Citation: Yakasai, M.G. (2024). Kunne Ya Girmi Kaka: Waiwayen Tarihi da Al’adun Jalla Babbar Hausa a Waƙar ALA ta Mashigan Kano. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 242-246.
www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.029.KUNNE YA GIRMI
KAKA: WAIWAYEN TARIHI DA AL’ADUN JALLA BABBAR HAUSA A WAƘAR ALA
TA MASHIGAN KANO
Murtala Garba
Yakasai
Sashen Koyar da
Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero Kano
Tsakure:
Daga tarihin harshe ne ake samun cikakken bayanin tarihin
al’ummar, da ta yi amfani da harshen a shekarun da suka gabata. Wannan tsari
yana tafiya ne a bisa doron adanawa a matsayin wata kafar kimiyyar harshe, ta
waiwayen abin da ya gabata. Saboda haka, ana amfani da harshe a matsayin wata
madogara ta adana tarihi da al’adun al’umma. . Wannan kafa ta fi maida hankali
ga samar da bayanan da suka keɓanta
ga ci gaban al’umma, wato bibiyar al’amuran da tarihi ya adana a lokaci da ya
gabata. Bugu da ƙari, wannan bayani ya ƙunshe al’adun al’umma
kamar yadda suka auku daga lokaci ko zamani zuwa wani. Ƙunshiyar wannan maƙala, tsokaci ne a kan tarihi da al’adun Jalla Babbar Hausa a
waƙar
Dakta Aminu Ladan Abubakar (ALA) ta Mashigan Kano. Domin cimma manufar wannan
maƙala,
an karkasa takardar zuwa gida biyar. Kashi na farko shimfiɗa ce, sai kuma taƙaitaccen
bayani a kan mawaƙin a kashi na biyu. Kashi na uku tsokaci ne a kan matsayin
harshe a waƙe,
a yayin da kashi na huɗu
ya kawo nazarin waƙar Mashigan Kano.
Fitilun Kalmomi: multi-word verbs, meanings,
undergraduate students, deficiencies
Gabatarwa
Tarihi ya tabbatar da irin
gudummawar da mawaƙa suke
bayarwa a wajen adana harshe da al’adu. Wannan ya nuna cewa, tun a wasu zamuna
da suka gabata, ana amfani da waƙa
domin wayar da kai da kuma ilimantar da al’umma. A matsayin mawaƙi na wanda aka aminta da cewa ya
naƙalci harshe, yana isar da saƙonsa
ta amfani da waƙa domin
ilimantarwa da kuma wayar da kan al’umma dangane da dukkan wani abu da zai
cutar da su. Saboda haka, mawaƙi
ƙwararren mutum ne da ya naƙalci harshe, kuma waƙoƙin da yake shiryawa suke da tasiri a zahirin rayuwa ta
duniyar da yake rayuwa (Woolger, 1978).
Ta ɗaya haujin kuma, waƙa
wata fasaha ce da take ɗamfare da zuciya domin gina
mutum da rayuwarsa. Tana ba da nishaɗi, kuma a ƙarshe ta zama jagora wajen faɗakarwa dangane da yadda za a gina al’umma gaba ɗaya. Kowace irin waƙa
tana da tasiri ga rayuwa ta hanyar nuni cikin nishaɗi, tamkar dai yadda masana falsafa suke faɗakar da al’umma.
Gaskiyar magana dai ita ce, tasirin waƙa
ya fi na ayyukan masana falsafa, musamman
idan aka yi la’akari da cewa, tana ba da gudummuwa wajen gina al’umma.
Waƙoƙi suna samar da muhimman tasire-tasire, kamar yadda masu ƙananan muhimmanci suke samar da ƙananan tasire-tasire a rayuwar
al’umma (Dennis, 1704).
A wannan gaɓa, kunne ya girmi kaka yana share fagen yin waiwayen tarihin
al’umma. Hususan dai, al’umma na tuna abubuwan da aka adana kuma masu
muhimmanci, daga nan kuma tarihin al’umma ya ginu. A wasu lokuta ma, waiwayen
al’amuran da suka gabata yana zama wata kafa ta ƙulla zumunta. Wato mutanen da suka rarrabu su suke haɗuwa a matsayin al’umma guda mai rayuwa a bisa doron harshe
da al’ada. Ƙunshiyar
wannan maƙala,
waiwaye ne na tarihi da al’adu na Jalla Babbar Hausa (Birinin Kano) a waƙar Dakta Aminu Ladan Abubakar
(ALA) ta Mashigan Kano. Sashe na farko shimfiɗa
ce, sai kuma taƙaitaccen
bayanin mawaƙi a sashe
na biyu. Sashe na uku tsokaci ne a kan matsayin harshe a waƙe, da kuma nazarin waƙar Mashigan Kano a sashe na huɗu.
Wane ne Aminu Ladan Abubakar (ALA)?
A lokuta da waƙoƙi daban-daban, Aminu Ladan Abubakar (wanda aka fi sani da
ALAN WAƘA), ya
bayyana tarihin rayuwarsa (Waƙar
CTV), ya kuma kawo bayanin yadda siffarsa take domin mutane su fahimta a cikin
sauƙi (Waƙar Sufiyanu Makaho). An haifi
Aminu Ladan Abubakar (ALA) a ranar 2nd ga watan Oktoban 1973 a Unguwar Yakasai
ta ƙaramar hukumar birni da kewaye.
Ya taso ne a hannun kakarsa da take zaune a Unguwar Ƙofar Wambai, sannan daga baya ya
koma wajen mahaifansa bayan sun koma Unguwar Tudun Murtala da zama. Kamar
kowane ɗan Musulmi, ALA ya taso a bisa
doron neman ilimi na Isilama da kuma na boko har matakin Difloma.
Laƙabin ALA haɗaka ce ta sunansa da na
mahaifinsa. A tsakanin kakanni da kuma iyayen ALA babu wanda ya gaji waƙa, to amma kuma ga duk masu
sauraron waƙoƙinsa za su tabbatar da yana da
waƙoƙi da yawa, kamar dai yadda yakan bayyana da kansa. A waƙarsa ta Alfiyya mai taken
SHAHARA, mawaƙin ya
kawo salsalarsa. Asalin mutum yana daga cikin ma’aunai da ke tabbatar da ƙima da martabarsa. Aminu ALA
yana da martaba a idanun mutane, kuma ga shi ɗan
sarauta ne. A buɗewar wasu ɗiyan waƙa,
mawaƙin yana cewa:
Godiya ga
Ubangijina da ya tsarma dare a rana,
Hikima ta
Ubangijina ta buwayi alam su zana,
Baiwarsa
Ubangijina ta wuce ƙalami su
tona,
Zan bayyana
ra’ayina ga batun rayuwa ta kaina,
Ɗan Malam Sani ALA Ladan baba a
guna,
Sani Ladan Habu ne
Abubakari kaka a guna,
Shi Bukari kuwa ɗa ne ga Mijinyawa bincikena,
Mijinyawa kure
Jarmai Baba a gun kakana,
Ɗan Sarki Dambuwa ne Gobir
Tsibiri garina,
Dambuwa
ɗa ne ga Gunke Gunkawa assalina.
Masarutar Bawa
Gwarzo ku ji salsalar ubana,
Sunana Al-Aminu da
shi aka raɗa suna,
Alhaji Ladan ubana
da Abubakari kakana,
Sunan da na sa wa
kaina Alan waƙar
yabona,
Saƙandamai na sunayena na cire ciki
laƙabina,
Asali na garin
ubana Jega Kebbi State garina,
Asali na garin
uwata Dabo ta Kano garina,
Gari kuwa na
haihuwata birni na Kano garina,
Shekarar ran
haihuwata ƙirgen
shari’ar Nabina,
Hijira ta alif dubu ɗaya da ɗari uku da ɗuguna.
Ma’anar manufar ɗuguna casa’in da huɗu nufina,
Ƙirge kuma na nasara 1973 ne,
A Municipal Kanawa
Yakasai garina,
Nan ne aka
haihuwata labarin assalina,
Nai ilimin
zamanina boko dan zamanina,
Gwargwado dai
Diploma nai domin kare kaina,
Nai kan Art &
Design ƙirƙirar zane fununa,
Duka dangogin
fasaha na fi ƙarfi
lamurana,
Nai rubutu na hikaya Fiction shi ne ƙarin bayana.
Matsayin Harshe a Waƙe
Tun a tsakiyar ƙarni na sha tara ne, masana masu
nazari da bincike a fannin kunne ya girmi kaka, suka tabbatar da cewa ana
amfani da harshe a waƙe
wajen adanawa da yaɗawa. Hanyar yaɗa bayanai ta kunne ya girmi kaka, tana da tasiri a kowane
zamani, saboda haka kiɗa da waƙa da labarai ana adana su a
tsawon zamani ba tare da sun kasance a rubuce ba (Rubin, 1995). Dalilin da ya
sa ake amfani da hikima ta kunne ya girmi kaka shi ne, hanyar tana wakiltar
wani muhimmin tsari ne na kimiyar harshe cikin yaɗawa
da adanawa, da za a iya waiwaya a kowane lokaci. Wato hanyar tana da tasiri mai
ɗorewa a rayuwar al’umma. Wani
tuntuɓe gushin gaba ma shi ne, ɗaiɗaikun mutane na iya waiwaye
domin tuna al’amuran da suka gabata a rayuwarsu a cikin ƙanƙanin lokaci.
Sakamakon nazarce-nazarce ya
bayyanar da cewa, hanyar kunne ya girmi kaka tana da matakai daban-daban da
suka ƙunshe ma’ana da kuma ƙa’idojin waƙa. Waɗannan ƙa’idoji
sun haɗa da hawa da sauka na murya da
karin sauti da tsawon wasali da ƙarfafawa
da suransu. Saboda haka, a fili take cewa, hanyar kunne ya girmi kaka tana
amfani da zubi da tsari na waƙa
domin samun sakamakon da ake bukata. Ta haka ne ake sarrafa harshe a waƙe a matsayin dabarun isar da saƙonni a waƙe. Bugu da ƙari, masana amfani da ra’o’i a
wannan hanya sun yi ittifaƙin
cewa waƙa ta
kasance hanya mafi inganci wajen adana bayanai. Amfani da harshe a waƙe na kuma ƙara taimakawa wajen tabbatar da ɗorewar ƙima da martabar al’umma a tsarin
zamantakewa. A wannan gaɓa ana iya cewa, amfani da wannan hanya (musamman sarrafa waƙoƙi), na taka muhimmiyar rawa a ƙasar Hausa.
Waƙar Mashigan Kano a faifan nazari
Masu hikimar magana suna cewa,
idan kana so ka zama bahari, to ka naƙalci
ƙa’idojin zubi da tsarin waƙa. Idan kuma kana son dacewa, to
ka bibiyi dokokin hawa da sauka na murya a cikin waƙa. A wannan gaɓar ne za mu bijiro da nazarin waƙar Mashigan Kano, domin ganin
yadda harshen waƙa yake
yin tasiri wajen riƙewa da
tunawa da kuma adana tarihi da al’adun al’ummar Jalla Babbar Hausa. Harshe a
matsayinsa na wata baiwa da take ɗamfare a tare da ɗan’Adam, ana amfani da shi domin sadarwa. Wato a tare da shi
akwai tasarrufi na sautuka a cikin tsari da kuma ma’ana. A gaskiya ma wani
tsari ne na alamomi da yake samar da dama ga majiya harshe su yi mu’amala mai
ma’ana (Yalwa, 2014). Saboda haka, da harshe ne ake samar da bayanan da ai’umma
take bukata domin sadarwa.
A zamanin mulkin mallaka, mawaƙan Hausa na wannan lokacin sun
fi maida hankali ga bayyana bukatun
mutane na samun ‘yancin mulkin kai. Da tafiya ta yi tafiya aka samu ‘yanci, sai
kuma mawaƙa suka
koma ga ƙalubalantar
juna cikin al’amuran tafiyar da mulki da ƙabilanci
da ɓangaranci da kuma gazawar
shugabanni wajen inganta rayuwar al’umma (Muhammad, 2014). Haka kuma waɗannan mawaƙan
na Hausa sun taɓo batutuwa irin na kunne ya
girmi kaka. A wannan sashen na wannan maƙala,
za a kawo bayanan yadda Aminu ALA ya ƙalubalanci
waɗansu halaye da tadojin al’umma
marasa kyau da kuma tasirinsu ga ci gaban al’ummar Hausawa (musamman a wannan
birni na Kano)
Ta ɗaya haujin kuma mawaƙin
ya faɗakar da al’umma muhimmancin
adana tarhin al’umma. Wannan waƙa
ta Mashigan Kano, an tanade ta ne domin bayyana hujjoji na tarihi dangane da
muhimman ƙofofin
birnin Kano da kuma dalilan samuwar su. A mabuɗin
waƙar, mawaƙin ya bayyana manufarsa ta
bayyana tsarin ƙofofin
birnin Kano na dauri (wato na gargajiya kamar yadda suke a zamanin iyaye da
kakanni). Ga abin da ya ce:
Rabbana ƙadiran Allah abin girmamawa,
Wanda ikonsa ne na
buɗe bakin ga nawa,
Nai nufin ambato
abubuwan kambamawa,
Tarihin Kano jaha abar
girmamawa.
Mawaƙin ya jaddada manufarsa da cewa
abin da zai gabatar na al’ummar mutanen Kano, ya aza shi ne a bisa doron tarihi
musamman domin adanawa da kaucewa salwanta. Tuni dai an lura cewa an yi watsi
da waɗannan abubuwa na tarihin
al’ummar Kano. Ganuwar Kano da ta kewaye cikin birnin, ta daɗe tun wasu zamunna da suka wuce. Saboda haka, sai ya tunasar
da al’umma cewa babu wani ci gaba da ya wuce na tafiya tare da abubuwan
tarihinmu. A ta bakin mawaƙin
yana cewa:
Zan batu kan
ababen Kanawa,
Wasu an banzatar
wasu an bi an adanawa,
Mai yiwa yin hakan
zai tinzirar da Kanawa,
A gurin kariya da
abin da zan ambatowa.
Farko ganuwa ta
Kano da ta kekewayewa,
Wacce tau wanzu
tun zamanin Annabawa,
Hikimar Farisi
Salmanu ɗan Farisawa,
Mutanen Kano muna
ta rurrugujewa.
Wasu na iƙirarin zamani ya sauyawa,
Wai sun ci gaba
kawunansu ya zam wayewa,
Ni kuwa sai na ce
tuna baya shi ne yabawa,
Tozartar da tarihi ya zai zam
wayewa.
Aminu ALA ya nuna takaicinsa
dangane da tasirin lalacewa da kuma salwantar ganuwar birnin Kano. A wannan waƙa, ya bayyana yanayin da abin
kaico, sannan ya nemi gwamnati da ta ɗauki matakai na gaggawa wajen
magance taɓarɓarewar
abubuwan tarihi. Ya ƙara da
cewa, tunda waɗannan abubuwa na tarihi suna
fuskantar barazana, to ya zamo wajibi a kare tadoji da al’adun mutanen Kano. Ga
yadda ya bayyana ɓacin ransa:
Wai ina gwamnati
tarihi zai gushewa,
Martabobinmu ne fa
ake ta ballagazawa,
Tarihinmu Sarki
amma fa ya zam gushewa,
Mu ne kariya ga martabobin
Kanawa.
A ra’ayin Abdulƙadir (1975), baya ga bayar da
nishaɗi ga al’umma, mawaƙi yana kuma faɗakar da al’umma dangane da abubuwan da ke faruwa a yanzu da
kuma al’amura na tarihin dauri. Ta haka ne yake ilimantar da matasa dangane da
al’adu da tadoji da tarihi da kuma hikimomin magabata. Daga bayanan da suka
gabata da kuma ƙunshiyar
waƙar, mawaƙin ya kambama waɗannan ƙofofi
na birnin Kano, musamman ma waɗanda suke a kewaye da ganuwar
birnin Kano. A nazarin mawaƙin,
Allah ya albarkaci Kano da muhimman abubuwa. Ga abin da ya ce:
Sarkin Kano
Gijimasu sarkin Kanawa,
Shi ne sila da ya
fara ƙaƙƙarowa,
Ƙofofi goma guda huɗu ka zam daɗawa,
Tafiyarsa Rumfa ya
maye gurbi Kanawa.
Shi ne ya rushe
guda takwas ba daɗawa,
Ya ƙara nasa guda huɗu a kai sanarwa,
Kafin zuwan Bayero
sha ukkun sun cikewa,
Ya ida sha shida
wanda zan bayyanawa.
Gado-ƙaya wani malami ne Kanawa,
Mai taƙƙawa zuhudu abin ba shi faɗuwa,
Sam ba shi bacci
bisa abin shimfiɗawa,
Shi ne ya furta gado ƙaya ba musawa.
A ci gaba da waiwayen tarihi
kamar yadda ya danganci ƙofofin
Kano, baitoci sha ɗaya zuwa na sha uku sun bayyana
musabbabin samuwar ƙofofin
Dukawuya da Ƙofar-ruwa.
Wannan waƙa tana da
muhimmanci wajen adana abubuwa na kunne ya girmi kaka. A wurare daban-daban ALA
ya bayyana sunayen sarakunan da suka yi mulki da ushen zuriyarsu. Ta haka ne
masu sauraronsa za su san adadin sarakuna da kuma yadda suka yi mulki ɗaya bayan ɗaya. Haka kuma al’umma za ta san
waɗannan ƙofofi da kuma dalilan samuwarsu
da kuma wuri ko bagiren da suke, kamar yadda ya bayyana a waɗannan baitoci:
Dukawuya suna ne
ba musawa,
Na wani sadaukin
jarumi mara ƙwawa,
Gidansa anka biɗa ya ce ba shi baiwa,
Sarki ya zo da ƙafarsa don faɗɗakarwa.
Ya ce da bawan nan
ni na izo fadawa,
Gidanka za ai maka
wani abin yabawa,
Sannan fa ƙofar sunansa za a sawa,
Kun ɗan ji tarihi gwanin armasawa.
Ƙofar-ruwa da ake faɗi kun ji Kanawa,
Sunan ɗiyar sarkin Kano ce Kanawa,
Sunanta Lunƙui babu ja ba musawa,
Shi ne fa sunan ƙofar tunda daɗewa.
Ƙofofi na gaba su ne waɗanda suka haɗa Mazugal da Ƙofar Wambai da Ƙofar Fagge. Irin abin da ya faru
ga Ƙofar-ruwa shi ne ya faru ga Ƙofar Mazugal, musamman ma da
yake ƙofar ta samu sunanta ne daga
sunan ɗiyar sarkin Kano. Ga abin da ya
ce:
Ƙofar Mazugal ma disem ‘yan
Kanawa,
Sunan ɗiyar sarkin Kano ce ‘yar baiwa,
Jika gurin
Suntilma mai martabawa,
Shi ne fa sunan ƙofar da daɗewa.
Ƙofa ta Wambai zan faɗo don sanarwa,
Ƙofar Daggaci da ake ambatawa,
Sarki uban Abdu
Rumfa nak Kanawa,
Shi yai naɗin Wamban da ba tumɓukewa.
Ƙofar Fagge da a yanzu aka tumɓukewa,
Ƙofa ta mata da haka ake sanarwa,
Wani hatsabibi na
mata kira shi wawa,
Shi ne dalili ko akwai mai
musawa.
Babu shakka martabar al’umma
tana ƙunshe ne a cikin tarihi da
al’adunta, wato zubi da tsarin zamantakewar rayuwarsu. Wannan shi ya ƙara jaddada muhimmancin
gudummawar waɗannan ƙofofi a bisa doron tarihin
al’umma
A baitoci na gaba, mawaƙin ya bayyana sauran ƙofofin da suka haɗa da Nasarawa da Agundi da Waika da Nadilƙe da Na’isa. Mawaƙin ya bayyana yanayi da taɓarɓarewar rayuwar al’umma a
sanadiyar irin salon mulkin Turawa. Ga misali, kirari irin su Nasara mai idon Kyanwa da Azzalumai masu halin ɓatarwa duk suna bayyana ruɗani da matsananciyar wahalar da al’umma suka fuskanta.Wato
su ne masu mulkin mallaka da ya kai al’umma ga taɓewa.
Ga abin da mawaƙin ya ce:
Ke Nassarawa abu
abin ƙayatarwa,
Ita ce ƙofa ta Nasara mai idon kyanwa,
Sunansa ne aka sa
wa ƙofar Kanawa,
Azzalumai masu
halin ɓatarwa.
Agundi sunan wata ɗiyar Maguzawa,
Wacce dalilin ɗanta ne anka sa wa,
Ƙofar fa suna Ɗan-Agundin Kanawa,
Shi ke tsaron ƙofar gari ‘yan Kanawa.
Ƙofa ta Waika ba abin rikitarwa,
Wani ɗan’Adam ne mai kashi da tsarewa,
Sunansa ne aka bai
wa ƙofar Kanawa,
Saura kaɗan sha shida in zam kammalawa.
A cikin baitocin ƙarshe, mawaƙin ya bayyana ƙofofin Nadilƙe da Dawanau. Ita Nadailƙe sabuwa ce kuma an yi ta ne
domin ɗalibai, a yayin da ƙofar Famfo aka yi ta domin
samuwar ruwa. Ƙofar
Dawanau ita ce cikon ta ƙarshe,
kamar yadda mawaƙin ya
tsaro a waɗannan baitoci:
Ƙofar Nadilƙe da ta zam ana cewa sabuwa,
Don ɗalibai aka yi ta don sauƙaƙawa,
Ƙofa ta Famfo kuma dalilin zuwan
ruwa,
Sauran Dawanau
Na’isa in kammalawa,
Ƙofar Dawanau asalinta Kanawa,
Maje Karofi da
Abdullahin Sikawa,
Kullum idan ya
rako mahaɗa ta rabuwa,
Zai ce a nan Malam
mu ɗan dawayawa.
Wasu sunka ce
Bafulatani ne Kanawa,
Ya taho da garken
shanu wai zai wucewa,
Sarki na ƙofa ya hana musu wucewa,
Da yai fushi yai
wa kansa hanyar wucewa,
Sarki Sulaimanu ya
aika ya zuwa,
Yat tambaye shi
dalilin ruggujewa,
Wai sai ya ce
Sarki isa ce ta sawa,
Daga nan akai masa lamunin
tabbatarwa.
Naɗewa
Abin da ya gabata tsokaci ne a
kan muhimmancin waƙoƙi da kuma tasirinsu, kamar yadda
ya bayyana a rayuwa da al’adun Hausawa. Harshe da tarihin al’umma tamkar jini
da tsoka suke, wato suna da alaƙa
makusanciya ta yadda ba za a iya raba su ba. Dalili kuwa shi ne, daga tarihin
harshen kowace al’umma ne ake samun tarihin al’ummar da suka yi amfani da
wannan harshen a zamunna da suka gabata. A taƙaice, ana amfani da harshe wajen adana dukkan abin da ya
gabata, kamar dai yadda ya bayyana a waƙar
Aminu ALA ta Mashigan Kano. Haka kuma harshe a waƙe yana bayyana alaƙar
harshe da waƙa cikin
kunne ya girmi kaka. Maƙalar
ta kuma kawo yadda aka sarrafa harshe a cikin waƙar, ta hanyar adanawa da tunawa da musanya abin da ya shafi tarihin al’umma. Wato wannan
waƙa ta Mashigan Kano, ta kuma fito
da aikin harshe a cikin zamantakewar al’umma.
Manazarta
Abdulƙadir, D. (1975). “The Role of an
Oral Poet in Hausa/Fulani Society”, Unpublished PhD Thesis, Bloomington &
Indiana University.
Abubakar, A. L. (2015). SHAHARA:
Alfiyar Alan Waƙa
(Shahara Sanadin Sanina), Kano: Taskar Ala Global Ltd
Barista, M. L. (2011). Waƙoƙin Aminu Ladan Abubakar (Alan Waƙa), Vol. 1 Kano: Iya Ruwa
Publishers.
Dennis, K. (1704). Available at
Literature of the 20th Centuryto the present (2008) “English
Literature”, Microsoft R. Encarta R. (DVD) Redmond WA, Microsoft Corporation.
Muhammad, A. (2014). “Nigerian
Poetry and Women Consciousness: A Study of Three Nigerian Poets” In JALAL,
Journal of Language and Literatures, Vol.5, No. 1
Rasheed, A. & S. A. Aliyu
(2014). Current Perspectives on African Folklore: A Festschrift for Professor Ɗadatti Abdulƙair, Zaria: ABU Press.
Rubin, D. C. (1995). Memory in
Oral Tradition: The Cognitive Psychology of Epic, Ballads and Counting out
rhymes, New York, OUP.
Woolger, D. & Ogungbeson, K.
(1978). Images and Impressions: An Oxford Senior Poetry Course, Oxford
University Press.
Yakasai, S. A. (2014). “Some
Major Themes in Hausa Responsorial Songs in Aminu Ala’S Performance” In Current
Perspectives on African Folklore, A Festschrift fo Professor Ɗandatti Abdulƙadir, Zaria: ABU Press
Yakasai, S. A. (2014). “Nazarin
Harshen Farfaganda Cikin Siyasar Kudanci da Arewacin Nijeriya a Waƙar ALA ta Rajista” In Garkuwan
Adabin Hausa: A Festschrift in Tribute to Abdulƙadir Ɗangambo,
S. M. Gusau (ed) Zaria: ABU Press
Yakasai, S. A. Jagoran Ilimin Walwalar Harshe, Sokoto: GARKUWA Media Services.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.