𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Shin ko akwai wasu adadin shekaru da sai in Mutum ya kaisune sannan yake zama baligi?
SHEKARUN
BALAGA
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Mālamai sunyi Saɓāni dangane dacewa Shin nawane adadin Shēkarun da Yāro ko
Yārinya zasuyi kāfin sukai ga balaga, akwai Mālaman da sukace Shēkarun balaga
yana fārawāne daga Shēkara-10 zuwa Shēkara-16, danhaka kenan abin yā dangantane
daga yanayin wani Mutum ɗin zuwa wani,
kokuma irin yanayin waje ko Ƙasar da Mutum yatāshi acikinta, to
amma aduk irin yanayin da Mutum yake cikinsa to dawuya yakai Shēkara-18 bā tāreda yā balaga ba.
Amma wasu dayawa daga cikin Mālamai Ma’abota Ilimi
sun tafine akan cewa balaga tanada wasu Shēkara nata na musamman, wato sune
idan Mutum yacika Shēkara-15 aduniya Mace ko Namiji to kawai yā balaga, waɗannan (Mālamai Ma’abota Ilimi) sunkafa Hujjarsu wajen faɗin hakane dawani Hadisi na Abdullāhi-Ɗan-Umar wanda Yace:
عرضت علي النبي(ﷺ) يوم أحد وأنا إبن أربع عشرة سنة فلم يجزني
ولم يرني بلغت، فعدت إليه يوم الخندق وأنا إبن خمس عشرة سنة فأجازني, (يعني ورآني قد
بلغت)،
MA’ANA:
An bijiro dani a wajen Mαиzoи Aʟʟαн(ﷺ) arānar
yāƙin Uhud alokacin inā ɗan Shēkara-14 a
duniya, amma bai bāni izinin naje yāƙinba saboda yanā ganin cewa ban
balaga ba, sai kuma nasāke dāwowa zuwa gareshi arānar Khandaƙ alokacin inā ɗan Shēkara-15 a duniya sai yabāni dāmar aje yāƙi dani, saboda yanā ganin cewa alokacin nā balaga.
Danhaka sai Mālamai sukace idan Yāro ko Yāriya
yakai Shēkara-15 a duniya to kawai yā balaga, hakanan kuma balaga zata’iya
riskar Yāro ko Yāriya koda kuwa basu kai Shēkara-15 a duniya ba indai har
gāshin gaba yatsiro musu, ko idan Yāro yayi inzālin Maniyyi ta hanyar sha’awa
kokuma mafarkin jima’i, ko Yāriya taga Jinin-Haila yāzo mata koda kuwa alokacin
Shēkarunsu basuwuce Shēkara-12 aduniya ba to shikean balaga tāzo.
шαʟʟαнυ-тα’αʟα α’αʟαмυ
AMSAWA:
Mυѕтαρнα
Uѕмαи
08032531505
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur’ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.