Ticker

6/recent/ticker-posts

Salo Ruhin Waka: Nazarin Salo a Wakar Salo Ta Alhaji Sani Sabulu Kanoma

Citation: Bashir, R. (2024). Salo Ruhin Waƙa: Nazarin Salo a Waƙar ‘Salo’ Ta Alhaji Sani Sabulu Kanoma. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 261-269. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.032.

SALO RUHIN WAƘA: NAZARIN SALO A WAƘAR ‘SALO’ TA ALHAJI SANI SABULU KANOMA

Rabiu Bashir

Department of Nigerian Languages and Linguistics, Kaduna State University, Kaduna

Tsakure:

Waƙa kamar yadda masana suka yi ta ƙoƙarin bayyanawa zance ne da ya saɓa da zance na yau da kullum domin ita shiryayyiyar magana ce mai ƙunshe da saƙo wadda ake aiwatarwa cikin hikima da balagar harshe ta hanyar zaɓen kalmomi da shirya su tare da sadar da su a kan wasu ƙa’idoji. Salo a cikin ayyukan adabi yakan kasance wata gada ce wadda ta kanta ne fasihi ke bi ya gwada ƙwanjin fasaharsa da baiwarsa ta mallakar harshe tare da samun damar isar da saƙonsa cikin sauƙi da burgewa. Masana irin su Leech (1968) da Yahaya (2001) da Garba (2014) sun tabbatar da cewa iya sarrafa salon fasihi shi zai ba shi dama ya samar da waƙa mai daɗi da armashi kuma har mutane su kwaɗaitu da waƙar tasa. Masana irin su Mukhtar (2001) da Yahaya (2001) da Adamu (2002) suna kallon salo a matsayin wani faffaɗan fage na nazari wanda kusan a iya cewa ba shi da iyaka amma duk da haka ana nazarinsa ta fuskar harshe da kuma adabi.Wannan maƙala ta yi nazarin yadda Alhaji Sani Sabulu Kanoma ya sarrafa salailai mabambanta ne a cikin waƙarsa ta ‘Salo’ musamman ta fuskar adabi, domin kuwa ba ta taɓo abin da ya shafi harshe ba. Maƙalar ta yi dubi ne na ƙwaƙƙwafi tare da ƙwanƙance ɗiyan waƙar da ƙoƙarin fayyace su a kan wani nau’i na salo. A wajen tattaro bayanai, maƙalar ta juyi wannan waƙa ta ‘Salo’ a rubuce, sannan ta bibiyi bayanan masana a kan salo da hanyoyin nazarinsa waɗanda suka zamar mata matashiya wajen ganin an zaƙulo nau’o’in salalai da makaɗin ya sarrafa a cikin waƙar. A ƙarshe maƙalar ta tabbatar da cewa makaɗin gwani ne wajen iya sarrafa salo wanda hakan ya sa waƙoƙinsa suka samu karɓuwa a wurin mutane kuma har duniya ta sansa a matsayin fitaccen makaɗi mai ɗimbin hikima sannan kuma waƙoƙin nasa suka ɗauki tsawon lokaci ana sauraren su ba tare da sun ɓace ba duk kuwa da cewa makaɗin ya daɗe da barin duniya.

Fitilun Kalmomi: Adabi, waƙa, Salo Sani Sabulu

Gabatarwa

Idan aka duba matsayi da aikin salo a cikin waƙa ba zai zama kuskure ba idan aka fayyace shi a matsayin ruhin waƙa, domin kuwa da shi ake gina harshen duk wata waƙa, kuma samuwar harshe a cikin waƙa shi ne samuwar waƙar. Haƙiƙa iya amfani da salo da sarrafa shi ne ke sa waƙa ta zama rayayyiya wadda za ta ɗauki tsawon lokaci ana saurarenta da amfanuwa da ita. Haka kuma a lokacion da makaɗi ya rasa samar da gwaggwaɓan salo a waƙa shi kan sa waƙar ta gaza kai bantenta a cikin waƙoƙi ballentana har ta rayu a tsakanin al’umma, don haka a ƙarshe ba abin da zai rage illa ta mutu a daina jin ta gaba ɗaya. Alhaji Sani Sabulu Kanoma fitaccen makaɗi ne wanda ya yi tashe a ciki da wajen ƙasar Hausa da ma maƙwabtanta. Duk da cewa Allah ya yi masa rasuwa tun wurin shekaru ashirin da uku (19/8/2000) da suka wuce, amma har yanzu waƙoƙinsa na rayuwa kasancewar ya sadar da su cikin kyakkyawan salo mai gamsarwa da armashi ta yadda mutum zai iya ɗauka jiya ko shekaran jiya aka rera su.

Asalin mahaifin Sani Sabulu mutumin ƙasar Borno ne, kuma sunansa Garba, wanda ya zo garin Kanoma da nufin ci-rani na farauta. Da ya zo garin Kanoma ya zauna a garin tsawon lokaci kuma a cikin haka ne sai mahaifiyar Sani ta fito daga gidan mijinta, don haka bayan ta gama idda sai suka yi aure kuma a sanadiyar auren ne aka haifi Sani Sabulu a garin Kanoma a shekarar Alif da ɗari tara da hamsin da ɗaya (1951). Kuma mahaifinsa ya laƙaba masa sunan ‘Sabulu’ a lokacin da aka haife shi. A lokacin da Sani Sabulu ya kai kimanin shekara bakwai, sai mahaifinsa ya kai shi Gusau domin neman ilmin addinin musulunci, inda ya zauna a hannun malam Shehu Mai Almajirai har ya yi sauka kafin daga bisani ya dawo gida Kanoma inda ya sa karatun littattafai a hannun kawunsa malam Haruna. Waƙar “Kurkunu mugun ciwo”, ana harsashen ita ce waƙarsa ta farko, wadda ya rera ta a sanadiyyar kamuwa da ya yi da ciwon na kurkunu, kuma ya yi ta ne da kiɗan gambara wanda shi ne abin kiɗan da yake amfani da shi a farkon da ya fara waƙa, duk da cewa daga baya ya kuma rera waƙar da kiɗan kalangu. Alhaji Sani Sani Sabulu ya shahara matuƙa a waƙa kuma ya samu karɓuwa sosai har a tsakanin makaɗa da mawaƙa domin kuwa har sai da Alhaji Dr. Mamman Shata Katsina ya naɗa shi Sarkin yaƙinsa a fagen kiɗa da waƙa kuma ta dalilin hakan ya kai shi Makka ya sauke farali sannan ya yi masa kyautar mota.Ta fuskar aiwatarwa da sadar da waƙoƙinsa kuwa a iya cewa makaɗi ne na ‘jibiliyya’ domin kuwa bai gaji waƙa ba kuma bai koya ba. Sannan kuma duk da cewa yana aiwatar da waƙar tasa ne a cikin ƙungiya a matsayin jagoran ƙungiyar amma ba shi da ‘yan amshi, sai dai masu yi masa kiɗa kawai sai kuma sanƙira. Kenan a iya cewa yana aiwatar da waƙa ne a kan tsarin +Ƙungiya +Jagora – ‘yan amshi + Masu kiɗa + Sanƙira.

Waƙar ‘Salo’ ta Alhaji Sani Sabulu Kanoma waƙa ce mai daɗin saurare da burgewa wadda makaɗin ya gina ta a kan turken bugun gaba da koɗa kai ta hanyar amfani da salailai daban daban domin ya nuna matuƙar ƙwarewarsa wajen iya sarrafa harshensa a yayin sadar da waƙa. Haka kuma waƙar ta amsa sunanta domin Alhaji Sani Sabulu ya yi nasarar gwada zalaƙarsa ta sarrafa salo da harshe tare da nuna cewa ba baya ba ne shi wajen ƙullawa da sadar da waƙoƙin baka.

 

Ma’anar Salo

Masana da manazarta adabi sun yi iya bakin ƙoƙarinsu wajen bayyana fahimtarsu game da ma’anar salo, duk da cewa akwai kaɗan daga cikinsu kamar su Yahya (2001), da Adamu (2002), da suke kallon sa a matsayin wani abu da ke da wahalar fayyacewa musamman ta fuskar ma’ana.

Stephen (2000), ya bayyana ma’anar salon fasihin waƙa da cewa shi ne yadda fasihin ke ƙullawa da sarrafa hikomomin harshe, da kuma ƙoƙarinsa wajen zaɓen kalmomi, da amsa- amo, da karin waƙa, da raujinta, da kuma irin yadda yake sarrafa su daidai da tunaninsa a waƙe. Wato dai salon sarrafa sifofin harshen asali gwargwadon zurfin tunanin fasihi da kuma bunƙasarsa.

Sa’id (1981), cewa ya yi salo shi ne yadda mawaƙi ya zana tunaninsa a takarda. Za a dube shi a gani, shin yana da manufa, kuma bayaninsa yana da ƙarfi ko rarrauna ne, ana kuma fahimtarsa cikin sauƙi ko sai an yi lalube a gane manufarsa? Haka kuma za a dubi gwanintarsa wajen sarrafa harshen da ya yi amfani da shi.

Shi kuwa Ɗangambo (1981), ya bayyana salo ne a matsayin hanya ko dabara ta isar da saƙo. Sannan ya ƙara da cewa lallai ne salo ya ƙunshi zaɓi, kuma kyan salo ko muninsa ya danganta ne da yadda kowane mutum ya zaɓi abubuwan da ya yi amfani da su a cikin rubutunsa, ko furucinsa don ya isar da saƙonsa.

Har wa yau Gusau (1975 da 2003), ya bayyana salo a matsayin wata dabara da ake yi wa harshen waƙa kwalliya da ita. Wato akan zaɓi kalmomi ne a zayyana waƙa, a ƙawata ta sosai ta yadda za a burge mai saurare a kuma jawo hankalinsa.

Shi kuwa Yahya (2001), cewa ya yi salo na nufin duk wata dabara ko hanya a cikin waƙa wadda aka bi domin isar da saƙo. Ita wannan hanya tana yi wa waƙa kwalliya ta yadda saƙon waƙar zai isa ga mai saurare ko karatun waƙar.

Baldick (2004), ya bayyana salo ne a matsayin hanya ta musamman da wani fasihi ko zamani ko wata mazhaba ko wani fannin ya shahara da shi wajen sarrafa harshe.

Idan muka yi dubi zuwa ga ma’anonin salo da masana suka bayar, za mu iya cewa salo ya ƙunshi duk wata hikima ko dabara wadda fasihi ko wata mazhaba suka yi amfani da ita wajen ssarrafa harshe domin yi wa waƙa ado da kwalliya don nuna naƙaltar harshe da burge mai karatu ko sauraren waƙa.

Nazarin Salo

Masana wannan fanni na nazarin suna kallon fannin ne tare da nazarinsa ta fuska biyu, watau nazarin salo ta fuskar adabi da kuma nazarin salo ta fuskar harshe wanda kuma yake da wahalar bambancewa saboda kusancin da ke tsakaninsu. Amma duk da haka sun bayyana wasu ‘yan sifofi da za a iya bambance tsakaninsu kamar haka: Olusegun (2008) ya ce nazarin salon adabi yakan fi mayar da hankali ne a kan sigar bayar da labari don haka aka fi amfani da shi wajen ƙwanƙwance salon ƙagaggun labarai. Masanin kuma ya ƙara da cewa, shi kuwa nazarin salon sarrafa harshe ana lura ne da sifofin harshe (tsarin sauti, da ginin jumla, da gundarin kalmomi) da ke cikin matanin da kuma irin gudunmuwarsu wajen bunƙasawa da kyautata ma’anar matani. Sannan kuma ana ƙwanƙwance adon harshe ne ta fuskar saɓaninsu da kafaffun dokokin harshe da kuma ƙirƙirarrun ma’anoninsu gwargwadon yadda suka bayyana a wani muhalli a cikin matani.

Shi kuwa Olusegun (2008) ya ruwaito cewa Freeman (1973) ya ce, ana amfani da salon sarrafa harshe ne domin yana taimakawa wajen fahimtar da mai karatu sifofin harshe da na adabin da ke tattare a cikin matanin da ake nazarta, domin kuwa ba salon matani kawai ake nazarta ba har da nahawunsa. Wannan dalili ya sa masana irin su Leech (1968) da Leech da Short (1981) da Muktar (2004) da Olusegun (2008) da Lawal (1997) da kuma Garba (2014) duk suka gwada cewa an fi amfani da irin wannan salon sarrafa harshen ne wajen ƙwanƙwance salon sarrafa harshen waƙa, musamman domin fito da ire-iren bambance- bambancen da ke tsakanin matanin waƙa da sauran matanoni.

Salo a Cikin Waƙar ‘Salo’

Alhaji Sani Sabulu Kanoma mutum ne mai yawan hikima da basira, wannan ya sa ya kira wannan waƙa ‘salo’ da bakinsa da nufin ya gwada cewa lallai ya iya sarrafa salo tare da wasa da harshe a waƙa. Haƙiƙa manufar makaɗin ta cika kuma haƙarsa ta cimma ruwa domin kuwa waƙar tana ƙunshe da salailai mabambanta a cikinta. Kamar yadda bayani ya gabata na yadda masana suka fayyace fagen nazarin salo ta fuska biyu, watau ta fuskar adabi da kuma ta fuskar harshe idan aka nazarci waƙar za a tabbatar ta amsa sunanta domin kuwa ko ta ina aka nazarce ta za a sami salai lai kala-kala a cikinta. Za a iya ganin misalai kamar haka :

Salon Zuga

Salon zuga salo ne da ke cicciɓa mutum tare da ƙoƙarin ɗaga matsayinsa da nuna cewa wanda ake zugawa ɗin ya shahara kuma karansa ya kai tsaiko a fagensa. Makaɗi kan sarrafa salon zuga ne ya don ya nuna wa duniya isa ta wani, shi kuma wanda aka zuga ɗin ya rinƙa jin lallai fa ya isa kuma har zugar ta sa ya iya aikata wani abu na bajinta. Masana da dama sun bayyana salon zuga misali:

Bello (1976), ya bayyana cewa zuga tana kama da yabo wajen faɗin abubuwa na ƙwarai da mutum ya yi, sai dai a wajen zuga ana ƙara gishiri a faɗi abin da ba haka nan yake ba, amma babu wanda zai damu tun da an san niyyar ta a kumbura kan mutum ne. Ya ƙara da cewa babban harsashin da aka gina zuga a kai shi ne a nuna wa wanda ake zugawa cewa ya fi kowa, babu kamar shi kuma yana iya yin abin da kowa ba zai iya yi ba. (Bello 1979: 29). Shi kuwa Gusau (2002), cewa ya yi zuga wata magana ce da ke ɗauke da wasu kalmomi da ake amfani da su a koɗa wani a cicciɓa shi, a nuna fifikonsa kan wasu.

Alhaji Sani Sabulu ya sarrafa salon zuga a cikin waƙarsa ta salo domin ya cicciɓa yaransa na waƙa waɗanda ke yi masa kiɗa inda ya ce:

J: Musa ɗan Garewa mai kaɗa fata na Nana, Mamman mijin Ayashe da Dela,

Baban Abdul’aziz ina tambura.

Birgediyan mutan Jangebe na Abu mai kaɗa fata, Sani Yabo na Saudi Mamman,

Da Audu Waziri, eh, Angon Rabi Mijin,

Ya mijin Aminatu Audu,

Dalla dalla ku ba ni wamba wamba, Don hannu ya iya jiki ya saba, Tafiya sannu sannu kwana nesa,

In magana ta salo ce,

Kai ba ni ba Sabulun sallaye, Ko ku ko kuna iyakar naku,

Tunda kuna kiɗa kamar harsashi, Akuya ta gane ku ta aje fata, Tunda tana gudun azabar Allah.

Makaɗin ya zuga yaran nasa tare da nuna musu cewa in dai batun kiɗa ake yi to su fa ba baya ba ne, domin kuwa sun iya shi kuma sun saba. Tun a farkon ɗan waƙar makaɗin sai da ya yi amfani da basirarsa da Allah ya hore masa ya kira sunayen makaɗan nasa ɗaya da ɗaya yana alaƙanta su da matayensu, wanda yin hakan wani salo ne na zuga mutum a ƙasar Hausa. A lokacin da ake so a tsuma mutum kuma a zuga shi domin ya ji ƙarfin aikata wani abu sai mutane su kururuta shi ta hanyar haɗa shi da matarsa ko kuma wata wadda aka tabbatar yana ƙauna, wanda yin hakan zai sa mutumin ya aikata abin da ake buƙata yadda ya dace ko da kuwa bai yi niyyar hakan ba. Bayan makaɗin ya kwarzanta yaran nasa ta hanyar haɗa su da masoyansu bai tsaya haka ba, sai da ya nuna musu cewa idan fa ana magana a fagen kiɗa to su fa ba kanwar lasa ba ce, domin kuwa sun riga sun iya shi kuma sun san yadda ake yinsa. Alhaji Sani Sabulu bai tsaya haka ba sai da ya kai ƙarshe wurin zuga yaran nasa ya nuna cewa saboda irin yadda suka iya kiɗa kuma suke bugun kalangu da gaske to fa da zaran akuya ta hange su sai ta jefar da fatar da ke jikinta. Haƙiƙa wannan zuga ta kai zuga, domin kuwa a zahiri babu ruwan akuya da kiɗan yaran Sani Sabulu duk kuwa da cewa ana haɗa kalangu ne da fatar akuya. Sai dai salon zugar da ya yi amfani da shi ya sa yaran nasa sun zage sun yi masa kiɗa irin yadda ya dace a cikin waƙar,

Salon Bugun Gaba

Salon bugun gaba ko salon koɗa kai wata hikima ce ko dabara a cikin waƙa wadda makaɗi ke amfani da ita domin ya zuga ko zuzuta kansa ko ya yi alfahari ya nuna wa duniya cewa shi fasihi ne kuma karansa ya kai tsaiko a fagen hikima da balaga da kuma sarrafa harshe. A irin wannan fasaha makaɗi na ƙoƙarin ya gwada irin matsayinsa ne da ƙwazonsa a wannan fage sannan ya gwada ya isa kuma ya cika mai fasaha, a wasu lokutan har da ƙalubalantar sauran makaɗa da idan suna jin sun isa to su kwatanta ko su yi abin da ya yi na fasaha. Bunza ya bayyana salon bugun gaba a matsayin ‘Furuci da wani mutum zai yi a cikin zancensa ko waƙarsa ko rubutunsa yana ƙoƙarin fito da irin martabarsa ko ƙwazonsa. Galibi idan fagen fasaha ne, mai bugun gaban zai yi bugun gaba ne da fasaharsa da ya yi fice da ita’. Mujaheed ya bayyana salon bugun gaba da cewa ‘Shi ne furucin mawaƙi na alfahari ta hanyar cika baki musamman ta fuskar ƙwarewa da hikima da baiwa ko asali ko gogewa ko bayyana ficensa da zarce tsara don nuna fifiko da mawaƙin yake da su kain saura’.

Alhaji sani Sabulu ya yi amfani da salon bugun gaba ko salon koɗa kai a cikin waƙarsa ta ‘salo’ inda ya ce :

J: Duk mai son salo,

:Ya zo ga Haji Sani Sabulu,

:Tunda salo ga sabulu yat tashi.

:Ga alama ina zaton,

:Ni as shugabn ƙasar masu salo,

:Cikin musulmin Allah.

:Sani Sabulu Kanoma Dutsi,

:Ashe Sani Sabulu Kanoma guda ne,

:Angon Haja,

:Mijin Amina Mamman,

:Sani uban su Jamilu,

:Manya manya wane yaro, wurin wuya sai manya.

A cikin ɗan waƙar makaɗin ya bugi gabansa ne tare da koɗa kansa ya gwada wa duniya cewa duk mai buƙatar waƙa cikin tsantsar hikima da azanci to ya neme shi, domin kuwa duk wata hikima da basirar waƙa da iya sarrafa harshe daga daga gare shi ta samo asali. Sani Sabulu bai tsaya nan ba sai da ya gwada cewa shi fa a fagen fasahar kiɗa da iya sarrafa harshe yana kallon kansa ne a matsayin shugaban ƙasa, watau yana jin yana gaba da kowa a tsakanin dukan makaɗan ƙasar Hausa.

Salon Ƙarangiya

Salon ƙarangiya wata hikima ce ko dabara da mawaƙa ke amfani da ita a cikin waƙa ta hanyar wasa da harshe da luguden kalmomi ko sauti na baƙi ko wasali. Mawaƙa kan zaɓo wasu kalmomi ne ko sautika na wani baƙi ko wasali su yi ta maimaita shi a cikin kalmomi musamman a goshin kalmomin ko a ƙeyarsu wani lokacin har a tsakiya a cikin layukan waƙa. Masana sun tofa albarkacin bakinsu wajen fayyace ma’anar ƙarangiya. Misali Gusau (2002) ya ce ‘Ƙarangiya dabara ce ta luguden harrufa ko kalmomi ko wasa da harshe cikin baƙaƙe da kalmomi. Haka kuma akan iya maimaita wata gaɓa ko ƙwayar sauti, sautinsu ya dinga tafiya bai ɗaya a cikin kalmomi da saɗarun ɗan waƙa’. Shi kuwa Ɗangambo (2008) cewa ya yi ‘Ƙarangiya dabara ce ta luguden sautukan harrufa a cikin ɗango ko baiti, inda za a ji wasu saituttuka masu kama da juna suna hawa da sauka suna maimaita kansu’. Shi kuwa Garba (2014) cewa ya yi ‘Wannan salo ne wanda ya shafi luguden wasu sautuka- musamman a goshi ko ƙeyar kalmomi, mafi yawanci a tasassun gaɓoɓi kuma masu maƙwabtaka da juna’. Baldick (2004) ya nuna cewa akwai salon ƙarangiya har nau’i uku, watau akwai luguden wasali wanda ya ce shi ne maimaita sautin wani wasali ko makamantan juna a cikin tasassun gaɓoɓin kalmomi masu makwabtaka da juna. Sai kuma luguden baƙi wanda ya bayyana cewa shi ne maimaita sautin wani baƙi ko makamantan juna a cikin kalmomi masu mabambantan wasali kuma a muhallin da ke bayyanar da maƙwabtaka a tsakaninsu a cikin matani, musamman idan sautin baƙaƙen ya daidaita. Sai kuma nanatau (luguden ma’ana) wanda ya bayyana cewa, ta ƙunshi maimaita wata kalma ko wani rukunin nahawu a goshin ɗangaye. A wannan muhalli saƙon ake maimaitawa ko riɓanyawa domin ƙara fito da shi fili.

Waƙar ‘salo’ ta Alhaji Sani Sabulu na cike da salon ƙarangiya a cikinta, inda za a iya ganin misalai a cikin wasu ɗiya kamar haka:

J: Ado ɗan mutan Kano sanƙira,

:In kana da salo,

:Sai Salame ta sa Maisallah,

:Ya yi salla,

:Ya sallame yana ta salati,

:Cikin musulmi,

:Ya sami salsalar bisimillah,

:Saboda son Musulunci.

J: Bara cikin sallar layya,

:Sa’ilin da ina sallama,

:Salamatu taz zo da Saliha,

:Sule na sassabe cikin saura,

:Ya ga Sulluɓawa sun sa salo,

:Ga sallar lufa yab bi salsala,

:Ya bi Salamu har masallaci,

:Don ya sa Musulmi sallah,

:Da sallama da salati.

J: Cikin salati,

:Muka sami salsalar, sa sabon salo,

:Ka san so, ke sa a sa ma soko riga,

:Yana suka ran sallah,

:Cikin suka yas sato sulen masunta,

:Suka so su sussuke shi su soke,

:Sai masunta suka sami susuwa sai suya.

 

 

J: Salamatu mai salak,

:Salamatu mai salak,

:Da tas so ta ji salsalar salo,

:Ta yo sammako da assalatu ta ishe Sani,

:Sabulu ta ce mani ya salsalar salo,

:Shi asalin salo ana samu nai ga sabulu koyaushe.

Idan aka duba misalan ɗiyan waƙar da aka jero za a tabbatar da cewa waƙar na ƙunshe da salon ƙarangiya sosai inda makaɗin ya nuna gwanintar wasa da harshe matuƙa ya yi ta maimaitawa da sassarƙa sautin /sa/ a cikin kalmomi mabambanta, wani wurin a goshin kalma wani wurin a tsakiyar kalma wani wurin kuma a ƙeyar kalma. Haka kuma akwai kalmomi da dama da ya yi ta jujjuya su da nanata su a wurare daban-daban, wanda yin hakan yana cikin salon ƙarangiya da masana suka tabbatar.

Salon Adon Harshe

Masana irin su Shifly (1970) da Muhammad (1973) da Cuddon (1977) da Ɗan’iya (1997) da Gusau (2003) da kuma Muhammad (2011) sun yi gamayya kan cewa adon harshe wata kwalliya ce da ake yi wa harshen waƙa. Sai dai Shifly (1970), ya ƙara da cewa ya shafi karkatar da wani abu daga sifarsa ta asali ya zuwa wata sifar ko wani abu, kuma yin hakan kan kasance ne ta hanyar kamantawa ko mutuntarwa, ko tamka ko jurwaye ko kuma kwalliya. Yayin da shi kuma Cuddon ya ƙara da cewa shi adon harshe, shi ne kan fito da kowace irin magana (zance) ko waƙa, kana ya bayyana manyan rukunansa da suka haɗa da kwalliya, da tamka, da kuma alamci. Ɗan’iya (1997) ta ƙara da cewa da adon harshe ne ake yi wa waƙa kwalliya don ƙara mata armashi da daɗi, kuma shi ne ma’auni na gwada hikimar zance da balaga da ɗan Adam yake da ita a harshensa.

Bashir (2019) ya bayyana cewa adon harshe wata hanya ce ko dabara wadda makaɗa kan bi ta kanta domin su yi wa harshen waƙarsu ƙawa, ta yadda za su sami damar koɗa wanda suke waƙewa cikin harshe mai kwalliya da burgewa, gami da kambama shi cikin sifofi daban- daban. Su kuwa ginshiƙan adon harshe ko sigoginsa sun haɗa ne da kwalliya da tamka ta mutuntarwa da alamtarwa da kambamawa da sauransu.

Kwalliya da Tamka suna daga cikin ginshiƙan sigogin adon harshe, wanɗanda makaɗa kan yi amfani da su a cikin waƙoƙinsu domin su ƙara jin daɗi da sauƙin isar da saƙo ga mai saurare. Masana sun fayyace fahimtarsu a kan salon adon harshe na ‘Kwalliya’ da ‘Tamka’. Alal misali Yahya (2001), ya ce’Tamka, wani ɓangare ne na babban salon siffantawa, wanda ke bayyana sifar wani abu ta fuskar kwatanta shi da wani abu daban tare da amfani da kalmomin mizani’. (Yahya 2001:07). Malamin ya bayyana cewa, da za a kwatanta salon tamka (‘kamance’), da kwalliya (‘kinaya’), sai a ga cewa yayin da tamka kan siffanta mutum da cewa ya yi kama da wani abu, amma ba shi ne abun ba, to shi salon kwalliya yakan siffanta mutum da cewa shi ne abin kacokan. Har wa yau masanin ya nuna cewa, su waɗannan ‘kalmomin mizani’ da tamka kan yi amfani da su, sun kasu zuwa gida uku ne, wato akwai mizani na ‘daidaito‘ waɗanda suka haɗa da, awa da kamar da i da ya, da kake da sauransu. Sai ‘mizani na fifiko’ wanda ya ƙunshi kalmomi irin su wuce da zarce da fi da gota da furce da tsere da kuma ɗara. Na cikon ukun su ne kalmomin ‘mizani na kasawa’, waɗanda suka haɗa da kasa da gaza da wane da kuma kalmomi masu soke samuwa kamar bai da kuma ba. Shi kuwa Gusau (2002) ya bayyana cewa kwalliya kwatancen kai tsaye ne inda ake ba wani abu darajar wani abu ba tare da amfani da wani mahaɗi ba. Yayin da ita kuma tamka kwatance ne, inda makaɗi kan auna darajojin abubuwa daban-daban, ta hanyar daidaitawa ko bambantawa, ko fifitawa ko naƙasarwar wani kan wani.

Kasantuwar Alhaji Sani Sabulu Kanoma makaɗi mai tsara waƙoƙinsa cikin harshe mai sauƙin fahimta da burgewa gami da ƙawa, tare da saka karsashi da annashuwa ga mai saurare, ya sa ya gwanance wajen sarrafa salon adon harshe kamar yadda ya bayyana a cikin wannnan waƙar tasa ta salo, inda ya ce:

J: Ni waƙa nake kamar tamsiri,

:Ni waƙa nake kamar alburda,

:Wasu in sun jiya su ce wa’azi ne,

:Wasu in sun jiya su ce tamsiri,

:Duk maganar ta salo ce.

A cikin ɗan waƙa guda na ‘Salo’, Sani Sabulu ya yi amfani da Salon adon harshe na ‘Tamka’ da kuma na kwalliya duk domin ya nuna yadda ya mallaki harshensa ya kuma iya wasa da shi. A layi na farko da na biyu ya yi amfani tamka ne inda ya sarrafa kalmomin mizani na daidaito ya kwatanta irin yadda yake yin waƙa da yadda malamai suke yin tafsiri (Karatun Alƙur’ani da fassara tare da sharhi). Abin da yake so ya nuna shi ne in dai a fagen waƙa ne to fa shi gwani ne kuma gangaran, domin kuwa ko a cikin malamai ba kowa ba ne yake yin tafsiri, sai wanda iliminsa ya kai kuma ya san fannonin ilimi daban-daban. Don haka a nan sai ya daidaita waƙarsa da tafsiri. A layi na biyu na ɗan waƙar sai ya sake kwatanta yanayin waƙarsa da ‘alburda’. A wannan gaɓar, makaɗin ya sarrafa salon adon harshe ne na tamka ta hanya amfani da kalmomin mizani na daidaito, inda ya daidaita yanayin waƙarsa da ‘Alburda’. Wadda fitacciyar waƙa ce ta yabon Manzo (S.A.W), wadda wani babban malamin sufanci ɗan ƙasar Masar mai suna Imam al-Busiri ya rera tun a wurin ƙarni na sha uku. Sani Sabulu ya yi ƙoƙarin daidaita waƙarsa da waƙar alburda ne don ya san fitacciyar waƙa ce a wurin Musulmi, wadda take da matuƙar tarihi da kuma tasiri. Har wa yau dai a cikin wannan ɗan waƙar, makaɗin bai gushe ba sai da ya yi amfani da adon harshe na kwalliya inda kai tsaye ya kamanta waƙar tasa da ‘wa’azi’ da kuma ‘tamsiri’. A waɗannan layuka guda biyu na ɗan waƙar makaɗin ya nuna matsayin waƙar tasa ne da irin yadda yake aiwatar da ita, don haka sai kai tsaye ya kira ta da wa’azi da kuma tamsiri domin ya kwatan ta da su ya nuna cewa matsayin su guda ne.

Salon Yabau

Kalmar Yabau ‘Euloƙues’ kalma ce ƙirƙirarriya a Ingilishi, kuma wanda ya fara ƙirƙirar kalmar shi ne wani masani da ake kira Kunene (1971) inda ya ce “Daga yau za a riƙa amfani da ƙirƙirarriyar kalmar ‘Yabau’ domin bayyana dukkan kalmomin da suka shafi yabon wani gwarzo, ko da kuwa sun kasance suna ne ko dangantawa”. Wato a nan ‘Yabau’ za ta kasance baddalawa ne ko faɗaɗawa a kan kalmar yabo ko yaba, ko yabi, ko yabe, ko kuma yabawa, da nufin bayyana ko dai Kalmar yabo, ko yankin yabo ko kuma yabo a cikin jumla gaba ɗaya. Yabau a cikin waƙa shi ke siffanta jarumi da ayyukan jarumtarsa ta hanyar amfani da kwalliya ko alamta shi da wasu abubuwa, haka kuma akan yaba wa gwarzo tsurarsa, a wani lokaci kuma a danganta shi da wasu mutane. Irin muhimman kalmomi da aka kwarzanta barde da su a cikin waƙa su ne ake nufi da ‘Yabau’ ba yabo ba. (Tsoho, 2002 Shf:2-143).

Tsoho ya jaddada cewa yabau a Hausa ya ƙunshi kalma ko yankin magana ko jumlar da aka yi amfani da ita wajen yaba wa gwarzo cikin kwalliya ko alamci, musamman danganta shi da ƙarfafan dabbobi ko abubuwa ko yanayi mai tsoratarwa da ake yi. Ya ƙara da cewa yabau kan siffanta zatin jarumi ya cicciɓa shi, ya kuma ɗaga kimarsa a idon duniya, haka kuma yabau kan fayyace kimar sarakuna da manoma, ya bayyana kyawawan halayensu da ɗabiu’nsu, saɓanin yabau a waƙoƙin ‘yan tauri da ‘yan dambe da ɓarayi, (Tsoho 2002, Shf:145-146). Haka kuma ya ce za a iya raba yabau a ƙalla zuwa gida biyar, inda ya ce a kwai yabau na kwalliya da yabau siffantau, da yabau aikatau da yabau dangantau da kuma yabau na yankin magana ko na jumla. (Tsoho 2002, Shf: 150-159 da 159-202).

A taƙaice dai a iya cewa yabau wata hikima ce ko salo da ake amfani da shi a cikin waƙa ko a kirari domin a kwarzanta ko kuma a koɗa wani mutum ta hanyar sarrafa kwalliya ko alamci ko kuma a danganta shi da wasu mutane masu kima da daraja, domin shi ma girmansa da martabarsa gami da jarumtakarsa da kuma asali da muhibba su bayyana tare da ɗaukaka a idon duniya. Haka kuma akan haɗa mutum da waɗanda mutane da ke da daraja da kima a idonsa kuma yake jin yana son su misali kamar iyaye da matan mutum da kuma ‘ya’yansa domin a ƙara masa ƙaimi a kuma yaba shi a cikin waƙa. Za a iya ganin misalin salon yabau a cikin waƙar salo a cikin ɗiya da dama. Misali :

J: Na tuna da Garba Mabera Ɗ 2,

:Baban A’i,

:Baban Balkisu na yaba maka hairan,

:Abu na Ma’inna,

:Bari wannan mutum yana kaɗa tifa,

:Dogo ɗan Magaji mai kaɗa ƙarfe,

:Bala mai roka Bala na Babban Rami Ɗ 2,

:Ya angon Amina,

:Bari wannan direba na kaɗa ƙarhe,

:Sani ɗan babanai na Tambuwal mai mota,

:Ya Allah jiƙan musulmi Mamman,

:Don na tuna Amadun tasha ya hwaɗi,

:Bari wannan direba na kaɗa ƙarfe,

:Sani Sabulu yana gaishe shi.

Idan muka duba wannan ɗan waƙar, za mu ga cewa Sani Sabulu ya yi amfani ne da salon yabau musamman na dangantau, inda ya yi ta jero sunayen masoyansa waɗanda yawancinsu direbobin mota ne yana yaba musu tare da nuna shaharar su a fagen sana’arsu ta tuƙin mota. Makaɗin ya yi ta amfani da iyali musamman mata da ‘yayan waɗanda yake yabawa da kuma abokan arzikinsu wani lokacin har ma da iyayensu yana yaba musu, tare da fayyace shahararsu da bajintarsu a kan sana’arsu ta tuƙi, wanda masana suka tabbatar da cewa yin hakan a cikin waƙa salo ne na yabau dangantau.

Kammalawa

Haƙiƙa salo da iya sarrafa shi a cikin waƙa shi ke ba makaɗi dama ya fayyace duk wani saƙo da yake da buƙata ba tare da tasgaro ba, kuma shi ke sa waƙa ta burge ta yi daɗi sannan kuma ta rayu tsawon lokaci ana yayinta ko da kuwa makaɗin da ya yi ta ya mutu. Haka kuma idan aka rasa shi a cikin waƙa takan kasance lami mai saurin gundura kuma hakan kan sa takan ɓace gaba ɗaya a daina jin ta cikin ɗan ƙanƙanin lokaci ko da kuwa makaɗin da ya yi ta yana nan a raye. Bisa la’akari da kima da daraja da salo ke da ita a cikin waƙa ya sa nake ganin ba a yi kuskure ba idan aka ayyana shi a matsayin ruhin waƙa, wanda a kansa waƙa ke rayuwa. Sannan kuma rasa gwaggwaɓan salo a waƙa yakan sa ta mutu murus. Waƙar ‘Salo’ ta Alhaji Sani Sabulu Kanoma waƙa ce da makaɗin ya baje kolinsa a cikinta ta hanyar wasa da harshe da sarrafa salo yadda ya ga dama, don haka ta kasance ɗaya daga cikin waƙoƙin makaɗin da har yanzu ake saurare tare da yayi a duk lokacin da aka kunna ta. Wannan maƙala ta nazarci salailai ne mabambanta waɗanda Sani Sabulu ya yi amfani da su a cikin waƙar ‘Salo’. Maƙalar ta gano cewa makaɗin ya yi amfani da salailai da dama wajen gina saƙon waƙar kuma haka ya sa waƙar ta amsa sunan da aka kira ta da shi kuma hakan ya sa ta rayu tsawon lokaci duk kuwa da cewa shi makaɗin ya daɗe da rasuwa. Haka kuma maƙalar ta tabbatar da cewa iya sarrafa salo na makaɗin ya sa ya shahara ya kuma sami karɓuwa, wanda hakan ya dace da harsashen masana. A ƙarshe maƙalar ta tabbatar cewa Alhaji Sani Sabulu Kanoma makaɗi ne da ya gwanance wajen iya sarrafa harshe da salo tare da gina waƙa cikin tsari mai ban sha’awa da armashi.

Manazarta

Amin, M.L. (19193) .Sake leƙa Adon Harshe; Nazarin kwalliya a rubutattun wakokin Hausa, Kungiyar Habaka Hausa, Ahmadu Bello University, Zaria.

Ayuba A. (2012). Zuga da Yabau: Matakan Yabo a Bakandamiyar Abubakar A kwara. A cikin Champion of Hausa Cikin Hausa, A Festcrift in Honour of Ɗalhatu Muhammad, Zaria: Department of African Languages and Cultures, Ahmadu Bello University.

Baldick, C. (2004), Oxford Concise Dictionary of Literary Terms, Oxford University Press, New York.

Bashir, R. (2000). Zuga da Yabau a Bakandamiyar Ibrahim Narambaɗa. A cikin YOJOLAC.

Bashir, R. (2014). Salon Sarrafa Harshe A Waƙoƙin Shata. Zaria. M.A Thesis, Ahmadu Bello University.

Bello, G. (1976). “Yabo Zuga Da Zambo a waƙoƙin Fada” A Cikin Harsunan Nigeriya VI, Kano Bayero University.

Bunza, A. M. (2003). Kashin Baƙi sai Taro: Riwayar Bakandamiyar Gambu a Zaren Tunanin Manazarta Al’ada. A Seminar Paper, Sokoto, Usman Ɗanfodio University.

Bunza, A. M. (2009). Narambaɗa. Lagos: Ibrash Islamic Publication Center Ltd.

Cuddon, J. A. (1977). A Dictionary of Literary Terms. Andre Doustsch, London.

Dunfawa, A. A. (2004). Zuga A Cikin Waƙoƙin Fada. A cikin Algaita Journal of Current Hausa Reserch in Hausa Studies No. 3 Volume 1, Kano: Department of Nigerian Languages Bayero University.

Ɗan’iya, D. (1997) .Adon Harshe a cikin Rubutaccen Adabin Hausa. M. A. Thesis, Bayero University, Kano.

Ɗangambo, A. (1973), Shata Da Waƙoƙinsa. B.A. Project, Abdullahi Beyero College, Kano.

Ɗangambo, A. (1978), Rikiɗar Azanci: Siddabarun Salo da Harshe Cikin’ Tabarƙoƙo’, Tahamisin Aliyu Ɗansidi Sarkin Zazzau. Published in Hausa Language, Literature and Culture, the first Hausa International Conference, Bayero University, Kano.

Ɗangambo, A. (2007), Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa. Fisbas Media Services, Zariya.

Ɗangambo, A. (2008). Rabe-Raben Adabin Hausa. Amana Publishers Ltd, Kaduna.

Funtua, A.I. (2011), Mamman Shata a Fagen Saka Karsashi a Rayuwar Al’umma, in Waƙoƙin Baka Na Hausa, Katsina, Federal College of Education.

Funtua, A.I. and Gusau, S.M. (2011). Wakokin Baka na Hausa. Centuary Research and Publishing Ltd, Kano.

Garba, S. (2011). Salon Sarrafa Harshe A Waƙoƙin Aƙilu Aliyu. PhD Dessertation, Department of African Languages and Culture, Ahmadu Bello University, Zaria.

Gusau, S.M. (1985), Salo Da Sarrafa Harshe a Waƙoƙin Baka Na Hausa. Wadda aka gabatar aa taron ƙarawa juna ilimi na uku kan harshe da adabi da al’adun Hausa, Bayero University, Kano.

Gusau, S.M. (1996), Dabarar Alkunya a waƙoƙin Makaɗan Baka. In Mujallar Afrika ta Yamma kan harshe da adabi da sharhi Volume I, Bayero University, Kano.

Gusau, S.M. (2003), Jagorar Nazarin Waƙar Baka, Benchmark Publishers Ltd, Kano.

Leech, G.P. (1968). A Linguistic Guide to the Study of Poetry, London.

Muhammad, D. (1990), Hausa Metalanguage, (edit) University Press Ltd, Ibadan.

Sa’id, B. (1978). Salo da tsarin Rubutacciyar Waƙar Hausa Ta ƙarni na 19: A cikin Yahaya, I.Y. da Rufa’I, A. (eds), Studies of Hausa Language, Literature and Culture, First Hausa International Conference, Centre for the Study of Nigerian Languages, Bayero University, Kano.

Umar, M. B. (1984).Symbolism in oral Poetry; A Study of Symbolical Indices of Social status in Hausa Court Songs. M. A. Thesis, Department of Nigeria and African Languages, Ahmadu Bello University, Zaria.

Yahya, A.B. (1997). Jigon Nazarin Waƙa. Kaduna: Fisbas Media Services.

Yahya, A.B. (2001). Salo Asirin Waƙa, Kaduna, Fisbas Media Servi

Amsoshi
ces.

Yakawada, M. T. (2002). Eulogues: The building Blocks of Hausa Praise Songs. PhD. Thesis, Zaria: Department of Nigerian and African Languages. Ahmadu Bello University.


Post a Comment

0 Comments