Citation: Rabeh, H. and Karofi, I.A. (2024). Nazarin Awon Baka a Waƙar ‘Annobar Korona’ ta Khalid Imam. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 373-377. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.047.
NAZARIN AWON BAKA
A WAƘAR
‘ANNOBAR KORONA’ TA KHALID IMAM
Hassan Rabeh 1
Isah Abubakar
Karofi 1
1 Sashen Hausa,
Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita, Dutsinma, Jihar Katsina
Tsakure:
Cutar Korona cuta ce da ta girgiza duniya baki ɗaya wadda har ya zuwa yau
mutane ba su gama warwarewa daga tasirin irin ɓarnar
da ta haddasa masu ba. Daga cikin hanyoyin faɗakar
da al’umma a kan wannan cuta ita ce amfani da hanyar adabi, musamman waƙoƙi don
wayar da kai da kuma faɗakar
da al’umma a game da yadda za a kare kai daga kamuwa da wannan cuta. Ɗaya
daga cikin mawaƙan da suka bayar da gudummuwa ta wannan fanni shi ne Khalid
Imam da waƙarsa
ta Cutar Korona. An yi nazarin wannan waƙa ta hanyar yin nazarin awon baka. An yi
haka ne ta hanyar feɗe
waƙar
da nuna karin da ta hau da kuma bayyana naƙasu ko larurorin da suka wanzu a cikin waƙar. An
yi amfani da ra’i
Khalili a yayin aiwatar da wannan takarda. A ƙarshe takardar ta gano larurori uku da
suka wanzu a cikin waƙar; biyu daga cikinsu zihaffai ne, ɗaya kuwa illa ce.
Fitilun Kalmomi: Awo, Baka, Waƙa, Annobar Korona, Khalid Imam
Gabatarwa
Cutar korona cuta ce wadda ƙwayar cutar coronaɓirus da ake wa laƙabi
da SARS-CoV 2 takan haddasa. An fara jin ɗuriyar wannan cuta a ranar 31 ga wata Disambar shekarar 2019
bayan wani rahoton kamuwar rukunin wasu mutane a Wuhan ta ƙasar Sin (China). Wannan cuta ta
zamo annoba ga duk faɗin duniya. Cuta ce wadda ta
haddasa rasa rayuka masu yawa da haifar da taɓarɓarewar arzikin ƙasashe
da dama baya ga haddasa fargaba da kuma yin barazana ga zamantakewar al’umma a
duk faɗin duniya. An yi ta samun
bayanai da gargaɗi daga ɓangarori da dama na rayuwar al’umma a ciki har da ɓangaren adabin Hausawa inda mawaƙa ma ba a bar su a baya ba wajen
faɗakarwa da kuma ilimantar da
jama’a a kan wannan cuta. Ɗaya
daga cikin mawaƙan da
suka bayar da gudummuwarsu ta wannan fanni shi ne Imam Khalid.
Waƙar cutar korona waƙa
ce da Imam Khalid ya rubuta domin faɗakarwa da nusar da al’umma da mu
koma ga Allah maɗaukakin sarki. Waƙa ce ‘yar ƙwar biyu wadda ba ta ɗauke da amsa-amo. Waƙar
tana ɗauke da baiti talatin da shida
(36) waɗanda suke ɗauke da sauƙaƙan kalmomi na harshen Hausa da
kuma wasu da aka yi aro daga harsunan Larabci da kuma Ingilishi.
Ganin irin muhimmanci da kuma
gudummuwa da wannan waƙa
ta bayar a fagen adabi ya sanya aka yi nazarin arulinta inda aka feɗe waƙar
tare da yin nazarin ƙafafuwa
da zihaffan da waƙar take ɗauke da su tare kuma da bayyana Karin waƙar.
2.0
Manufar Bincike
Manufar wannan takarda ita ce
yin nazarin arulin waƙar
‘Cutar Korona’ ta Imam Khalid. Za a yi nazarin waƙar ne ta hanyar feɗe waƙar tare da gano karinta wato
gano a bisa wane kogi aka gina waƙar.
Za a yi haka ne ta hanyar gano ƙafar
waƙar. Za a kuma bayyana irin
illoli ko zihaffan da suka yi tasiri a ƙafar
waƙar.
3.0
Hanyoyin Gudanar da Bincike
Daga cikin hanyoyin da aka bi
wajen aiwatar da wannan takarda akwai ta karanta waƙar tare kuma da yin fiɗar ta da kuma yin nazarin ƙafafuwa don gano karinta, sannan kuma da bayanin irin
larurorin da suka wanzu a cikinta. Sannan kuma za a karanta littattafai domin
samun wasu muhimman abubuwa da takardar ta ƙunsa.
4.0
Aruli
Ita dai kalmar aruli kalma ce da
ta samo asali daga kalmar ‘Arudh’ ta Larabci. Wannan kalma tana nufin ilimin da
ake sanin karin waƙa da shi.
Da wannan ilimi ne ake tabbatar da daidaituwar karin ko akasin haka da kuma
dalili ko dalilan da suka sanya karin ya fanɗare
(wato ya ƙi
daidaituwa). A wannan fanni ana amfani da alamomi da nufin fayyace karuruwa a
cikin rubutattun waƙoƙi na Hausa. Ta wannan hanya ce
ake gane waƙoƙi masu kyau da masu naƙasu.
Bello da Sheshe (2013:5) suna da
da’awar cewa, “A Hausa Aruli ilimi ne wanda yake nuna hanyoyin da za a fahimci
kari a waƙoƙin Hausa bisa wani ƙayyadajjen tsari, tare da irin
abubuwan da ke sa wannan tsari, wani lokaci ya fanɗare”.
5.0
Ra’i
Akwai ra’o’in da ake amfani da
su domin fayyace karin waƙa.
Ra’in da aka yi amfani da shi a yayin wannan nazari shi ne ra’i Khalili wato
yadda ake bayyana karin Bahaushiyar waƙa
ta amfani da Balarabiyar hanya. Wannan ra’i Al-Khalil bn Ahmad AlFarahidhi
wanda ya rayu a 706-791 CE ya samar da shi.Wannan ra’i yana danganta karin waƙar Larabci da na Hausa ta yin
amfani da ƙafafuwa/sawaye
masu ɗauke da gaɓoɓi, domin bayar da karin waƙa (Bello, 2015:2).
6.0
Awon Waƙar
Dangane da awon waƙoƙin Hausa suna hawa kan karin waƙoƙin Larabci. Sanin karuruwa shi ne babban jigon awon baka.
Karin kuwa, sun ƙunshi Basid, Hafif, Hajaz, Kamal, Madid, Mutadarik, Mutaƙarib, Rajaz,Ramal, Ɗawil da kuma Wafir (Auta, 2017 sh. 151).
|
baitin
waƙa |
tsarin
ƙafafuwa/sawaye |
1 |
Masu gaɗa suna ta shewa, 'Yan caca
da masu karta.
|
– v – v v + – v –
– - v +v – v –
– |
2 |
'Yan
daudu da ma kilaki, Sun tsere
babu kowa.
|
– –vv + – v –
– – – –
+ – v – – |
3 |
Tituna leƙa ka duba, Kasuwanni
har mashaya.
|
– v –
– + – v – – – v –
– + – v – – |
4 |
Makarantu
har sinima, 'Yan ƙwallo da masu dambe.
|
v v –
– + – v – – – – v v
+ – v – – |
5 |
Sun ɓace
duk don Korona, Ko'ina
duka tsit kake ji.
|
– v –
– + – v – – – v – v
v + – v – – |
6 |
Ta bi
Gwamna har gidansa, Ta shaƙi wuyan Minista.
|
– v –
– + – v – – – – v v
+ – v – – |
7 |
Can a Ladan ga Yarima, Ta bi shi
cikin turaka.
|
– v –
– + – v – – – – v v
+ – v – – |
8 |
A Abuja
har a Billa, Ta shige
ciki ta yi sheƙa.
|
v v –
– + – v – – – v – v
v + – v – – |
9 |
Tai ƙwayaye ta yi 'ya'ya, Ta miƙe ƙafa a
fada.
|
– v –
– + – v – – – – v v
+ – v – – |
10 |
Tabbas
cutar Korona, Annoba ce
ta gaske.
|
– – –
+ – v – – – – –
+ – v – – |
11 |
A
masallatai da coci, Duk an
koma ga Allah.
|
v v –
– + – v – – – – –
+ – v – – |
12 |
Sarki mai
shirya komai, Dole ne
bauta gare shi.
|
– – –
+ – v – – – v –
– + – v – – |
13 |
Ba tsumi
kuma ba dabara, Duniya
yau an bi Allah.
|
– v – v
v + – v – – – v –
– + – v – – |
14 |
Masu sheƙe aya su more, A Italiya
ko Amurka.
|
– v – v
v + – v – – v v – v
v + – v – – |
15 |
Har ƙasar Sin can a Chana, Ta kai da
yawa kushewa. Ko Farisa
har Faransa, Ba kowa
yau a titi. |
– v –
– + – v – – – – v v
+ – v – – – – v v
+ – v – – – – –
+ – v – – |
16 |
Kufai a
kira yi Turai, Champions League an tsaya cik. |
– v – v
v + – v – – – v –
– + – v – – |
17 |
Ba a yin zancen Ronaldo, Har Messi
ba batunsa.
|
– v –
– + – v – – – – –
+ – v – – |
18 |
Ita
annobar Korona, Cuta ce
babu shakka.
|
v v –
– + – v – – – – –
+ – v – – |
19 |
Ba ta
kunya ba ta tsoro, Ba ta
sabo ba sanayya.
|
– –
– + – v –
– – v –
– + – v – – |
20 |
Yau mutum
ya gane cewa, Bai da ƙarfi sai na Allah.
|
– v –
– + – v – – – v –
– + – v – – |
21 |
Bai da
sauran duk dabara, Kariyarsa
tana ga Rabbu.
|
– v –
– + – v – – – v –
– v + – v – – |
22 |
Gatan
kowa Ilahu, Mui ta
bauta mai da ɗa'a.
|
– – –
+ – v – – – v –
– + – v – – |
23 |
Ma
rabauata a yau da gobe, Don ko
dai cutar Korona.
|
– v – v
v + – v – – – v –
– + – v – – |
24 |
Wa'azi ce
babu shakka, Me je shi
ke asara.
|
v v –
– + – v – – – – –
+ – v – – |
25 |
Kurciya
in ta yi kuka, Saƙo nata ban da wawa, |
– v –
– + – v – – – v – v
v + – v – – |
26 |
Bare
gaula da soko. Masu
shashanci a hanya.
|
v – – + –
v – – – v –
– + – v – – |
27 |
Hankali
kura kira shi, Ta yin
zabari na guga.
|
– v –
– + – v – – v – v v + –
v – – |
28 |
Mai rabo
shi ke rabauta, In an wa'azi ya ɗauka. |
– v –
– + – v – – – – v v
+ – v – – |
29 |
Zunubansa ya nemi tuba, Kan ya ji shi cikin kushewa. |
v v – v v + – v –
– – v – v
v + – v – – |
30 |
Ni Khalid
bani shakka, Tabbas cutar
Korona. Jan kunne
ce gare mu. Mu bar saɓo
da sharri. |
– – –
+ – v – – – – –
+ – v – – – – –
+ – v – – v – –
+ – v – – |
31 |
Mu so
junanmu gaske, Hakan zai
taimake mu.
|
v – – + –
v – – v – – + –
v – – |
32 |
Ni Imam
Khalid na Indo, Jikan
Hauwa’u tabbas.
|
– v –
– + – v – – – – –
+ – v – – |
33 |
Na san
cutar Korona, Ƙanwa ce gun talauci.
|
– – –
+ – v – – – – –
+ – v – – |
34 |
Wajen ƙeta da sharri, Har ma
yawo a dangi.
|
v – – + –
v – – – – –
+ – v – – |
35 |
Ni nan
zan sanya aya, Cikin waƙar Korana.
|
– – –
+ – v – – v – – + –
v – – |
36 |
Allahu
kasa mu gane, Mu tuba
zuwa gare Ka. |
– – v v
+ – v – – v – v v + –
v – – |
6.1
Bayanin Kari
A dukkan baitocin talatin da
shida (36) na waƙar an
samu maimaicin ƙafa ta
bakwai (7) mai suna fa’ilatun (faa-i-laa-tun– v – –)
wato:
a – v – – / – v
– –
– v
– – / –
v – –
b 7+7
7+7
c faa-i-laa-tun / faa-i-laa-tun
faa-i-laa-tun / faa-i-laa-tun
d Karin Ramal
6.2
Bayanin Larurori
An samu bayyanar wasu zihaffai
waɗanda suka sauya tsarin wasu ƙafa a cikin wasu baituka na waƙar. Dukkan zihaffan sun bayyana
ne a ɓangaren farko na ɗangon waƙar.
Zihaffan da aka samu a wannan waƙar
sun haɗa da:
6.2.1 Habni: Wannan zihafi yana ɗaya daga cikin zihaffan da suka
yi tasiri a ƙafar da
ta samar da karin wannan waƙar.
Wannan zihafi yakan sauya doguwar da’ira ta farkon ƙafa zuwa gajera, muddin dai ba
turke ne a farkon ƙafar
ba.
fa-i-laa-tun oo o oo oo oo o oo oo o o oo oo v v – –
An sami wannan zihafi a ɗango na biyu (baiti na 1) da ɗango
na ɗaya (baiti na 2 da 4 da 8 da 11
da 18 da 24) inda aka sami v v – – a
maimakon – v – –
6.2.2 Kaɗa’i: Ana samun wannan illa ne a
lokacin da aka soke da’ira ta 3 a turke, sannan aka haɗe gajera mai zaman kanta, suka haɗu suka zama doguwar da’ira. Ana samun wannan illa ne a inda
turke ya fara da gajerar gaɓa sannan doguwar gaɓa ta biyo baya. Misali:
faa-i-laa-tun oo o oo
oo oo o oo oo
oo o o oo oo oo oo. An samu wannan illa a ɗango na biyu (baiti na 2 da 11 da 17 da 18 da 24 da 32 da
34) da ɗango na ɗaya (baiti na 10 da 12 da 19 da 22 da 35) da ɗango na huɗu (baiti na 15) da ɗango na 1 da 2 da na 3 (baiti na 30) ɗango na 1 da na 2 (baiti na 33) inda aka sami – – –a
maimakon – v
– –.
6.2.3 Shakali: Ana samun wannan zihafi ta dalilin haɗuwar zihafi habni da kaffi a ƙafa ta 7 oo o oo
oo oo o
oo oo o o oo oo Habni
o o oo oo o o
oo oo o o oo o
Kaffi o o oo o v v – v
Shakali.
7.0
Sakamakon Bincike
A ƙarshen wannan nazari binciken ya nuna cewar waƙar Cutar Korona waƙa ce mai baitoci 36, ‘yar ƙwar biyu , babu amsa amon ƙarshen baiti a cikinta. Waƙa ce da ta hau Karin Ramal, wato
wadda aka samu maimaituwar ƙafa
ta bakwai (7) a cikinta. Haka nan kuma, an samu wanzuwar illa kaɗa’i da zihaffan habni da shakali.
8.0
Kammalawa
Wannan takarda ta yi nazarin awo
ko arulin waƙar Cutar
Korona ta Khalid Imam a inda aka gabatar da manufa da hanyoyin gudanar da
bincike da ra’in da aka gudanar da binciken a kansa. An kuma feɗe waƙar
tare da gano karinta da kuma larurorin da suka wanzu a cikinta.
Manazarta
Auta,
A.L. (2017). Faɗakarwa
a rubutattun waƙoƙin Hausa. Bayero University, Press.
Bala,
I. da Imam. K. (2020). Corona Blues (A
Bilingual Anthology of Poetry). Whetstone Publishers.
Bello,
A.(2014).Poetry, Prosody and Prosodic
Analyses of Hausa Poems. Ahmadu Bello University, Printing Press.
Bello,
A. (2015). Arulin Hausa a Faɗaɗe. Ahmadu Bello University,
Printing Press.
Ɗangambo, A.
(2007). Ɗaurayar
Gadon Feɗe Waƙa (Sabon tsari). Amana Publishers.
Yahya, A.B. (2014). Gudale Waƙar soyayya: Misalin Gazl (Ghazal)
Cikin Rubutattun Waƙoƙin Hausa. Garkuwan
Adabin Hausa A Festschrift In Tribute To Abdulƙadir Ɗangambo. Department of Nigerian Languages, Bayero University.
pp125-138.
Zaria,
A.B. da Sheshe, N.I. (2013). Arulin Hausa a Sauƙaƙe. SM Graphics Printers.
Ratayen Waƙar
1. Masu gaɗa suna ta shewa,
'Yan
caca da masu karta.
2. 'Yan
daudu da ma kilaki,
Sun
tsere babu kowa.
3.Tituna leƙa ka duba,
Kasuwanni
har mashaya.
4. Makarantu
har sinima,
'Yan
ƙwallo da masu dambe.
5. Sun ɓace
duk don Korona,
Ko'ina
duka tsit kake ji.
6. Ta bi
Gwamna har gidansa,
Ta
shaƙi wuyan Minista.
7. Can a Landan ga Yarima,
Ta
bi shi cikin turaka.
8. A Abuja
har a Billa,
Ta
shige ciki ta yi sheƙa.
9. Tai ƙwayaye ta yi 'ya'ya,
Ta
miƙe ƙafa a fada.
10. Tabbas
cutar Korona,
Annoba
ce ta gaske.
11. A masallatai
da coci,
Duk
an koma ga Allah.
12. Sarki mai
shirya komai,
Dole
ne bauta gare shi.
13. Ba tsumi
kuma ba dabara,
Duniya
yau an bi Allah.
14. Masu sheƙe aya su more,
A
Italiya ko Amurka.
15. Har ƙasar Sin can a Chana,
Ta
kai da yawa kushewa.
Ko
Farisa har Faransa,
Ba
kowa yau a titi.
16. Kufai a
kira yi Turai,
Champions League an tsaya cik.
17. Ba a yin zancen Ronaldo,
Har
Messi ba batunsa.
18. Ita
annobar Korona,
Cuta
ce babu shakka.
19. Ba ta
kunya ba ta tsoro,
Ba
ta sabo ba sanayya.
20. Yau mutum
ya gane cewa,
Bai
da ƙarfi sai na Allah.
21. Bai da
sauran duk dabara,
Kariyarsa
tana ga Rabbu.
22. Gatan kowa
Ilahu,
Mui
ta bauta mai da ɗa'a.
23. Ma
rabauata a yau da gobe,
Don
ko dai cutar Korona.
24. Wa'azi ce
babu shakka,
Me
je shi ke asara.
25. Kurciya in
ta yi kuka,
Saƙo nata ban da wawa,
26. Bare gaula
da soko.
Masu
shashanci a hanya.
27. Hankali
kura kira shi,
Ta
yin zabari na guga.
28. Mai rabo
shi ke rabauta,
In an wa'azi ya ɗauka.
29. Zunubansa ya nemi tuba,
Kan ya ji shi cikin kushewa.
30. Ni Khalid
bani shakka,
Tabbas
cutar Korona.
Jan
kunne ce gare mu.
Mu
bar saɓo da sharri.
31. Mu so
junanmu gaske,
Hakan
zai taimake mu.
32. Ni Imam
Khalid na Indo,
Jikan
Hauwa’u tabbas.
33. Na san
cutar Korona,
Ƙanwa ce gun talauci.
34. Wajen ƙeta da sharri,
Har
ma yawo a dangi.
35. Ni nan zan
sanya aya,
Cikin
waƙar Korana.
36. Allahu
kasa mu gane,
Mu tuba zuwa gare Ka.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.