Ticker

6/recent/ticker-posts

Homa Ko’ina Da Ruwanku: Laluben Sarkanci a Cikin Wakokin Fada Na Makada Sa’idu Faru

Citation: Gummi, M.F. & Sarkin Gulbi, A. (2024). Homa Ko’ina Da Ruwanku: Laluben Sarkanci a Cikin Waƙoƙin Fada Na Makaɗa Sa’idu Faru. Four Decades of Hausa Royal Songs: Proceedings from the International Conference on the Life and Songs of Makaɗa Sa'idu Faru, 3(3), 82-91. www.doi.org/10.36349/tjllc.2024.v03i03.011.

HOMA KO’INA DA RUWANKU: LALUBEN SARKANCI A CIKIN WAƘOƘIN FADA NA MAKAƊA SA’IDU FARU

Na

Musa Fadama Gummi Ph.D
Sashen Harsuna da Al’adu
Jami’ar Tarayya Gusau, Jihar Zamfara, Nijeriya
Email: gfmusa24@gmail.com, mfadamagummi@fugusau.edu.ng
GSM NO.: +2347065635983 

Da

Abdullahi Sarkin Gulbi Ph.D
Sashen Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu
Ɗanfodiyo Sokoto, Nijeriya
sgulbi@gmail.com, gulbi_abdullahi@udusok.edu.ng
GSM NO. +2348089949294

Tsakure

Sarkanci muhimmiyar sana’ar gargajiya ce. Irin ayyukan da masu aiwatar da sana’ar suke yi a cikin al’umma, sun haɗa da samar da kifi, wata halitta da ke ƙunshe da sanadarai masu inganta jiki da ƙara masa lafiya sannan ga gudunmuwar da suke bayarwa a fagen kiwon lafiya na gargajiya a al’ummar Hausawa. Waƙoƙin sarauta ko waƙoƙin fada, waƙoƙi ne da mawaƙan Hausa suke rerawa tare da kiɗa domin yabo da gwarzanta sarakunan ƙasar Hausa da nufin ƙwarzanta su da nishaɗantar da su tare kuma da yaɗa martaba da muhibbarsu ga duniyar Hausawa masu saurare da sha’awar waƙoƙin baka. Babban aikin Sarakuna shi ne mulki da jagorancin al’umma tare da ba su kariya da yi masu adalci. Aiwatar da sana’o’in gargajiya aiki ne da ya rataya a wuyan talakawa, amma duk da haka a cikin waƙoƙin sarauta na Hausa, ana samun jirwaye na wasu muhimman sanaoin gargajiya a cikin kalaman azanci a waƙoƙin makaɗan fada, ciki kuwa har da makaɗa Sa’idu Faru. Adabi madubi ne na rayuwar al’umma don haka ba abin mamaki ba ne idan waƙoƙin fada sun ƙunshi lamurran aladu na rayuwar al’umma. Ƙudurin wannan muƙala shi ne yin nazari a cikin waƙoƙin fada na makaɗa Sa’idu Faru da nufin zaƙulo lamuran da suka jiɓinci sarkanci ko kamun kifi a cikinsu. An tattaro waƙoƙin fada na makaɗa Sa’idu Faru da dama domin sauraron su a natse ta yadda za a fito da turaku daban-daban da suka danganci sana’ar sarkanci. Muƙalar ta gano dalilan da suke sa makaɗan fada saka lamarin sarkanci a cikin wasu waƙoƙinsu. Daga ciki akwai samun damar yin zambo da shaguɓe ga ‘ya’yan sarauta, tun ma ba a ce masu adawa da sarki ba. Haka ana saka batu da ya jiɓinci sarkanci domin a nuna alhairi da sarautar wanda ake wasawa ta haifar ga al’ummar da yake jagoranta, da sauran abubuwa makamantan waɗannan.

Fitattun Kalmomi: Homa, Lalube, Sarkanci, Waƙoƙi, Fada.

1.0 Gabatarwa

Sarauta tsari ne na shugabanci irin na gargajiya a Bahaushiyar al’ada kuma ko da iska ta zo, ta tarar da kaba tana kaɗawa. Tsarin sarauta a al’adar Bahaushe abu ne daɗaɗɗe wanda Hausawa ba aro shi suka yi ba daga kowace al’umma. Ko da Larabawa da Turawan Mishan da ‘yan mulkin mallaka suka kutso kai ƙasar Hausa, sun tarar da alummar Hausawa suna da tsarin shugabancinsu da ya dace da muhallinsu da al’adunsu. A ƙasar Hausa, Allah mai iko da buwaya ya hore wa wasu mutane basira da zalaƙa da fikira ta tsara daɗaɗan kalamai da ake iya rerawa cikin murya mai zaƙi da armashi tare da jan hankali; wadda kuma akan gwama ta da kiɗa ko busa ta yadda za a sami wani amo da sautinsa zai tafi bai ɗaya da abin da baki yake rerawa. Waƙar baka ta Hausa aba ce mai muhimmancin gaske a fagen ba da nishaɗi da isar da saƙo da adana tarihi da al’adu na al’ummar Hausawa. Daga cikin mutanen da Allah ya yassare wa hikimar tsara waƙa, akwai waɗanda suka duƙufa wajen yi wa shugabanni musamman sarakuna waƙoƙi domin nishaɗantar da su da yaba masu domin ƙara masu ƙwarin guiwa kan ɗorewa da aikata ayyuka na alheri da suke yi wa talakawansu na yi masu adalci da jagoranci na gari. Yayin da waɗannan makaɗa suke tsara waƙoƙin nasu, sukan saka batutuwa da dama waɗanda suke saƙa turke da salo na waƙar da kuma warware turken.

Daga cikin irin waɗannan batutuwa da makaɗan fada suke sakawa a waƙoƙin nasu domin fayyace ko warware turke ko turakun da suka gina waƙoƙinsu, akwai batun da ya jiɓinci sarkanci ko kamun kifi. Duk da cewa sarakuna a ƙasar Hausa suna da wani matsayi maɗaukaki da bisa al’ada yakan hana su aiwatar da wasu sana’o’i masu wahalar gaske waɗanda galibi talakawa aka sani da su. Sarkanaci ko kamun kifi yana ɗaya daga cikin ire-iren waɗannan sana’o’i da idan har aka ga basarake yana aiwatar da su to kuwa yakan zama abin zargi da ka iya janyo masa zambo daga maroƙa ko makaɗan masarauta. Wannan yana nuni da cewa makaɗan fada suna saka zantuka da suka jiɓinci lamarin sarkanci ko kamun kifi a cikin waƙoƙinsu na fada domin wasu dalilai. Makaɗa Sa’idu Faru kasancewarsa fasihi wanda ya naƙalci harshen Hausa sosai, ba a baya yake ba wajen irin wannan ƙoƙari na amfani da sarkanci a cikin waƙoƙinsa na fada, waɗanda su ne mafi rinjaye sosai a ɗaukacin waƙoƙinsa. Ƙudurin wannan muƙala ne ta bijiro da dalilan da suka sanya makaɗan fada suke amfani da lamarin sarkanci a cikin waƙoƙinsu.

2.0 Ma’anonin Tubulan Take.

Taken wannan muƙala an gina shi ne ta hanyar amfani da wasu kalmomi muhimmai kuma fiatattu, waɗanda su ne tubula. Kalmomin su ne homa da sarkanci da waƙoƙin fada. Waɗannan kalmomi ne ake son a bayyana ma’anoninsu ɗaya bayan ɗaya a nan.

2.1 Homa (Koma)

Ƙamusun Hausa na jami’ar Bayero, (CNHN:2016) ya faɗa cewa homa/koma raga ce da ake saƙawa da zare a ɗaura itace, a yi amfani da ita wajen kamun kifi. Wato raga ce ta kamun kifi wadda ake ɗaurawa a jikin wasu lanƙwasassun itatuwa waɗanda su ne ake riƙawa a hannu biyu yayin da ake kamun kifi. Masuntan da suke amfani da irin wannan kaya wajen kamun kifi sukan sami shugaba wanda ake kira Homa. Wannan yana nufin ko baya ga kasancewar homa kaya na kamun kifi, kalmar tana kuma kasancewa sunan da ake kiran shugaban duk masunta da suke amfani da irin wannan raga wajen kamun kifi (Fadama, 2016:439). Yadda aka yi amfani da kalmar a taken wannan muƙala, tana ɗaukar ma’ana ta biyu, wato sarautar da akan naɗa wa shugaban masu kamun kifi waɗanda suke amfani da homa/koma a matsayin kayan aiki.

2.2 Lalube

Lalube kalma ce ta Hausa wadda take nufin bincika wani abu da hannu a cikin duhu (CNHN, 2006:300). Baya ga wannan gundarin ma’ana da Ƙamusun Jamiar Bayero ya kawo, kalmar lalube kalma ce ta fannu da ake amfani da ita a sha’anin sarkanci ko kamun kifi. Dabara ce ta kamun kifi wadda yayin aiwatar da ita ake shiga ruwa domin kama kifi ta amfani da hannu kawai. Masunci kan shiga ruwa da nufin kama kifi ta amfani da hannayensa biyu. Zai riƙa tattaɓa ƙasan ruwan da niyar ya yi gamon-katar na kama kifi da hannu. A wannan muƙala, lalube na nufin yin nutso cikin tarin waƙoƙin fada na makaɗa Sa’idu Faru da nufin nemo ko gano ko zaƙulo wuraren da aka yi amfani da shaanin sarkanci ko kamun kifi a cikin waƙoƙin.

2.3 Sarkanci

Asalin kalmar sarkanci ba Bahaushiya ba ce. An samo ta ne daga kalamar ‘Sorko’ wata al’umma da take cikin tsohuwar daular Sanwai (Songhai). Al’ummar Sorko ta shahara matuƙa a fannin kamun kifi da fito a kogin nan na Kwara wato River Niger, da kuma fadamun da suke raɓe da shi. Kogin ya ratso cikin ƙasashen Afrika da dama kafin ya shigo Nijeriya a ƙauyen Bahindi ta ƙaramar hukumar mulkin Bagudo a jihar Kebbi. Domin faɗaɗa wurin aiwatar da sana’arsu, al’ummar ‘Sorko’ sun yi ƙaura zuwa cikin ƙasar Kabi wadda a wancan lokaci take wani yanki da ke ƙarƙashin daular Sanwai. Masana tarihi sun tabbatar da cewa waɗannan mutane na ‘sorko’, sannu a hankali sun saje da masu masaukinsu ta hanyar auratayya sakamakon karɓuwa da suka samu a yankin Kabi. Shigar ‘Sorko’ a Kabi ta yi tasirin gaske a lamarin kamun kifi ba yankin kaɗai ba, har ma ɗaukacin ƙasar Hausa. Wannan ya faru ne sakamakon ƙwarewarsu ga sha’anin kamun kifi, da kuma ingantattun kayayyakin kamun kifi da suka zo da su. Tun a wannan lokaci, sai aka riƙa kiran duk wani ƙwararren masunci tilo da suna ‘Basarke’, jam’i kuwa ‘Sarkawa’ yayin da sana’ar aka riƙa kiran ta da suna Sarkanci’. Ma’anar kalmar ita ce ƙwarewa a sanaar kamun kifi da laƙantar lamarin ruwa da fito a kogi da kuma farautar dabbobin ruwa kamar ayu da kada da dorina da karen ruwa da dai sauran su. Yakan haɗa har da sanin asiran ruwa da sanin magungunan cututukan da sanyi kan haifar.

2.4 Waƙoƙin Fada

Waƙar baka bisa ma’ana magana ce ta hikima da akan tsara ta cikin azanci ta amfani da zaɓaɓɓun kalmomi kuma zaunannu waɗanda akan rera da wata murya mai rauji da daɗin sauraro da wani lokaci akan gwama da kiɗa da amshi. Yahya, (1997:58) ya faɗa cewa waƙoƙin sarauta waƙoƙi ne da ake yi wa sarakuna da masu jinin sarauta. Sarauta ta haɗa da Sarki da hakimi da waziri da ɗangaladima da duk wanda sarki kan naɗa domin taimaka masa gudanar da lamarin mulki a farfajiyar ikonsa. A can da akwai wasu rukuni na mawaƙan baka da ba sa yi wa kowa waƙa sai wanda ya jiɓinci sarauta. Waƙoƙin da aka rera domin Sarki ko wani mai alaƙa da fada su ake kira waƙoƙin sarauta ko waƙoƙin fada. Makaɗa Sa’idu Faru wani babban misali ne na makaɗan fada kasancewarsa ba ya yi wa talaka waƙa duk kuwa yawan ƙasurarsa ko yawan dukiyarsa.

3.0 Taƙaitaccen tarihin Makaɗa Sa’idu Faru

Allah a cikin ikonsa da buwayarsa ya rayar da wasu mashahuran mawaƙan ƙasar Hausa a yankin Zamfara. Makaɗa Sa’idu Faru yana ɗaya daga cikin waɗannan mawaƙa na ƙasar Hausa da suka rayu a farfajiyar yankin Zamfara na ƙasar Hausa. Akwai saɓanin ra’ayi dangane da shekarar haihuwar wannan mashahuri kuma haziƙin mawaƙi. A wani ƙauli, ana ganin cewa an haifi makaɗa Sa’idu Faru a garin Faru na gundumar Faru a ƙaramar hukumar mulkin Maradun ta jihar Zamfara a cikin shekara ta 1932 (Gusau, 1996:117). A wani ƙauli kuwa, ana kyautata fahimta cewa an haifi Saidu Faru ne a shekara ta 1916[1]. Sunan mahaifin Sa’idu Faru shi ne Makaɗa Abubakar wanda mutumin Faru ne ta ƙasar Maradun. Mahaifiyarsa kuwa, mutumniyar Banga ce ta ƙaramar hukumar mulki ta Ƙauran Namoda a jihar Zamfara. Makaɗin ya yi rayuwarsa ta ƙuruciya a garin mahaifiyarsa wato Banga. Da ya tasa, sai makaɗa Sa’idu Faru ya koma Faru wurin iyayensa.

Makaɗa Sa’idu Faru ya yi biyar mahaifinsa a wajen yawon waƙa. Wannan ne ya ba shi damar koyon kiɗa da waƙa a wajen mahaifin nasa, Makaɗa Abubakar. Sa’idu Faru bai fara cin gashin kansa a sha’anin kiɗa da waƙa ba sai bayan da Allah ya yi wa mahaifinsa rasuwa. A wannan lokaci ne Sa’idu ya maye gurbin mahaifin nasa a matsayin jagora na tawagarsu ta waƙa. A cewar Gusau, (1996: 119), waƙarsa ta farko da ya yi bayan samun cin gashin kansa ita ce wadda ya yi wa Sarkin Yamman Faru Ibrahim wadda gindinta shi ne:

Gindin Waƙa: Bi da maza ɗan Joɗi na Rwafi

Iro magajin Shehu da Bello

 

Hasken hitila ba ɗai da wata ba

Tauraro haskenka subahin

 

Dawaya kora ɗimau na Wakili

Uban Sarkin Zagi Bello da Yari

Ruwa da kada ɗibgau na Magaji

Sai tsohon wawa ka shigas su.

(Gusau, 1996:119)

Makaɗa Sa’idu Faru mashahurin makaɗin fada ne da ba ya yi wa kowa waƙa face sarakuna da masu alaƙa da sarauta kamar Yangaladimomi da masu riƙe da muƙaman gargajiya. Wannan ya fito ƙarara a cikin wani ɗan waƙa tasa da ya yi wa Sarkin Sudan na Wurno, Alhaji Shehu Malami inda yake cewa:

Gindin Waƙa: Muzakkarin Sarki ɗan Abdu,

Abin biya Shehu na Ali.

 

Jagora: Ɗan talakka komi yac cika huska, x2

‘Y/Amshi: Sa’idu ni ba ni kiɗa mai. x2

Jagora: Ɗan talakka komi ya aje ƙarhe,

‘Y/Amshi: Sa’idu ni ba ni kiɗa mai.

 

Makaɗa Sa’idu Faru ya faɗa a wani ɗa na waƙar da ya yi wa Turakin Kano, Alhaji Ahmadu cewa idan dai waƙar fada ce, kowace aka ji ko saurara koma bayan tasa ce domin kuwa su suka iya ta. Ɗan waƙar na cewa:

Gindin Waƙa: Tsakin tama na Abashe,

Ana shakkar haye ma Amadu,

Mai daraja na Wambai,

Ɗan Hashim ƙanen Sarkin Kano.

 

Jagora: Sa’idu Faru ka waƙa iko,

‘Y/Amshi: Komi kaj jiya ƙarya akai,

Jagora: Sa’idu ka waƙam mulki,

‘Y/Amshi: Komi kaj jiya ƙarya akai.

(Gusau, 2009:162)

 

A tsawon rayuwarsa, Sa’idu Faru ya yi wa manya da ƙananan sarakuna da hakimai (Iyayen ƙasa) daban-daban daɗaɗan waƙoƙi masu ratsa zukata, waɗanda suke cike da hikima da basira da zalaƙa.

Duk da kasancewa Makaɗa Sa’idu Faru ya yi wa sarakuna da dama waƙoƙi daban-daban, Magirma Sarkin Kudun Sakkwato, Alhaji Muhammadu Macciɗo ɗan Sarkin Musulmi Abubakar na III (Allah ya lulluɓe su da rahama) shi ne ubangidansa. Tabbacin haka ya bijiro a wani ɗan waƙa tasa da ke cewa:

Gindn Waƙa: Farin cikin Musulmin duniya,

Mai martaba na Abubakar,

Ci fansa Alhaji Macciɗo.

 

Jagora: Ban wuce gonata da irina ba, x2

‘Y/Amshi: Inda Sarkin Kudu nits tsaya.x2

Makaɗa Sa’idu Faru makaɗi ne da ya rabauta da baiwa ta naƙaltar harshen Hausa sosai. Yana da yaransa da suke taimaka masa wajen amshin waƙa da yi masa ƙari da tarbe. Yaransa su ne:

i. Mu’azu Daudun kiɗa (ƙanen Saidu)

ii. Ɗandaudu

iii. Ali

Allah mai iko da buwaya ya ƙarɓi rayuwar Makaɗa Sa’idu Faru gabanin maigidansa Sarkin Kudun Sakkwato, Alhaji Muhammadu Macciɗo ya hau karagar mulki ta Sarkin Musulmi. Sa’idu ya bar duniya ne a shekara ta 1987. Ya rayu tsawon shekaru 71.

4.0 Karatun Sarkanci A Bakin Sa’idu Faru

Yanzu muƙalar za ta yi nitso cikin waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru domin lalubo yadda malamin waƙa mai kwana ɗumi na Mamman na Balaraba ya kawo lamarin sarkanci a cikin waƙoƙinsa. Za a rarraba zantukan na sarkanci kamar yadda makaɗin ya kawo a saka su rukuni-rukuni kamar muhallin sarkanci, dabarun sarkanci kayan aikin sarkanci da dai sauransu.

4.1 Muhallin Sarkanci

Sarkanci kamar yadda aka bayyana baya kaɗan, sana’a ce da ta jiɓinci shiga ruwa domin a kama kifi. Kifi kuwa ba ya da wani muhalli da ya wuce ruwa. Nan marayarsa take don haka a nan ake kambaɗarsa. Ruwa, marayar kifi kan haɗa da na gulbi da tafki da ƙoramu da fadamu da madatsun ruwa. Yanzu bari a bibiyi waƙoƙin a ga yadda ya saka waɗannan muhallai na kifi a cikin waƙoƙinsa sannan a zaƙulo hikimar amfani da kowane muhalli da aka kawo.

4.1.1 Gulbi

Gulbi na nufin ƙaramin kogi. Ƙarancin kuwa ta fuskar yawan tazarar wuraren da ruwansa ya ratsa ne. Tazarar da ruwan kogi ya ratsa ya fi na gulbi tsayi sosai. Ƙoramu ne da rafuka ko gebe suke kwaso ruwa su zuba shi a gulbi. Gulbi kuwa yakan malala ruwan da ya kwaso ne a cikin kogi. Wani lokaci idan aka yi mamakon ruwan sama, gulbi kan cika da ruwa ta yadda ruwan kan rinjayi gaɓar gulbin don haka sai ruwan ya malala a karkara musamman fadama. Irin wannan yanayi alheri ne sosai ga masunta da ma manoma. Yanayi ne da yake wanzar da bazuwar kifi zuwa tafkuna da nufin hayayyfa. A irin wannan yanayi ne ake samun kifi ya yi gala, wato ya fito daga wani ruwa zuwa wani ko da kuwa zai biyo ta taɓo ne. Da haka sai masunta su riƙa kama kifin a kan tudu, cikin sauƙi. Wannan yanayi wani lokaci makaɗa Sa’idu yake ambato a wasu waƙoƙinsa. A wani ɗa na waƙar da ya yi wa ubangidansa Sarkin Kudun Sakkwato, Alhaji Muhammadu Macciɗo, Sa’idu yana cewa:

Gindin Waƙa: Ya yi Sarki daidai wa da mai yanzu yar riƙa,

Alhaji Macciɗo jikan Mamman mai dubun bara

 

Jagora: Gulbi ya ba da ruwa,

Hwadama dut ta shahe.

‘Y/Amshi: Masu hito has sun hwara hwaɗin,

Yanzu tai yi kai.

A nan Makaɗa Sa’idu ya kawo zancen gulbi da yadda idan ya cika ya tumbatsa ruwansa yakan malala a cikin fadama. Irin wannan yanayi yana faranta wa masunta da manoma shinkafa rayuwa domin irin tarin arzikin da za a iya samu ta fuskar adadin kifin da za a iya kamawa, wani lokaci cikin sauƙi idan kifi ya yi gala; da kuma yadda shinkafa za ta sami wadataccen ruwa har ya zuwa lokacin da ta isa yanka. Masu fito da jiragen ruwa za su sami aiki na ƙetarar da mutane da kaya daga wannan tsallake zuwa wancan. Wannan a fakaice yana nufin naɗa Muhammadu Macciɗo kan karagar Sarkin Kudun Sakkwato ya zama alheri ga al’umma ta hanyar samar da buɗuwar arziki ga talakawa ta yadda aka sami wanzaruwar yalwa da wadata da buɗi na taskokin arziki ta fuskar bunƙasar tattalin arziki da walwala ga jama’a.

Ba a wannan waƙa kaɗai Makaɗa Sa’idu ya kawo zancen gulbi ba. A waƙar Sarkin Ƙayan Maradun Tambari, akwai irin wannan daidai wani ɗan waƙa da ke cewa:

Gindin Waƙa: Wada kab bi da maza,

Na za ka gaishe ka da ƙwazo,

Bajimin Bello na Attahiru Sarkin riƙa taro.

 

Jagora: Gulbi ya ɓaɓɓako ruwa da yawa,

Ya taushe hwadammu,

Duk an ɗaure jirage,

‘Y/Amshi: Jama’a tsugunne ikon Allah ɗai suka dibi,

Ba mai hwara shiga ciki, x2

Mai ƙarhi aka tsoro. x2

 

Makaɗa Sa’idu ya shigo da lamarin sarkanci a cikin wannan waƙa ta fada, musamman yanayin muhallin kamun kifi domin ya kwatanta shi da irin yadda idan sarauta ta faɗi ba kowane ɗan Sarki yake iya kutsawa wajen neman ta ba, sai mai ƙarfi da kuma muruwa. Ga sarauta ta faɗi amma magadanta sun yi jangwam kowa ya kasa kutsawa wajen nema domin shakku da tsoro. Yadda ruwa yake da barkwanci, ko sarauta ta gaji hakan. Ruwa ko da mutum ya iya shi (iyo) to yana da haɗarin gaske domin irin barkwancin da aka san yakan yi wa gwaninsa.[2] Dalilin irin barkwancin da ruwa kan yi, Bahaushe a wata karin magana yake cewa:

‘Gwanin ruwa shi ruwa kan ci’.

A wani ɗa na waƙar da Makaɗa Sa’idu Faru ya yi wa Alhaji Usman Ɗangwaggo Bunguɗu, ya kawo zancen ruwa kamar haka:

Gindin waƙa: Toron giwa kana da martaba,

Usmanu na Bungudu,

Uban Marafan Keku,

Na Atto mai wuyak karo.

 

Jagora: Kwaɗɗo na can na kiran ruwa, x2

Ya tattake kiran su ɗai ya kai

An yi yayyahi waɗanga sun wuce, x2

Ya tattake kiran su ɗai ya kai, x2

An yi yayyahi waɗanga sun wuce,

Sai ga Allah ya shirga ruwa

Gulbi ko ya ɓaɓɓako ruwa, x2

Sai ga kwaɗɗo tun da jijjihi, x2

‘’Y/Amshi: Wai za ya biɗat tudun da yah haye

Jagora: Nic ce mashi kwaɗɗo ina iyali?

‘Y/Amshi: Yac ce ƙyale ni Maikiɗi, x2

Tahi dan nan ba ni son batun ba’a

 

A tunanin wannan muƙala, Makaɗa Sa’idu Faru ya kawo wannan zance ne domin ya nuna yadda wasu ‘yangaladimomi masu adawa da Sarki kan yi fata har da addu’a domin sarautar da suke jira ta faɗi. Sukan manta da cewa sau da yawa kwaɗo yakan kira ruwa sai ruwan ya ci shi kamar yadda makaɗa Sa’idu Faru ya fassara Karin maganar ta hanyar kawo hoto cikin bayani. Ɗansarki ya yi fatar sarauta ta faɗi, hakan ya tabbata amma kuma ya kasance bai sami sarautar ba. Sakamakon jayayya da gwagwarmayar neman sarauta da ya yi da sarki, wato ya kasance abokin adawa da Sarki, tun bai sami sarauta ba, sai ya zare jikinsa a gefe, ya zama ɗan kallo.

4.1.2 Kaya/Makaman Kamun Kifi

Kamun kifi galibi ana aiwatar da shi ne ta amfani da wasu kayayyaki ko makamai domin samun nasara. Makaɗa Saidu Faru fasihi ne sosai kuma masanin al’adun Hausawa. Duk da kasancewarsa ba masunci ko basarke ba, Sa’idu ya laƙanci harkar Sarkanci dalilin kasancewar sanaar tana gudana a kusa da muhallin da ya rayu. Gulbin Sakkwato da ya ratso tsakiyar Zamfara, ya bi ta Gusau ne da Bungudu da Maru da Maradun da Bakura sannan ya malala Gandi da Raɓa a cikin jihar Saakkwato. Ba mamaki Sa’idu ya fahinci harkar Sarkanci ne ta hanyar la’akari da yadda sana’ar take gudana a waɗannan wurare da gulbin ya ratso wanda ba wata tazara sosai da garin Faru. Daga cikin kayayyakin kamun kifi da Makaɗa Sa’idu Faru ya ambata a cikin waƙaƙinsa akwai taru da fatsa.

A cikin waƙar da ya yi wa Sarkin Kudun Sakkwato, Alhaji Muhammadu Macciɗo, Makaɗa ya kawo maganar taru a wani ɗan waƙa da ke cewa:

Gindin Waƙa: Bajimin gidan Bello Mamman na Yari,

Sarkin Kudu Macciɗo ci maraya.

 

Jagora: Na Marafa Ɗanababa,

‘Y/Amshi: Mai tura haushi, na Sarkin Gabas,

Duniya hori wawa.

Jagora: Babban dutci a hange nesa, x2

‘Y/Amshi: A ishe ka soronka ya tcarma kowa, x2

Da ɗai babu geben da yak kai ga gulbi, x2

Ruwan Maliya sun wuce masu taru. x2

 

Daga cikin kayan kamun kifi na gargajiyar Bahaushe dala ce kaɗai ragar kamun kifi mafi girma da ta ɗara taru. Taru raga ce da ta sami sunanta daga irin yadda sai jama’a kama daga huɗu zuwa biyar suke iya sarrafa ta domin kamun kifi, wato aiki ne na taro. Duk da yawan da ragar taru take da shi da kuma haɗaka na jama’a wajen amfani da ita a kama kifi, to ruwan maliya ya fi ƙarfin a yi sarkanci a ciki ta amfani da taru. A nan Makaɗa Sa’idu Faru ya nuna fifikon da gwarzonsa yake da shi idan aka kwatanta shi da waninsa. Irin abin nan ne da Bahaushe yake cewa ‘bakin rijiya ba wurin wasan makaho ba ne’, kuma gwarzon nasa tamkar itaciyar rimi ne kere itace. Iyakacin masunta amfani da taru a gulbi amma ruwan teku kam (maliya) ya fi ƙarfin masuntan taru.

Waƙar Sarkin Kiyawan Ƙaura Namoda, Alhaji Abubakar Garba tana ɗauke da wani ɗan waƙa inda Makaɗa Sa’idu Faru ya yi amfani da wata kalma ɗaya daga cikin kayan kamun kifi inda yake cewa:

Gindin Waƙa: Gwabron giwa na Shamaki baba uban Gandu,

Abu gogarman Magaji mai kansakalin daga.

 

Jagora: Abu baban Shamaki na Jekada,

Dangalin gabas na Isau ɗan Mudi.

‘Y/Amshi: Ƙashi tahi giggilme ƙargage,

Hwarah hwatsa cin ki sai ga mai ƙararrin kwana,

A ciki a kwan rirriƙan mutum za shi garin kewa.

 

Fatsa[3] da Makaɗa Sa’idu ya faɗa a wannan ɗan waƙa wata ƙugiya ce tilo da ake ɗaura wa wani dogon zare. Daga saman wurin da aka ɗaura ƙugiyar, kimanin taƙa biyu ko abin da ya fi haka, ana ɗaura abin da masunta suke kira karu[4] . Sauran zaren kuwa sai a ɗaura shi jikin wata ‘yar sanda ko karan dawa mai ƙwari. Wannan kara ko sanda ne ake riƙawa yayin da ɗan fatsa ya saka fatsarsa a ruwa domin kama kifi. Akan saka ƙoto na tana ko fara ko sabulu mai ƙanshi a jikin ƙugiyar domin jawo kifi. Kifin duk da ya kuskura ya ci ƙoto ko abincin da aka maƙala a fatsar sai ƙugiya ta kama shi. Karun da aka ɗaura zai nutse a ruwa. Hakan na nuna alamar fatsar ta yi kamu.. Irin wannan kifin kuwa kwanansa sun ƙare domin ƙarshe a cikin tukunya zai ƙarasa.

A wannan ɗan waƙa, Makaɗa ya yi amfani da zancen fatsa domin ya nuna cewa gwarzonsa ba ya ɗaukar raini kuma duk wanda ya faɗa masa ba daidai ba to kuwa zai wahala matuƙa, ya kasa samun sukuni; ya kasa zama ya kasa tsayi domin ya takalo abin da ya fi ƙarfinsa. Wannan yana nuna in ba wanda ila ta faɗawa ba, ba wanda zai iya ja da Sarki, sai kuwa wanda yake da rabon wahala.

4.1.3 Sunayen Kifaye

Allah a cikin ikonsa da buwayarsa ya albarkaci ƙasar Hausa da nimar koguna da gulabe da tafkuna da ƙoramu da fadamu masu ajiye ruwa. A cikin ruwan, akwai nau’ukan kifaye daban-daban da suke rayuwa. A Bahaushiyar al’ada, akwai azuzuwan kifi nau’i biyu. Akwai farin kifi da kuma baƙin kifi. Ana samun kowane daga cikin waɗannan nau’uka a ƙasar Hausa. Makaɗa da mawaƙan Hausa sukan saka sunayen kifaye daban-daban a cikin waƙoƙinsu tun ma ba na fada ba. A waƙar Sarkin Banga, Alhaji Ahmadu, Makaɗa Sa’idu yana cewa:

Gindin Waƙa: Bai sake ba na Gardaye,

Ginshiƙin Sarkin Baura,

Hattara ba togewa,

Kamdaren Bunu ɗan Mamman.

 

Jagora: In dai ana babbkag giwa,

‘Y/Amshi: Ba a jin ƙaurin gawo,

Jagora: In dai ana yammatar goge,

‘Y/Amshi: Ba a jin daɗin molo.

 

Gawo wani nau’i ne na baƙin kifi da ake kira da sunaye daban-daban a ƙasar Hausa. A Hausar gabas, ana kiran sa da suna gaiwa. A Sakkwatanci kuwa ana yi masa suna gawo. A ƙasar Argungu da ɗaukacin ƙasar Kabi suna kiran sa da suna boɗami. Kifi ne mai yawan juriya da idan ruwan da yake ciki ya ƙafe a lokacin rani, sai ya yi wata ‘yar sheka da zai zauna a cikin har sai ruwan sama na damina mai zuwa ya sauka, sannan ya fita daga shekar ya koma ruwa. A jikinsa ba ya da ƙaya sai dai wata jijiya da ta ratsa shi tun daga cikin wuyansa har zuwa jelarsa. Rasin ƙaya a jikinsa ya sanya ba ya sukar mutum sai dai ya yi cizo da baki don kuwa yana da wasu ‘yan haƙora sirara masu kaifin gaske. Galibi wasu suna tadar cin kifin domin an camfa cewa cin jijiyarsa yana raunana ƙarfin alaurar namiji. Akan babbaka shi domin a cire fatar jikinsa wadda take da ɗan kaushi-kaushi gabanin a soya shi ko a yi bandar sa.

A wannan ɗan waƙa na sama, Makaɗa Sa’idu ya yi ƙoƙarin nuna ɗaukaka da girman da gwarzonsa yake da ita fiye da waninsa. Wato ya yi ƙoƙarin fassara karin maganar nan da take cewa ‘wurin bindiga wane ƙyastu’? Wato ya nuna rinjaya da ɗaukaka da girma da Sarkinsa ya fi koma bayansa.

A wata waƙa ta daban, wato waƙar Sarkin Yaƙin Banga, Sale Abubakar, Makaɗa Sa’idu Faru ya kawo wani ɗan waƙa mai ɗauke da sunan wani kifi da yake rayuwa a cikin gulabe da tafkunan ƙasar Hausa. Ɗan waƙar na cewa:

Gindin Waƙa: Gwabron giwa uban Galadima,

Ɗan Sambo ginshimi,

Gansheƙa Amadu na Maigandi,

Kai a uban Zagi.

 

Jagora: Ko jiya na iske gamdayaƙi da tuji,

Sun iske jinjimi,

To sun ko murɗa gardama,

Sun iske su bubuƙuwa ruwa.

‘Y/Amshi: Dan nan ni ko ina gaton gaɓa,

Sai nik kwaɗa gaisuwa,

Su ko sun daƙile ni dud,

Ni ko niƙ ƙara gaisuwa,

Dan nan kulmen da ac cikin gurbi,

Ya amsa gaisuwa.

 

Kulme da Makaɗa Sa’idu Faru ya faɗa a cikin wannan ɗan waƙa wani naui na kifi ne da ake kira tarwaɗa. Tarwaɗa kuwa tana cikin kifin nan da Sarkawa kan saka cikin rukunin baƙin kifi. Idan tarwaɗa ta girma sosai, ana kiran ta kulme. Wato kulme tarwaɗa ce da ta ƙosa ta girma sosai. Galibi tarwaɗa ta fi zama a gurbi mai zurfi musamman idan ta girma ta zama kulme. Kifi ne da yake da wasu gasu biyu a gefen bakinsa. A daidai kumatunsa kuwa, yana da wata ƙaya mai ƙwari wadda take taimaka masa wajen yin iyo a ruwa kuma da ita yake kare kansa daga duk wata barazana domin ita yake soka wa duk abin da ya kai masa farmaki. Yana da wata ƙaya mai ƙwari da ta ratsa ɗaukacin jikinsa tun daga wuyansa har zuwa jela. Ƙayar tana da wasu rassa da suka yi layi a duk faɗin jikin nasa. A bisa al’ada, wasu Hausawa sukan yi tadar cin wannan kifi domin ɗaukar da suke yi cewa yana haifar da ko ƙara haɓaka cutar zafi (kuturta).

Duk tsuntsayen da Makaɗa Sa’idu ya kawo a cikin wannan da ma ɗan waƙa na gaba, ya kawo su ne domin ya jaddada karin magana da sauran maganganun azanci kamar: ‘ko baba da babansa’ da ‘ko gaba da gabanta’. Makaɗa Sa’idu Faru ya yi ƙoƙari ya nuna Sarkin da yake wasawa ya fi ƙarfin duk mai adawa da shi kuma ma duk ya haɗiye su kamar yadda bubuƙuwa ta gangame su duka ta laƙume.

4.1.4 Dabarun Kamun kifi

Kamun kifi ko sarkanci sana’a ce mai wahalar gaske sannan kuma tana tattare da haɗura da dama na kamuwa da cutar sanyi da cizo ko sukar ƙayar kifi da dai sauransu. Wannan ne ya sanya akwai dabaru da dama da sarkawa ko masunta sukan bi domin samun nasara a kan sanaar. Wasu daga cikin irin waɗannan dabaru sukan sami ambato a cikin waƙoƙin fada. Makaɗa Sai’du Faru ya kawo ko ya ambaci wata dabara ta kama kifi a wani ɗan waƙa da ya yi wa Sarkin Yaƙin Banga Alhaji Sule inda yake cewa:

Gindin Waƙa: Gwabron giwa uban Galadima,

Ɗan Sambo ginshimi,

Ganshiƙa Amadu na Maigandi,

Kai a uban Zagi.

 

Jagora: Jan zakara ya yi ƙiƙiriƙi, x2

Ya tsare garkag gidan Ubanai, x2

‘Y/Amshi: Ya bak kwaɗɗo shina cikin rami, x2

Ya lanƙwashe tsara.x2

Jagora: Ni,

‘Y/Amshi: Bana sai na yi lalaben kwaɗɗo,

Na kai gaban wuta.

jagora: Kai ni bana sai,

‘Y/Amshi: Sai na yi lalaben kwaɗɗo na kai gaban wuta.

 

Lalube ɗaya ce daga cikin dabarun kamun kifi. Akan shiga ruwa ne a yi kambaɗar kifi domin kama shi da hannu kawai ba tare da raga ko tarko ba. Wani zai yi mamakin ai makaɗa kwaɗo ya ambata ba kifi ba. Masunta sukan kama kwaɗi domin sayarwa ga ƙabilun da kwaɗo yake cimakarsu. Abokin adawar Sarki ne makaɗa ya kira kwaɗo domin ƙara ƙasƙanta shi, duba da cewa darajar kwaɗo ba ta kai ta kifi ba a tunanin Bahaushe. Da yake mazaunin kwaɗo a ruwa ne, to lalabo shi za a yi domin saka shi a wuta kamar yadda ake yi wa kifi da sauran halittun ruwa.

4.1.5 Sauran halittun Ruwa

 

Baya ga halittar kifi akwai wasu halittu daban-daban masu tarin yawa da Allah cikin ikonsa yake rayarwa a cikin ruwa. Misalin waɗannan halittu ya haɗa da dabbobi kamar dorina da ayu da karen ruwa da kada da tsari da kunkuru da tsuntsaye kamar bubuƙuwa da ƙirinjijiya da kazar ruwa da zalɓe da takau da sauransu. Wasu daga cikin waɗannan halittu na ruwa sukan sami ambato a cikin waƙoƙin fada na Makaɗa Sa’idu Faru. Halittar ruwa kamar kada ta sami ambato sosai musamman idan ana son a nuna haɗarin da yake ga ruwa sai a ce akwai kada a cikinsa. Ruwa da kada kuwa yana da wuyar shiga. Irin wannan ne makaɗan fada suke ambato a cikin waƙoƙinsu domin su nuna gwarzonsa ba banza yake ba, yana da wuyar a shige masa ko a yi masa kutse cikin sauƙi. Makaɗa Sa’idu Faru ya ambaci halittar kada a wasu ɗiya na waƙoƙinsa kamar waƙarsa ta farko wadda ya yi Sarkin Yamman Faru Ibrahim inda yake cewa:

Gindin Waƙa: Bi da maza ɗan Joɗi na Rwafi,

Iro magajin Shehu da Bello.

 

Jagora: Ruwa da kada, x2

‘Y/Amshi: Ɗibgau na Magaji,x2

Sai tsohon wawa ka shigas su.

A wannan ɗan waƙa Makaɗa Sa’idu kwatanta Sarkinsa da ruwa wanda kada yake rayuwa a cikisan. Ruwa da kada a ciki kuwa wawa ne kaɗai zai iya ratsa shi. Dalili kuwa shi ne akwai haɗari mai yawan gaske, shiga ruwa irin wannan.

Waƙar Sarkin Kudun Sakkwato Muhammadu Macciɗo tana ɗauke da irin wannan zance a mabambancin muhallin da ma’ana. Ɗan waƙar na cewa:

Gindin Waƙa: Kana shire baban Yanruwa,

Na Bello jikan Ɗanfodiyo.

 

Jagora: Gurbin giwa sai ɗanta,

‘Y/Amshi: Daudu zaman gurbi sai ɗan kada.

Jagora: Gurbin giwa sai ɗanta,

‘Y/Amshi: Zomo anka aza yab bag gidan.

 

A nan Makaɗa Sa’idu ya yi amfani da kalma ɗaya mai dibilwa wadda a kowane bagire da aka saka ta tana da wata ma’ana ta daban. Wannan kalma ita ce ‘gurbi’. A saɗara ta farko na ɗan waƙar, gurbi na nufin mazauni ko wurin da ake kwanciya. Haƙiƙa mazaunin giwa sai ɗanta kaɗai zai iya shigarsa ya zauna lami lafiya. A saɗara ta biyu kuwa kalmar ‘gurbi’ na nufin ƙasa ko ƙarshen zurfin ruwa. Zama ƙasan ruwa kuwa sai ɗan kada don su aka gadar wa haka. A nan Makaɗa Sa’idu Faru ya nuna cewa Muhammadu Macciɗo kaɗai ya dace ya da shugabantar jama’a a duk sha’anin kamar siyasar zamani, da kuma uwa uba, hawan halifar Sarkin Musulmi Abubakar na III domin shi babban ɗansa ne kuma ya gado halaye da kyawawan ɗabi’un mahaifinsa.

Makaɗa Sa’idu Faru ya sake kawo sunayen wasu halittu na ruwa waɗanda suke ‘yan zuriya ɗaya ko ‘yan dangi duk da cewa suna da ɗan bambanci kaɗan a wajen halittarsu. Wannan ya zo a cikin waƙar Sarkin Tudun Falale, Alhaji Muhammadu Ƙwazo. Ɗiyan waƙar na cewa:

Gindin Waƙa: Ya riƙa da gaskiya Muhammadun Muhammadu,

Dangalin gidan Maisaje shirinka ya yi kyau.

 

Jagora: Da ihihiya da kunkuru, x2

‘Y/Amshi: Shawara guda sukai, x2

Jagora: Da bisshiya da beguwa,

‘Y/Amshi: Shawara guda sukai,

Jagora: Da kurciya da hasbiya,

‘Y/Amshi: Shawara guda sukai,

Jagora: Bubuƙuwa da jinjimi,

‘Y/Amshi: Shawara guda sukai

Dub babu wanda yaz zo haji, x2

Dub babu mai nihwaz zuwa. x2

 

A saɗara ta farko, Makaɗa ya kawo halittun ihihiya wadda wasu suka fi sani da suna ƙififiya da kuma kunkuru ‘yan zuri’a ɗaya ne don haka sun yi kama da juna. Halittu ne da suke da wata ƙunba a gadon bayansu wadda take mai ƙwari ce sosai. Hasali sukan ɓuya ta saka kansu da ƙafafuwa a cikin ƙumbar yayin da suka fuskanci barazana daga wata halitta da ka iya cutar da su. Dukkansu suna rayuwa ne a fadama inda ake samun wadatar ruwa. Bubuƙuwa da jinjimi tsuntsaye ne da suke rayuwa a bakin fadama. Sun yi kama da juna sai bambancinsu shi ne bubuƙuwa tana da ƙaton baki, yayin da jinjimi ya yi kama da zalɓe.

Makaɗa Sa’idu ya siffanta wasu ‘yan Sarki ne da waɗannan halittu domin ya yi masu bugun kaɗanya ta aibata su da zambo cewa duk jirgi ɗaya ya kwaso su. Ba su taɓa aikata wani abin kirki ba kuma ba su da niyar aikata hakan ko da a wani lokaci nan gaba.

5.0 Sakamakon Bincike

Wannan muƙala ta yi ƙoƙarin ƙara tabbatar da maganar da manyan masanan adabin Hausa suka yi cewa adabi madubi ne na rayuwar al’umma (Ɗangambo,1982). Yunƙurin muƙalar na zaƙulo yadda Makaɗa Sa’idu Faru malamin waƙa, mai kwana ɗumi na Mamman na Balaraba ya yi amfani da kalmomin fannu na sha’anin sarkanci a cikin waƙoƙin fada ya daɗa gaskata waccan magamar. Haƙiƙa, makaɗin ya nuna bajintarsa da ƙwarewarsa ga harshen Hausa inda ya zaƙulo kalmomin fannu na sha’anin Sarkanci ya kuma yi amfani da su a cikin waƙoƙinsa na fada. Abu ne tabbatacce cewa Sarakuna da ‘ya’yansu sha’anin mulki da tafiyar da shi suka gada, don haka sha’anin Sarkanci da aiwatar da shi bai shafe su ba kai tsaye, abu ne da ya rataya a wuyan talakawa. Duk haka aka tarar da cewa waƙoƙin da ake yi wa jamaar fada suna ɗanfare da kalmomin Sarkanci a cikinsu. Dalilan da ke sa makaɗan fada saka lamarin sarkanci a waƙoƙinsa ya haɗa da yi wa abokan adawar Sarki zambo da aibata su da sana’ar da ba ta kamace su ba. Ana daɗa nuna yadda kwaɗo kan kira ruwa amma kuma a ƙare ta ruwan ya ci shi. Hakan yakan kasance ne yayin da ɗangaladima zai yi ta fatan sarautar gidansu ta faɗi amma idan hakan ta tabbata sai ya kasa kai ga gaci na cikar burinsa na zama Sarki. Makaɗan fada suna amfani da muhallin sarkanci wato ruwa da irin mugayen halittun da ake samu a ruwan domin su nuna gwarzonsa tsayayye ne ko kaɗan ba abin rainawa ba ne da za a iya a faɗa masa kai tsaye, yin haka kuwa sai wawa ko tsohon mahaukaci. Makaɗan sukan kuma kwatanta cancantar gadon sarauta da wani gurbi mawuyaci da sai ɗan sarki wanda yake kusa ga magabata ko iyaye zai iya hawa kan wannan karagar.

6.0 Kammalawa

Makaɗa Sa’idu Faru kusan ana iya cewa shi ne makaɗi tilo da mafi rinjayen waƙoƙinsa na fada ne. A kan haka, malamin waƙa mai kwana ɗumi na Mamman na Balaraba ya ciri tuta a tsakanin makaɗa da mawaƙan Hausa domin kacokam waƙoƙinsa na fada ne. Makaɗi ne da Allah ya yi wa basira da fasaha da zalaƙa ta shirya waƙa da rera ta ta tafi daidai kai ka ce karantawa yake yi. A fagen sani da ƙwarewa haɗe da amfani da harshen Hausa, Sa’idu ba kanwar lasa ba ne. Wannan ne ya ba shi damar amfani da kalmomin fannu na sarkanci a cikin waƙoƙinsa na fada kai ka ce Saidu masunci ne. Kamar yadda aka gani a cikin wannan muƙala, amfani da kalmomin fannu na sarkanci a cikin waƙoƙin abu ne da ya ƙara wa waƙoƙin armashi da maana sosai. Ganin yanzu yadda zamananci da kayan kaɗe-kaɗe da yanayin waƙa irin na Turai ya yi kutse har yake yi wa waƙoƙin Hausa na gargajiya barazana, ya dace matuƙa a taskace waɗannan waƙoƙi na Saidu Faru da ma wasu makamantan nasa domin kare su daga salwanta. Yin haka ba ƙaramar kariya ba ce ga aladu da kuma harshen Hausa. Ya dace ya kasance a manyan makarantu da ake nazartar ilimin harshen Hausa a bijiro da kwasakwasai masu cin gashin kansu a kan Sa’idu Faru da sauran taƙwarorinsa ba wai kawai a dunƙule ba a kwas ɗaya a wajen nazari a aji. Yin haka zai ƙara farfaɗo mana tare da isar da nagartaccen ilimin harshen Hausa, musamman adabinsa da al’adunsa ga ɗalibai ta yadda za su ƙara alfari da tinƙaho da Harshen. Ba wannan kaɗai ba, haƙiƙa ɗaliban za su iya koyon kimiyya da falsafa da ilmin zamantakewa da naƙaltar mulki da dai fannonin ilmi da dama duk a cikin waƙoƙin.

Manazarta

Abubakar, A.T. (2015) Ƙamusun Harshen Hausa. Zaria: Northern Nigeria Publishing Company Ltd.

Alkali, M.B. 1969 “A Hausa Community in Crisis: Kebbi in the Nineteenth Century.” M.A. Thesis. Zaria: Ahmadu Bello University.

Bargery, G.P. (1993) A Hausa-English Dictionary and English- Hausa Vocabulary (2nd Ed.). Zaria: Ahmad Bello University Press.

Bunza, A.M. (2009). Narambaɗa. Lagos: Ibrash Islamic Publication Centre Ltd.

CNHN, (2006) Ƙamusun Hausa Na Jamiar Bayero. Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.

Fadama, M.G. (2015) Sarkanci A Gundumar Sakkwato. Kundin Digiri Na Uku. Sashen Harsunan Nijeriya. Sokoto:, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo University.

Fadama, M.G. (2016) Tsarin Shugabanci A Sana’ar Sarkanci. In Malumfashi, I. A. M., Yakasai, S. A., Abdullahi, I. S. S. (eds) The Hausa People, Language and History. Past, Present, and Future. Pp.435-448 ISBN: 978-978-956-169-8.

Gusau, S. M. ( ) Waƙoƙin Makaɗan Fada: Sigoginsu Da Yanayinsu Musamman A Ƙasar Sakkwato. Kundin Digiri Na Uku. Sashen Harsunan Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.

Gusau, S.M. (1996) Makaɗa Da Mawaƙan Hausa. Kaduna: Fisbas Media Services.

Gusau, S.M., (2003) Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Kano: Benchmark Publishers Ltd.

Gusau, S.M. (2009) Diwanin Waƙoƙin Baka: Zaɓaɓɓun Matanoni Na Waƙoƙin Baka Na Hausa. Kano: Century Research and Publishing Company.

Yahya, A.B. (1997) Jigon Nazarin Waƙa. Kaduna: Fisbas Media Services.



[1] Alhaji Ibrahim Muhammad Ɗanmadamin Birnin Magaji ya kawo wannan ƙauli a sakamakon hira da ya yi da iyalan makaɗa Sa’idu Faru. Ya saka zancen a wata tattaunawa a dandalin watsup da aka buɗa domin musayar ra’ayi game da wannan taro da aka shirya kan Makaɗa Sa’idu Faru. Ya saka bayanin a ranar 9/02/2024.

[2] Dubi abin da makaɗa Ibrahim Narambɗa yake cewa game da gulbi:

Gindin Waƙa: Ya ɗau girma ya ɗau yabo,

Mu za mu ga Alƙali Abu.

Jagora:    Kul ka ishe gulbi ya cike,

                In ba kowa ka iya,

‘Y/Amshi: Koma ka tsaya ganga ka kwan

[3] Fatsa kayan kamun kifi ce da ke yi da ƙugiya. Ita kuwa ƙugiya, Hausawa na amfani da ita domin kama kifi tun gabanin su shaƙu da wata al’umma daga ƙetare. Hasali ma maƙera baƙi masu ƙera kayan ayyukan noma suke ƙera ta da baƙin ƙarfe. Wannan ta yanzu mai launi mai haske ko fari irin na silba, wadda kamfani yake samarwa daga waje ta shigo ne daga baya. A da can, wadda fasahar maƙeranmu suke samarwa ake amfani da ita.

[4] Karu wani soso ne ko kara ko duk abu marar nauyi da masunta suke da ɗaura wa wasu kayan haƙo na kamun kifi domin dalilai biyu. Na farko ana saka shi ne domin ya hana ƙugiya ko raga sauka ƙasan ruwa. Haka kuma idan ƙugiya irin ta fatsa ta kama kifi to karu ne yake ba da labarin haka domin shi yake nutsewa a ruwa ko riƙa motsi yayin da kifin yake fisge-fisgen kuɓuta daga tarkon.

Sa'idu Faru

Post a Comment

0 Comments