwa, masana irin su (Gusau, 2008 sh. 385 da Auta, 2017 sh. 26 da Ɗangambo, 2012) duka sun yi tarayya wajen bayyana gargaɗi
da hanya ce wadda ta ƙunshi
tunasarwa kan yi ko bari da yi wa mutane nasiha, hannunka-mai-sanda tare da jan
hankali da kuma tsoratarwa a kan faɗawa cikin
ruɗani ko halaka a sakamakon aikata wani abu.
Amma a tawa
fahimtar, gargaɗi ya danganci yi wa mutum jawabi a kan munin aikata ko
yin wani abu ta hanyar fito da sakamako kai tsaye na hatsari da zai iya faruwa
nan gaba idan ba a kiyaye ba wanda ƙarshensa
ba zai yi daɗi ba.
Marubucin waƙar wato
Abdullahi ya yi amfani da tubula masu armashi waɗanda
suka taimaka masa wajen ƙara fito da
babban saƙonsa na gargaɗi a
cikin waƙarsa ta Korona Biros. Marubucin ya zaɓo
tubula masu ratsa jiki da jan hankali daban-daban da suka haɗa
da sanarwa daga shugaban al’ummar Musulmai (Sarkin Musulmai) da izinin ci gaba
da addu’a a gida da jan hankali daga likitoci da umurnin sanya takunkumi da
gargaɗin zuwa asibiti a duk lokacin da aka sami canjin jiki da
saƙon nasiha da kafa hujja daga malaman
addini a kan annobar da gargaɗin yawaita yin sadaka da neman gafarar Ubangiji da kuma
horo a kan ƙaurace wa masu ƙaryata zuwan korona biros da sauransu.
Ga wasu
daga cikin tubula da Abdullahi ya gina waƙarsa
kuma aka bayyana su a wannan nazari su ne kamar haka:
6.3.1
Sanarwa/Kira Daga Shugaban Al’ummar Musulmi
Ƙamusun Ingilishi da Hausa (2021:118) ya bayar da ma’anar
kira da
“A buɗa
baki a kira wani ko wata dabba da ƙarfi”.
Haka kuma,
a dunƙule kira daga shugabannin al’umma ya
danganci gudanar da jawabi kai-tsaye ko ta wata kafar sadarwa domin al’umma su
ji, su kuma aiki da abin da shugaba ya sanar. Aikin shugaba ne ya sanar da duk
wani abu wanda zai amfanar ko cutar da al’ummar da yake yi wa jagoranci.
Jagorancin al’umma yakan fara daga zamantakewar iyali zuwa ta unguwa, sai ta
gari wadda mai gari ko dagaci yake shugabanta. Gamayyar garuruwa suke haifar
shugabancin gunduma, shugaban gunduma shi ne ake kira da hakimi, taruwar
gundumomin hakimai suke samar da sarkin yanka wato sarki mai daraja ta ɗaya
ko ta biyu. Dukkan umurni na yi ko hani yana fitowa daga bakin sarkin ƙasa, sannan ya biyo ta hannun hakimai zuwa dagatai zuwa
masu unguwanni waɗanda su ne suke da alhakin isar da saƙon sarki ga sauran mutane. Bayan zuwan addinin Musulunci
a ƙasar Hausa, sai tsarin ya mayar da
Sarkin Musulmi a matsayin shugaban ƙasa
na Musulmai shi ne yake da alhakin yin sanarwa ta gargaɗi
kamar yadda waƙar da ake
yin nazari ta fara buɗewa da jawabin Sarkin Musulmi (Karofi, 2013 sh. 14-15).
Abdullahi
ya yi amfani da jawabin kira daga Sarkin Musulmi a baitinsa na farko kamar
yadda za a gani.
Ga shi dai Sarkin
Musulmi,
Yai kiran dukkan Musulmi,
Da su ɗau magana ta ilmi,
Ba zancen masu gardama ba. (Baiti na
1).
A baitin da
yake a sama, ya nuna yadda Sarkin Musulmi ya yi kira da babbar murya ga dukkan
Musulmai da su gaskata maganarsa dangane da wanzuwar cutar Korona Biros a
Nijeriya. Ya kuma gargaɗi mutane (Musulmai) baki ɗaya
da su ɗauki maganar likitoci da masu ruwa-da-tsaki a kan harkar
su kuma gujewa maganganu masu ƙaryata
wanzuwar cutar a Nijeriya da ma duniya baki ɗaya.
6.3.2 Nasiha
Daga Malaman Addini
Kalmar
nasiha tana nufin kyakkyawar shawara (CNHN, 2006:357). Dangane da
asalin kalmar kuwa, Hausawa sun ɗauko kalmar ce daga harshen Larabci. Haka kuma, Larabawa
dai ne suke da kalmar shawara wadda ake fassara nasiha da ita. Amma dukkan waɗannan
kalmomi sun shiga cikin rumbun kalmomin Hausawa sun zauna daram, sun saje. Duk
da haka, za a iya Hausantar da ma’anar kalmar nasiha ko ta shawara da
“gyara-kayanka” wato wasu maganganu waɗanda ake
gayawa mutum domin a yi masa gyara a kan wata fahimtarsa kan wani abu ko
matsala. Yin nasiha na canza mutum daga rashin sani zuwa sani ko kuma yarda da
wani abu wanda a baya bai yarda da shi ba ( Malumfashi, 2018 sh. 460-461).
Marubucin
waƙar, ya kawo baituka waɗanda
ya fito da nasihohi daga malaman addinin Musulunci sanannu suka yi dangane da
cutar Korona Biros wanda suka kafa hujjoji daga Hadisai da Kur’ani kamar yadda
baituka suka zo da su.
Mallamai sun yo bayani,
Bisa Hadisi da Kur’ani,
Da jawaban masu fannin,
Likitoci ba
da yaudara ba. (Baiti na 2).
Sunka ce cutar Korona,
Maganinta a je a zauna,
Dukkanin taro a daina,
Ba kawai
salla ta Jumma’a ba. (Baiti na 3).
Mallamanmu suna nasiha,
Da jawabi ga fasaha,
Kan dabarun kare
sihha,
Ga sunayensu ban rage ba. (Baiti
na 9).
Sheikh Sharif
Muftin ƙasarmu,
Dr. Khalid
shugabanmu,
Sheikh Abubakar
Igwaninmu,
Birnin Kudu bai rawar ƙafa ba. (Baiti na 10).
Sannu Dakta Bashir
Aliyu,
Mai Hadis, Tafsir,
Zakiyyu,
Rabbana Sarki Ganiyyu,
Ya tsare
mana lafiyarka Baba. (Baiti
na 11).
Sai mu je gun Sakwwatawa,
Dakta Mansur masu bai wa,
Masu gadon Annabawa,
Bai bar mu
cikin dibi-dibi ba.
(Baiti na 12).
Shehu Ibrahim Makwarri,
Yai jawabai tun a fari,
Masu gamsarwa da tsari,
Bai yi sassauci
ga mai musu ba.
(Baiti na 13).
Dakta Sani gwanin hadisi,
Wanda ko da bai da sisi,
Ba shi yin ƙarya ga
nassi,
Kuma ba zai
kare biddi’a ba.
(Baiti na 14).
Ga Gwani Salissu Shehu,
Shugaban wa’azi da sulhu,
Masanin boko da fiƙhu,
Har maƙaṣid Shehu
bai bari ba.
(Baiti na 15).
Shehu Ahmad Murtalawa,
Dakta Ahmad Dogarawa,
Sai Gwani Mansuru Yelwa,
Sheikh
Disinan ma bazan bari ba. (Baiti
na 16).
Wanga su am Malamanmu,
Masu ƙarfafa zuciyarmu,
Masu tsabar tausayinmu,
Kuma ba
naira suke hari ba. (Baiti
na 17).
Ga shi dai sun ba da hujja,
Lokacin da ake da haja,
In da duk aka ba da hujja,
Ai sai bi
ba da gardama ba. (Baiti na 18).
Waɗannan
baituka da suke a sama, marubucin waƙar
ya ambaci sunayen malaman addini sanannu da dama na ƙasar Hausa waɗanda suka
yi wa’azi da yin nasiha daga Hadisai da Kur’ani domin mutane su gaskata abin da
likitoci suka faɗa dangane da cutar Korona Biros kuma hakan ya yi daidai
da cewar Annabin rahama (S.A.W.) da kuma cewar Kur’ani, idan annoba ta shigo
cikin gari ku ƙauracewa
taro da cakuɗuwar jama’a a wuraren taruwa kamar masallaci da kasuwa da
sauransu. Malaman addinin sun ƙara gaskata
maganar likitoci na zama gida da ƙauracewa
cincirindon mutane a kodayaushe domin hakan zai hana yaɗuwar
wannan annoba a cikin al’umma. Hatta salloli biyar da ta ranar Jumu’a duka sun
yi nasiha a kan barin su cikin jam’i hakan ya yi daidai da koyar addinin
Musulunci na hana yaɗuwar annoba cikin al’umma.
6.3.3 Jan Hankali
ta Fuskar yin Tsafta da Kiwon Lafiya
Tsafta na ɗaya
daga cikin abubuwan da suka sa mutum (ɗan’Adam)
mai hankali ya bambanta da maras hankali, shi ya sa mawaƙi Abdullahi ya yi amfani da salon jan hankali na yin
tsafta da kyautata kiwon lafiya domin ƙauracewa
wannan annoba kamar yadda za a gani a cikin ‘yan baitoci.
Bayan haka ɗau mataki,
Ka sako “mask” nan a baki,
Hannuwa ka lizimci wanki,
Ba sai a
wurin naɗar tuwo ba. (Baiti na 7).
In kana jin zazzaɓi fa,
Ko yawan tari da zuffa,
Ba batun wani kaffa-kaffa,
Maza je can hospital a duba. (Baiti
na 8).
Waɗannan
baituka da suke a sama, marubucin waƙar
ya yi amfani da su domin jan hankali ta fuskar sanya takunkumi (mask) da yawan wanke hannaye a kai akai
ba don komai ba, sai don yawaita tsafta da kiwon lafiya. Baya ga haka,
marubucin ya kawo yanayi na rashin lafiya wanda ya kamata a ɗaukar
wa mataki na zuwa asibiti da gaggawa kamar zazzaɓi
da yawan tari da zufa duka dai alamu ne da ke nuna yiwuwar Korona.
6.3.4 Bayar
da Izinin ci gaba da yin Addu’o’i a Gida
Bayar da
izini ya shafi amincewa a gudanar da wani abu a bisa ƙayyadadden tsari wanda zai kai ga samun nasarar wani abu
da aka sanya a gaba. Malaman addinin Musulunci sukan bayar da izinin yin
addu’o’i a duk lokacin da wata masifa ko annoba ta shigo cikin al’umma suna yin
haka don nuna koyi ga Annabin rahama (S.A.W.).
Marubucin
waƙar Korona Biros, ya kawo wani baiti
wanda yake bayar da izini ga dukkan Musulmai da su duƙufa wajen yin addu’o’i har da halwa don roƙon Allah ya sauwaƙa
wannan annoba cikin ƙasarmu
Nijeriya kamar haka:
Shehunai sun ba da fatwa,
Kan buƙatar fara halwa,
A gida, kowa da kowa,
Ya yi salla don ya roƙi Rabba. (Baiti na 4).
Maganin cutar Korona,
Babba dai shi ne a zauna,
A gida yawo a daina,
Ba tare da
yale addu’a ba. (Baiti na 5).
Addu’a kam ba kamarta,
Ba makami samfurinta,
Tashi duk dare don ka yi ta,
Ba a samu
kamarta gun tsari ba. (Baiti na 6).
Marubucin
ya fito da bayanan izini da malaman addinin Musulunci suka ba al’umma na duƙufa a kan yin addu’o’i kowa da kowa a gidaje don roƙon Ubangiji Allah ya hana yaɗuwar
wannan annoba ta Korona Biros a nan Nijeriya da sauran ƙasashen Musulmai. Abdullahi ya jaddada muhimmancin yin
addu’a da daddare domin dacewa da neman tsarin Allah ga cutar zamani ta Korona
Biros.
6.3.5 Horo a
kan Ƙaurace wa
Masu Ƙaryata
Zuwan Korona Biros
Ga shi dai sun ba da hujja,
Lokacin da ake da haja,
Inda duk aka ba da hujja,
Ai sai bi
ba da gardama ba. (Baiti na 18).
Kar ku yarda da masu musu,
Ban da sauraron batunsu,
In ka ɗau zancen irinsu,
Baka ɗau
hanyar riga-kafi ba. (Baiti na 19).
Ban da ma tsabar jahala,
Wa ya kai su Imamu salla?
Wa ya kai su biya ga Allah?
Ba a kai
sukiran Ubangji ba. (Baiti na 20).
6.3.6 Kwaɗaitarwa
ga Shugabanni da Attajirai kan Ciyarwa a Lokaci Korona
Tubalin gargaɗi na kwaɗaitarwa ga shugabanni da attajirai kan ciyarwa ga mutanen da suke kulle a gida, babu fitowa don sallah da ciniki ko kasuwanci. Marubucin waƙar ya yi amfani da wannan tubali inda ya gina wasu baituka masu jan hankali da kwaɗaitarwa ga waɗanda suke masu hannu-da-shuni da shugabanni da su sadaukar da dukiyoyinsu wajen ciyar da mutane a yayin zaman Korona kamar yadda za a gani a ƙasa.
Amma na fa akwai bayani,
Dole ne fa zan yi nuni,
Gun masu hannu-da-shuni,
Hanzari ne
ba batun gudu ba. (Baiti na 21).
Masu kuɗɗi na kira ku,
Tallakawa na jiranku,
Don ku kawo taimakonku,
Kuma ba
canjin kuɗin suga ba. (Baiti na 22).
Albishir ya masu naira,
Wagga dama ce ku lura,
Ku yawaita halina hairan,
Ba dunƙule naku hannuwan ba. (Baiti na 23).
Shugabanni zan kira ku,
Ku ji tsoron Khalikinku,
Ku bi kadun ‘yan ƙasarku,
Ba kui wasa
da lafiya ba. (Baiti na 24).
Kar saboda corona ɓirus,
Ai ta amfani da biros,
A yawaita su sata-ɓirus,
Ba ku ba
mabiyanku tallafa ba. (Baiti na 25).
Toh, ku fara rabon
abinci,
Don a ɗan rage wanga ƙunci,
Tun da dai kuka sa ƙunci,
To karya
zamo ba kui shiri ba. (Baiti na 26).
Masu rauni duk ku duba,
Da waɗanda ba sui shiri ba,
Ba su tanadi ‘yan kuɗi ba,
Masara ma
sam ba sui awu ba. (Baiti na 27).
Kar ku bar su cikin zalama,
Kar ku sa su shiga nadama,
Kun hana su zuwa su nema,
Sannan ba
ku basu ko kwabo ba. (Baiti na 28).
29. Sun guje cutar Korona,
Sun shige ɗaki su zauna,
Ga cikinsu yana ta ƙuna,
Bai sami
abin da zai taɓa ba. (Baiti na 29).
Tun daga
baiti na 21 har zuwa na 29, marubucin waƙar
ya yi amfani da salon jan hankali ne na kwaɗaitarwa
ga masu mulki da attajirai da su ciyar da mutane waɗanda
annobar Korona ta killace su a cikin gidajensu ga shi babu kuɗi,
ba abinci a wajensu ballantana su zauna cikin jin daɗi
da aminci. Don haka, marubucin ya yi ta nanata muhimmancin yin taimako ga
mutane don kaucewa wata sabuwar cutar da za ta iya bijirowa ta sata-ɓirus,
sakamakon matsin da zaman zai haifar ga talakawa.
7.0
Kammalawa
Wannan
takarda ta nazarci tubalai ne waɗanda suka tattaru suka tayar da jigon gargaɗi a
waƙar Korona Biros ta Abdullahi Abubakar
Lamiɗo ya rubuta. An bayyana ma’anar tubali da ta jigo da ta
kalmar gargaɗi. An kuma yi bayanin yanayin tubalan ginin jigon gargaɗi a
waƙar Koron Biros. Sannan kuma, an
tantance tubala daban-daban waɗanda su ne Abdullahi (marubucin waƙar) ya sadar da jigonsa na gargaɗi a
waƙarsa. An kuma kawo bayanan tubalan da
misalan baitukan waƙa daga
tubalan suka haɗa da tubali na kira daga shugaban al’umma da na nasiha
daga malaman addini da na jan hankali ta yin tsafta da kyautata kiwon lafiya da
bayar da izinin ci gaba da yin addu’o’i a gida da horo a kan ƙauracewa masu ƙaryata
zuwan Korona da kuma kwaɗaitarwa ga shugabanni da attajirai kan ciyar da al’umma
abinci a yayin kullen Korona. A sakamakon bincike an gano cewa waƙar ta cancanci a yi nazarinta domin ta ƙunshi wasu tubala waɗanda
suka gina babban jigo na gargaɗi.Kuma waƙar ta
mallaki muhimman ɓangarori da tarke yake buƙata a yayin nazarinsa. Ana bayar da shawara ga manazarta
da masu bincike da su ɗauki wani ɓangaren nazari a wannan waƙa domin a gudanar da wani bincike a kansa.
Manazarta
Auta, A.L. (2017). Faɗakarwa A Rubutattun Waƙoƙin Hausa. Bayero Uniɓersity, Printing Press.
Bala, I. da Imam, K. (2020). Corona Blues (A Bilingual Anthology of Poetry). Whetstone Publishers
C.N.H.N (2006). Ƙamusun Hausa. Ahmadu Bello Uniɓersity, Printing Press.
Ɗangambo, H.A. (2012). Kwatanta Tubalan Gina Jigo
Tsakanin Rubutattun Waƙoƙi da Ƙagaggun Labarai na Hausa. [Kundin digiri na uku da
ba a buga ba]. Sashen Koyar da Harsunan
Nijeriya. Jami’ar Bayero.
Gusau, S.M. (2003). Jagoran Nazarin Waƙoƙin Baka. Benchmark Publishers Limited.
Gusau, S.M. (2008). Dabarun Nazarin Adabin Hausa. Fisbas
Media Serɓices.
Gusau, S.M. (2015). Mazhabar Ra’i da Tarke A Adabi Da Al’adun
Hausa. Century Research and Publishing Limited.
Karofi, I.A. (2013). Sarautar
Iyali Da Ta Sana’o’in Gargajya Tsakanin Al’ummar Hausawa. Cikin Mujallar Multi-Disciplinary. (IKCOE-MDJ). Isa
Kaita College of Education, Dutsinma. Ɓolume (5). Number 4. pp14-21.
Kurfi, M.M. (2021). Ƙamusun
Ingilishi da Hausa. Himma Publishers.
Malumfashi, Z.A. (2018). Tarken
Wasu Ɗiya Na Faɗakarwa Ta Nasiha A Wasu Waƙoƙin Dr. Mamman Shata. Cikin Studies in the Songs of Dr. Mamman Shata Katsina. Department of
Nigerian Language, Umaru Musa Yar’adua Uniɓersity. pp 459-468.
Yahya, A.B. (2014). Gudale Waƙar soyayya: Misalin Gazl (Ghazal)
Cikin Rubutattun Waƙoƙin Hausa. Garkuwan
Adabin Hausa A Festschrift In Tribute To Abdulƙadir Ɗangambo. Department of Nigerian Languages, Bayero Uniɓersity.
pp125-138.
Yahya, A.B. (2015). Rerawa
Ruhin Waƙa Da Matsayinta A Waƙoƙin Hausa Na Baka Da Rubutattu. A cikin mujallar Algaita Journal of Current Research in Hausa
Studies.Department of Nigerian Languages, Bayero Uniɓersity. Special Edition, pp
10-15.
Ratayen Waƙar
Waƙar Korona Bairos
Abdullahi Abubakar Lamido
1 Ga shi dai
Sarkin Musulmi,
Yai kiran dukkan Musulmi,
Da su ɗau magana ta ilmi,
Ba zancen masu gardama ba.
2. Mallamai sun yo bayani,
Bisa Hadisi da Kura’ani,
Da jawaban masu fannin,
Likitoci ba da yaudara ba.
3. Sun ka ce cutar Korona,
Maganinta a je a zauna,
Dukkanin taro a daina,
Ba kawai salla ta Jumma’a ba.
4. Shehunai sun ba da fatwa,
Kan buƙatar fara halwa,
A gida, kowa da kowa,
Ya yi salla don ya roƙi Rabba.
5. Maganin cutar Korona,
Babba dai shi ne a zauna,
A gida yawo a daina,
Ba tare da yale addu’a ba.
6. Addu’a kam ba kamarta,
Ba makami samfurinta,
Ta shi duk dare don ka yi ta,
Ba a samu kamarta gun tsari ba.
7. Bayan haka ɗau mataki,
Ka sako “mask” nan a baki,
Hannuwa ka lizimci wanki,
Ba sai a wurin naɗar tuwo ba.
8. In kana jin zazzabi fa,
Ko yawan tari da zuffa,
Ba batun wani kaffa-kaffa,
Maza je can
hospital a duba.
9. Mallamanmu suna nasiha,
Da jawabi ga fasaha,
Kan dabarun kare
sihha,
Ga sunayensu ban
rage ba.
10. Sheikh Sharif
Muftin ƙasarmu,
Dr. Khalid
shugabanmu,
Sheikh Abubakar
Igwaninmu,
Birnin Kudu bai
rawar ƙafa ba.
11. Sannu Dakta
Bashir Aliyu,
Mai Hadis, Tafsir,
Zakiyyu,
Rabbana Sarki Ganiyyu,
Ya tsare mana lafiyarka Baba.
12. Sai mu je gun Sakkwatawa,
Dakta Mansur masu bai wa,
Masu gadon Annabawa,
Bai bar mu cikin dibi-dibi ba.
13. Shehu Ibrahim Makwarri,
Yai jawabai tun a fari,
Masu gamsarwa da tsari,
Bai yi sassauci ga mai musu ba.
14. Dakta Sani gwanin hadisi,
Wanda ko da bai da sisi,
Ba shi yin ƙarya ga
nassi,
Kuma ba zai kare biddi’a ba.
15. Ga Gwani Salissu Shehu,
Shugaban wa’azi da sulhu,
Masanin boko da fiƙhu,
Har maƙaṣid
Shehu bai bari ba.
16. Shehu Ahmad Murtalawa,
Dakta Ahmad Dogarawa,
Sai Gwani Mansuru Yelwa,
Sheikh Disinan ma bazan bari ba.
17. Wanga su am Malamanmu,
Masu ƙarfafa zuciyarmu,
Masu tsabar tausayinmu,
Kuma ba naira suke hari ba.
18. Ga shi dai sun ba da hujja,
Lokacin da ake da haja,
In da duk aka ba da hujja,
Ai sai bi ba da gardama ba.
19. Kar ku yarda da masu musu,
Ban da sauraron batunsu,
In ka ɗau zancen irinsu,
Baka ɗau hanyar riga-kafi ba.
20. Ban da ma tsabar jahala,
Wa ya kai su Imamu salla?
Wa ya kai su biya ga Allah?
Ba a kai sukiran Ubangji ba.
21. Amma na fa akwai bayani,
Dole ne fa zan yi nuni,
Gun masu hannu da shuni,
Hanzari ne ba batun gudu ba.
22. Masu kuddi na kira ku,
Tallakawa na jiranku,
Don ku kawo taimakonku,
Kuma ba can jin ku]in su ga ba.
23. Albishir ya masu naira,
Wagga dama ce ku lura,
Ku yawaita halina hairan,
Ba dunkule naku hannuwan ba.
24. Shugabanni zan kira ku,
Ku ji tsoron Kalikinku,
Ku bi kadun ‘yan }asarku,
Ba kui wasa da lafiya ba.
25. Kar saboda corona ɓirus,
Ai ta amfani da biros,
A yawaita su sata-ɓirus,
Ba ku ba mabiyanku tallafa ba.
26. Toh, ku fara
rabon abinci,
Don a dan rage
wanga ƙunci,
Tun da dai kuka sahu ƙunci,
To karya zamo ba kui shiri ba.
27. Masu rauni duk ku duba,
Da waɗanda ba sui shiri ba,
Basu tanadi ‘yan kuɗi ba,
Masara ma sam ba sui awu ba.
28. Kar ku bar su cikin zalama,
Kar ku sa su shiga nadama,
Kun hana su zuwa su nema,
Sannan ba ku ba su ko kwabo ba.
29. Sun guje cutar Korona,
Sun shige daki su zauna,
Ga cikinsu yana ta ƙuna,
Bai sami abin da zai taɓa ba.
30. Addu’ar mazlumikun san,
Babu shamaki gunta
tun can,
In dai suka yi ta kun
san,
Allah ba zai ƙi addu’ar ba.
31. Rabbana Sarkin saurauta,
Wanda Kai ne mai nagarta,
Damuwa fa ta tsananta,
Yayewa na gare Ka Rabba.
32. Mun yi roƙo gun Ka
Allah,
Mun yi tuba gun Ka
Jalla,
Don yawan Azumi da salla,
Ka raba mu da jarrabar ga babba.
33. Toh a nan ne zan yi birki,
A cikin ɗan wanga aiki,
Addu’ata wanga aiki,
Rabbana Sarki Gwani ya karɓa.
34. Gombe ne
babban gari na,
Lamdo Abdullahi suna,
Kuma Amir ne laƙƙabi na,
A gidanmu suna kira ni Baba.
(Bala da Imam,
2020 sh. 122-125)
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.