Citation: Nalado, N., Rabe, H. and Hassan, S. (2024). Ta’addanci Da Rayuwar Bahaushe: Gargaɗi Daga Waƙar Ɗiyan Jemage ta Mamman Shata Katsina. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 440-447. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.055.
TA’ADDANCI DA
RAYUWAR BAHAUSHE: GARGAƊI
DAGA WAƘAR ƊIYAN JEMAGE TA MAMMAN SHATA KATSINA
Nuhu Nalado
Hassan Rabe
Sani Hassan
Sashen Nazarin
Harshen Hausa, Tsangayar Nazarin Ilimin Sakandare, Ɓangaren
Harsuna, Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita
Tsakure:
Aikin ya himimmantu ne wajen nazarin gudummawar waƙar
baka ta Dr. Mamman Shata Katsina ɗauke
da taken ‘Ta’addanci A Rayuwar Bahaushe: Gargaɗi
daga“Waƙar
Ɗiyan
Jemage”Ta Mamman Shata
Katsina. Manufar aikin ita ce nazartar Jigon Gargaɗi dake a cikin waƙar. Aikin bincike ne na
bayani a ɓangaren
ayyukan Adabin Hausawa a gurbin waƙar Baka. Haka kuma aikin ya gudana ne ta
hanyar nazartarwasu ayyukan masana da manazarta a wannan fanni.Tare da sauraron
waƙar
ta yin amfani da Na’urar
wayar Salula, a inda aka yi amfani da abubuwan da aka saurara daga waƙar aka
rubuta su domin samun damar yin Nazari. Duk dai a wannan gaɓa, an ɗora Binciken a bisa ra’in
Bincike na Mazhabar Waƙar Baka Bahaushiya. Daga bisani, nazarin ya gano tare da
tabbatar da cewa waƙoƙin baka na Hausa wani babban kamdami ne na ilimi da ke
taimakawa wajen tafiyar da rayuwar al’umma
a halin da ake ciki da kuma maizuwa. Haka kuma, waƙar na ɗauke da wannan jigo na
gargaɗia kan illar
gudanar da ayyukan ta’addanci a rayuwar Bahaushe.
Fitilun Kalmomi: Ta’addanci, Rayuwar Bahaushe, Gargaɗi, Waƙar
Baka, Mamman Shata Katsina
Gabatarwa
Waƙar baka, wani zance ne shiryayye cikin hikima
da azanci da yake zuwa gaɓa-gaɓa
bisa ƙa’idojin tsari da
daidaituwa a rere cikin sautin murya da amsa-amon kari da kiɗa
da amshi (Gusau, 2023:ɗiɓ).
Haka kuma, dangane da siga da zubi da tsarin aiwatarwa, Bahaushiyar waƙar baka ba ta zuwa a shimfiɗe
ko ta zo gaba ɗaya, a’a, tana zuwa ne
gutsure-gutsure tare da maimaita gindinta a tsakaninsu. Gutsure shi ne ‘ɗa’.
A waƙar baka ba a ƙayyade yawan layuka a ɗan
waƙa, musamman ga makaɗan
da suke cikin ƙungiya, suna maimaita
gindin waƙa a ƙarshen kowane ɗan
waƙa.
Samun
asalin yadda aka fara waƙar
baka a kowace al’umma yana da wuya da kuma neman bincike mai zurfi. Akwai saɓanin
ra’ayoyi game da asalin waƙar
baka a rayuwar Hausawa. Ana jin Ɗan’adam
ya ƙagi waƙa ne tun lokacin da ya fara neman abinci ta
hanyar ‘farauta’. Daga bisani da mutane suka sami fasahar noma sai waƙa ta ƙara
haɓaka. Wasu kuma na ganin hanyar bauta ta
gargajiya ta daɗa bayar da haske wajen
kyautata sha’anin waƙa (Gusau, 2023:7).
Daga
cikin ra’ayoyin da ake bayarwa dangane da asalin waƙa a ƙasar
Hausa, akwai inda ake ganin waƙa
ta samo tushe ne daga wajen wani maroƙi
‘Sasana’. Domin haka , a wannan ra’ayi ana jin makaɗan
Hausa jikokin wannan mutum ne da ake kira Sasana wanda ya rayu a ɓangaren
Asiya. Daga baya wasu daga cikin ‘ya’yansa suka yiwo ƙaura zuwa ƙasashen
Hausa. Kalmar ‘Sasana’ tana nufin ‘maroƙi’
da harshen Faransanci (Gusau, 2023:7). Duk dai a wannan gaɓa
masanin ya habarto Sasana a matsayin maroƙi
na farko da aka yi tun a lokacin Jahiliyyar duniya. Ta fuskar maroƙan na harshen Hausa kuwa ba a barsu a bayaba
ta wannan fuska. Kasancewar nazarin ya habarto Bature maroƙin Dr. Mamman Shata na danganta uban kiɗinsa
da cewa:
“Duna na Bilkin
Sambo;
Kafiri ƙanen Sasana.
Mai tada ta aljannu da mutane” (Gusau, 2023:8
da Nalado, 2019: 2).
Ko
shakka babu,wannan nazari na ganin waƙa
a matsayin wani tsararren zance ne na hikima, wanda kan kasance a tsare kuma a
shirye da ke zuwaa lafazance.Da kan gudana da taimakon wasu mutane ko ƙugiya
a sigar amshi ko kiɗa a wani keɓantaccen
lokaci domin cimma wata manufa da aka gina waƙar
a kai.
Manufar
aikin ya taƙaita ne ga nazarin
ilimantarwa a cikin sigar gargaɗida ke a cikin wannan waƙa ta Dr. Mamman shata mai taken:‘Ɗiyan Jemage’,da ya gabatar akan wani mutum a
lokacin rayyuwarsa. Akanillar ayyukan ta’addanci a rayuwar Hausawa.
Waƙar
an yi ta ne a shekarar ‘1969’ a matsayin kashin farko na samuwar waƙar. Mutuen da aka yi wa waƙar kuwa shi ne Mati ɗan
‘Yarbanye da ke a garin ‘Yamma,Ƙaramar
Hukumar Bakori ta Jihar Katsina,Tarayyar Najeriya. Waƙar ta gudana a cikin sigar yabo da salon
kambamawa.
Yana
daga cikin muhimmancin wannan bincike na ƙara
samun bunƙasa nau’oin saƙonnin da waƙa
ke ɗauke su da kuma ciyar da fagen bincike a
wannan fanni gaba. Duk a cikin wannan gaɓa za a kawo jerin wasu
muhimman kalmomi da suka shafi binciken tare da bayanansu a taƙaice. Domin ƙara
samar da fahimta a lamarin. Haka kuma,an kawo ratayen waƙar da nazarin ya ginu akai a ƙarshen Manazarta.
Muhimman Kalmomi:
Ta’addanci darayuwar Bahaushe da gargaɗi da ɗiyan
jemage dauwa da mugu da kalmar kunya.
Ta’addanci: Sa’id (2006:416), ya
bayyana cewa kalmar na nufin ɓarna ta ganganci da ta
shafi aikata mugun aiki a tsakanin al’umma. Shi kuwa Nalado (2015:3), bayyana
ma’anar ta’addanci da cewar wasu munanan ɗabi’u ne da suka zamanto
daga cikin baƙin al’adun Hausawa ko kuma
mummunar tada da ta shafi aikata wasu al’amurra na rashin sanin ya kamata da ke
salwantar da dukiya da rayukan al’umma a rayuwar yau da kullum. A ɓangare
ɗaya, Maƙalarna
ganin tsari ne na aikata rashin daidai a zamantakewar al’umma da ya shafi duk
wani nau’in sata da aikata miyagun laifuka a tsakanin al’umma. Kamar yadda ya
faru a tsarin ɗiyan waƙar da nazarin ya ginu akai.
Rayuwar Bahaushe: Tsarin
rayuwace managarciya da ke gudana a wasu muhimman turaku ko sigogi guda goma
sha huɗu da suka shafigurbin hankali da gurbin wayo
da gurbin gaskiya da kunya da kamun-kai da nuna halin kirki da son zumunci da
taimakon juna da ƙoƙarin haɗiye kwaɗayi
da guje wa nuna son kai. Sauran sun haɗa da mora wa kai da kishin ƙasa da mutanenta da sadaukar da kai da kuma
hangen nesa a kan lamurran rayuwa Bunza (2013: 2). A nasa ɓangaren,
Sallau (2000:27). Ya furta cewa, “Bahaushe mutum ne da Allah Subhanahu Wata’ala
ya kimtsawa tunaninsa a turba ko bagiren gudanar da rayuwa a bayan ƙasa. Da yake rayuwarsa a farfajiyar ƙasar Hausa gabanin wannan zamani.” Duba da waɗancan
ma’anoni na masana, aikin na ganin rayuwar Bahaushe wata rayuwace da ake
gudanarwa a bisa tsari da kiyaye haƙƙoƙin al’umma. Tayadda akasin hakan ba ya daga
cikin ayyukan al’adunsa.
Gargaɗi:
Kalmar na nufin jan kunne ko yin kashedi ko horo Sa’id
(2006:156). Duba da wannan ma’ana, nazarin ke ganin kalmar a matsayin al’amari
ne da ya shafi nusar da mutum ko wasu mutane a game da illar aikata wani aiki.
Ko ƙoƙarin nisantar da al’umma ne ga dakatar dasu a
wajen aikata wani abu da ake ganin yana da matsala a rayuwa.
Onle: Kalmar na nufin ɓarawo
da harshen Yarabanci.
Enyusi: Na nufin ɓarawo
da harshen Inyamuranci.
(Ɗan baiti na biyar a waƙar ɗiyanjemage
ta Mamman Shata).
Mugu: Bunza (2014:iɗ)
da Said (2006:348). Sun yi tarayya a wajen ayyana kalmar a matsayin ɓarawo.
Binciken na ganin ma’anar ta shafi duk wani mutum mai mummunan hali da yake
cutar da al’umma.
Ɗiyan jemage: Sa’id
(2006:156). Ya nuna cewa kalmarna nufin “Ɗanjaura,
ma’ana mutumin da yake yawo kasuwa-kasuwa yana baza tarkacensa domin sayarwa”.
Tayadda binciken yake ganin ɗan waƙar na uku na a matsayin jigon gargaɗi
ga mutane. A inda aka danganta halayyar tauraron da ta Ɗanjaura.
Kunya: Bunza (2006:249).Ya bayyana kunya
da cewar, “Wata magana ce ko wani aiki da ya saɓa
wa tsarin kamun kai na al’ada, kuma al’ada ta zarge shi da muni na zubar da
girma da mutunci”. Binciken na ganin al’amari ne da yake tattare da damuwa da
samar da ɓacin rai ga mutum ko danginsa a tsarin
zamantakewar Bahaushe,wanda kan haifar da zubewar ƙima da mutunci acikin al’umma.
2.0
Tarihin Mawaƙi
a Taƙaice
Mamman
Shata na ɗaya daga cikin al’ummar Hausawa mazauna ƙasar Hausa, wanda aka haifa a garin Musawa, a
gidan wani mutum da ake kira da suna Ibrahim Yaro. Mahaifiyarsa ta kasance
Bafillata mutuniyar Tofa ta ƙasar
Kano mai suna Lariya. Mahaifinsa mutum ne mai nasaba da mutanen Sanyinna da ke
a ƙasar Sakkwato. A na
hasashen haihuwarsa a shekarar ‘1922’. Ya kuma rasu a ranar Juma’a ‘8/06/1999 ‘
a wani asibiti da ke Kano. An kuma rufe shi a garin Daura a ƙarƙashin
jagorancin ubangidansa tsohon Sarkin Daura, watau Sarki Muhammadu Bashar. Mawaƙin ya rayu da mata huɗu
na aure a garin Funtuwa. Yana da ‘ya’ya da dama. Daga cikinsu akwai Lawal da
Sanusi waɗanda ke ƙoƙarin aiwatar da waƙa bayan rasuwar mawaƙin. A lokacin rayuwarsa ya yi fice a
sana’arsa ta kiɗa da waƙa a duk faɗin
ƙasar Hausawa (Nalado da
wasu, 2018:3).
3.0 Bitar
Ayyukan da Suka Gabata
Masana
da manazarta a mabambanta lokutta sun tofa albarlacin bakunansu a game da
wannan maudu’i na waƙar bakar Bahaushiya. A
fannonin daban daban. Gusau, (2008: 1-150) da Gusau(2023:1-119).Ya nazarci waƙar baka a duniyar adabin Hausawa ta fuskar
yanaye yanayenta da hanyoyi ko matakan da za a yi amfani da su a matsayin
jagora ta fuskar gudanar da nazarin waƙa
Bahaushiya. A inda ya yi bitar ma’ana da asalin samuwar waƙar baka ga Bahaushe da muhimmancin waƙoƙin
tare da nau’oinsu. A wata mai kama da wannan, Nalado da wasu, (2018:1-14) da
Nalado(2019:1-12 da Rabeh, (2010: 1-12). Sun yi tarayya wajen nazartar muhimmancin
waƙar baka Bahaushiya wajen
ilimantarwa a tsakanin al’umma a fannoni daban daban.
4.0
Hanyar Gudanar Da Bincike
Duba
da cewa bincike ne na nazari da ya shafi bayyanawa a turbar ilimantarwa. Tsarin
ya gudana ne ta fuskar bitar wasu ayyukan masana da manazarta a ɓangaren
littafai da muƙalu da kundayen bincike.
Lamarin bai wanzu ba face sai da aka yi nazarin waƙar da ta jagoranci aikin ta hanyar sauraro.
Tayadda daga bisani aka rubata baitukan da nazarin ya shafa.
4.1.
Ra’in Bincike
An
ɗora aikin a bisa Ra’in Mazhabar Waƙar Baka Bahaushiya. Ra’ai ne da ya wanzu a
shekarun ‘1993’, a ƙarƙashin jagorancin Farfesa Sa’idu Muhammad
Gusau.
Manufar
ra’in ya shafi bayyana tarihi da asali da salsalar waƙar baka ta Hausa. Da kuma zurfafa bayani a
kan turke da abubuwan da waƙa
ta ƙunsa. Ita wannan mazhaba ta
tarken waƙar baka Bahaushiya ta
jinginu da wasu ra’oi na wasu Mazhabobin ra’i da suka haɗa
da Mazhabar Gargajiya. Ayyukan da aka samu nada suka yi amfani da wannanMazhaba
suna da yawa. Kaɗan daga cikinsu akwai aikin
Garba, 1998 da Satatima, 2008 da Abubakar 2011 Gusau, (2023:23). Dangantakar
Ra’in da aikin da ake gudanarwa shi ne, aikin ya ginu ne a kan nazarin
gudummuwar waƙar baka ta Dr. Mamman Shata
Katsinaa gurfin Ilimantarwa ta fuskar illar ayyukan ta’addanci a tsakanin
al’umma. Shi kuma ra’in yana magana ne a kan nazarin waƙar baka Bahaushiya. Duba da wannan dalili ne
aka zaɓi ɗora aikin a bisa wannan
ra’in bincike.
5.0
Waƙar Ɗiyan Jemage ta Dr. Alhaji Mamman Shata Katsina
Waƙar na daga cikin rukunin waƙoƙin
Dr. Mamman Shata na biyu da ta kasance daga shekarun alif ɗari
tara da sitti zuwa alif ɗari tara da tamanin
(1960-1980) Nalado, (2018: 10). An fara aiwatar da waƙar a garin Funtuwa a shekarar 1969. Wanda aka
yi wa waƙar wani mutumen garin
‘Yammama ne kamar yadda bayani ya gabata. Jigon waƙar ya shafi bayani a kan illar da ke tare da
gudanar da ayyukan ta’addanci a cikin al’umma domin kada a yi, sannan a yi
hattara da masu yi.
Waƙar na ɗauke da salon aiwatarwa mai
armashi da kuma kambamawa da ta zarta tunanin mai tunani (Kambamar zulaƙi). Wani abin sha’awa a game da waƙar shi ne, an kawo wasu ɗiyan
waƙa da suke yin nusarwa ga
al’umma, dangane da yadda ɓarayi ke tafiyar da
al’amurransu a yayin da suka yi sata. Musamman ta fuskar yin satar da sigar
satar da kuma bin sawu. Nazarin ya fahimci waƙar
ta halarto da wasu ayyuka da tadoji na ta’addanci da ke faruwa a wannan lokaci.
Duk da cewar a lokacin da aka yi waƙar
ba bu wannan matsala a cikin rayuwar al’ummar, kamar yadda take faruwa a yau.
Ko ba komai a iya yin itifaƙin
cewa ayyukan adabin harshen Hausa a fagen waƙar
baka muhimmin ɓangare ne da ya ƙunshi hasashe da hangen nesa. Kamar yadda ya
faru a wannan gaɓa da aka samu tsawon
shekaru hamsin da huɗu. A tsakanin wanzuwar waƙar da faruwar ayyukan ƙunshiyar waƙar
a rayuwa ta zahiri. Kasancewar a yau al’ummar Arewacin ƙasar nan na fama da matsalolin da suka shafi
tsaro da ta’addanci da ya samo asali daga waccan satar shanu da dabbobi na
Makiyaya,(Nalado, 2019:10).
5.1
Dangantakar Waƙar Ɗiyan Jemage da Ayyukan Ta’addanci
Maƙalar na ganin ta’addanci a matsayin wani
al’amari da ya shafi aikata rashin daidai a zamantakewar al’umma, wanda ya haɗa
da dukkan wani nau’in sata da aikata miyagun laifuka a tsakanin al’umma. Duba
da hakan, an yi tsokacin dangantakar waƙar
da ayyukan na ta’addanci a matakai guda huɗu.
5.1.1
Bayyana Suna da Tadar Masu Aikata Ta’addanci
Tada
wasu ayyukan al’ada ne da suka shafi gudanarwa da sassan jiki da kuma wadda ta
shafi ƙudurtawa a zuciya a fagen
wasu ayyuka,(Bunza, 2006:75). Waƙar
ta halarto da sunan da ake kiran mutumin da ke aikata wannan laifi a cikin
harsuna da ke da maƙwabtaka da harshen Hausa a ƙoƙarin
wayar da kan al’umma. Hakan ya bayyana ne a ɗiyan
waƙa na ɗaya
da na biyu da ɗanwaƙa na takwas da na tara. Ga abin da Mamman
Shata ya faɗa,
Jagora: Na Abdu Ɗanjemage a gaba ake goyonka ɗan-ɗan Mani.
Jagora: Gata mai ɓarna baban ‘Yarbanye.
Jagora: Tafiyata Kurmi ga ɗiyan Yarabawa.
Na ji sun ce Ole.
Na
biyo ‘Yan Hausa, Mamman suna kiran ka ɓarawo.
Inyamurai
kau sun ce ma Anyusi.
Jagora: Wai duk ɓarawon ne ke nan ‘yan Hausa.
Amshi: Haka nan ne Mamman ƙanen Idi wan Yalwa’.
Ɗiyan waƙar
sun halarto da Tadar masu aikata wannan nau’in aiki ta amfani da Tauraronsa. In
da aka bayyana su da cewar mutane ne maɓarnata da ke buƙatar a rinƙa
kulawa ta hanyar lura da al’amurransu domin kar su sami damar cutar da al’umma.
Lamarin bai tsaya a nan ba, face sai da aka kawo sunan da ake kiran mutumin da
abun ya shafa acikin yaren wasu daga cikin al’ummomi masu maƙwabtaka da Hausawa domin ƙara faɗakarwa da gargaɗi
ga al’umma.
5.1.2
Faɗakarwa
a Game da Tsarin Gudanar da Aikin Ta’addanci
Muƙalar ta fahimci hakan ya faru ne a cikinɗiyan
waƙa na uku da na huɗu
da kuma na biyar daidai inda Mamman Shata ya ce:
Jagora: A faɗa wa Mamman, matuƙar ka ɗauko sa’a.
Sa’ar tai sa’a.
Idan ka je gun ƙofa, har in ka buɗe
ƙofa.
Mamman in ka shiga ɗakin, harka iske kaya.
To
zari akwatin tsakiya shi ya fi kaya.
Jagora: In dai ka buɗe ɗakin ka ishe shi a shirye.
To
zari akwatin tsakiya shi ya fi kaya.
Jagora: Nasaman hoto ne.
Na ƙasa maganin ƙwari ne.
Zo
zari akwatin tsakiya shi ya fi kaya.
Amshi: Haka nan ne Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Duba
da waɗannan ɗiyan waƙa, ya nuna cewar waƙar na faɗakar da al’umma a game da
tsarin yadda masu aikata wannan mummunan hali suke bi wajen gudanar da aikinsu.
Duba da yadda suke neman sa’a daga ayyukan addininsu da kuma yadda suke amfani
da tunani a wajen ɗaukar kayan da za su sata.
Hakan wata dama ce da za ta faɗakar da al’umma a game da
wannan matsala domin su kiyaye kuma su sake tsarin ajiye dukiyarsu daga fasalin
sa ta a cikin akwatin tsakiya.
5.1.3
Hoton Ayyukan Ta’addanci a Harshen Waƙa
A
wannan gaɓa mawaƙin
ya yi amfani da hikimarsa inda ya habarto wannan jigo a cikin jerin ɗiyan
waƙa naGoma har zuwa ɗanwaƙa na Goma Sha Biyar. Ga yadda abin ya
kasance:
Jagora: Ka ga yana yankan Aljihu birni’
Jagora: Na Audu ya ɓalle ƙofa
in ambarci.
Jagora: Ba yash shiga banki baƙon Ɗammani.
Jagora: In ya shiga daji ya
ishe Hillani,
Mamman
Na Audu kore dut baƙon
Ɗammani.
Jagora:
Ka kore dut baƙon
Ɗammani ko jaki kore Ɗanshata.
Jagora: Bari bar masu ko jaki kore Ɗanshata.
Amshi: Haka nan ne Mamman ƙanen Idi wan Yalwa’.
Waɗannan
ɗiyan waƙa
da suka gabata na a matsayin dangantakar waƙar
da ayyukan ta’addanci. Kasantuwar waƙar
ta fito da hoton nau’ukan ayyukan ta’addanci a bayyane domin a kula a kuma
kiyaye aikatasu. Sannan mawaƙin
yana nuna wa al’ummace irin yadda waɗannan miyagun mutane suke
korewa tare da kwashe dukiya da kuma dabbobin al’umma.
5.1.4
Dabarun ‘Yanta’adda a Ayyukan Ta’addanci
Har
ila yau, wannan mawaƙi a waƙar tasa ya nuna wasu daga cikin dabarun da
‘yanta’adda suke amfani da su wajen ɓatar da kayan da suka sata.
Don a wannan gaɓa muƙalar ta habarto Mamman Shata a ɗanwaƙa na goma sha shida zuwa na ashirin da biyar
yana cewa:
Jagora:In ya kori bisashe,
sawu sun Yamma.
Shi
Gabas baƙon
Ɗammani.
Jagora: Yi Gwambe da su baƙon ‘Yarbanye.
Jagora:Ko ko ka yi Bauci da su baƙon Ɗammani.
Jagora: Ko ko ka yi Barno da su baban
‘Yammani.
Jagora: Ko ka tsallake Kamaru Baƙan ‘Yarbanye.
Jagora: Ko ka laɓe Baga baƙon
Ɗammani.
Jagora: A nan babu mai zuwa cigiya domin
shanunai.
Jagora: A nan wani daji!
Nan
babu mai zuwa cigiya domin shanunai!
Jagora: A nan ba bu mai zuwa cigiya domin
shanunai!
Jagora: Da ka tahi Baga.
Ko ko ka tahi Barno!
In ka laɓe
wani daji, anan babu mai zuwa cigiya domin shanunai.
Jagora: Wa za ya gane Mamman ɗan-ɗan Mani?
Jagora:
Yi hannun riga tafi ɗauki abin ɗauka
baƙon Ɗammani.
Amshi: Haka nan ne Mamman ƙanen Idi wan Yalwa’.
Waɗannan
ɗiyan waƙa
sun ƙara tabbatar da cewar akwai
dangantaka a tsakanin waƙar
da nazarin ya ginu a kai da ayyukan ta’addanci. Ganin cewa halayar da ke faruwa
a halin yanzu a cikin wannan al’umma ke nan. A inda za a aikata wani ta’addanci
a Katsina sai a tsinci mutumin da aka yi garkuwa da shi a Zamfara ko dajin
Kaduna ko na neja ko ma Sakkwato. A game da abin da ya shafi satar bisashe
kuwa, ba wani bambanci da bayanan da waƙar
ta zo da su.
5.2.
Gargaɗi
a kan Illar Ayyukan Ta’addanci
Sani,
(2017:10). Ya bayyana ta’addanci da cewar “Al’amari ne na aikata ba daidaiba a
tsakanin al’umma. Mai nasaba da sata da cutarwa, da ƙoƙarin
salwantar da rayuka da dukiyoyin al’umma”. A wannan nazari, ana
kallonta’addantanci da cewa al’amari ne da ya shafi aiwatar da rashin daidai da
saɓawa managartan al’adun zamantakewa a tsakanin
al’umma. A waƙar Makaɗa
Dr. Mamman Shata bai yi ƙasa
a guiwa ba wajen bijiro da wannan jigo a wasu jagororin ɗiyan
waƙarsa kamar haka:
Jagora: A faɗa maka Mamman.
Na kau hore ka!
Duk wanda bai ajiye ba.
Idan ya ce zai ɗauka!
Mamman
ka tabbatar kau kunya sai ta kammai.
Amshi: Haka nan ne Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
(Mamman Shata: Waƙar Ɗiyan-jemage).
A
cikin Sa’id, (2006:255),an bayyana kalmarkunya na nufin nuna kawaici da jin
nauyi da rusunawa saboda wata dangantaka a rayuwa. A gefe guda makaɗa
Dr. Mamman Shata ya yi amfani da wannan mizani na tantance Bahaushe a adabinsa
domin samun cimma wata manufarsa kamar haka:
Jagora: Haka niggan shi ba
kunya,
Yac ce da rabo a tsakanin ‘yar nan.
Da
mijinta na can baya.
(Mamman
Shata: Waƙar Alƙali Maɗanɗani).
A
wata faɗar jaddadawa Makaɗa
Mamman Shata ya ƙara cewa,
Jagora: Baya sarkin rashin
kunya.
Su kare ba a san harara ba
Mai
gidan shi ya ce abokinai.
(Mamman
Shata: W.aƙar Bala Gaye Balan Barde).
Duba
da Ɗiyan waƙarda suka gabata, binciken ya yi itifaƙin cewa kunya a rayuwar Bahaushe aba ce mai
matuƙar muhimmanci. Ganin yadda
addinin Musulunci har ma rayuwar maguzanci suka jaddada amfaninta. A rayuwar
Bahaushe a ce wa mutum ba ya da kunya tamkar zagi ne. Wasu waƙoƙin
Mamman shata sun samu daidaito a wannan gaɓa.
Bunza
(2013:8), ya kawo wasu matakai guda goma sha huɗu
da suka kasance mizanin da Bahaushe yake amfani da su wajen tantance sahihanci
ko nagartar kowane ɗan ƙabilarsa.
Ya ƙara da cewa rasa ɗaya
daga cikin waɗannan sifffofi a tsarin
zamantakewa da tarbiyyar al’ummar na iya canza matsayi a falsafar mutuntakar
Bahaushe. A inda wannan nazari ke tabbabatar da cewa,nuna halin kunya da
nisanta daga duk wani aiki da zai sajin kunya na a matsayin muhimmin al’amari
ga rayuwar Bahaushe.
A
tsarin rayuwar Gargajiyar Bahaushe, yin abin kunya nasa mutum ya bar garinsu ko
karkararsu har abada. Maƙalarna
ganin wannan dalili ne ya taimaka wa mawaƙin
ya cimma manufa ko saƙon
da yake ƙoƙarin isarwa ga al’umma ta wannan fuska.
Samuwar hakan ya kasance hanyar da mawaƙin
ya yi amfani da ita wajen gargaɗi ga al’ummar a kan wannan
mas’ala cikin salo mai armashi.
6.0
Shawarwari
Al’amarin
waƙar baka Bahauhiya, abu ne
mai girma da faɗi a fagen koyar da darussa
masu alfanu ga rayuwar al’umma. Lamarin bai keɓanta
ga iyakacin al’ummar Hausawa kaɗai ba, face sai da ya shafi
kowace irin al’umma da take rayuwa a doron ƙasa.
Matuƙar dai za ta fahimci ƙunshiyar saƙoni
ko darussan da waƙoƙin suke ɗauke da su. Ganin an iya
fahimtar cewa wasu waƙoƙin na halarto da hasashen ayyukan rayuwa
wadda za ta faru a sakamakon aiwatar da waɗansu ayyuka da suka saɓa
wa al’adu managarta na tsarin zamantakewar al’umma.
Hakan
ne yasa Muƙalar ke kira tare da bayar
da shawara musammam ga matasan Hausawa da basu da sha’awa ko ɗabi’ar
nazari da kuma sauraron waƙoƙin Gargajiya. Da su lazimci amfani da su
domin suna ɗauke da muhimman darussa a fagen rayuwa.
7.0
Kammalawa
Waƙar baka daɗaɗɗiya
ce wadda aka fara ta tun lokaci mai nisa da ya shuɗe. A inda ta ci gaba da bunƙasa har zuwa yau. Nazarin ya fahimci cewa waƙar baka Bahaushiya na gudana ne ta amfani da
wasu matakai wato a yayin aiwatarwa da suka haɗa
da Jagora da ‘Yan amshi da kiɗa da mabanci tare da
sarrafa hikima da amfani da fasaha da murya da rerawa a yayin aiwatarwa. Haka
kuma, wannan nazari ya gano cewa waƙoƙin baka na Hausa wani babban kamdami ne na
ilimi da suke taimakawa a wajen tafiyar da rayuwar al’umma a halin da ake ciki
da kuma hali ko yanayi maizuwa.
Kamar
yadda sauran al’ummomin da suke rayuwa a doron ƙasa
suke fama da miyagun ayyuka daga wasu ɓaragurbi a cikinsu, wannan
al’umma ta Hausawa ba a barta a bayaba ta wannan fuska.A inda suke aiwatar da
mabambanta ayyukan ta’addanci a tsakanin al’umma. Hakan ya samo asali da bunƙasa a sanadiyar cakuɗuwa
da baƙin al’adun al’umma
daban-daban. Musamman ta sanannen tsarinnan na Game-duniya (Globlisation).
Waccan
matsala ta cakuɗuwa da baƙin al’adun al’ummu ta kasance babban dalilin
faruwar matsalolin ayyukan ta’addanci da al’ummar Arewacin ƙasar nan ke fama da shi a yau.Waɗandasuka
haɗa da satar dukiya da dabbobi da garkuwa da
mutane da ma ayyukan kisan kan mai-uwa-da-wabi a tsakanin al’umma. Wanda ke ci
gaba da haifar da matsaloli a rayuwar Hausawa da sauran al’ummomin cikin ƙasa.
Duba
da haka ne ake ganin waƙar
Mamman Shata Katsina ta zama cibiyar gargaɗi da hana mutane ko jawo
hankalinsu a game da barin aikata ayyukan ta’addanci a tsakanin al’umma da kuma
sa mutane su yi hattara ko hankali da aikata hakan.
Manazarta
Bunza, A. M. (2013). “Hutawa ka Alewa, Mangyaɗa
ka Tuyar Ƙosai: Barazanar Yanayi da
Lokaci a kan Al’adun Hausawa”. Takardar da aka Gabatar a Taron Ƙara wa Juna sani na Ƙasa da Ƙasa
a kan Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa,
Katsina: Jami’ar Umaru Musa ‘Yar’adua.
Bunza (2014). In Ba Kasan Gari ba Saurari Daka: Muryar Nazari A Tafashen Muhammadu
Gambo. Kano: Darul Ummati Publishers.
Bunza,
A .M. (2006), Gadon Feɗe Al’ada. Jerin Littattafan Cibiyar Nazarin Al’adun
Hausa. Lagos: Tiwal. Nigeria Limited.
Ɗagoro, A. S. (2017).
“Nazarin Tsaro na Gargajiya na Jihar Katsina Jiya Da Yau”. Kundin Digiri na
Biyu. Katsina: Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Umaru Musa
‘Yar’adua.
Gusau, S. M. (2008). “Tarihi da Hanyar
Nazarin Waƙar Baka Bahaushiya a Taƙaice”. A cikin Waƙoƙin Baka Na Hausa. Katsina: Department of Hausa, Federal College
of Education.
Gusau, S. M. (2023). Mazhabobin Ra’i da Tarke A Adabi
da Al’adu na Hausawa. Kano: Century Research and Publishing Limited.
Gusau, S. M. (2023). Jagoran Nazarin Waƙar
Baka. Kano: WT Press, Printing and Publition.
Nalado, N. (2019). “Shata Mawaƙi ko Ɗansiyasa”.
Muƙalar da aka Gabatar a Taron
Ƙasa da Ƙasa a kan Mamman Shata Katsina, Kano: Center
for Nigerian Languages, Bayero University.
Nalado, N, Da wasu. (2018). “Shata A Fagen
Wa’azi: Waiwaye a kan Wasu Daga Cikin Waƙoƙinsa. Muƙalar
da aka Gabatara a Taron Ƙasa
da Ƙasa a kan Mamman Shata
Katsina. Kano: Center for Nigerian Languages, Bayero University.
Nalado, N. Da wasu. (2015). “Muguwar
Makaranta Maituƙa da Warwara:Barazanar
Ayyukan Ta’addanci a Falsafar Gambo”. Muƙalar
da aka Gabatar a Taron Ƙara
wa Juna sani, Dutsinma: IKCOE.
Sa’id, B. (2006). Ƙamusun
Hausa. Kano: Jami’ar Bayero.
Sallau, B. A (2000). “Wanzanci: Matsayinsa Na
Al’ada da Sana’a A Ƙasar Hausa”.Kundin Digiri na
Biyu. Kano: Jami’ar Bayero.
RATAYE
Waƙar Ɗiyan Jemage ta Dr. Mamman Shata Katsina
Jagora: Na Abdu ɗanjemage a gaba
ake goyonka Ɗanɗan
Mani.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Gata mai ɓarna baban
‘Yarbanye.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: A faɗa wa Mamman, matuƙar ka ɗauko sa’a.
Sa’ar tai sa’a.
Idan ka je gun ƙofa, har in ka buɗe ƙofa.
Mamman in ka shiga ɗakin, harka iske
kaya.
To zari
akwatin tsakiya shi ya fi kaya.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: In dai ka
buɗe ɗakin ka ishe shi a
shirye.
To zari akwatin tsakiya shi ya fi kaya.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Nasaman hoto ne.
Na ƙasa maganin ƙwari ne.
Zo zari akwatin tsakiyashi ya fi kaya.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Ka ga yana
yankar aljihu birni.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Na Audu
shege sai uwatai.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Tafiyata
Kurmi ga ɗiyan Yarabawa.
Na ji sun ce Ole.
Na biyo ‘Yan Hausa, Mamman suna kiran ka ɓarawo.
Inyamurai kau sun ce ma Anyusi.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Wai duk ɓarawon ne ke nan
‘yan Hausa.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Ka ga yana
yankan aljihu birni.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora:Na Audu ya ɓalle ƙofa in ambarci.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Ba yash
shiga banki baƙon Ɗammani.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: In ya
shiga daji ya ishe Hillani,
Mamman
Na Audu kore dut baƙon Ɗammani.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Ka kore
dut baƙon Ɗammani ko jaki
kore Ɗanshata.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Bari bar
masu ko jaki kore Ɗanshata.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: In ya kori
bisashe, sawu sun Yamma.
Shi
Gabas baƙon Ɗammani.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Yi Gwambe
da su baƙon ‘Yarbanye.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Ko ko ka
yi Bauci da su baƙon Ɗammani.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Ko ko ka
yi Barno da su baban ‘Yammani.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Ko ka
tsallake Kamaru baƙon ‘Yarbanye.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Ko ka laɓe Baga baƙon Ɗammani.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: A nan babu
mai zuwa cigiya domin shanunai.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: A nan wani
daji!
Nan ba mai zuwa cigiya domin shanunai!
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: A nanbabu
mai zuwa cigiya domin shanunai!
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Da ka tahi
Baga.
Ko ko ka tahi Barno!
In ka laɓe
wani daji, anan babu maizuwa cigiya domin shanunai.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Wa za ya
gane Mamman ɗan-ɗan Mani?
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Yi hannun
riga tafi ɗauki abin ɗauka baƙon Ɗammani.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa.
Jagora: Na dai hwaɗa maka Mamman.
Na kau hore ka.
Wanda duk bai ajiye ba, matuƙar yanaso zai ɗauka.
Mamman
ka tabbatar kau kunya sai ta kammai.
Amshi: Haka nan ne
Mamman ƙanen Idi wan Yalwa
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.