Citation: Rabeh, H. & Nalado, N. (2024). Nazarin Turakun Zambo a Bakin Makaɗa Sa’idu Faru. Four Decades of Hausa Royal Songs: Proceedings from the International Conference on the Life and Songs of Makaɗa Sa'idu Faru, 3(3), 92-97. www.doi.org/10.36349/tjllc.2024.v03i03.012.
NAZARIN TURAKUN
ZAMBO A BAKIN MAKAƊA SA’IDU FARU
Daga
Hassan Rabeh
08069612112
rabehassan26@gmail.con
Da
Nuhu Nalado
Sashen Hausa na Tsangayar Ilimin Harsuna,
Kwalejin Ilimi
ta Isa Kaita, Dutsinma, Jihar Katsina
08067762873
naladonuhu@gmail.com
Tsakure
Muƙalar ta yi nazarin tubalan da makaɗa Sa’idu Faru
ya yi amfani da su a matsayin gina turken zambo a cikin waƙoƙinsa. Manufar
wannan muƙala ita ce yin nazarin kalaman
zambo a waƙoƙin Sa’idu Faru tare da bayyana abubuwan da mawaƙin yake amfani da su domin ƙulla zambo a waƙoƙinsa. An yi amfani da dabarar sauraren waƙoƙimsa da
nazarce-nazarcen masana a matsayin hanyoyin da aka bi domin tattara bayanan da
aka yi amfani da su a wannan muƙala. Don cim wannan
manufa, an yi amfani da mazhabar Waƙar Baka Bahaushiya wadda ta bayyana hanyoyin da ake yin nazarin
yadda ake nazarin waƙar baka Bahaushiya. Wanda ya jagoranci wannan mazhaba shi ne
Farfesa Sa’id Muhammad Gusau. Bayan kammala wannan muƙala, an gano turakun da mawaƙin yake la’akari da su a yayin samar da zambo a cikin waƙoƙinsa da suka ginu a kan ɗabi’a a gurabun wasu dabbobi da tsuntsaye da mutane. Tare da
yin amfani da turakun ƙarangiya da na ba’a da wasu turakun da ke nuna matsayin mutum
a rayuwa.
1.0 Gabatarwa
Waƙar baka, zance ne
shiryayye cikin hikima da azanci da yake zuwa gaɓa-gaɓa bisa ƙa’idojin
tsari da daidaituwa a rere cikin sautin murya da amsa-amon kari da kiɗa da amshi (Gusau, 2023: xix).
Haka kuma, ta fuskarsiga da zubi da tsarinaiwatarwa, Bahaushiyar waƙar baka ba ta zuwa a shimfiɗe
ko ta zo gaba ɗaya, takan zo ne gutsure-gutsure tare da maimaituwar gindinta
a tsakaninsu. Gutsure shi ne ‘ɗa’. A waƙar baka ba a ƙayyade yawan layuka a ɗan waƙa, musamman ga makaɗan da
suke cikin ƙungiya, suna maimaita
gindin waƙa a ƙarshen kowane ɗan waƙa.
Waƙoƙin baka na Hausawa suna daga cikin hanyoyin da Hausawan suke
nuna fasaharsu ta baka. Waƙar
baka tana daga cikin hanyoyi daban-daban na isar da saƙonni da kuma samar da nishaɗi.
Haka nan suna taskace abubuwa da dama, daga ciki akwai tarihi da al’adu da
sarauta da kalmomi. Don haka ne makaɗa da
mawaƙa suke da matuƙar muhimmanci a rayuwar Hausawa, musamman ta gargajiya.
Kowane fannin a rayuwar Hausawa yana da mawaƙa na musamman da waƙoƙinsu suka shafi wannan
ɓangaren.
Daga cikin mayan rabe-raben makaɗa da masana. Gusau (2008:137) ya raba su zuwa makaɗan jama’a da na maza da kuma na fada. Makaɗan fada su ne makaɗa (ko
mawaƙan) da ba su yi wa
kowa waƙa sai jinin sarauta
ko masu riƙe da muƙamai na sarauta. Sa’idu Faru yana daga cikin irin waɗannan mawaƙa,
domin shi da kansa yana cewa:
Jagora: Sa’idu Faru ka waƙar iko,
‘Y/Amshi: Komi kaj jiya ƙarya akai,
Jagora: Sa’idu Faru ka waƙam Mulki,
‘Y/Amshi: Kami kaj jiya ƙarya akai.
(Waƙar Ɗan Hashim).
Makaɗan fada suna yin tasiri ƙwarai a harkokin sarauta. Baya ga kasancewar masu samar da
nishaɗi sukan yaɗa manufofin sarakuna
da bayyana salsalarsu. Haka nan kuma sukan zama wata garkuwa ga masauta da sarakuna.
Daga cikin hanyoyin da suke zama garkuwa ita ce sukan mayar da raddi ga maƙiyan masarauta da kuma sarakuna, wani lokaci ma sukan zama kanwa
uwar gamia wajen assasa yaƙe-yaƙe a tsakanin masarautu. Ana iya ganin misalin haka a wasu ɗiyan waƙar
Sa’idu Faru ya yi wa Sarkin Ƙauran
Namoda, Abubakar inda yake cewa:
Jagora: Ni kiɗin yaƙi nay yi ma Abu na Isau,
Ba ni son kana zamnawa banza
Ka ɗauki takobi
da bindigogi da bakunkuna
Ka sa surdi ba mu sansani sai baki Tsauri
Kano da Katsina, Kwantagora
Hab Barno riƙon Namoda na
Shi na ac can
Garba ka amshe riƙon dud da Ummarun Ummaru
Yab bar ma.
(Waƙar Sarkin ƘauranNamoda, Abubakar).
A
wannan ɗan waƙar
mawaƙin
ya ambaci irin kiɗin da ya yi wa sarkin nasa wato kiɗin yaƙi ne
ba wai don sarautarsa kurum ya yi masa ba. Dubi farkon ɗan waƙar,
ya kuma cigaba da nuna masa wasu wuraren kamar Kano da Katsina da Kwantagora
har Borno duk riƙon
kakansa ne.da yake ganin a da duk nasu ne don ya yi niyyar kwato su ta hanyar
yaƙin.
Sa’idu Faru yana ɗaya daga cikin shahararrun
mawaƙan fada da ƙasar Hausa ta samar. Daga cikin ƙunshiyar waƙoƙinsa akwai zuga da yabo da nuna salsala
da gwanintar harshe, idan kuwa maganar zambo ce makaɗa Sa’idu ba shi da
na ɗaya. A matsayinsa na makaɗin fada zambo yana daga cikin batutuwan
da makaɗin yake gwarzant agwarzayensa da kambamasu. Haka
kuma ya kankushe abokan hamayyar sarakunansa don kare martabarsu (Gusau,
2008:147). Ganin haka ne ya sanya wannan muƙala ta yi nazarin turakun da Sa’idu Faru ya yi amfani da su domin
gina zambo a cikin waƙoƙinsa.
Manufar wannan muƙala ita ce, yin nazri a kan turakun da makaɗa Sa’idu Faru yayi amfani da su domin gina ɗiyan waƙoƙinsa masu nasaba da zambo. za a yi haka ne ta hanyar gabatar
da turken sannan a kafa hujja ta hanyar kawo ɗiyan
waƙa ko waƙoƙi da suka nuna tueken
da aka ambata, sannan a kawo sharhi a kan ɗiyan waƙar da aka gabatar.
2.0 Taƙaitaccen Tarihin Sa’idu Faru
Gusau (2005:117) ya bayyana cewa an haifi makaɗa Sa’idu Faru a ƙasar Maradun a shekarar (1932).
Sunansa na yarinta shi ne Ɗan’umma.
Wannan suna ya samo asali ne daga matar ƙanen ubansa, wacce baya kiran sunanta naasali sai dai ya kira
ta da Umma. Sunan mahaifinsa makaɗa
Abubakar ɗan makaɗa Abdu. Wannan yana
nuna cewa makaɗa Sa’idu Faru ya yi gadon kiɗa
ya yi daga wurin mahaifinsa da kakansa. Makaɗa
Sa’idu ya yi ƙuruciyarsa a garin
Banga ta ƙasar Ƙauran Namoda. Sa’idu ya koyi waƙa daga wurin mahaifinsa. A lokacin da Sa’idu ya fara cin gashin kansa, sai fasaha da hikimarsa
ta ƙara fitowa a fili.
3.0 Ra’i
An ɗora muƙala a bisa Mazhabar
Waƙar Baka Bahaushiya. Mazhaba ce da ta
samo asali a shekarun (1993), a ƙarƙashin jagorancin Farfesa
Sa’idu Muhammad Gusau. Manufar mazhabar ta ƙunshi bayyana tarihi da asali da salsalar waƙar baka ta Hausa, da kuma zurfafa bayani a kan turke da
abubuwan da waƙa ta ƙunsa. Ita wannan mazhaba ta tarken waƙar baka Bahaushiya ta jinginu da wasu Ra’o’i na wasu mazhabobin
da suka haɗa da Mazhabar Gargajiya. Daga cikin ayyukan da aka samu sun
ginu ta yin amfani da wanna mazhaba suna da yawa. Kaɗan daga cikinsu akwai aikin Garba (1998) da
Satatima (2008) da Abubakar (2011) (Gusau, 2023:23). Dangantakar wannan Mazhabar
da wannan muƙala ita ce,
aikin ya ginu ne a kan nazarin turakun waƙoƙi masu nasaba da
zambo a waƙoƙin Sa’idu Faru. Mazhabar kuma tana magana ne a kan nazarin waƙar baka Bahaushiya. Wannan dalili ne ya sanya aka zaɓi gudanar da wannan muƙala a bisa wannan Mazhaba.
3.1 Hanyar
Gudanar da Bincike
An yi amfani da hanyoyi biyu a
yayin tattara bayanan da aka yi amfani da su a wannan gudummawa da ta yi nazarin
turakun da Sa’idu Faru yake yin amfani da su a yayin gina zambo a cikin waƙoƙinsa. Hanya ta farko ita ce ta
sauraron waƙoƙin tare da
tattara wuraren da yake yin zambo a cikinsu.
Hanya ta biyu kuwa, ita ce, ta hanyar yin nazarin rubuce-rubucen masana masu
nasaba da waƙoƙin baka na
Hausa. Har ila yau, an samo waɗannan bayanai
daga wallafaffun littattafai da kundayen bincike da aka gudanar daga jami’o’i daban-daban da muƙalu da aka
gabatar a tarurruka daban-daban na ƙara wa juna sani. Haka kuma an yi amfani da kafar
sadarwa ta yanar gizo wajen samu da tattara bayanan da aka yi amfani da su a
yayin gudanar da wannan bincike.
4.0 Turakun
Gina Zambo a Bakin Sa’idu Faru
Kalmar zambo kishiyar yabo ce. Ma’ana tana nufin bayyana mutum
da wasu munanan siffofi waɗanda za su muzanta
mutum tare da jawo masa rashin ƙima
da mutunci a idanun sauran al’umma. A yayin gina zambo a waƙoƙin baka akan lura
da halaye da siffofin mutum na zahiri ko kuma a yi masa siffofin ƙage. Daga cikin hanyoyin da akan bi domin yi wa mutum zambo akwai
duba kamanni da nuna halin rashin kirki da kamanta mutum da halayen dabbobi ko tsuntsaye
marasa kyau da ɓata asali da nasaba da kuma ƙaga wa mutum mummunar siffa ko da kuwa bay a da ita (Gusau,
2008:382).
Makaɗa Sa’idu Faru yana amfani da wasu tubula a yayin da yake ƙulla ɗiyan waƙa
masu nasaba da zambo. Daga cikin waɗannan tubula
akwai:
4.1 Ɗabi’u
Sa’idu Faru yakan yi amfani da ɗabi’a a matsayin tubalin gina
zambo a cikin waƙoƙinsa. Waɗannan ɗabi’u sun haɗa da na dabbobi da
na tsuntsaye da munanan ɗabi’u waɗanda Hausawa suke ƙyamata a rayuwa.
4.1 Turken Ɗabi’ar Dabbobi
A nan mawaƙin
yakan yi amfani da ɗabi’u masu kyawo a yayin zuga ko kwatanta gwarzayensa sannan
ya yi amfani da ɗabi’u masu rauni ko muni waɗanda
Hausawa suke ta’allaƙawa ga wasu dabbobi
domin yin zambo ga waɗanda yake nufin yi wa zambo. a lura da abin da yake faɗa a cikin waɗannan ɗiyan waƙoƙin:
Jagora: Alibawa kuna ganin hwansakku wurin Sule babu dama
Giwa ta sha ruwa tai miƙa ta taushegurbi
Kuma ‘yan ɗiyanta sun shiga sun sha sun hwara ƙarfi
Sai ‘yan namu suna jin ƙisa ba damas su ɗebo
Sai bil’amu ubandubara
Shi ɗai yaz zo ga giwa
Albarkacinki niz zaka in samu ruwan da
nis sha
Giwa ta ba shi hili, ya samu
ruwan da yas sha
Ya sha ya kuma ba ɗiyanai
Yaw wa dangi kirari yac ce ya ƙwato da ƙarhi
Zomo yac ce tsaya shege lallashin ta kay yi
In ƙarhi gaskiya na koma ɗebo gabana.
(Waƙar Sule, sarkin Zurmi)
A ɗiyan waƙoƙin da suka gabata mawaƙin ya yi amfani da ƙarfin da giwa take da shi a matsayin fifiko a kan sauran dabbobi.
Haka nan ya yi amfani da wayo ko dabarun dila da kuma kaifin hankali da Zomo ya
yi amfani da shi domin tona asirin Bil’amu (Dila).
Haka kuma, a wani wurin ya kawo irin wannan:
Jagora: Na zo na ishe ‘yan sarki naz
zaɓi guda
Komi za mu yi da shi mukai
Ihihiya da kunkuru shawara guda sukai
Buƙuƙuwa da jinjimi
shawara guda sukai
Da bisshiya da beguwa shawara
guda sukai
Da kurciya da hazbiya shawara
guda sukai
Duk babu wanda yaz zo haji babu mai nuhwaz
zuwa.
(Waƙar Sarkin Tudu)
A nan makaɗa ya kawo dabbobi masu
kusancin ɗabi’a da juna domin kwatanta waɗanda yake yi wa zambo. a cikin ɗiyan waƙar
ya nuna yadda ihihiya da kunkuru suna da kammanu da ɗabi’u iri ɗaya ta yadda wasu
ma ba su iya bambance su. Shi ya sa ya ce shawara guda suke yi. haka ma bubuƙuwa da jinjimi suna da kamannu da ɗabi’u iri ɗaya kamar yadda
bushiya da beguwa kowannensu yana da ƙaya a jikinsa. Kurciya da hazbiya ma suna da kamannu da ɗabi’a iri ɗaya. Dukkan waɗannan halittu ya nuna babu wanda yaz zo haji babu mai nufin zuwa,
wato waɗanda ya kwatanta da waɗancan halittu
babu wanda ya yi sarauta kuma babu mai alamar yin sarautar.
4.2 Turken Ɗabi’ar Tsuntsaye
A nan kuma, Sa’idu Faru yana amfani da ɗabi’un tsuntsaye kamar yadda yake yi ga dabbobin a nuna fifiko
da ƙarfin halin wasu tsuntsaye a kan masu rauni
ko waɗanda ake ta’allaƙa wa wayo a kan waɗanda ake
nuna wa rashin wayo. Dubi waɗannan ɗiyan waƙoƙi:
Jagora: Duk tsuntsun da ka daji
Ko babba ko ƙarami duka na gane nuhinai
Jemage ga halinai ba mu san wanda shike so ba
Ga shi mai haƙora na, Ga shi kunnuwa na
Ga ya ba ya sabka ƙasa balle a ga dama tai
Don munahukin Allah kai munka naɗa babba.
(Waƙar Amadun
Sambo)
A nan mawaƙin ya yi amfani
da halittar jemage wanda yana tashi kamar tsuntsu, kuma yana
da haƙora da kunnuwa kamar
dabba a matsayin munafunci. Domin ya kasance da kamannu na abubuwa biyu.
Ke nan ya kwatanta wanda yake yi wa zambo a matsayin munafuki kamar
yadda halittar jemage take.
4.3 Turken Ɗabi’un Mutane
Akwai waɗansu ɗabi’u da al’ummar Hausawa suke ɗauka a matsayin na ƙwarai, wasu kuma munana.
Daga cikin munanan akwai sata da maita da daudu da karuwanci.
Sa’idu ya yi amfani da mummunar ɗabi’ar ɗandaudu domin ƙulla ɗiyan waƙarsa mai nasaba da zambo. Ya yi haka ne kuwa domin yana
sane da cewar ɗabi’ar ‘yandaudu tana daga cikin daɗaɗɗaun munanan ɗabi’un da Hausawa suke ƙyama (Rabeh da
Darma, 2016:239). Greenberg (1946:42 da Bosmer (1993:18)
sun bayyana cewa ɗabi’ar ‘yan daudu ta samo asali
ne daga wani iska da ake kira Daudu wanda yake
yin ɗabi’un mata. Sanin kowa ne cewar ɗan daudu mutum ne namiji mai nuna sha’awa da yin ɗabi’un mata, wani lokaci ma harsunan mata yake amfani
da su. Haka nan yakan yi kwalliya irin ta mata da ɗaura zane da kuma kallabi, har ma a wani lokaci akan danganta su da
kawalci da luwaɗi (Gaudios, 1988:19). Mawaƙin ya yi amfani da wannan ɗabi’a da Hausawa suke ƙyamata domin
yin zambo a cikin waƙarsa ta Sarkin
Zurmi Sule. A cikin waƙar yana cewa:
Jagora: Ko can
zamanin ana yaƙi kakan
Sule ad da hwama
Mai yanke mutane
Ummaru ba wargi ag garai ba
Kakan wani ba shi
da yaƙi
Ko can ɗandaudu na shi
In da dai shahwa kwalli na da kaka nai ka suna
Da madibinai da hoda
Da hwarar riga
da kore
Da gani nai ka ga kure
geme cinjim da shuni
(Waƙar Sarkin Zurmi Sule)
Haka nan, a wasuɗiyanwaƙaryayiamfani da mummunarɗabi’ar karuwanci
don gina ɗiyan waƙar, inda yake cewa:
Jagora: Baicin kokuwa akwai maraba
Ɗan Arkuma ya bah hwaɗa maka Muhammadu
Ko wurin uwaye mata kuna
da tsettserai
Ɗan mara abun wuya
Ɗan karuwa duɓ ɓaci kaj jiya da
kai muke.
Karuwanci abin ƙyama ne ga
al’ummar Hausawa. Don haka ake ƙyamar karuwa
da ma duk zur’ar da ta tsira daga jikinta. Saboda wannan dalili
ne Sa’idu ya kwatanta wanda yake yi wa zambo da Ɗan karuwa watau wanda ba shi da
nagartaccen asali. Sa’idu ya yi haka ne kuma domin ya muzanta wanda yake yi wa
zambo domin ya ɗauke shi abokin hamayyar ubangidansa.
4.4 Turken Ba’a
Makaɗa Sa’idu Faru
yakan yi amfani da ba’a ya ƙulla zarensa a
yayin da yake yin zambo. Sa’id (2006) ya bayyana da zolaya ko muzantawa cikin
wasa. Akan kalli sifa ko surar mutum a danganta shi da halittar dabba ko wani
abu mai muni. A irin wannan yanayi Sa’idu yakan kalli siffar jiki ya kwatanta
mutum da wani abu da zai zamo ba’a a gare shi kamar yadda za a gani a ɗiyan waƙar da yake ƙasa:
Jagora: Sharrin
da an ka ƙulla
ma Ƙaura duka ya kwance
Mai kamab buhun garin kwaki aka wa yanzu
Akuɗunɗun-akuɗunɗun
Ɗan
sarki da wuyan gora
Zamna mu ji labarin ƙaryad da
kakai soto.
A nan mawaƙin ya kwatanta wanda yake yi wa zambo da buhun garin kwaki. Daga jin wannan
kwatance za a fahimci cewar duk wanda ake yi wa zambon mutum ne mai jiki,
sannan mutum ne mai dogon wuya. Haka kuma ya nuna cewa akwai wani ɗan sarki mai
gajeren wuya ta yadda ya kamanta shi da wuyan gora.
4.5 Turken Bayyana Matsayi
A irin wannan yanayi Sa’idu yana amfani
da rashin wadata wacce ba a cika danganta sarauta da ita ba domin ya yi zambo.
Yakan nuna talauci ya kuma danganta shi da sarki ko ɗan sarkin da yake
yi wa zambo. Dubi abin da yake cewa a waɗannan ɗiyan waƙa mai amshin ‘Koma shirin daga na Bubakar, gamda’aren alƙali wan maza’:
Jagora: Ga
wani sarki ba shi da zagi.To
kuma sannan bai da
guzuri.
Garin rogo ɗai suka
ta ci da guru kowane na aza ruwa
Amma shi kau had da dama-dama
Y/Amshi: Ga
wani sarki na ta kumburi da yaranai sun sha mashi hura
Ga wani santolon uban ƙasa da yaranai wajjen guda huɗu
Ba kau mai suturar kwabo huɗu
Ya hita mota ya yi tagumi da kwandon ɗunya yay yi guzuri.
Idan aka lura za a ga cewa mawaƙin ya nuna tsananin talauci, ya kuma danganta shi da
sarki (uban ƙasa) wanda ya nuna ba shi da zagi kuma
ba shi da guzuri don nuna rashin wadata sai ya nuna cewar garin rogo suke ci da
guru. Haka nan ya nuna cewar wannan ma yana da dama a kan uban ƙasar da yake fushi da yaransa da suka sha masa fura. Haka
nan dukan yaran guda huɗu babu mai suturar kwabo huɗu. Wannan yanayi
ya yi muni ga sarki ko uban ƙasa komai
lalacewarsa.
4.4 Turken Ƙarangiya
Wannan yana ɗaya daga cikin azancin magana. Ƙarangiya tana nufin yin lugudenkalmomi ko sautuka a cikin zance.
Hakan yana samuwa ne ta hanyar maimaita wata ko wasu gaɓoɓi ko sautuka iri ɗaya ko masu kusancin furuci masu tafiya bai ɗaya (Gusau 2023:70). Makaɗa
Sa’idu Faru gwani ne na amfani da ƙarangiya a
cikin waƙoƙinsa. A yayin ƙulla zambo ma bai
yi ƙasa a gwiwa ba wajen amfani da wannan azancin magana.
Lura da abin da yake cewa a waɗannan ɗiyan waƙa:
Jagora: ‘Yan
banza da ac cikin garin Maru
Yam maidama nan suke ga Mamman
Na ishe raggo da rangama
da ragagge
Garkam marar ragowa
Katako da kattako
da mai kanta da katanga
da kanta karya
(Waƙar Alƙali Mu’azu)
A yayin ƙulla zambo mawaƙin ya yi amfani da salon Magana inda ya
yi amfani da sautukan /r/ da /g/, sannan ya yi amfani da sautin /k/ da na /t/. Kodayake salon magana ya yi amfani da shi, za a iya fahimta ɓurɓushin zambo, musamman a kalmomin raggo da ragagge da mai kanta.
4.5 Turken
Batsa
Batsa tana nufin maganar banza, musamman wadda ta danganci ambaton al’aurar
mace ko namiji (Sa’id, 2006). A irin wannan ɗiyan waƙa mawaƙin ya yi amfani da batsa a kaikaice domin ƙulla zambo, za a iya ganin
haka a cikin wasu ɗiyan waƙar Alƙali Mu’azu inda yake cewa:
Jagora: Wani
Alƙali wanda
bai kashe amre
Wai sai ya
ji wada tac ce
Yarinya ke
ji wadda nic ce
Ke ko sai na
ji wadda kic ce
In na koma gida
ki koma
Sai in binciki ƙasas shari’akki
In ji daɗin riƙa dalili.
(Waƙar AlƙaliM u’azu).
A ɗiyan waƙar da suka gabata mawaƙin ya nuna cewar wani alƙalin yana neman matan aure a
matsayin cin hanci daga baya ya kasha masu aure. A nan mawaƙin ya yi amfani da kalmomi na batsa a kaikaice a inda ya ambaci ‘Sai in
binciki ƙasas shari’akki, In ji daɗin riƙa dalili.. Wannan ba ya rasa dalili da cewar mawaƙin dattijo ne don haka bai fito fili ya yi batsa kai
tsaye ba domin duk da yana son ya aibunta abokin adawar alƙali, a ɓangare ɗaya kuma yana taka tsantsan da kare mutuncinsa na dattijo.
5.0 Kammalawa
Wannan muƙala ta kamala
wadda a cikinta an lura da cewa makaɗa Sa’idu Faru yakan yi amfani da munanan ɗabi’u na mutane da dabbobi da tsuntsaye
a yayin da yake shirya ɗiyan waƙoƙinsa masu nasaba
da zambo. haka nan an lura da cewar ya yi amfani da ƙasƙantar da
darajar mutane, musamman ‘yan sarki a yayin da yake yin zambo a waƙoƙinsa. Haka
kuma, yana amfani da ƙarangiya da batsa. Don haka ana iya cewa waɗannan batutuwa da aka ambatasu
ne ƙashin bayan
turakun da mawaƙin yake ƙulla zarensa na
zambo a cikin waƙoƙin da ya aiwatar
a lokacin rayuwarsa.
Manazarta
Bosmer, F. E.
(1983). Horses, Musicial& Gods. The Horses
Cult of Possession. Trans. Massachasetts: Bergin & Gaerney
Publishers.
Gaudio, R. P. (1998). Male Lesbians and
Other Ƙueer Notions in
Hausa. Murray. Stephen O. A. & Roscoe, Will (eds), Boy Wiɓes and Female Husbands. Studies of African Homosexualities.
New York: St Martins Press.
Gusau, S. M.
(2008). Waƙoƙin Baka a Ƙasar Hausa: Yanaye-yanayensu da
Sigoginsu. Kano: Benchmark Publishers Limited.
Gusau, S. M.
(2023). Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Kano: WT Press Printing & Publishing.
Rabeh, H. da
Darma, A. Y. (2016). “Munanan Ɗabi’un Hausawa: Waiwaye a kan ‘Yan Daudu da Yanayin Rayuwarsu”.
Argungu Journal of Language Studies. Vol.
II. Pp. 239-243.
Sa’id, B.
(2006). Ƙamusun Hausa. Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Kano: Jami’ar Bayero.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.