Ticker

6/recent/ticker-posts

Nazarin Ararrun Kalmomi a Wakar Sarkin Musulmi Muhammadu Maccido ta Sa’idu Faru

Citation: Darma, A.Y. & Hassan, S. (2024). Nazarin Ararrun Kalmomi a Waƙar Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo ta Sa’idu Faru. Four Decades of Hausa Royal Songs: Proceedings from the International Conference on the Life and Songs of Makaɗa Sa'idu Faru, 3(3), 70-75. www.doi.org/10.36349/tjllc.2024.v03i03.009.

NAZARIN ARARRUN KALMOMI A WAƘAR SARKIN MUSULMI MUHAMMADU MACCIƊO TA SA’IDU FARU

Daga

Dr. Abdullahi Yakubu Darma
Sashen Nazarin Harshen Hausa,
Tsangayar Nazarin Ilimin Sakandare Ɓangaren Harsuna,
Kwalejin Ilimi Ta Isa Kaita, Dutsin-Ma, Jihar Katsina, Nijeriya
08036375129 / 07056082213
ayakubudarma@gmail.com

Da

Sani Hassan
Sashen Nazarin Harshen Hausa,
Tsangayar Nazarin Ilimin Sakandare Ɓangaren Harsuna,
Kwalejin Ilimi Ta Isa Kaita, Jakar Waya 5007, Dutsin-Ma, Jihar Katsina, Nijeriya
08039478054 / 08025164796
hassansanig@gmail.com

Tsakure

Makaɗa Sa’idu Faru yana ɗaya daga cikin makaɗan fadar da suke amfani da kalmomin aro wajen isar da saƙon da waƙarsu take ɗauke da shi a ƙasar Hausa. Ya yi wa sarakuna da ‘ya’yan saraki mabambantan waƙoƙi a lokacinsa. Sannan yana daga cikin makaɗa ko mawaƙan da suke zaɓen kalmomin da suke amfani da su wajen sassaƙa ƙananan saƙonni a lokacin da suke ƙulla waƙa. Saboda haka, babbar manufar wannan takarda ita ce, bayyana ararrun kalmomin da makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da su wajen ƙulla waƙar da ya yi wa Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo, mai suna Bajimin Gidan Bello Mamman na Yari, Sarkin Kudu Macciɗo ci maraya. An gudanar da wannan bincike ta hanyar karantawa daga bugaggun bayanai da sauraron wasu daga cikin waƙoƙin makaɗa Sa’idu Faru. Bugu da ƙari, binciken ya gano cewa, makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da ararrun kalmomin da Hausa ta aro daga harshen Larabci da kuma Ingilishi wajen ƙulla zaren tunanin waƙarsa. Kalmomin da suka samo asali daga harshen Larabci sun haɗa da Duniya da Ilmi da Dalili da Allah da kuma Istingifari. Har wa yau, akwai kalmomi irin su Almuɗɗafa da Lahira da Wasicci da Azumu da kuma Sunna. Ararrun kalmomin da mawaƙin ya yi amfani da su na harshen Ingilishi kuwa, sun ƙunshi Bandur da Yadi da Fam da Biskit da Minti da kuma Sitawut. Haka kuma, akwai kalmomi irin su Lemu da Soda da Sigari da kuma Benci.

Fitilun Kalmomi: Waƙa, Makaɗa Sa’idu Faru, Ararrun Kalmomi, Harshen Ingilishi, Harshen Larabci

1.0 Gabatarwa

Aron kalmomi ba baƙon al’amari ba ne a yawancin harsunan duniya, domin yana ɗaya daga cikin abubuwan da suke kawo bunƙasa tare da ɗaukakar harshe. Harshen Hausa yana ɗaya daga cikin harsunan da suka samu ɗaukaka da bunƙasa ta sanadiyyar kalmomin aro. Saboda harshen Hausa cike yake da kalmomin da ya ara daga wasu harsunan da ya yi mu’amala da su da kuma waɗanda suka maƙwabce shi. Kalmomin sun yi matuƙar tasiri ga maganganun Hausawa na yau da kullum, domin da wahala a fara zance a ƙare shi, ba tare da mai magana ya sako wata kalma da harshen Hausa ya ara daga wasu harsunan ba. Irin wannan tasiri da kalmomin aro suke da shi a harshen Hausa, ya sa wannan takarda ta yi nazarin ararrun kalmomin da makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da su wajen rera waƙar da ya yi wa Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo mai suna Bajimin Gidan Bello Mamman na Yari, Sarkin Kudu Macciɗo ci Maraya.

Shi makaɗa Sa’idu Faru, yana ɗaya daga cikin shahararrun makaɗan fada a ƙasar Hausa. Makaɗan fada a ƙasar Hausa su ne makaɗan da suke yi wa sarakuna da sauran waɗanda suka jiɓanci ko suka gaji sarauta waƙa. Makaɗan fada suna isar da mabambantan saƙonni a waƙoƙin da suke rera wa iyayen gidansu ta hanyar zaɓar kalmomin da suke ganin sun dace wa wanda suke wa waƙa. Ma’ana, ba kara zube suke rera waƙar ba, a’a, suna zaɓen kalmomin da suke amfani da su wajen sassaƙa saƙonni da suke son su isar ga iyeyen gidansu ko masu sauraron waƙoƙin nasu. Makaɗa Sa’idu Faru ya rera waƙoƙi masu tarin yawa. Daga cikin waƙoƙin da ya rera, akwai waƙar Sarkin Yaƙin Banga Alhaji Sule Ƙauran Namoda da waƙar Sarkin Musulmi Alhaji Muhammadu Macciɗo da waƙar Sarkin Fulanin Bunguɗu Alhaji Shehu da waƙar Turakin Kano Alhaji Amadu da waƙar Sarkin Yawuri Muhammadu Tukur, da dai sauran makamantansu.

1.1 Ma’anar Waƙa

Yahya (1997:4) ya nuna cewa, “Waƙa tsararriyar maganar hikima ce da ta ƙunshi saƙo cikin zaɓaɓɓun kalmomin da aka auna domin maganar ta reru ba faɗuwa kurum ba.” Shi kuma (Gusau, 2003:xiii) ya nuna cewa, waƙa tsararren zance ne shiryayye cikin hikima da azanci da yake zuwa gaɓa-gaɓa bisa ƙa’idojin tsarin daidaitawa a rere cikin sautin murya da amsa amon kari da kiɗa da amshi. Waƙa aba ce da fasihai ke amfani da ita domin bayyana wata manufarsu cikin sauri ga jama’a. Domin kuwa waƙa ta fi saurin karɓuwa ga jama’a, an fi son sauraron ta fiye da wa’azi. Wannan ne ma ya sa yawancin ayyukan malaman jihadi waƙoƙi ne, (Sa’id, 1978:66). Waƙa wata kafa ce ta yaɗa manufa cikin gaugawa kamar yadda iska ke kaɗawa ta game ko’ina cikin ɗan ƙanƙanen lokaci, (Adamu, 2015:122). Sannan an nuna cewa, waƙa tana zuwa ne a sigar gunduwoyin zantuka waɗanda ake kira baitoci ko ɗiyoyi kuma ake rerawa da wani irin sautin murya na musamman, (Umar, 1980:3) a cikin (Zainab, 2014:431). Har wa yau, an nuna cewa, waƙa wani saƙo ne da aka gina shi kan tsararriyar ƙa’ida ta baiti, ɗango, rerawa, kari (bahari, amsa-amo (ƙafiya) da sauran ƙa’idojin da suka shafi daidaita kalmomi, zaɓensu da amfani da su cikin sigogin da ba lalle ne haka suke a maganar baka ba (Ɗangambo, 2008: 5).

Ta la’akari da waɗannan ma’anoni, a iya bayyana ma’anar waƙa da cewa, tsararren zance ne da ake shiryawa, a rera a cikin hikima da basira da sautin murya mai zaƙi bisa tsarin daidaitawa da zaɓen kalmomi domin a isar da saƙon da ake buƙata cikin gaugawa.

2.0 Taƙaitaccen Tarihin Makaɗa Sa’idu Faru

Gusau (2005: 117), ya bayyana cewa, an haifi Makaɗa Sa’idu Faru a garin Faru ta ƙasar Marsden a jihar Zamfara a shekarar 1932. Makaɗa Abubakar ɗan Abdul ɗan Alu mai kurya shi ne mahaifin malam Sa’idu. Mahaifiyarsa kuwa mutumiyar Banga ta ƙasar Ƙauran Namoda ce. Sa’idu ya yi rayuwar ƙuruciyarsa a garin mahaifiyarsa, watau Banga. Sa’idu bai yi karantun boko ba, haka nan ma bai yi karatun Muhammadiyya mai zurfi ba. Mahaifin Makaɗa Sa’idu makaɗin Kotso ne, kuma makaɗin sarauta ne. Ashe Makaɗa Sa’idu ya yi gadon kiɗan Kotso ne kuma ya yi gadon kiɗan sarauta ne daga mahaifinsa Abubakar ɗan Abdu ɗan Alu. Makaɗa Sa’idu ya riƙa bin mahaifinsa yawon kiɗa, daga nan ne ya koyi dabarar rera waƙa, sannan kuma ya daɗa bunƙasa ne domin shi kansa Allah ya yi masa baiwa da fasaha ta yin waƙoƙi. Makaɗa Sa’idu yakan shirya waƙoƙinsa daga gida ne kafin ya je fagen reraŵa. Wannan kuwa ba ya rasa nasaba da cewar yanayin waƙoƙinsa suna da amshi da ƙari ne, kuma yakan binciki sunayen iyaye da kakannin da yake sakawa a cikin waƙoƙinsa. Kodayake wani lokaci waƙa takan zo masa nan take, kuma ya rera ta. (Gusau, 2005:117-122)

Daga cikin yaran Sa’idu waɗanda suke kama masa waƙa akwai Mu’azu (Ɗan Galadimansa) da Ɗan Daudu da kuma Ali. Daga cikin iyayen gidansa kuwa akwai Muhammadu Macciɗo ɗan Sarkin Musulmi Abubakar na III da Abubakar Sarkin Ƙauran Namoda (Gusau, 2005, sh. 117-122). Allah ya yi wa Makaɗa Alhaji Sa’idu Faru rasuwa a shekarar 1987.

3.0 Manufar Bincike

Babbar manufar wannan takarda ita ce, bayyana ararrun kalmomin da makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da su wajen isar da saƙon waƙar da ya yi wa Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo. Ma’ana, takardar ta zaƙulo ararrun kalmomin da makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da su wajen gina turken waƙarsa ta Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo mai suna Bajimin Gidan Bello Mamman na Yari, Sarkin Kudu Macciɗo ci Maraya.

4.0 Dabarun Bincike

A ƙoƙarin gudanar da wannan nazari ko samo bayanan da wannan bincike ya ginu a kan su, an bibiyi wasu bugaggun bayanai da aka samu a wasu daga cikin littattafai da kuma sauran takardun ilimin da aka samu. Haka kuma, an saurari wasu daga cikin waƙoƙin makaɗa Sa’idu Faru a wayar salula da kwamfuta da kuma na’urar MP3. Wanda daga bisani aka tsayar da alƙiblar wannan aiki a kan waƙar da Sa’idu Faru ya yi wa Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo. Har ila yau, aikin ya inganta ƙwarai a sanadiyyar samun wannan waƙa a cikin Diwanin Waƙoƙin Baka Zaɓaɓɓun Matanoni na Waƙoƙin Baka na Hausa da Gusau ya buga a shekarar 2009.

5.0 Yanaye-Yanayen Ararrun Kalmomi a Waƙar Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo

Tabbas Makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da wasu daga cikin kalmomin da harshen Hausa ya aro daga wasu harsunan duniya waɗanda wata mu’amala ta taɓa haɗa su a tarihin ce. A nan za a iya ganin irin yanaye-yanayen waɗannan kalmomi da makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da su wajen ƙulla zaren tunanin waƙarsa, wadda ya yi wa Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo, mai suna Bajimin Gidan Bello Mamman na Yari, Sarkin Kudu Macciɗo ci Maraya kamar haka.

5.1 Ararrun Kalmomi Daga Harshen Larabci

Lallai bincike ya tabbatar da cewa, makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da wasu daga cikin kalmomin da harshen Hausa ya aro daga harshen Larabci wajen isar da saƙon da waƙarsa take ɗauke da shi. Za a iya ganin misalan hakan a waɗannan ɗiyan waƙa da suke biye a ƙasa.

Jagora: Na Marafa Ɗanbaba mai tara haushi,

Na sarkin Gabas duniya hori-wawa,

Bai gadi sake ba Mamman na Baura, …

Idan aka kalli waɗannan ɗiyan waƙa, za a ga cewa makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da ararriyar kalmar da harshen Hausa ya aro daga harshen Larabci ta ‘duniya’ wajen isar da saƙon waƙansa. Kenan, kalmar ‘duniya’ ita ce ararriyar kalmar da aka aro daga harshen Larabci, wadda ‘dunnya’ ita ce asalin kalmar a Larabce, kuma ita ce mawaƙin ya yi amfani da ita a waƙarsa.

Bayan wannan kuma, akwai wasu ɗiyan waƙar da yaronsa Mu’azu yake cewa,

Mu’azu: Faɗi gaskiya Bello kai Shehu yac ce,

Bari masu son duk su maishe ka yaro,

Da kyauta da ilmi da neman dalili,

Da gode wa Allah da istingifari,

Da su Bello ɗan Shehu yat tsarma kowa,

Ka kai kamab Bello ka gadi Moyi,

Y/Amshi: Saura ka kai inda mai Hausa yak kai.

A nan kuma, idan aka kalli waɗannan ɗiyan waƙa da Mu’azu ya kawo a cikin wannan waƙa ta Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo, za a ga cewa akwai wasu daga cikin kalmomin da harshen Hausa ya aro daga harshen Larabci. Misali, mawaƙin ya kawo ɗiyan waƙar da ya yi maganar ‘ilmi’ da ‘dalili’, dukkan waɗannan kalmomi ne na Larabci da harshen Hausa ya aro, wato daga kalmar asali ta ‘ilmun’ da ‘dalil’ a Larabce. Haka kuma, mawaƙin ya ambaci ‘Allah’ da ‘intingifari’, su ma kalmomi ne da Hausa ta aro daga Larabci, wato daga kalmar asali ta ‘Allahu’ da ‘istigfar’ a Larabce. Kenan, a wannan waƙa ta Sa’idu Faru an yi amfani da kalmomin aro na Larabci wajen isar da saƙon da waƙar take ɗauke da shi.

Har ila yau, akwai kuma wasu ɗiyan waƙa da makaɗa Sa’idu Faru ya sake yin amfani da kalmomin da asalinsu na Larabci ne wajen jojjona zaren tunanin waƙarsa kamar yadda za a gani a nan ƙasa:

Jagora: Da mutum da dabba da tsuntsu da ƙwaro,

Y/Amshi: Mutum da dabba da tsuntsu da ƙwaro,

Da ƙasa da abin da duk ag ga bayanta,

Komai na duniya na Almuɗɗafa na,

Garai Shehu yas samu girma da yarda,

Komi na gun Shehu shi ag ga Bello,

Komi na gun Bello shi ag ga Garba

Ko lahira ko muna taƙamatai.

A nan kuma, idan aka kalli waɗannan ɗiyan waƙa, za a ga cewa inda makaɗa Sa’idu Faru ya kawo kalmar ‘duniya’ da ‘Almuɗɗafa’ da kuma ‘lahira’, ya yi amfani da kalmomin aro. Saboda kalmomin da Hausa ta aro daga harshen Larabci ne. Wato kalmar ‘duniya’ asalinta daga kalmar ‘dunya’, kalmar ‘Almuɗɗafa’ asalinta daga kalmar ‘Almusɗafa’, sai kalmar ‘lahira’ ita kuma asalinta daga kalmar ‘akirati’. Tabbas waɗannan bayanai sun tabbatar da cewa makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da kalmomin aro na Larabci wajen isar da saƙon waƙar da ya yi wa Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo.

Daga nan kuma, akwai wani ɗiyan waƙa shi ma da yake nuna yadda makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da ararriyar kalmar Larabci wajen isar da saƙon waƙarsa kamar yadda za a gani a ƙasa.

Jagora: Da biskit da minti da taba sigari,

Y/Amshi: Biskit da minti da taba sigari,

Da lemu da soda da kwalbat sitawut,

Bai yada aza su ko sau guda ba,

Ya ɗau wasiccin da Usumanu yac ce,

Ya ce abincinsu ba namu ne ba,

Yawanci abincinsu daɗi gare shi,

Kowanmu ne yai ta ci ba ruwanai,

Wancan na ci sai ta ci bai ci can ba.

A nan kuma, idan aka kalli waɗannan ɗiyan waƙa, za a ga cewa, makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da ararriyar kalmar ‘wasicci’ ne kaɗai daga harshen Larabci. Wato ya yi amfani da kalmar ‘wasicci’ daga cikin kalmomin da Hausa ta aro daga harshen Larabci. Wannan ya ƙara tabbatar da cewa makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da ararriyar kalmar Larabci wajen ƙulla zaren tunanin wannan waƙar.

Hakazalika, bayan waɗannan kuma, akwai wasu ɗiyan waƙar da suke nuna yadda makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da ararrun kalmomi na Larabci wajen isar da saƙon waƙarsa. Wato waƙar da ya yi wa Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo, mai suna Bajimin Gidan Mamman na Yari, Sarkin Kudu Macciɗo ci maraya. Za a iya ganin wuraren kamar haka:

Jagora: Shi wane girma shi kai bai da wayo,

Y/Amshi: Wane girma shi kai bai da wayo,

Ya togu daidai shina nan bani na,

Ya bar azumi da kono da sunna,

Sai ya ji goge shi ɗauko kujera,

A shisshirya benci motsata su zauna,

A aika a ɗauko kwalebe a buɗe,

Da ka gane ka koma ma Allah,

Shi ad da shi babu mai tsarguwatai.

Idan aka kalli ɗiyan wannan waƙa da suke a sama, za a ga cewa makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da ararrun kalmomi na Larabci wajen ƙuƙƙulla zaren tunanin da waƙarsa take ɗauke da shi. Musamman a wuraren da ya ambaci kalmar ‘azumi’ da ‘sunna’. Tabbas waɗannan kalmomi suna daga cikin kalmomin da Hausa ta aro daga Larabci, wato daga kalmar ‘assaum’ da kuma ‘sunnah’. Sai kuma inda ya ambaci sunan ‘Allah’, wanda daga kalmar ‘Allahu’ ne ta samo asalinta a Larabci. Haƙiƙa, makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da ararrun kalmomi na Larabci wajen haɗa wannan waƙa da ya yi wa Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo.

5.2 Ararrun Kalmomi na Harshen Ingilishi

Dangane da abin ya shafi ararrun kalmomi na harshen Ingilishi kuwa, makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da wasu daga cikin kalmomin da harshen Hausa ya aro daga harshen Ingilishi. Ya yi amfani da su wajen ƙullawa, tare da jojjona zaren tunaninsa, domin waƙarsa ta samu karɓuwa ga wanda aka rera wa waƙar da kuma masu sauraron waƙar tasa. Don haka, za a iya ganin misalan ararrun kalmomin da ya yi amfani da su na harshen Ingilishi wajen shirya wannan waƙa kamar haka:

Jagora: Baba ya ba mu bandur guda duk na lailai,

Y/Amshi: Ya ba mu bandur guda duk na yadi,

Ya ba mu fam goma yac ce mu ɗunke,

Ga takalumma na fam shidda-shidda,

Hula kalabus goma yab ban,

Kyauta irin taka jikan Mu’azu,

Don ba a cewa mutum ba kamatai,

Sai Larabawan Masar masu girma.

Idan aka kalli waɗan ɗiyan waƙa, za a ga cewa lallai makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da wasu daga cikin kalmomin da Hausa ta aro daga harshen Ingilishi wajen isar da saƙon da waƙarsa take ɗauke da shi. Saboda kalmar ‘bandur’ asalinta kalmar Ingilishi ‘bandle’. Haka ma kalmar yadi’ asalinta daga Ingilishi ne ‘yard’. Kalmar ‘fam’ asalinta daga harshen Ingilishi ne ‘pound’. Don haka, bincike ya tabbatar da cewa, makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da wasu ararrun kalmomin da Hausa ta aro daga harshen Ingilishi wajen rera wannan waƙa ta Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo.

Bayan wannan kuma, akwai wasu ɗiyan waƙa waɗanda suka ƙara nuna yadda makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da wasu daga cikin ararrun kalmomin da Hausa ta aro daga harshen Ingilishi wajen isar da saƙon waƙarsa kamar yadda suka zo a ƙasa.

Jagora: Da biskit da minti da taba sigari,

Y/Amshi: Biskit da minti da taba sigari,

Da lemu da soda da kwalbat sitawut,

Bai ya da aza su ko sau guda ba,

Ya ɗau wasiccin da Usumanu yac ce,

Ya ce abincinsu ba na mu ne ba,

Yawanci abincinsu daɗi gare shi,

Kowanmu ne yai ta ci ba ruwanai,

Wancan na ci sai ta ci bai ci can ba.

A nan idan aka kalli waɗannan ɗiyan waƙa, za a ga cewa suna nuna yadda makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da ararrun kalmomin da Hausa ta aro daga harshen Ingilishi wajen jojjona zaren tunanin waƙarsa. Saboda makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da kalmar ‘biskit’ da ‘minti’ da ‘sigari’ da soda da kuma ‘sitawut’ wajen harhaɗa wasu ɗiyan waƙarsa. Waɗannan kalmomin suna daga cikin kalmomin da Hausa ta aro daga harshen Ingilishi. Saboda kalmar ‘biskit’ ta samo asali daga kalmar ‘biscuit’, kalmar ‘minti’ daga ‘kalmar ‘mint’, kalmar ‘sigari’ daga kalmar ‘cigret’. Haka nan, kalmar ‘lemu’ ita ma ta samo asali daga kalmar ‘lemon’, kalmar ‘soda’ daga kalmar ‘sodar’, sai kalmar ‘sitawut’ daga kalmar ‘starwut,’ kuma dukkansu kalmomi ne na harshen Ingilishi. Tabbas, wannan mawaƙi ya yi amfani da ararrun kalmomi na harshen Ingilishi wajen rera waƙar da ya yi wa Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo.

Har ila yau, akwai wani wuri da za a iya cewa makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da ararriyar kalmar da harshen Hausa ya aro daga harshen Ingilishi bayan waɗanda aka gani a bayanan da suka gabata. Za a iya ganin wurin kamar haka:

Jagora: Shi wane gima shi kai bai da wayo,

Y/Amshi: Wane girma shi kai bai da wayo,

Ya togu daidai shina nan bani na,

Ya bar azumi da kono da sunna,

Sai ya ji goge shi ɗauko kujera,

A shisshirya benci motsata su zauna,

A aika a ɗauko kwalebe a buɗe,

Da ka gane ka koma ma Allah,

Shi ad da shi babu mai tsarguwatai.

A nan ma, idan aka lura da waɗannan ɗiyan waƙa, za a ga cewa makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da ararriyar kalmar ‘benci’ a wajen isar da saƙon da waƙarsa take ɗauke da shi. Saboda ita wannan kalma ta ‘benci’ asalinta kalmar Ingilishi ce ‘bench’ harshen Hausa ya aro. Don haka, bayanai sun tabbatar da cewa makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da wannan ararriyar kalmar da ta samo asali daga harshen Ingilishi wajen isar da saƙon da waƙarsa take ɗauke da shi ga wanda aka shirya ko aka rera wa waƙar da sauran masu sauraro.

6.0 Sakamakon Bincike

Bincike ya gano cewa, makaɗa Sa’idu Faru a waƙar da ya yi wa Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo, mai suna Bajimin Gidan Bello Mamman na Yari, Sarkin Kudu Macciɗo ci maraya Mawaƙin ya yi amfani da ararrun kalmomin da harshen Hausa ya aro daga harshen Larabci da kuma na Ingilishi. Bincike ya tabbatar da cewa, ararrun kalmomin da mawaƙin ya yi amfani da su na harshen Larabci wajen ƙulla zaren tunanin waƙarsa sun haɗa da Duniya da Ilmi da Dalili da Allah. Har wa yau, akwai kalmomi irin su Istingifari da Almuɗɗafa da Lahira da Wasicci da Azumi da kuma Sunna. Su kuma ararrun kalmomin da mawaƙin ya yi amfani da su na harshen Ingilishi kuwa, sun ƙunshi Bandur da Yadi da fam da Biskit da kuma Minti. Haka kuma, akwai kalmar Sitawut da Lemu da Soda da Sigari da kuma Benci. Waɗannan bayanai sun tabbatar da cewa, makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da wasu daga cikin ararrun kalmomin da harshen Hausa ya aro daga harshen Larabci da kuma na Ingilishi wajen shirya wannan waƙa.

7.0 Kammalawa

Wannan bincike ya yi nazari a kan waƙar da makaɗa Sa’idu Faru ya yi wa Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo. Bincike ya gano cewa, makaɗa Saidu Faru ya yi amfani da wasu daga cikin ararrun kalmomin da harshen Hausa ya aro daga harshen Larabci da kuma na Ingilishi. Mawaƙin ya yi amfani da waɗannan ararrun kalmomin wajen ƙulla zaren tunanin waƙarsa. Wato ya yi amfani da su ya isar da saƙon da waƙarsa take ɗauke da shi ga Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo da sauran masu sauraro. Sannan binciken ya fito da ilahirin ararrun kalmomin da mawaƙin ya yi amfani da su na harshen Larabci da kuma na Ingilishi a wannan waƙa mai suna Bajimin Gidan Bello Mamman na Yari, Sarkin Kudu Macciɗo ci maraya.

Manazarta

Adamu, M. (2015). “Yabo Tubalin Ginin Tallar ‘Yan Takara Cikin Waƙoƙin Ƙarni na 21: Nazari Daga Wasu Waƙoƙin Siyar Jamhuriya ta Huɗu”. Algaita Journal of Current Research in Hausa Studies, Ɓol. 1. No. 1, p. 122-128. Department of Nigerian Languages, Bayero University, Kano. Zaria: Ahmadu Bello University Press Limited.

Ɗangambo, A. (2008). Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa. (Sabon Tsari). Zaria: Amana Publishers Limited.

Gusau, S. M. (2003). Jagoran Nazarin Waƙoƙin Baka. Kano: Benchmark Publishers Limited.

Gusau, S. M. (2005). Makaɗa da Mawaƙan Hausa. Kano: Benchmark Publishers Limited.

Gusau, S. M. (2008). Waƙoƙin Baka na Ƙasar Hausa: Yanaye-Yanayensu da Sigoginsu. Kano: Benchmark Publishers Limited.

Gusau, S. M. (2009). Diwanin Waƙoƙin Baka Zaɓaɓɓun Matanonin Waƙoƙin Baka na Hausa. Kano: Centuary and Publishing Limited.

Sa’id, B. (1978). “Gudummuwar Masu Jihadi kan Adabin Hausa”. Kundin Digiri na Biyu. Jami’ar Bayero Kano.

Yahya, A. B. (1997). Jigon Nazarin Waƙa. Kaduna: Fisbas Media Services.

Zainab, I. (2014). “Jiga-Jigan Hausa a Bakin Mawaƙin Hausa: Waiwaye a kan Waƙoƙin Ala na Farfesa Abdulƙadir Ɗangambo da Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau”. Garkuwan Adabin Hausa, a Festschrift in Tribute to Abdulƙadir Ɗangambo, 431-440. Zaria: Ahmadu Bello University Press Limited.

Sa'idu Faru

Post a Comment

0 Comments