Citation: Umar, M.A. & Kaura, H.S. (2024). Nazarin Turakun Waƙoƙin Masarautar Ƙauran Namoda na Makaɗa Sa'idu Faru. Four Decades of Hausa Royal Songs: Proceedings from the International Conference on the Life and Songs of Makaɗa Sa'idu Faru, 3(3), 62-69. www.doi.org/10.36349/tjllc.2024.v03i03.008.
NAZARIN TURAKUN WAƘOƘIN
MASARAUTAR ƘAURAN NAMODA NA MAKAƊA SA'IDU FARU
Daga
Muhammad Arabi UMAR
Sashen
Harsuna da Al’adu,
Jami’ar
Tarayya Gusau, Jahar Zamfara, Nijeriya
Imel:
arabiumar@fugusau.edu.ng, arabizulaiha@gmail.com
Da
Halidu
Sanda Ƙaura
Sansanin
Ƙaura Namoda
Mai kula da Tarihin Masarautar Ƙauran Namoda, Jihar Zamfara, Nijeriya
08080857718
Tsakure
Wannan
takarda an tsara ta ne da manufar fito da turakun da ke cikin waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru na
masarautar Ƙauran Namoda da ke Jihar Zamfara,
Nijeriya. An yi wannan tunani ne saboda a ƙara fayyace gurbin da masarautar take da shi a daular
Usmaniya, tare da matsayin masarautar a bakin Makaɗa Sa’idu Faru.
Haka kuma, wannan ya ƙara tabbatar da
basirar makaɗa Sa’idu Faru a ɓangaren makaɗan fada, musamman
yadda waƙoƙinsa suke cike da turaku daban-daban. Domin nazarin ya
cimma nasara, an yi amfani da hanyoyin bincike na sauraren waƙoƙin mawaƙin tare da nazartar ayyukan da aka gudanar rubutattu masu
alaƙa da batun da ake nazari a kai. Kauce
wa kwasar karan mahaukaciya ya sanya aka yi wa takardar kadada, inda aka taƙaita binciken ga waƙoƙin makaɗin guda biyu.
Wato, waƙar Sarkin Ƙauran Namoda Abubakar Garba wanda ya yi mulki daga shekarar
1952-1960 da kuma ta Uban ƙasar Banga Sarkin
yaƙi Sale Abubakar wanda ya yi mulki daga
shekarar 1934-1963. Binciken ya yi amfani da Ra’in Waƙar Baka Bahaushiya
(WBB) wanda Gusau,
(1993, 2003, 2008, 2011, 2014, 2015) ya assasa. Takardar ta yi ƙoƙarin fito da
turaku bakwai a cikin waɗannan waƙoƙi guda biyu.
Turakun da aka iya fitowa da su, su ne: Turken addini da yabo da koɗa kai da jarunta
da kyauta da zuga da kuma roƙo. An kammala
nazarin da bayyana sakamakon bincike waɗanda suka haɗa da, Masarautar
Ƙauran Namoda tana cikin manyan
masarautu da tarihin daular Usmaniya ba zai kammala ba idan ba a ji motsin ta
ba. Turakun da ke cikin waƙoƙin Masarautar Ƙauran Namoda sun ƙara tabbatar da martaba da kuma buwayar masarautar a idon
duniya. Haka kuma, Waƙoƙin Masarautar Ƙauran Namoda na Sa’idu Faru tamkar wata taska ce da ta
adana tarihi da iyakokin masarautar da kuma matsayin masarautar a daular
Zamfara da ma ta Usmaniya gaba ɗaya.
1.0 Gabatarwa
Makaɗan baka dai tamkar wasu taskoki ne na adana tarihi da
fasahohin al’umma. Don haka a kowane lokaci waƙoƙinsu cike suke da ilmomi mabambanta. Wannan dalili ya sa
waƙoƙin baka na Hausa suka zama tamkar kirarin da Hausawa suke
wa saniya, inda sukan ce: “Nagge daɗi goma” saboda tarin abubuwan da suka ƙunsa. A kowane lokaci mawaƙi ya furta wata waƙa ko waƙoƙi, manazarta fannonin ilimi sukan amfana da su a fannonin
da suka ƙware. Misali, a fannin waƙoƙin baka kaɗai masu mamaren harshe sukan amfana da
kalmomin harshe na asali tare da sanin yadda Hausawa suke amfani da su ta
hanyar furtawa da tasrifi (ƙirar kalma) da kuma ginin jumla. Haka
yake ga masu neman sanin wani abu na al’ada da tarihi da sauran abubuwan da
suka shafi shugabanci da kuma zamanatakewa baki ɗaya. Sukan yi amfani da waƙoƙin baka saboda su naƙalci al’adar Hausawa ta asali. Ɓangaren adabi kuwa, su ne masu baje
kolin wurin da tunanin mawaƙi ya dosa inda sukan fayyace fasahohin
da ya yi amfani da su wajen isar da saƙonninsa. Fasahohi irin na karin magana da kirari da yabo
da zuga da zambo da habaici da sauransu da dama duka a nan akan naƙalce su. Domin haka, waƙoƙin baka suka zama tushen fannonin ilimin harshe da adabi
da kuma al’ada.
Buƙatar wannan takarda ce ta yi nazarin
wasu turakun waƙoƙin masarautar Ƙauran Namoda waɗanda Makaɗa Sa’idu Faru ya rera. An yi wannan tunani ne saboda
muhimmancin da Masarautar Ƙauran Namoda take da shi a Daular
Zamfara da ma Daular Usmaniya gaba ɗaya. Shaharar da Ƙauran Namoda ta yi a cikin Daular
Zamfara ta yi amo sosai a cikin waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru. Don haka wannan takarda
take ganin ya kamata ta jefi tsuntsu biyu da dutsi (hoge) ɗaya. Wato, a fito da Masarautar Ƙauran Namoda a bakin shahararren makaɗin ƙasar Hausa, Sa’idu Faru, sannan kuma a
fayyace hikimar da ya yi amfani da ita wajen tsara turakun waƙoƙin ƙarƙashin tsarin masana adabin Hausa.
1.1 Farfajiyar Bincike
Kasancewar wannan takarda an shirya ta ne da nufin amsa
goron gayyatar taron ƙara wa juna sani a kan Makaɗa Sa’idu Faru, binciken da aka gudanar a cikinta taƙaitacce ne. Duk da haka, sha’anin masarautar
Ƙauran Namoda a Daular Zamafa da kuma na
Makaɗa Sa’idu Faru abubuwa ne guda biyu da
suke da faɗi ƙwarai. Hakan ya sa marubucin ya yi ta raggo da aka ce ya
sha hura ya tafi gona, sai ya ce, “a dai faɗa masa wanda zai yi daga ciki.” Don haka, an tsara takardar
a fannin adabi, takardar ta taƙaita ga waƙoƙin Sa’idu Faru na fadar Ƙauran Namoda guda biyu. Wato, ta Sarkin
Ƙauran Namoda Abubakar Garba wanda ya yi
mulki a shekarun 1952-1960 da kuma ta Uban ƙasar Banga Sarkin yaƙi Sale Abubakar wanda ya yi mulki a
shekarun 1934-1963. Baya ga haka kuma, takardar ta mayar da hankali a kan fito
da waɗannan turaku: Addini da yabo da koɗa kai da jarunta da kyauta da zuga da kuma roƙo. An yi haka ne saboda kada a yi wa
abin kwasar karan mahaukaciya. Waƙoƙin makaɗa Sa’idu Faru cike suke da bayanin isa
da ƙasaitar sarakunan masarautar Ƙauran Namoda. Wanda duk bai san tarihin
wannan masarauta ba, zai ga an wuce makaɗi da rawa wajen kambamawar da Sa’idu
Faru ya yi wa masarautar. Haƙiƙa turakun waƙoƙin da Sa’idu Faru ya yi wa
masarautar Ƙaurann Namoda cike suke da zuga da kuma
tada maza daga kwana.
1.2 Hanyoyin Gudanar da Bincike
A bisa amana ta ilimi, akan bayyana yadda aka same shi
domin gudun abin da Hausawa suke cewa: “jita-jita, hadisin Bamaguje” Sakamakon
haka, wannan takarda ta yi ƙoƙarin bin hanyoyin tattara bayanai daban-daban. Binciken
ya fara da sauraron waƙoƙin Sa’idu Faru waɗanda aka adana su a na’urar memori ta
hanyar waya. Bayan da aka ji waƙoƙin daga bakin wanda ya rera su, sai aka nemi rubutattun
waƙoƙin da Gusau, (2009) ya tattara ya kira su da Diwanin Waƙoƙin Baka na Hausa. Hakan shi ya bayar da damar naƙaltar ɗiyan waƙoƙin da aka buga mislai da su. Abu na gaba da aka yi amfani
da shi a matsayin hanyar bincike shi ne, nazartar ayyukan da aka gabatar na
kundayen digiri a matakan ilimi daban-daban da mujallu da maƙalu da kuma litattafai waɗanda suke da alaƙa da batun da ake magana. Har wayau, an yi amfani da
kafar sadarwa ta WhastApp group inda aka samu ƙarin bayani a kan wasu waƙoƙin da makaɗin ya gudanar daga bakin masana
daban-daban na kusa da na nesa. Takardar ba ta kawar da kai ga tuntuɓar wasu masana adabi da al’ada da tarihi ba, inda ta
tuntuɓe su ta kuma samu bayanan da take nema.
1.3 Ra’in Bincike
A
tunanin Bunza, (2022:7) ra’i shi ne: “Wani tunani na wani ko wasu da ya yi
canjaras da wata maɓuɓɓuga ta ilmi da aka jarraba aka ci nasara cib-da-cib, ko
aka ci rabi ko wani abu daga cikin rabin. Ke nan, babbar
manufar ra’i ita ce hanyar
ɗora aiki. Hanyar ɗora aiki takan kasance ɗaya ko fiye matuƙar sun yi kunnen doki da ƙunshiyar aiki, sadaka ta gamu da amin.” Ke
nan wannan bayani ya nuna cewa, ra’i wata hanya ce da magabata suka samar da
ita domin yin jagora ga ayyukan bincike na ilimi. Sakamakon haka, wannan bincike an ɗora shi a kan mazahabar awon baka wadda
Gusau ya samar, wadda ake kira da hanyar nazarin waƙar baka Bahaushiya (WBB). Wannan mazahaba
ta faro ne tun daga 1993 amma ta samu faɗaɗa inda aka ci gaba da amfani da ita a
shekarun 2003 da 2008 da 2011 da 2014 da kuma 2015. An gina wannan mazahaba ne
a kan waɗannan tubalai kamar haka:
a.
Salsalar waƙa
b.
Yanayin aiwatar da waƙa
c.
Yanayin ƙulla waƙa
d.
Raujin waƙa
e.
Turke da warwararsa
f.
Awon baka
g.
Tsarin sadarwa
h.
Adon harshe
i.
Aiwatar da harshe
Kasancewar wannan takarda taƙaitaccen bincike ne, saboda haka aka fi
mayar da hankali a kan fito da turken masarautar Ƙauran Namoda a waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru. Sakamakon haka, an kawar
da kai wajen fito da wasu abubuwa da wannan ra’i ya ƙunsa.
2.0 Waiwayen Tarihin Masarautar Ƙauran Namoda
Masarautar Ƙauran
Namoda tana da matsayi na musamman a Daular Usmaniya. Matsayinta ya kai ga
cewa, tarihin jihadin Shehu Ɗanfodiyo ba ya kammala idan ba a ji
amonta a ciki ba. An kafa garin Ƙaura
Namoda a 1807 sanadiyar jihadin Shehu Usman Danfodiyo. Malam Namoda da ƙanensa
Mamuda sun yi fice ƙwarai da
gaske a cikin Jihadin Shehu. Sun amsa kiransa tun kafin fara jihadin Shehu kamar yadda Mai
Kware Autan Shehu ya ambata cikin waƙarsa inda yake cewa:
Yat tashi nan daɗa yai zaman Sabon Gari
Jama’ar Musulmi sun ka ƙaru da
so nasa
Nan anka samu Namoda yaz
zaka shi kuwa
Ya tanyi Shehu haƙiƙa don
bege nasa.
(Isa
Maikware: Waƙar Gewayen Shehu).
Namoda ya ba da gagarumar
gudummawa wajen Jihadin wanda hakan ya sa tarihin Daular Usmaniya ba ya
kammaluwa ba tare da an ambaci sunan Muhammadu Namoda ba. Misali sanadiyar
nasarar Namoda a yaƙin
Fafara 1806, Shehu ya karrama shi da kalmar Al-ahul muzaffar (Ɗan’uwa mai
nasara) bayan wannan ya rataya masa takobi mai suna Fate-fate ya kuma naɗa shi Sarkin Yaƙi, Malam
Abdullahi Fodiyo. Ya yabi Namoda inda ya ce, “Fani’imal jam’u, jam’u Namoda
yaumal taƙal jam’ani fi arja’i Zurmi.” (Madalla da wannan haɗuwa da Namoda, ranar da jama'a biyu suka haɗu a farfajiyar Zurmi).
Sarkin Musulmi Bello ya ci
Alƙalawa a Oktoba
1808 (Sha’aban 1223) Zaratan zaruman da suka taimaka masa su ne:
a.
Aliyu Joɗi jagoran rundunar Gabas
b.
Ummaru
Dallaje Jagoran rundunar Yamma
c.
Muhammadu
Namoda jagoran rundunar Arewa
d.
Sarkin
Musulmi Bello Jagoran ɓangaren
Kudu
Shehu Usman ya umurci
Namoda ya je magangamar Gulbin Gagare da ƙoramar Gabake ya kafa
garinsa. Shehu da kansa ya raɗa wa
wannan wuri suna “Ƙaurar
Namoda” Bayan kafuwar garin Ƙaurar
Namoda, Muhammadu Namoda ya yi shahada a Buhut lokacin da dakarun Sarkin Kiyawa
suka kashe shi bayan ya dawo daga Yaƙin Tawayen Abdussalam. Da
mayaƙan
Kiyawa suka kai wa sarkin Kiyawa Dagazau kan Namoda da suka sare, maimakon
murna sai ya razana ya fashe da kuka ya ce masu “wannan ai kaina ne kuka sare”.
Mamuda ƙanen
Namoda ya ɗau fansa
ya sare kan Sarkin Kiyawa Dagazau Na Ma’inna. Sanadiyar haka Shehu ya karrama
Mamuda da sarautar Sarkin Kiyawa. Wannan shi ne dalilin da ya sa ake kiran
sarkin Ƙauran
Namoda da sunan Sarkin Kiyawan Ƙaura Namoda.
Ƙauran
Namoda na da matsayi na musamman a daular Usmaniyya. Sarkin yaƙin
Namoda ya auri Hannatu ɗiyar
Shehu, kuma ya aurar da ɗiyarsa
Nana ga Buhari ɗan Shehu
kuma jikanyarsa ita ce kakar waziran Sakkwato. Kauran Namoda ta zama wurin
zaman ribaɗi da
sarkin Musulmi ke yi da sarakunan sarkin Musulmi na goma Umar Aliyu (1881
-1891) ya rasu a Ƙauran
Namoda, an kuma naɗa sabon
sarkin Musulmi na II Abdulrahman Ɗan Atiku
a Ƙauran
Namoda ƙarƙashin
jagorancin waziri Buhari. Kabarin Sarkin Musulmi Umar yana nan a fadar Ƙauran
Namoda. Lokacin mulkin Umarun Mamuda,(1870-1903) masarautat Ƙauran
Namoda ta ƙunshi
Zurmi, Ƙauran
Namoda, Moriki da Kwatarkwashi. Har ila yau, bayan ƙirƙiro
jihar Zamfara lokacin sarkin Kiyawa Alhaji Ahmadu Asha (1997-2001) ta ƙunshi ƙananan
hukumomin Birnin Magaji, Shinkafi, Ƙauran Namoda da Zurmi.
Turawan Mulkin Mallaka, sun gina godaben jirgin ƙasa zuwa
Ƙauran
Namoda a 1929. Sanadiyar wannan, garin ya zama cibiyar kasuwanci bayan haka Ƙauran
Namoda ta zama cibiyar ilimi. Ana yi ma Ƙauran Namoda kirari da: “Ƙaura ta
Namoda mai kamar yau salla...” Tun lokacin ribaɗi 1870 har zuwa 1960 ana
kai da kawo a Ƙauran
Namoda a 1903 sarkin Kano Aliyu Majehim Mashi ya yi mubayi’a ga
sarkin Musulmi Abdulrahman da doki 1000.
2.1 Taƙaitaccen Tarihin Makaɗa Sa’idu Faru
Alhaji Sa’idu Faru ɗaya ne daga cikin makaɗan sarakuna da suka yi fice
a ƙasar
Hausa. Ya gaji kiɗi da waƙa ba
haye ya yi ba. Wato, ya gaji kiɗi da waƙa wajen
uwaye da kakanni. Ya fito daga yankin Fadamar Gulaben Sakkwato, Rima da Gagare.
Sa’idu Faru cikakken makaɗin
sarauta ne. Mafi yawan waƙoƙinsa na sarauta
ne. An haife shi garin Faru, da take ƙaƙarshin Masarautar Maradun ta jihar Zamfara ta yanzu a
daidai shekarar 1916. Ana yi masa laƙabi da Ɗan’umma. Sunan mahaifinsa Abubakar Maikotso, wanda ake yi masa laƙabi da Abubakar Kusu.
Abubakar Kusu ɗa ne a wajen Alu Maikurya ne. Wannan magana ta
tabbatar da bayanin da aka bayyana cewa, Sa’idu Faru ya gaji kiɗa ne daga wajen
uwayensa. Makaɗa Sa’idu Faru ya shahara a tsakanin makaɗan zamaninsa musamman waɗanda suke kiɗan fada. Ubangidansa da
yake wa kiɗa da waƙa shi ne Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo. Duk da yake wata ƙudura ta Allah ba ta nufi Sa’idu Faru riskar lokacin da ubangidansa (Mai’alfarma
Muhammadu Macciɗo) ya zama Sarkin Musulmi ba. Don haka lokacin da ake bukin murnanr naɗa shi Sarkin Musulmi,
duk waɗanda suka san shi da Mai’alfarma Muhammadu Macciɗo sukan sake yin juyayin
rashin Sa’idu Faru a wannan rana, musamman saboda gudunmawar da zai bayar ta waƙa. Sa’idu Faru ya rasu a shekarar
1987 a garinsu Faru, bayan ya yi fama da wata taƙaitacciyar jiyya.
3.0 Turakun
Waƙoƙin masarautar Ƙauran Namoda na Sa’idu Faru
Gusau, (2008:370) ya bayyana
cewa: “Turke a ƙa’idar masu nazarin waƙar baka na nufin saƙon da waƙa take ɗauke da shi. Idan an ce saƙo kuma ana magana ne kan manufar da ta
ratsa waƙa tun daga farkonta har zuwa ƙarshenta, ba tare da karkacewa daga
ainihin abin da ake zance a kansa ba.” Wannan ma’ana ta haska wa wannan bincike
cewa, turke yana nufin babban saƙon da mawaƙin baka yake so ya isar a cikin waƙarsa. Ke nan idan an ce turke, ana
magana a kan saƙo guda ɗaya. Jam’in turke sai ya zama turaku, wato saƙonni ke nan. A ɗan kazar-kazar ɗin da wannan takarda ta yi a fagen nazarin
turakun waƙoƙin Sa’idu Faru na fadar masarautar Ƙauran Namoda, ta iya hango waɗannan turaku:
3.1 Turken Addini
Addini a wannan muhalli ana
nufin addinin Musulunci wanda Allah Maɗaukakin Sarki ya aiko Annabi Muhammadu
Tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya isar da shi ga al’umma.
Kasancewar fadojin da mawaƙanmu na baka suke wa waƙa da su kansu mawaƙan suna kan tafarkin wannan addini na
Mususlunci akan ji amonsa a cikin ɗiyan waƙoƙinsu. Don haka Gusau, (2008:289) yake ganin wannan dama
ce da waƙoƙin baka suka samu, suke amfani da ita wajen ambaton wasu
ayyukan ibada don ƙaruwar jama’a. Sa’idu Faru ya fito da
wannan turke a waƙar da ya yi wa Sarkin Ƙauran Namoda inda yake cewa:
Jagora /Y/Amshi: Namoda ya mutu dud nan ƙasag ga bai
da iyaka,
: Hab bisa
kurmin gwanja ya kai,
: Ya kamo
Inyamuri ɗari ya zuba
gonatai,
: Ya ce su yi
noma suna faɗin mita ta noma?
: Ya ce su yi sallah
: Suna faɗin duƙi Y/Hausa,
: Ya sa su
karatu suna hwaɗin suruttan
banza,
: Sa an nan
yamma babu kowa,
: Tutam
Mujaddadi ɗai ta ah
Hausa,
: Nan ko kudu
ba abin da an nan ba azna ba,
: Gabas ɗakin Kaba shi muke tsinka don haske,
: Nan ko
Gobir akwai na Yakuba ga Jan Gwarzo,
: Da imanin
Shehu yai tudu
: Ummaru yad
daho.
(Sa’idu Faru Waƙar Sarkin Ƙauran Namoda Garba Abubakar).
A wannan ɗan waƙa makaɗa ya ambato wasu daga cikin ayyukan sarakunan Ƙauran Namoda waɗanda suka ƙunshi kira zuwa ga Allah da jihadi da
yaɗa kalmar Allah a wurin da ba ta kai ba,
da kuma umarni ga yin salla. Ga al’ada, tabbata a kan hanyar ƙwarai ita takan kai mutum ga zamowa
wani zaɓaɓɓen bawan Allah. Makaɗa Sa’idu Faru ya gwada cewa, Sarakunan Ƙauran Namoda sun taka wannan matsayi,
don haka yake ƙara tabbatarwa, Sarkin Ƙauran Namoda yana da tushen waliyantaka
tun daga uwayesa. Ga abin da ya ce:
Y/Amshi: Garba
mai Ɗ/Isa da Ƙawari
da waɗan
Torawa,
: Waliyi
ɗan
auliya'u,
: Jikan mai girma,
: Daɗai darajam Mamudu
: An sani an
ga ta tun farko,
(Sa’idu Faru Waƙar Sarkin Ƙauran Namoda Garba Abubakar)
3.2 Turken Yabo
Yabo a waƙoƙin baka yana nufin ambaton kalmomin sambarka da nufin
nuna amincewa da hali ko wani abin da mutum ya yi nagari. Ko kuma ana iya cewa,
yabo wani lafazi ne da ake yi ga wani mutum domin a nuna halayensa da
siffofinsa kyawawa da cewa abin so ne kuma abin ƙauna, (Gusau, 2008:376). Makaɗa ya fito da turken yabo a lokacin da yake yabon Sarkin Ƙaura Abubakar inda yake cewa:
Jagora: Abu gogarman Magaji mai kansakilin
daga,
: Garba ka gyara gidan Namoda ka gyara Hubbare,
: Ka wuce aikin mutum a ce wa na aiko shi,
: Ka wuce ɓacin mutum a ce wa naɓ ɓato shi.
(Sa’idu Faru Waƙar Sakin Ƙauran Namoda Garba Abubakar)
Wannan ɗan waƙa ya fito da turken yabo dangane da
ayyukan da Sarki ya yi na gyara wuraren da ya kamata, tare da nuna yadda Sarki
ya shagalta ga ayyukan raya ƙasa ba fuskantar ‘yan adawa ba.
3.3 Turken Koɗa Kai
Ambato ne na abubuwan ƙasaita ko burgewa da mutum yake da su
ko yake aikatawa, (Gusau, 2008:388). Makaɗa Sa’idu Faru ya fito da wannan turke a
waƙoƙinsa na masarautar Ƙauran Namoda, inda yake nuna waƙarsa gaba take da ta duk wani mawaƙi da ake ganin ya shahara irin su,
Narambaɗa da Auta Daɗi da Jankiɗi da sauransu. Ga abin da yake cewa:
Jagora: Narambaɗa
‘Y/Amshi: Waƙad da yay yi ma ba ta yi kamat tau ba,
Jagora: Auta Daɗi
‘Y/Amshi: Waƙad da yay yi ma ba ta yi kamat
tau ba,
Jagora: I, Jankiɗi Waƙad da yay yi ma
‘Y/Amshi: Na
ishe tai daɗi,
: Amma in an
yi bincika ba ta yi kamat tau ba
Jagora: Ni Kiɗin yaƙi niy yi ma Abu Na Isau
‘Y/Amshi/Jagora: Ba ni son kana zannawa banza,
: Ka ɗauki takobi da bindigogi da bakunkuna ka sa sirdi,
: Ba mu sansani sai bakin Tsabre,
: Kano da
Katcina Kwantagora hab Barno,
: Riƙon Namoda
shi na ac can,
: Garba ka
anshe riƙon dud da
Ummarun Ummaru yab bar ma.
(Sa’idu Faru Waƙar Sakin Ƙauran Namoda Garba Abubakar)
A wannan ɗiyan waƙa makaɗa ya zama tamkar abin da Hausawa suke cewa, “magori wasa
kanka da kanaka.” Sa’idu Faru ya lissafo wasu fitattun makaɗa waɗanda suka gabace shi a fagen waƙa, inda yake gwada tsawo da su a waƙoƙin masarautar Ƙauran Namoda. Makaɗa bai yi musun ƙwarewarsu a fagen waƙa ba, amma dai yana ganin waƙar da ya rera wa Sarkin Kiyawan Ƙauran Namoda ta zarce ta su. Hujjarsa a
nan ita ce, waƙoƙin da suka yi masa ba su ambaci jarumtar masarautar a
fagen yaƙi kamar yadda ya ambata ba. Don haka ya
ce:
Jagora: Ni Kiɗin yaƙi niy yi ma Abu Na Isau
‘Y/Amshi/Jagora: Ba ni son kana zannawa banza.
3.4 Turken Jarunta
Gusau, (2008:387) ya bayyana cewa, wannan kalma tana nufin juriya ko ƙarfin hali ko wata bajinta a lokacin
aiwatar da wani abu. Idan an ce mutum mai jaruntaka ne, to ana nufin gwarzon
namiji ne mai taurin hali ko mai naciya ko maras tsoro wanda ba ya firgita
ballantana ya sami faduwar gaba. Makaɗa sa’idu Faru ya fito da yanayin
jarumtar Sarakunan Ƙauran Namoda ta fuskar yaƙi inda yake cewa:
Jagora: Ni Kiɗin yaƙi niy yi ma Abu Na Isau
Y/Amshi/Jagora: Ba ni son kana zannawa banza,
: Ka ɗauki takobi da bindigogi da bakunkuna,
: Ka sa sirdi ba mu sansani
sai bakin Tsabre,
: Kano da
Katcina Kwantagora hab Barno
: Riƙon Namoda
shi na ac can,
: Garba ka
anshe riƙon dud da
Ummarun
: Ummaru yab
bar ma.
(Sa’idu Faru Waƙar Sakin Ƙauran Namoda Garba Abubakar)
A wannan ɗan waƙa, an nuna yadda masarautar Ƙauran Namoda take da faɗi a wancan lokaci. Wannan ya nuna masarautar ba ta
raggaye ba ce musamman a fagen yaƙi. Don haka take da faɗin ƙasa. Wannan magana ta Sa’idu Faru ta
tabbata, musamman idan aka dubi yadda masarautar Ƙauran Namoda take da tagomashi a wurin
Sarkin Musulmi. Tarihi ya tabbatar akwai Sarkin Musulmin da ya yi wafati a Ƙauran Namoda. Haka kuma, Sarkin Kano ya
yi wa Sarkin Musulmi mubayi’a a Ƙauran Namoda da doki 1000. Zaman Ribaɗi da aka yi a Ƙauran Namoda (1870-1903) ya nuna ana hawan daba da nuna
girma da ƙasaitar masarautar a Ƙauran Namoda tun kafin zuwan Turawan
Mulkin Mallaka. Zaman Ribaɗi, ana yin sa ne domin nuna ƙarfi da ƙasaitar Daular Usmaniya.
Waɗannan bayanai sun isa su nuna yadda
masarautar take a idon shugabannin masu jihadi. Gwargwadon buwaya da jarumtar
sarki, waɗanda suke ƙasa da shi sukan zamo kamarsa ko kuma
kwatankwacinsa. Don haka Hausawa sukan ce: “Kamar kumbo kamar kayanta.” Sanin
haka ya sa Sa’idu Faru yake bayyana jarumtar wani uban ƙasa na masarautar Ƙauran Namoda saboda gamsuwa da ya yi da
ƙoƙarin masarautar ta fuskar jarumta. Ga abin da yake cewa:
Jagora: Gurnanin Damisa ka sa mahwarauta
sun ɗora
ɗemuwa,
Y/Amshi: Ga wani ya yi kokuwa da wan ƙarfi
nai,
:Ya
hwaɗi
ya kare,
: Tun
ba a tantance ba shi na nishi ya lanƙwanshe
tsara,
Jagora /Y/Amshi: Tun dai ba a tantance ba
shi na nishi ya lanƙwanshe
tsara,
(Sa’idu Faru: Waƙar Dagacin Banga Sale Abubakar)
A wannan ɗan waƙa, makaɗa ya yi amfani da salon kinaya inda ya kira sunan sarki
(uban ƙasa) da damisa, sauran masu adawa da shi kuma ya ambace su da mafarauta,
saboda ƙoƙarin neman iko suke ba su samu ba. Wannan dalili ya sa a
lokacin da ƙoƙarin kai wa damisa farmakin farauta sai ta kore su ta
sanya su ɗimuwa.
3.5 Turken Kyauta
Kyauta a nan tana nufin abubuwan da
makaɗi yakan ambato an ba shi na kyautuka a
cikin waƙoƙinsa .A tunanuin Bunza (2009:123), sunan kowane irin makaɗi maroƙi, idan kuwa maroƙi bai yi roƙo ba me zai ci? Su kansu makiɗan sukan kira kiɗa roƙo, kuma suna gudanar da shi ne saboda
su samu wani abin biyan buƙatar rayuwa. Makaɗa Sa’idu Faru ya fito da turken kyauta a wannan ɗan waƙa inda ya ambaci sarki da ruwan sama
wanda yake yanke fari. Ma’ana sarki yana kyautar da takan yanke ƙamfar talauci saboda lilwantar da akan
yi da kyautar da ya bayar. Ga abin da yake cewa:
Jagora: I,
Abuu,
Y/Amshi:
Amil na Namoda na,
: Ummaru
ya dawo.
Jagora: I,
Abuu,
Y/Amshi: Amil
na Namoda na,
: Ummaru
ya dawo,
: Mu
koma Ƙaura ga ɗan
: Isau
in aza kayana.
Jagora: Abu
na Dikko ruwa maganin hwari ɗan
Mamudu.
Y/Amshi: Garba
mai Ɗ/Isa da Ƙawari
da waɗan
Torawa
Jagora: Abu
Na Dikko ruwa maganin hwari ɗan
Mamudu
(Sa’idu Faru Waƙar Sarkin Ƙauran Namoda Garba Abubakar).
3.6 Turken Zuga
Zuga tana ɗauke da wasu kalmomi ne da ake amfani da su a koɗa wani mutum, a cicciɓa shi, a nuna fifikonsa a kan wasu. Zuga takan tsuma
mutum ta sa masa kuzari da ƙwarin gwiwa, (Gusau, 2008:377). Sa’idu
Faru ya yi amfani da wannan turke inda ya bayyana fifikon Sarkin Ƙauran Namoda a kan wasu sarakuna. Ga
abin da yake ce masa:
Jagora: Ginshiƙin Alƙali uban Galadima ɗan Mamman
Y/Amshi: Jirgin bisa ba kula da kwalta ye kai ba,
: Ko cikin
daji kab bi ban ga mai ce maka komi ba.
(Sa’idu Faru Waƙar Sarkin Ƙauran Namoda Garba Abubakar).
A wanna ɗan waƙa, makaɗa ya nuna cewa, irin fifikon da jigin sama yake da shi a
kan mota, haka Sarkin Ƙauran Namoda yake da shi a kan abokan
adawarsa. Don haka ya nuna Sarki sha’anin gabansa na tsarin mulki da ci gaba da
ɗaukar takalifin mutane yake bai san da masu
adawa ba. Kamar yadda jirgi bai damu da hanyar kwalta ta mota ba, haka shi ma
sarkin Kiyawa Ƙauran Namoda bai da mu da su ba, saboda
yana gabansu.
3.7 Turken Roƙo
CNHN (2006:374) ya fassara kalmar roƙo da: “Sana’ar maroƙa ta yi wa mutane kirari ko yabo a yi
musu kyauta, ko kuma nenan kyauta daga wani. Ga al’adar mawaƙan baka na fada, a kowane lokaci suka
yi waƙa sukan keɓe wani ɓangare a cikinta su fito da buƙatun da suke nema sarki ya cika musu.
Kodayake ba kasafai sukan bayyana buƙatarsu kai tsaye ba, sukan laɓe da wasu abubuwa kafin su faɗi tasu. A wannan wuri makaɗa ya ambaci buƙatunsa kai tsaye ga Sarkin Ƙauran Namoda inda yake cewa:
Jagora: Abin da kay yi.
‘Y/Amshi:
Nufi Bubakar na da gani cika
man shi.
Jagora: Naɗa mani Sarkin kiɗi ka ba mu gida.
‘Y/Amshi:
Kuma ba mu mata mui
amre,
: Garba ka ba mu rifenin da
za mu ci tare
da matana.
(Sa’idu Faru Waƙar Sarkin Ƙauran Namoda Garba Abubakar).
A wannan ɗan waƙa, Makaɗa Sa’idu Faru ya nuna aniyarsa ta komawa Ƙauran Namoda saboda ƙaunar da take tsakaninsa da Sarki.
Wannan dalili ya sa yake tabbatar wa da Sarki ya cika masa nufinsa na wannan
aniya tasa. Babban abin da yake buƙata shi ne, a naɗa shi Sarkin kiɗan masarautar Ƙauran Namoda, sannan a ba shi gida, a
yi masa aure a kuma ba shi abinci mai yawan da zai zuba shi a rufeni (rumbuna)
domin ya ciyar da yalansa. Wannan ɗan waƙa ya fito da turken roƙon da Makaɗa Sa’idu Faru ya yi ga Sarkin Ƙauran Namoda. A ɓangare ɗaya kuma, wannan ɗan waƙa ya fito da al’adar sarakuna na ɗaukar takalihun mawaƙansu ta fuskar wurin zama da yi musu aure da suna idan buƙatar hakan ta taso da yi musu sutura da
kuma ciyar da su.
4.0 Sakamakon Bincike
Ga ƙa’idar masana bincike, ana buƙatar a ƙarshen kowane aiki a bayyana abin da
aka iya ganowa. Don haka, wasu daga cikin sakamakon da wannan bincike ya kai ga
ganowa sun haɗa da:
a.
Masarautar
Ƙauran Namoda tana cikin manyan
masarautu da tarihin Daular Usmaniya ba zai kammala ba idan ba a ji motsin ta
ba.
b.
Makaɗa Sa’idu Faru ya ƙara fito da masarautar Ƙauran Namoda a tsakanin sarakuna,
musamman idan aka dubi waƙoƙin da ya rera mata.
c.
Sa’idu Faru cikakken makaɗin fada ne, saboda haka yake amfani da kalmomin da a fada
kaɗai ake amfani da su a cikin waƙoƙinsa. Wannan dalili ya sa ya yi amfani da turakun da
wannan takarda ta tattauna akansu.
d.
Turakun da ke cikin waƙoƙin Masarautar Ƙauran Namoda sun ƙara tabbatar da martaba da kuma buwayarta a idon duniya.
e.
Waƙoƙin Masarautar Ƙauran Namoda na Sa’idu Faru tamkar wasu
taskoki ne na adana tarihi da iyakokin masarautar da kuma matsayin masarautar a
Daular Zamfara da ma ta Usmaniyya gaba ɗaya.
5.0 Kammalawa
Daga ƙarshe, ficen da masarautar Ƙauran Namoda ta yi a tsakanin masarautu
ya ba ta tagomashin samun waƙoƙi daga wurin fitattun makaɗan fada irin su, Ibrahim Narambaɗa da Musa Ɗanƙwiro da sauransu. Kasancewar wannan takarda ta taƙaita ga waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru don haka ba ta waiwayi waɗancan mawaƙa ba. Haƙiƙa masarautar Ƙauran Namoda ta amfana da basirar da Allah ya yi wa Makaɗa Sa’idu Faru musamman idan aka dubi yadda ya taskance
tarihi da buwayar masarautar a cikin waƙoƙin da ya rera mata. Wani abin sha’awa ga turakun da suke cikin waƙoƙin Ƙauran Namoda na Sa’idu Faru, duka suna nuna matsayin
masarautar ta fuskar addinin Musulunci da yaɗa shi da kuma aiki da shi sau-da-ƙafa. Tabbas, turakun da wannan takarda
ta iya ganowa guda bakwai, ba su kaɗai ne waƙoƙin suka ƙunsa ba. An yi haka ne domin taƙaitawa saboda kada a wuce makaɗi da rawa. Don haka wannan takarda take kira ga masana
adabi da harshe da al’ada a kan cewa, su ƙara faɗaɗa nazari a kan waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru na masarautar Ƙauran Namoda saboda ilmomin da ke ƙunshe a cikinsu suna gwada cewa, akwai
ruwa a ƙasa sai ga wanda bai tona ba! Allah Ya
jiƙan Sa’idu Faru Ya lulluɓe shi da rahamarsa, amin.
Manazarta
Bunza, A.
M. (2009). Narambaɗa. Lagos: Al-Ibrash Publication Plc.
Bunza, A. M. (2022). “Tarihin Shigowar Musulunci a Afirka (Duba
Cikin Bangayenta da Ƙasashen da Ya Fara Yada Zango a Taƙaice).” Takardar da Aka Gabatar a Taron Ƙara wa Juna Sani na 18 na Shekara-shekara da Majalisar Matasan Ahlil-Sunna Wal
Jama’ah Zamfara State Mai Taken: The
Contribution of
Muslim Ummah For Sustainable Security(Gudunmuwar Musulunci ga Tanadin Tsaro) a Babban ɗakin Taron UBE Titin Zagege,
Gusau.
Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya (2006). Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero. Zaria: Ahmadu Bello University Press.
Ɗangambo, A. (1984). Rabe-raben
Adabin Hausa da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Kano: Triumph.
Gusau, S. M. (1987). Makaxa da Mawaqan Hausa.
Kano: Benchmark Publishers.
Gusau,
S. M. (2003). Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Kano: Benchmark Publishers Limited.
Gusau,
S. M. (2008). Dabarun Nazarin Adabin
Hausa. Kano: Benchmark Publishers
Ltd.
Gusau,
S. M. (2008). Waƙoƙin Baka a Ƙasar Hausa: Yanaye-yanayensu da
Sigoginsu. Kano: Benchmark
Publishers Ltd.
Gusau, S. M. (2009). Diwanin Waƙoƙin Baka (Zaɓɓun Matanoni na Waƙoƙin Baka na Hausa). Kano: Century Research and Publishing Limited.
Gusau,
S. M. (2015). Mazhabobin Ra’i da Tarke a
Adabi da Al’adu na Hausa. Kano: Century Research and Publishing Limited.
Lawali,
H. (2002). “Masarautar Ƙauran Namoda da Sarakunanta.” Kundin
Digiri na Ɗaya, Kano: Sashen Koyar da Harsunan
Nijeriya, Jami’ar Bayero.
Sankalawa,
D. H. (2021). “Tarken Turken Faɗakarwa a Wasu Waƙoƙin Sani Sabulu Kanoma.” Kundin Digiri na Biyu, Kano: Sashen
Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.
Usman, Y.B (1974). “The Transformation
of Katsina C 1796-1903.” Ph.D thesis, Zaria: Department of History, Ahmadu
Bello University.
Yahya, A. B. (1997). Jigon Nazarin Waƙa. Kaduna: Fisbas Service.
Yahya, A. B. (2001). Salo Asirin Waƙa. Kaduna: Fisbas Service.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.