Citation: Yaya, A.B. (2024). Sassan Waƙa ‘‘Ta Tsaru!’’ a ‘Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa’. Four Decades of Hausa Royal Songs: Proceedings from the International Conference on the Life and Songs of Makaɗa Sa'idu Faru, 3(3), 1-12. www.doi.org/10.36349/tjllc.2024.v03i03.001.
SASSAN WAƘA ‘‘TA TSARU!’’ A ‘KANA SHIRE BABAN ‘YAN RUWA’
Daga
Abdullahi Bayero
Yahya
Sashen Koyar da
Harsunan Najeriya
Jami’ar Jihar
Sakkwato, Sakkwato
Can
dauri mallami a
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo,
Sakkwato
+2347031961302; bagidadenlema2@gmail.com
Tsakure
A
gargajiyance, ta alƙalamin Sadaukin Shaihin Malami Abdulƙadir Ɗangambo, Hausawa kan
hukumta waƙa da ɗayan matakai huɗu na yabo ko kushewa (Ɗangambo, 2007: 7-9). Wannan
muƙala
ta saka waƙar “Kana shire Baban ‘Yan Ruwa Na Bello Jikan ɗan Hodiyo” wadda
Sa’idu Faru ya yi wa Alhaji Muhammadu Macciɗo, a mataki na ɗaya, kuma tun kafin ya zama Sarkin
Musulmi. Muƙalar ta yi bayani cewa wannan waƙa ita ce za a iya yabawa
da cewa “Ta tsaru” ko “Ta burge ni” ko a ce “Ta yi” ko kuma da “Habawa!”, da
dai sauransu. Hujjar da aka kafa wannan iƙirari ita ce amfanin
da Sa’idu Faru ya yi da sassa uku na waƙa waɗanda su ne jigo, da
zubi da tsari, da salo, waɗanda kuma mabambanta ne a yadda mawaƙin ya yi amfani da
su. A taƙaice sassan uku kowanensu iri-iri ne ba tilau-tilau ba.
Su ne ake ganin muhimmai waɗanda suka sa waƙar ta hau mataki na ɗaya a idon Bahaushe a
gargajiyance. Haka kuma mawaƙin ya tsara waƙar yana mai cusa wani
sashi cikin wani ba tare da haddasa ruɗani ba.
1.0 Gabatarwa
Waƙar da aka fi kira da
sunan, ‘Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa, Na Bello Jikan ɗan Hodiyo’
mashahuriyar waƙa ce a ƙasar Hausa. Waƙa ce wadda shahararren
mawaƙin fada na Hausa Alhaji Sa’idu Faru ya yi wa Sarkin Kudun
Sakkwato Alhaji Muhammadu Macciɗo. Ya yi ta ne tun kafin Alhaji Muhammadu Macciɗo ya zame Sarkin
Musulmin Daular Usmaniya a Sakkwato.
Sa’idu malamin waƙa
Mai kwana ɗumi
Na Mamman na Balaraba[1]
Haka ne yake yi wa kansa kirari (wato
‘caji’ ga mawaƙan zamani) lokacin da yake rera waƙoƙinsa, kuma su ma ‘yan
amshinsa sukan yi masa kirarin a lokacin aiwatarwar. Masana da manazarta da ma
sauran jama’a sun fi sanin sa a matsayin mawaƙin Sarauta/Fada.[2]
Shi kansa mawaƙin da wannan matsayin ya ɗauki kansa domin ya ce,
Sa’idu Hwaru ka waƙa’ iko
Komi kaj jiya ƙarya akai
Sa’idu Hwaru ka waƙam mulki
Komi kaj jiya ƙarya akai
(Sa’idu Faru: Ɗan Hashim ƙanen Sarkin Kano)
Mai wannan muƙala yana neman uzuri
daga masu karatu da saurare cewa ba manufar muƙalar ce ba ta bi diddigin
tarihin Sa’idu Faru ko na waƙarsa, Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa. Manufarta
dai ita ce bayani a kan muhimman sigogin da waƙar ta ƙunsa da suka kai ta a
kan matakin ƙonƙoli, wato na ɗaya ga kyawo ta mizanin gargajiya. Wannan
mizanin waƙa na gargajiya shi ne wanda Sadaukin Shaihin Malami
(Professor Emeritus) Abdulƙadir Ɗangambo ya tsamo daga
bincikensa kan yadda Hausawa ke ƙimanta waƙa idan suka ji ta ko
suka karanta ta.[3]
Mai gabatar da wannan muƙala ya shaƙu da waƙar Sa’idu Faru tun cikin
shikarun 1976 lokacin da yake karantarwa a makarantar sakandare ta garin Anka.
To kuma tun a lokacin ne ya ci gaba da mu’amala da ita ta yanayi da dama. A
garin Anka mai muƙalar kan ja mota ya je bayan gari ya samu wani wuri cikin
daji, a lokacin babu ko samatar ‘yan bindiga masu satar mutane don neman fansa!
Zai nemi wuri ya fito da rakodarsa, ya sa kases na waƙoƙi da dama kamar na
Ibrahim Narambaɗa da na Alhaji Musa Ɗanƙwairo da na Dokta
Mamman Shata da kuma na Malamin waƙa mai kwana ɗumi, Sa’idu Faru. Da
zarar rakoda ta fara buɗe waƙoƙin shi kuma sai ya
shiga rawa shi kaɗai a wurin (a zatonsa).
Yayin da ya sha rawa, ya yi zufa, ya gaji, yakan dakata ya ɗauki rakoda ya nufi
motarsa don ya koma cikin gari. To amma ko da yake tayar da kansa sai ya hangi
Fulani tsaitsaye suna kallon sa! Ashe ba shi kaɗai yake ba! Akwai wasu masu shan daɗin waƙoƙin da suka sa shi yin
rawa har da jiɓi. Waɗannan Fulani sun dawo
daga kiyo ne suka tarar da shi, su ma suka tsaya su huta. Sau da yawa abota kan
ƙullu
sanadiyyar irin wannan saduwa da kuma jin waƙoƙin mallamin waƙa da sauransu!
Wani yanayi na shaƙuwa da waƙar ‘Kana shire Baban
‘yan ruwa’ da mai wannan muƙala ya yi shi ne dai na sauraren ta
yayin da yake cike da kewar gida. Wannan lokaci shi ne yayin da yake karantar
da harshen Hausa a birnin Sabha na ƙasar Libiya, a
shekarar 1997 zuwa 2002. A irin wannan yanayi na kewa da begen ganin gida ne wannan
marubuci ya ƙudurta ya rubuta muƙala a kan waƙar nan ta Sa’idu
Faru. Nan take ya tuntuɓi wani amininsa da yake
kira Babban Gogana. Na san tilas yana da waƙoƙin mawaƙan baka na Hausa bila
adadin a rubuce. Gogan nawa ba wani ba ne ban da Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau.
A lokacin yana zaune yana malanta a Jami’ar Bayero ta Kano, shi kuma mai muƙalar yana Libiya.
Yana iya juya waƙar kan takarda amma saboda ƙwiya sai ya nemi
Babban Gogansa da ya turo masa waƙar ta gidan waya!
Haka kuma ya yi har muƙala mai suna, “Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa, Na Bello Jikan Ɗanfodiyo: Waƙa A Kan Guri Da Hange Da Dahir” ta samu.[4]
Shi kuma Mai
Martaba Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo, wanda Sa’idu Faru ya yi wa wannan waƙa tun bai gaji mahaifinsa ba, sananne ne ga
marubucin wannan muƙala tun 1979 lokacin da mai martaba yake kwamishina na musamman a
gwamnatin tarayyayar Najeriya ta Alhaji Shehu Shagari. Lokacin ne marubucin ya
yi ido biu da mai martaba da ya zo assibiti dubin lafiyar mahaifin marubucin.
To amma sani na haƙiƙa shi ne lokacin da mai martaba yake shugaban kwamitin wata lacca da
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato ta gudanar.[5] Shi
kuwa marubucin yana shugaban kwamitin tsarawa na laccar. A wannan yanayi ne
marubucin ya shaƙu da mai martaba kuma duk a lokacin yana jiran sarautar Sarkin Musulmi. A
wannan kusanta ne marubucin ya koyi yadda ake fadanci! Duk lokacin da kwamitin
tsarawa ya ziyarci Shugaban Babban Kwamitin Taro yakan yi wa Ƙaramin Kwamitin tarba ta girma,
musamman da shugaban ƙaramin kwamitin yake Bagiɗaɗe, taubashi abokin wasar
Shugaban Babban Kwamitin Taro wanda shi kuwa daga Garka yake. To ana haka sai
wata rana ƙaramin kwamiti ya ziyarci Mai Martaba a gidansa. Bayan shugaban ƙaramin kwamitin, wato mai
wannan muƙala wanda a lokacin matsayin Dokta ne da bai zama Farfesa ba, akwai
Farfesa Abubakar Aliyu Gwandu. Farfesa A. A. Gwandu shi ne a gaba, ya durƙusa ya yi gaisuwa yana cewa, ‘Ranka
shi daɗe’. Mai Martaba ya amsa da
fara’a amma ya ce ‘Sannu Dokta’ cikin amsawar. Shi kuwa shugaban ƙaramin kwamiti da shi ne Dokta
a lokacin, shi ma ya yi gaisuwa da cewa ‘Allah Shi isar ma da isatai’. Mai
Martaba sai ya amsa da cewa, ‘Sannu Furofesa’! Tun a lokacin ne marubucin nan
ya naƙalci yadda ake yin fadanci gaban masu sarauta!
2.0 Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa
Waƙar ‘Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa’
waƙa ce wadda ta tsaru,
take ƙunshe
da jigon al’adu da
na romon kai da tsarin waƙa-kwaikwaye da salon tsattsafi da na zayyana. Waɗannan su ne suka sa wannan waƙa ta kasance a kan mataki na ɗaya, wato a ƙonƙoliya na mizanin yanke hukumcin ƙimar waƙa na gargajiyar Bahaushe. Cikinsu ne wannan muƙala take taka rawarta.
2.0.1 Jigon Romon Kai
Jigon romon kai yana nufin saƙo cikin waƙa (ko mu ce adabi gaba ɗaya)
wanda ya ƙunshi abin da mawaƙi ya ƙaddara samuwarsa ko yiwuwarsa
amma a tunanin mai saurare ba abu ba ne da ya faru ko zai iya ya faru a tunanin
ɗan Adam. A taƙaice ƙirƙiren zuciyar mawaƙi ne kurum.
Sa’idu Faru ya saka wannan jigo
cikin wannan waƙa domin, da farko dai
ubangidansa Sarkin Kudu Macciɗo ya ji daɗi ya
kuma ɗauka cewa haƙiƙa kome
mawaƙin ya faɗi haka
take, saboda ko ba kome ai mawaƙa a ƙasar Hausa suna cikin idanun al’umma. Haka kuma mawaƙin ya saka wannan jigo cikin waƙarsa domin masu sauraren sa su lura da girma da martabar
gwarzonsa, Sarkin Kudu. Dubi wannan misali:
Babban
daji kake ɗan Abu
Ko icce
ko namun dawa
Ko
manya ko ‘yan ƙanƙane
Da
mutum da dabba da itatuwa
Kowa ƙamnam Mamman yakai
Mamman
jikan Attafiru
Baba na
Sidi
Mamman
gwarzon Cika
(Sa’idu
Faru: Kana Shire Baban ‘Yan ruwa).
Haƙiƙa a cikin mutane akwai masoyan
Sarkin Kudu Macciɗo tun ma ba cikin Musulmi ba da yake ɗa ne na
‘Cika’, wato Abubakar III Sarkin Musulmin Daular Usmaniya. Balle daɗa ga
Sa’idu Faru!! Nan kam sai mu ce mawaƙin ya
faɗi gaskiya. To amma namun dawa da sauran dabbobi da ma
itatuwa fa?! Ba mu jin maganarsu kuma ba mu iya gane ko waɗannan
halittu suna ƙaunar mu. Watakila
hana-rantsuwa, idan shanu ne ko tumaki, amma fa sai waɗanda
gwarzon na mawaƙin ke kiyo suka saba da shi! To
zaki fa! Ko kuwa damisa wadda ake yi wa kirari da ƙi-sabo fa!! Su kuwa ‘itatuwa’ ko maganarsu ba za mu kawo
ba!!! Duk maganar Sa’idu cikin waɗannan layukan waƙarsa suna a matsayin romon kai, ba abin da ya auku ba ne, sai
dai mai saurare ba zai ce Sa’idu ya zuƙa tamalle
ba ne, zai ce waƙarsa ta tsaru ba tare da wani
dogon tunani ba.
Akwai wasu wurare cikin waƙar inda mawaƙin ya kawo wannan jigo, kamar
inda ya tarar da tsuntsayen daji, suda da burtu, da Larabawan Jiddah da
makamantan haka. To amma mu sa waɗannan a mala sai nan gaba kaɗan a ɓangaren
salo.
2.0.2 Jigon Al’adu
Sa’idu Faru ya yi amfani da
wannan jigo domin ya tabbatar da ya shimfiɗa waƙarsa a kan al’adun Hausa, kuma masu sauraren sa su amince da
cewa lalle waƙar fada ce sosai. A Hausance ba
a faɗawa cikin Fada ba tare da samun izini ba kuma ba cikin
suturar da ta dace da a zo a gaban sarki ba. Sa’idu Faru ya kiyaye da duk waɗannan
al’adu da ma ƙari ga haka cikin waƙarsa. Manazarta kamar Bello (1976) da Yahya (1995) sun yi
bayani cewa cikin waƙoƙin Fada
da mawaƙan baka kan yi wa basarake sukan
yi haka ne ta fuskoki aƙalla uku: yabo da zambo da
zuga.[6] Yahya
(1995) a nasa bincike ya jaddada cewa duk waɗannan jigogi akan same su cikin
waƙoƙin Hausa na baka da rubutattu, kuma
ma a dalilin haka ne ya kira sakamakon bincikensa da Ƙawancen Jigo… .
To a wata rerawar wannan waƙa mawaƙin ya buɗe ta da
wata al’ada da ake gudanarwa a kowace fada a ƙasar
Hausa inda ya ce:
Gardaye
zo ka yi min iso
Hwaɗa mashi
murna niz zaka
(Sa’idu Faru: Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa)
Duk wanda ya isa fada ko gidan
basarake tilas ne ya nemi yaron sarkin ko basaraken wanda a wasu wurare akan
kira shi sallama ko jekada da dai makamancin haka. Shi wannan yaron ko bafaden
ne zai fara zuwa ya sanar da sarki cewa ga wane kuma ga abin da yake tafe da shi,
gaisuwa ko isar da saƙo ko murna kamar yadda Sa;idu
Faru ya faɗa wa Gardaye da ke a gidan Sarkin Kudu. A kan haka waƙar za ta sa mai saurare ya ji mawaƙin bai yi hawan ƙawara ba
a al’adance a wannan zuwa da ya yi a gidan basarake kuma gwarzonsa.
An san mawaƙan fada da zambo, kamar yadda su Giɗaɗo Bello
suka nuna, domin su samu su cimma gurinsu na yaba da zuga basarake. Wannan kuwa
abin da Hausawa ke son ji ne, musamman ‘ya’yan sarauta, a irin wannan waƙa ta Sa’idu Faru.[7] A
dalilin haka ne mawaƙin ya yi wa wani bafaden
maigidansa zambo kamar haka:
Ina ƙamnak ka Muhammadu
Na
tabbataƙ ƙamna ta
kakai
Ko kai
niyyab ba mu dawakuna
Samnan
bahwade sara yakai
Ya ce
ko ka ba mu dawakuna
Ran da
Sallah ka tashi Ƙaura mukai
Ya ce
ko ka ba mu dawakuna
Ran da
Sallah ka tashi Ƙaura mukai
(Sa’idu Faru: Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa)
A ci gaba da wannan zambo domin
Sa’idu Faru ya tabbatar da ya samu shiga ga Sarkin Kudu sai ya kwaɓa
wannan zambo da yabo zuwa ga wasu na kusa ga ubangidansa. Ta haka yana sa ran
su waɗannan na kusa za su gyara mawaƙin
sosai ga ubangidan, kamar dai yadda wannan ɓangaren ɗan waƙa ke nuni:
Mamman
Haraka sai yaj jiya
Yac ce
kai ko ƙarya kakai
Ƙaura da Gusau da Kwatarkwashi
Ɗangulbi da Bunguɗu ham Maru
Duɗ ɗai na ga
Mamman Sarkin Kudu
Ɗan Dikko yana can yaj jiya
Wannan magana
ta tabbata
Da’
inda rana ka fita gabas
Har
inda rana taka faɗuwa
Duɗ ɗai na ga
jikan Ɗanhodiyo
Babu
inda mulkinai yat tsaya
(Sa’idu Faru: Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa)
A lura da cewa duk da shike mawaƙin bai faɗi ko wane bafade ne ba, a
kaikaice ya taka rawarsa ta mawaƙi a
matsayin idanun sarakuna. Cewar da ya yi /Samnan bahwade/ karantarwa ce yake yi
ga ubangidansa domin ya yi nazari ya gano shin a cikin fadawansa wane ne sauna
kuma makiri mai hana shi yin alheri.
Idan mai karatu ko saurare ya
tuna an ambata cewa sutura kamila ake zuwa da ita gaban sarki ko basarake.
Wannan al’ada ce cikin al’adun ƙasar Hausa. To mawaƙan fada suna cikin masu kiyaye wannan al’ada, idan dai ba
mawaƙan wannan zamani da muke ciki
ba. Dubi yadda Sa’idu Faru ya saka wannan al’ada cikin waƙar Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa:
Kowa ya
ji waƙas Sarkin Kudu
Ni ko
daɗinta da nij jiya
Can dauri
zaman daji mukai
Da kay
yi waƙas Sarkin Kudu
Mamman
yaɗ ɗaukan yar riƙa
Mun san
manyan mutane ƙwarai
Mun san
ƙananan mutane kuma
Mun
kammala dum mun ƙasura
Barwa
mu shidda muna gume
Sarkin
makaɗammu shina gaba
Duk
kowane tashi ƙawa daban
Yai taiɓa yai ƙaton ciki
Kowag
ga shi zamne ga innuwa
Ko da
makiɗin sarkin Masar
Yag ga
Sa’idu sai rainai yai haki
(Sa’idu Faru: Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa)
Sai bayan da Sa’idu Faru ya yi
wannan waƙa ta Sarkin Kudu sannan kowa ya
san da zamansa mawaƙi. Dalilin da haka ya auku shi
ne cewa Sarkin Kudu ya riƙi Sa’idu Faru riƙo irin wanda basarake yake yi wa mawaƙi, riƙon da kowa ya gane shi ya san
da cewa riƙon girma da ƙasaita Sarkin Kudu ya yi masa. Za a ga Sa’idu Faru cikin
sutura kamila, ƙosasshe ba busasshe mai rama
ba. Hasili ba makiɗin wani sarki a nan ƙasar
Hausa ba, ko makiɗin ‘sarkin Masar’ ya ga Sa’idu tilas ransa ya ɓaci, kila
har ya rena sarkinsa! Wannan ita ce al’adar ƙasar
Hausa, sarki ko basarake ya riƙi mawaƙinsa da kyawo yadda babu wanda zai yi masa kallon wulakanci
domin a gidan akwai yake sana’arsa. Mawaƙan sarauta
haka aka san su a ƙasar Hausa.[8]
2.0.3 Jigon Yabo ta Fuskar
Kakanni
Al’ada ce a ƙasar Hausa mawaƙi ya
yabi sarki ta fuskar danganta shi da kakanninsa musamman waɗanda
suka yi sarautar kafin shi ya hau. Mawaƙa na da
da yau duk suna riƙe da wannan al’ada. Hatta da
mawaƙan tauri sukan ari wannan
al’ada domin Kassu Zurmi ya kira gwarzonsa /Torankawan tciya uban Mairogo/. To
balle Sa’idu da ke gaban tsatson Torankawan da ya yi wa hangen zama Sarkin
Musulmi kuma hangen ya zama dahir domin Sarkin Kudu ya gaji Bubakar!! Sai dai
kash Sa’idu a lokacin bai duniya balle ya sami /gari da mutanenai duka!!!
A cikin ‘Kana Shire Baban ‘Yan
Ruwa’ Sa’idu Faru ya ce:
Kana
shire Baban ‘yan ruwa
Na
Bello jikan Ɗanhodiyo
(Sa’idu Faru: Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa)
Da nufi Sa’idu ya ba waƙar nan amshin da ya ambaci Bello da Ɗanhodiyo. Wato da Shehu ɗan Fodiyo da Sarkin Musulmi
Muhammadu Bello. Waɗannan su ne manyan kakannin gwarzonsa Sarkin Kudu. Masu
sauraren waƙarsa, Hausawa kuma Musulmi
asalin da suke ƙaunar kowane Bahaushe ya zan an
danganta shi da su. Bancin wannan kuma da gangan mawaƙin ya saka wannan amshi ya ƙunshi
sunayen waɗannan shugabanni. Ya yi haka ne domin su ne tushen sarautar
da yake fatar Sarkin Kudu ya kai gare ta, su ne kakannin Sarkin Kudu kai tsaye
babu wani ratse, Sarkin Kudu jika ne sat babu wata kwana na Sarkin Musulmi
Muhammadu Bello, daga gidansa ya fito ba daga gidan ƙani ko wa ba. Haka kuma jika ne kai tsaye na wanda ya kafa
wannan sarauta, wato Shehu Usmanu ɗan Fodiyo. Wannan shi ne
muhimmin gutsuren da ya shimfiɗa waƙar ga zamowa wadda “ta tsaru”. Da wannan ne Sa’idu ya cusa
al’adar yaba sarakuna ta fuskar kakanni cikin wannan waƙa tasa.
Mawaƙin ya jaddada wannan asuli da gwarzonsa yake da a wani ɗan waƙar inda ya ce:
Ka kai
kamab Bello sassakiya
Da kyauta
da mulki da ban gaskiya
(Sa’idu Faru: Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa)
A nan ya jaddada cewa gwarzonsa
Sarkin Kudu halattaccen jikan Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ne domin har ma da
kyawawan ɗabi’unsa akwai su gare shi, gwarzon. Ya ƙarfafa sunan da Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ya yi na yin
alheri /kyauta/ ga talakkawa, da iya shugabancin /mulki/ al’umma, da kwatanta
da tsaron gaskiya da amana /ban gaskiya/, duk Sarkin Kudu yana da su. A gaba kaɗan mawaƙin sai ya fito fili ya ayyana ‘dahir’ da cewa waɗannan ɗabi’u
ko halaye su ne ke ba da haske ga lalle sai gwarzonsa Sarkin Kudu ya hau gadon
sarautar nan ta kakansa Muhammadu Bello. Mawaƙin sai
ya kafa hujja da kawo al’adar Hausawa da ke cewa kowa gadon gidansu yake yi wai
ga jini take domin hatta shi makiɗi kome ya tara duniya ba su sa
ya ji ya kammala face ya ɗauki turun kiɗa ya yi kiɗi ya
rera waƙa. A taƙaice, wannan al’ada ce, ɗabi’a ce kuma a jininsa take;
Sarkin Kudu ma wannan al’ada tare da shi take, sai ya “yi”!, kuma ya yi!!
Sa’idu Faru ba ga kakanni kurum
ya tsaya ba domin ya sa waƙarsa ta amsu ga masu saurare.
Yakan ambaci har da shahararrun iyaye don ya cimma wannan manufa. Dubi wannan ɗan waƙar:
Gardaye
zo kai man iso
Faɗa mashi
murna niz zaka
Ɗan Sardauna jikan Hasan
Babban ɗa ga
Baura Sarkin Kudu
(Sa’idu
Faru: Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa)
A nan mawaƙin yana nufin Sardaunan Sakkwato Ahmadu Bello Firimiyan
Jihar Arewa. Uba ne ga Sarkin Kudu ba kaka ba. Hausawa da ma sauran mutanen
jihar Arewa suna matuƙar ƙauna da girmama Sardauna saboda shugabancin da ya yi musu.
Wannan shugabanci da ya yi ya haɗa da riƙa kowa, Hausawa da Fulani da duk wani ɗan wata
ƙabila, Musulmi da wanda ba Musulmi ba duk a matsayin nasa ne
suke; da tabbatar da zaman lafiya da kuma samar da abubuwan ci gaba a faɗin
Arewa da ya riƙa. Wannan cigaba kuwa babu mai
musun sa a gaban ‘yan Arewa har bisa yau, sai fa butulu ko wanda ya jahilci
tarihi.
Bari mu tsaya nan da sharhi
game da al’adar yabo ta fuskar kakanni domin kuwa Sa’idu ba waɗanda
muka kawo ba kurum suke cikin wannan waƙa.
Akwai Sarkin Musulmi Attahiru da Alu Maisaje da sauransu.
3.0 Tsarin Waƙa-kwaikwaye
Aliyah (2021) ta yi bayanin
wannan tsari da cewa:
Abin da ake nufi da
waƙa-kwaikwaye
a wannan maƙala shi ne, waƙar da aka tsara ta
yadda za a ji ko kalli aiwatarwarta tamkar ana sauraren ko kallon waɗanda ke magana tamkar
cikin wasan kwaikwayo ne ake gabatar da su. Maganar cikin waƙa-kwaikwaye kan
kasance ta wasu ce ba ta mawaƙin ba. Haka kuma waƙa ce wadda ita ce
gimshiƙin wasan kwaikwayon da ta ƙunsa kuma harshenta
da salonta duk na waƙa ne da ke taimakawa ga bayyana duk wani saƙo da mawaƙin yake son ya isar
ga jama’a. Wannan tsari da aka kira waƙa-kwaikwaye akan same
shi cikin waƙar baka da kuma rubutattar waƙa.
(Aliyah, 2021: ‘Waƙa-kwaikwaye: Daɗaɗɗen…’).
Ya kamata a lura da
cewa ba lalle waƙa guda sukutum ake nufi ba a nan, a’a har a cikin waƙar da aka saba gani
akan samu tsarin waƙa-kwaikwaye nan da can cikinta. Haka kuma maganar cikin
waƙa-kwaikwaye
takan zama tsakanin mawaƙi da wani ko wasu.
A wannan waƙa ta Kana Shire Baban
‘Yan Ruwa za a lura da inda Sa’idu Faru ya saka waƙa-kwaikwaye. Mai
karatu zai tuna wannan ɗan da aka kawo ƙarƙashin jigon al’adu:
Ina ƙamnak ka Muhammadu
Na
tabbataƙ ƙamna ta
kakai
Ko kai
niyyab ba mu dawakuna
Samnan
bahwade sara yakai
Ya ce
ko ka ba mu dawakuna
Ran da
Sallah ka tashi Ƙaura mukai
Ya ce
ko ka ba mu dawakuna
Ran da
Sallah ka tashi Ƙaura mukai
Mamman Haraka sai yaj jiya
Yac ce
kai ko ƙarya
kakai
Ƙaura da Gusau da Kwatarkwashi
Ɗangulbi da Bunguɗu
ham Maru
Duɗ ɗai
na ga Mamman Sarkin Kudu
Ɗan Dikko yana can yaj jiya
Wannan magana ta tabbata
Da’ inda rana ka fita gabas
Har inda rana taka faɗuwa
Duɗ ɗai
na ga jikan Ɗanhodiyo
Babu inda mulkinai yat tsaya
(Sa’idu
Faru: Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa)
Gicceyen rubutu shi ke nuna
maganar Mamman Haraka da ta Ɗan Dikko, yayin da wanda aka ja
wa layi ƙarƙashi yana nufin maganar ‘samnan bafade’ da mawaƙin ya ruwaito.
Ba za a kasa fahimtar
cewa mutum uku ne mawaƙin ya kawo maganganunsu ba. Akwai wani bafade wanda mawaƙin ne ya ruwaito
maganarsa, da Mamman Haraka da kuma Ɗan Dikko. Wannan
bafade da Sa’idu ya kira sauna (saboda makircin da mawaƙin ya ce bafaden ya ƙulla masa) shi ne ya
harzuƙa Mamman Haraka da Ɗan Dikko har suka
mayar masa da martini, suna ƙaryata makircin da ya yi don kada
Sarkin Kudu ya yi wa Sa’idu Faru alheri.
Wannan sa-in-sa
tsakanin saunan bafade makiri da kuma Mamman Haraka da Ɗan Dikko ita ce ta haifar
da waƙa-kwaikwaye cikin waƙar nan. Mai karatu ko
mai saurare zai iya nasarta cewa ga Mamman Haraka nan yana nunin saunan bafade
yana faɗa masa da murya mai ƙarfi cewa ƙarya ce yake yi, (cikin
salon zayyana) domin ba wai garin da bafaden ya ce Sa’idu Faru zai tafi da
zarar Sallah ta ƙarato ba, ya san da sani cewa da ma sauran garuruwa kamar
/Gusau
da Kwatarkwashi da Ɗangulbi da Bunguɗu ham
Maru/, duk abu guda ne ga Sarkin Kudu saboda dukansu ƙarƙashin mulkin mahaifin Sarkin
Kudu suke. Haka kuma mai sauraren zai gani a zuciyarsa cewa ga Ɗan Dikko nan shi ma makircin bafaden ya yi masa ciyo, amma
sai maganar Mamman Haraka ta sanyaya masa zuciya har ya ƙara da cewa ai ba nan kurum darajar Sarkin Kudu ta tsaya ba,
ai daga /inda rana ka fita gabas har inda rana taka faɗuwa duɗ ɗai na
ga jikan Ɗanhodiyo babu inda mulkinai yat
tsaya/!!! Mai karatu ko saurare zai ji dai kamar wasan kwaikwayo ne yake kallo
da idanun zuciyarsa.
Wannan tsari na waƙwa-kwaikwaye ya kasance ƙwarewar
Sa’idu Faru domin a kai a kai yana saka shi cikin wannan waƙa. Ya kawo shi yayin da ya bi gwarzonsa ta amfani da salon
tsattsafi na jigon romon kai har ya ci karo da tsuntsayen suda da burtu.
Tsakanin mawaƙin da tsuntsayen ne waƙa-kwaikwayen ya fito. Ga dai yadda ta kaya da shi da suda:
Sai nis
saki hanya niy Gabas
Can na
taɓa yat tafiya kaɗan
Sai ni’
ishe suda na kiyo
Tana ta
waƙas Sarkin Kudu
Rainai
ya daɗe Sarkin Kudu
Alisabbinane
ɗan Amadu
Allah
shi ƙara mai nasara
Nic ce suda waƙa akai
Tac ce lalle
waƙa nikai
Waƙam Muhamman Sarkin Kudu
Waƙan nan da Ɗan Umma yai mishi
Bancin
uwat tsuntsaye nike
Inda
kamam mulki na nikai
Da nai
mai wasiƙa yai man kiɗi
(Sa’idu
Faru: Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa)
Rubutu
mai layi ƙarƙashi shi ne maganar suda, shi kuma gicceyen rubutu, /suda waƙa akai/, shi ne maganar mawaƙin.
4.0 Salo
4.0.1 Tsattsafi
An bayyana ma’anar salon tsattsafi kamar haka:
Tsattsafi salo ne da ke nufin kawo wata ƙumshiyar tunani ko
cusa wata haliyya a wurare daban daban cikin waƙa ko kuma amfani da
wani salo a kai a kai (wato, a yayyafa ko a barbaɗa) cikin waƙa ko kuma mafi yawan
waƙoƙin marubuci idan gaba
ɗayansu ne ake nazari. Tsattsafi a waƙa haka yake kamar ƙyallin taurari cikin
sararin samaniya ko ɗiyan rana (ƙawalwalniya) cikin
yashi ko kuma ƙyallin kwalli wanda ya barbaɗe kan daɓe.
(Yahya cikin Ɗunɗaye Journal of Hausa Studies ɓol.1: 5{2013}, sh.83).
Cikin wannan muƙala za a lura da an gwama salon tsattsafi da sauran sassa da
ta yi magana a kai saboda duka ƙunshe suke da salon. Idan aka ɗauki
jigon romon kai ga misali, za a tuna cewa mawaƙin ya
kira Sarkin Kudu da sunan /Babban daji…/ (salon kinaya) saboda /da mutum da
dabba da itatuwa/ duk suna son shi. An bayyana cewa wannan romon kai ne saboda
bisa ga al’adar Bahaushe mutum ne kurum ke iya bayyana ƙauna. To mawaƙin ya
yi amfani da wannan jigo ya ƙirƙira salon tsattsafi da shi cikin waƙarsa. Mun ji cewa ya tarar da tsutsuwar nan suda tana rera
waƙar Sarkin Kudu har da mawaƙin ya
jinjina mata da yi mata tambaya wai waƙa ce
take yi, ita kuwa suda ta karɓa da cewa ai saboda jin daɗin
wannan waƙa kuma da ita ba uwar tsutsaye
take ba da ta aika masa da wasiƙar neman ya yi mata waƙa kamar yadda ya yi wa Sarkin Kudu. To daga wannan saduwa ce
Sa’idu Faru ya ƙara amfani da salon tsattsafi
na wannan jigo na romon kai har sau biyu. Ya ce ya tarar da tsuntsun nan da ake
kira burtu shi ma yana rera waƙar Sarkin Kudu. Nan ma mawaƙin ya jinjina wa burtu kamar yadda ya jinjina wa suda. Burtu
ya ce ai wannan waƙa da mawaƙin ya yi wa Sarkin Kudu shi a wurinsa, burtu, waƙar ta zame masa wuridi domin a duk sa’ilin da ya rera ta in
za shi wurin kiyo to lalle zai samu abinci mai tarin yawa wanda saboda yawansa
sai ya bar saura!
Sa’idu Faru ya ƙara amfani da salon tsattsafi inda yake cewa:
Can na
taɓa ‘yat tafiya kaɗan
Na kai
bakin Bahar Maliya
Sai ni’
ishe Larabawa wurin
Suna ta
waƙas Sarkin Kudu
Rainai
ya daɗe Sarkin Kudu
Alisabbinane
ɗan Amadu
Allah
shi ƙara mai nasara
Ɗan mai darajja Sarkin Kudu
Jikan
mai darajja ɗan Amadu
Sannan
Mai darajja Shi yay yi shi
Shina
gida zamne a Sokoto
In ya
yi salla yai tasbaha
Hasken
nashi han nan kallo mukai
(Sa’idu
Faru: Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa)
Romon kai ne cikin wannan ɗan waƙa ta amfani da salon tsattsafi, Romon kai shi ne cewar da mawaƙin ya yi ya tarar da Larabawa suna rera waƙar Sarkin Kudu, ‘Kana Shire…’, cikin harshen Hausa alhali su
ba Hausawa ba ne, sannan kuma ya ce sun faɗa masa wai idan Sarkin Kudu ya
yi salla can a garin Sakkwato, ya yi lazimi da tasbaharsa wani haske kan fito
har ya kai can /bakin Bahar Maliya/ wurin da Larabawan suke su yi ta kallo!
(karama ce Sa’idu Faru yake nuni a nan). Sa’idu Faru ya yi amfani da salon
tsattsafi aƙalla sau huɗu cikin
wannan waƙa kamar wada aka nuna.
4.0.2 Zayyana
Ma’anar wannan salo shi ne:
Salon zayyana yana
nufin amfani da kalmomi a cikin waƙa waɗanda tattare da
sauran maganar da suka fito cikinta za su ƙirƙiro siffar abu ko
yanayi a cikin zuciyar mai karatu ko sauraren waƙar.
(Yahya, 2016, sh.111)
Sa’idu Faru ya yi
amfani da wannan salo cikin waƙarsa. Misali a wurin da yake kawo
dalilin da ya sa ya ce ya ji daɗin sanya shi a jika da Sarkin Kudu ya yi har shi mawaƙin ya yi waƙar nan. A cikin ɗan waƙar Sa’idu ya zayyana
mana suturar da ya samu da shi da ‘yan amshinsa, kowa cikin ƙawa, ko ado, irin
wadda makaɗan basarake ya kamata
a gane su cikinta. Lokacin ne duk waɗanda suka gane su, musamman shi mawaƙin, sai mamaki ya
kama su. Wannan kammala, in ji Sa’idu, za ta ɓata ran ba wani makiɗin wani basarake na ƙasar Hausa ba, har ma
da na basaraken ƙasashen Larabawa kamar Masar! Zuciyar mai sauraren wannan
ɗan waƙar na iya hangen
Sa’idu da yaransa cikin taƙama da isa irin ta mawaƙa a gaban gwarzonsu, a
nan Sarkin Kudu!! Bari mu sake jin ɗan waƙar:
Ni ko
daɗinta da nij jiya
Can
dauri zaman daji mukai
Da kay
yi waƙas Sarkin Kudu
Mamman
yaɗ ɗaukan yar riƙa
Mun san
manyan mutane ƙwarai
Mun san
ƙananan mutane kuma
Mun
kammala dum mun ƙasura
Barwa
mu shidda muna gume
Sarkin
makaɗammu shina gaba
Duk
kowane tashi ƙawa daban
Yai taiɓa yai ƙaton ciki
Kowag
ga shi zamne ga innuwa
Ko da
makiɗin sarkin Masar
Yag ga
Sa’idu sai rainai yai haki
(Sa’idu Faru: Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa)
Haka kuma mun ga irin
faɗin gaba ɗin nan yayin da
Sa’idu ke faɗin a matsayinsu na
makaɗa, su ma kamar Sarkin
Kudu ɗan Sarki suke. Wada
ya gadi samun ɗaukaka da ƙasura, shahara da
cigaba, su ma haka nan suka gadi samun garuruwa a matsayinsu na makaɗan sarakunan kiɗan garuruwa; sun gadi
a ba su dawaki da jikkunan kuɗi, saboda haka idan Allah ya cika nufarsa ta ba Sarkin
Kudu sarautar Sarkin Musulmi to shi kuwa Sa’idu Faru a ba shi nasa gari ya riƙa! Wannan salon
zayyana ne da ke sa zuciyar mai saurare ganin mawaƙin ba mawaƙi ranke-ranke ba, sai
dai wanda ya cika ya batse yana jiran ganin Sarkin Kudu a kan sarautar Sarkin
Musulmi shi kuwa ya kai ga tasa sarautar.
Wani ɗan wannan waƙa mai salon zayyana ƙarara shi ne wannan:
Sai nis
saki hanya niy Gabas
Can na
taɓa yat tafiya kaɗan
Sai ni’
ishe suda na kiyo
Tana ta
waƙas Sarkin Kudu
Rainai
ya daɗe Sarkin Kudu
Alisabbinane
ɗan Amadu
Allah
shi ƙara mai nasara
Nic ce
suda waƙa akai
Tac ce
lalle waƙa nikai
Waƙam Muhamman Sarkin Kudu
Waƙan nan da Ɗan Umma yai mishi
Bancin
uwat tsuntsaye nike
Inda
kamam mulki na nikai
Da nai mai
wasiƙa yai man kiɗi
Dan nan
ni kau sai niw wuce
Can na
taɓa yat tafiya kaɗan
Sai ni’
ishe burtu na kiyo
Shina
ta waƙas Sarkin Kudu
Rainai
ya daɗe Sarkin Kudu
Alisabbinane
ɗan Amadu
Allah
shi ƙara mai nasara
Nic ce
burtu waƙa akai
Yac ce
lalle waƙa nikai
Waƙam Mahamman Sarkin Kudu
In na
yi ta za ni wurin kiyo
In niz
zo abinci sai na ije
Dan nan
ni ko sai niw wuce
Can na
taɓa ‘yat tafiya kaɗan
Na kai
bakin Bahar Maliya
Sai ni’
ishe Larabawa wurin
Suna ta
waƙas Sarkin Kudu
Rainai
ya daɗe Sarkin Kudu
Alisabbinane
ɗan Amadu
Allah
shi ƙara mai nasara
Ɗan mai darajja Sarkin Kudu
Jikan
mai darajja ɗan Amadu
Sannan
Mai darajja Shi yay yi shi
Shina
gida zamne a Sokoto
In ya
yi salla yai tasbaha
Hasken
nashi han nan kallo mukai
(Sa’idu
Faru: Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa)
A nan zuciyar mai saurare za ta
kalli mawaƙin nan yana tafiya mai sauri
amma girshi ya tarar da suda tana kiyo tana kuma rera waƙar nan ta Sarkin Kudu da shi mawaƙin ya yi; ga shi nan ya tambayi suda, ita ko ta tabbatar mai
cewa lalle waƙa take rerawa kuma ba wata waƙa ba ce illa wadda shi mawaƙin ya
yi wa Sarkin Kudu, har ma ta ƙara da cizon farce tana cewa da
ba uwa ce ga tsuntsaye ba da tuni ta aika wa shi mawaƙin da umurnin ita ma ya yi mata tata waƙa, da a ce ita ma sarauta take yi tunda shi Sa’idu mawaƙin fada ne; mawaƙin ya
ci gaba da sauri da yake yi sai kuma ya cimma burtu shi ma yana rera waƙar; da mawaƙin ya yi masa irin waccan
tambaya sai burtu ya amsa kamar suda amma ya ƙarasa
da cewa waƙar ta zamar masa wuridinsa idan
zai tafi kiyo don idan ya tafi ba ya ƙaranci
balle rashin abinci!; haka nan kuma zuciyar mai saurare za ta kalli mawaƙin ya ci gaba da saurin da yake yi har ya kai gaɓar
tekun Maliya inda ya tarar da Larabawa su ma suna waƙar nan da mawaƙin ya
yi wa Sarkin Kudu; zuciyar za ta kalle su suna faɗin cewa duk da cewa Sarkin Kudu
a Sakkwato yake kuma cikin gidansa, ya gama salla yana jan tasbaha sai ga hasken
waliyyantakarsa (karama) ta kai can wurin da Larabawan suke (ga alamu birnin
Jiddah), duk fa zuciyar mai saurare ke gano haka.
5.0
Kammalawa
Yadda Sa’idu Faru ya gwama
sassan jigo da na al’adu da tsari da kuma salo cikin waƙarsa, yana mai saka ire-irensu a tare, gwaninta ce da ba
kowane mawaƙi ke iya bajewa ya tayar da waƙa cikin nasara ba. To amma mawaƙinmu ya yi haka nan har kuma waƙar ta karɓu ga jama’a. Tasirinta a kan
wannan marubuci tun yana matashi har manyancinsa lokacin da gurin mawaƙin ya cika bayan rayuwarsa, da kuma yadda mutane sukan yi
saurin kawo ɗiyanta da zarar suka ji an ambaci Sa’idu Faru da Sarkin Kudu.
Zauren Makaɗa Sa’idu Faru da Waƙoƙinsa sheda ne ganin yadda aka sha ambatar wannan waƙa. Duk waɗannan tabbaci ne cewa waɗannan
sassa da muƙalar nan ta tattauna muhimman
sassa ne da suka aza waƙar a mataki na ɗaya na mizanin
ƙimanta waƙa a gargajiyar Hausawa. Sun tabbatar
da ita can ƙoli da laƙabin ta tsaru, ta burge ta ƙayatar
ta kuma shere kowa, kamar wada Sadaukin Shaihin Malami Abdulƙadir Ɗangambo ya tsamo mana!
Ta ɓangaren
‘Cikin Ƙira Aka Ɗaɗi’ kuwa muƙalar ta yi kira ne ga masana da
shugabanni da su yi hattara da na’urorin zamani da al’ummomin yammacin duniya
dangane da taskace tarihinmu. Maso abinka ya fi ka wayo. Kada mu sake da wai
muna son su san adabinmu da al’adunmu saboda haka bari mu tallata su cikin
harsunansu. Su ba haka suka yi ba. Ƙarin
gashi ƙuna, takan ɗauro su
ma fi mu ko su kusan daidaita da wasu masananmu ga karanta da fahimtar
littaffanmu domin suna iya kashe maƙudan kuɗi ga
koyon littaffanmu. Haka kuma muƙalar tana ganin muna yin riƙon sakainar kashi ga wasu gidajen adana kayan tarihi a ƙasar nan tamu. Akwai bukatar ƙarfafa
musu tsaro. Kamar wada ake zargin cewa ana amfani da ‘yan gida wurin taɓarɓarewar
tsaro a Arewa haka nan muƙalar ke hange ga kayan
tarihinmu musamman waɗanda suka danganci Addini. Allah ya kiyaye, amin Ya Arhamar
rahimina.
Manazarta
1. Aliyah,
A. A. (2017), Rupert Moultrie East
1898-1975: Tarihinsa da Sharhi a kan Gudummawarsa ga Adabin Hausa, Kaduna: Whales
Adɓerts Limited.
2. Aliyah,
A. A. da Yahya, A. B. (2020), Kukan
Kurciya cikin Waƙoƙin Korona Biyu,
Zaria: ABUPRESS.
3. Aliyah,
A. A. (2021), “Waƙa-kwaikwaye: Daɗaɗɗen Adabin Hausawa na Auren Waƙa da Wasan kwaikwayo”,
cikin kundin Karramawa ga Farfesa Sa’idu Muhammada Gusau na Bayero University, Kano
wanda ke kan hanyar fitowa.
4. Ɗangambo, A. (2007), Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa
(sabon tsari), Zaria:
Amana Publishers Ltd.
5. Gusau,
S. M, (1996), Makaɗa da Mawaƙan
Hausa 1. Kaduna:
Kamfanin Fisbas Media Services.
6. Gusau,
S. M, (2003), Jagoran Nazarin Waƙar Baka, Kano: Benchmark
Publishers Limited.
7. Gusau,
S. M, (2009, 2018, 2019), DIWANI WAƘOƘIN BAKA
1, 3, 4. Kano:
Century Research and Publishing limited.
8. Gusau,
S. M, (2015), Waƙar Baka
Bahaushiya No 14,
Kano: Bayero University.
9. Haɗeja, M. (1980), Waƙoƙin
Mu’azu Ha]eja, Zariya:
Northern Nigerian Publishing Company (NNPC).
10. Kano,
B. U. (1995), HARSUNAN NIJERIYA vol. xvii,
Kano: Centre for the Study of Nigetian Languages.
11. Magaji,
A. (2016), Kassu Zurmi da Waƙoƙinsa. Zaria: Spectrum Books
Limited.
12. Muhammad,
Ɗ.
(1978), Waƙa Bahaushiya”, cikin Studies
in Hausa Languages, Literature and Culture I, Kano: Bayero University.
13. Sokoto,
U. Ɗ.
U. (2002), Ɗegel: Journal of Faculty of Arts And Islamic Studies Volume vi
14. Yahya,
A.B (1997), Jigon Nazarin Waƙa, Kaduna: Fisbas
Media Services.
15. Yahya,
A.B (2002), ‘Siffantawa Bazar Mawaƙa: Wani Shaƙo Cikin Nazarin Waƙa’, cikin Studies in Hausa Language, Literature and Culture 5: 220-240, (ed.) Bichi A.Y., Kafin Hausa, A.U. and Yalwa, L.D., Kano: Jami’ar
Bayero.
16. Yahya,
A.B, (2004), “Tsattsafin Raha Cikin Waƙoƙin Alƙali Alhaji Haliru
Wurno”, maƙalar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani a
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
17.
Yahya, A. B. (2013), ‘Tsattsafi: Wani Ɗigo cikin Gulbin
Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa’ cikin ƊUNƊAYE: Journal
of Hausa Studies vol.1: 5, Sokoto: Usmanu Ɗanfodiyo University.
18. Yahya,
A. B. (2016), Salo Asirin Waƙa
(sabon bugu), Sokoto:
Guaranty Printers.
[1] Sa’idu Faru: /Farin cikin Musulmin
duniya/Mai martaba na Abubakar/Ci fansa Alhaji Macciɗo/.
[2] Sa’idu Muhammad Gusau, fitacce kuma
Babban Goga, masanin waƙar
baka ya tabbatar da kasancewar Sa’idu Faru a matsayin mawaƙin sarauta na Hausa cikin ayyukansa
kamar, Makaɗa
Da Mawaƙan Hausa (1996, sh. 117-
126), da Diwanin Waƙoƙin Baka 1 (2009, sh. 144 -164) da Diwanin
Waƙoƙin Baka 5 (2020, sh. 79-85).
[3] Ɗangambo,
A, (2007) Ɗaurayar Gadon Feɗe
Waƙa (sabon tsari). Zaria: amana publishers ltd., sh. 7-9.
[4] Cikin ƊEGEL: JOURNAL OF
FACULTY OF ARTS AND ISLAMIC STUDIES USAMNU ƊANFODIYO UNIVERSITY, SOKOTO, Volume vi, 2002, sh. 226 - 275.
[5] Laccoci ne da aka gudanar ƙarƙashin Taro na Ƙasa
da Ƙasa cikin shekarar 1995.Taken taron
shi ne, Islam and Political Challenges of Modern Times. Sashen Koyar da Ilmin
Addinin Musulunci na Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo
ya shirya taron, Farfesa Jibril Aminu ne Babban Mai Jawabi a wannan taron. Wani
zai yi mamakin kiran likitan magani don ya kasance Babban Mai Jawabi a irin
wannan haɗuwa. To haƙiƙa
zaɓen Farfesa Jibrin Aminu ya dace ainun.
A ranar ce mai wannan muƙala
ya ji hafizin Al’Ƙur’ani, ba
likitan magani ba, yana lacca a matsayin Babban Mai Jawabi na laccocin Islam
and Political Challenges of Modern Times!!! Allah Ya saka masa da mafificin
alheri duniya da Lahira, amin.
[6] Duba Abdullahi Bayero Yahya (1995) ‘Ƙawancen Jigo Tsakanin Waƙoƙin
Sarauta na Baka da Rubutattu’ cikin HARSUNAN
NIJERIYA vol. xvii,
Kano: Centre for the
Study of Nigetian Languages, Bayero Uniɓersity, sh. 34-56. A wannan muƙala Yahya ya faɗaɗa fuskokin jigogin uku da Giɗaɗo Bello ya ambata.
[7] A lura da cewa zambo cikin waƙar fada tasirinsa mai halshen damo
yake da; abokan hamayyar gwarzon da mawaƙi
ke yi wa waƙar za su ji
zafin zambon; shi kuma gwarzon zai ji daɗi tamkar yabo ne aka yi masa.
[8] Wata rana wasu abokaina sun halarci
wani ɗaurin amre sai ɗayansu ya ga wani mutum cikin sutura mai kyawo kamila, sai
wannan abokin ya jimƙe hannu ya durƙusa ya yi gaisuwa yana cewa, “Ranka
shi daɗe”. Daga baya sai sauran abokansa suka
ja shi a gefe suna dariya, suka ce masa “Yau ka yi gaisuwar fada ga makiɗi wane!”
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.