𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Malam. na ɗebi kuɗin mijina dubu saba’in (70K) bai sani ba amma da niyar yin sana’a daga baya in mayar masa. To kuma kuɗin gaba ɗaya sun narke hankalina ya tashi dan Allah ya sani ban ɗauka da niyar sata ba, na ɗauka da niyar mayar masa duk lokacin dana samu jarina. Bayan kuɗin sun lalace na gaya masa cewar yana bina kuɗi dubu saba’in (70K) amma bai yarda ba daga baya ya nemi sanin ya akayi yake bina kuɗi haka in gaya mai, saboda na nemi ya yafe min shi kuma yaƙi yafewa, wai sai na faɗa masa yadda akayi. Shine na rabu da maganar amma malam shin zan iya biyansa a hankali ta hanyar sana’ar da nakeyi in dinga bashi manja inna kin karɓar kuɗin har na biya sa kuɗinsa ko kuwa?
NA
SACI KUƊIN MIJINA DOMIN IN YI KASUWANCI DA SHI:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Gaskiya kin tafka babban kuskure tun farko,
watakil ma shi ya sanya jarin naki ya rushe bai yi albarka ba. Domin hakika kin
aikata cin amana adukiyar mijinki. Kuma tabbas idan har kika mutu baki tuba ba,
Allah zai yi miki hisabi akansa.
Dukiyar mijinki amana ce wacce Allah ya danka
ahannunki amatsayinki na matarsa. Kamar yadda Manzon Allah Sallallahu alaihi
Wasallam Yace : "MACE MAI KIWO CE AƊAKIN MIJINTA KUMA ZA’A TAMBAYETA GAME DA KIWON DA AKA BATA".
Kinga bisa wannan dalilin, haramun ne ki ɗauki kuɗinsa ba tare da
saninsa ba, alhali yana kulawa da abincinki da abin shanki da suturarki bai
tauye miki hakki ba. Idan kuma kika aikata haka, to kin fitar da kanki daga
cikin sahun mafiya alkhairin mataye, kuma kin shigar da kanki cikin sahun
maciya amana kamar yadda Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam Yace
"Mafi alkhairi daga cikin mataye, ita ce matar da idan ka kalleta zata
faranta maka zuciya, Kuma idan ka umurceta zatayi maka biyayya, kuma Idan baka nan
zata kiyaye maka amanar kanta da kuma dukiyarka". (Ibnu Jareer da Ibnu
Abee Hatam ne suka ruwaitoshi).
Shawarar da zan baki anan ita ce : Kiji tsoron
Allah ki fito ki gaya masa gaskiyar abinda kika aikata masa na laifi, sannan ki
nemi yafewar laifin bisa alkawarin cewa zaki biyashi kuɗinsa da kika ɗauka. Idan yace
ya yafe miki to shikenan. Idan kuma bai yafe ba, to wajibi ne ki biyashi koda
da kaɗan-kaɗan ne.
Allah Maɗaukakin Sarki
Yace. "NAGARTATTU DAGA CIKIN MATAYE, SUNE MASU YIN BIYAYYA GA MAZAJENSU,
MASU KIYAYE AMANA BISA ABINDA ALLAH YAYI UMURNIN KIYAYEWA (WATO MASU KIYAYE
AMANAR JIKINSU DA KUMA DUKIYAR MAZAJENSU).
WALLAHU A’ALAM.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.