𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum Malam. Menene Fassara Da Kuma Ma’anar
Waɗannan Sunayen. (ÃSIYA DA ZALIHA)
MA’ANAR SUNAN ASIYA DA ZALIHA:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa’alaikumus Salam Warahmatullahi Wabarkatuhu.
Yakamata mutum ya zaɓawa ‘ya’yansa sunaye kyawawa masu ma’ana kyakkyawa, ya
nisanci zaɓar sunaye munana, Annabi
sallallahu Alaihi wasallam yakasance yana duba zuwa ma’anar sunayen mutane,
idan yaga ma’anar suna mummunace saiya canzawa mutum da kyakkyawan suna.
Muslim yaruwaito hadisi(2139) daka Abdullahi dan
Umar manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam yacanzawa wata suna wanda ma’anarsa
take nufin ( mai saɓo) ya canja mata
da jamila.
Sunaye sunada dalilai na ambatarsu suna kuma da
alaƙa tsakaninsu.
Ibnul ƙayyeem rahimahullahu Yace: " Allah cikin hikimarsa da hukuntawarsa da
kaddarawarsa, yanaiwa rai ilhamar sanya suna abisa yanda za’a kirata dashi
danya dace da hikimarsa tsakanin lafazi da ma’anarsa, kamar yanda ake samun
dacewa tsakanin sababi da dalilansa.
Halaye da dabi’u da ayyuka munana suna janyo sunan
daya dace dasu, kishiyoyinsu suna janyo sunayen daya dace dasu. Kamar yanda
hakan yake tabbataccen acikin sunayen sifofi hakama yake asunayen Alam.
Ba’a ambaci Annabi sallallahu Alaihi wasallam da
Ahmad da muhammad ba, sai saboda yawan halaye da ababen yabo masu tarin yawa
atare dashi, saboda hakane tutar yabo take ahannunsa, al’ummarsa suka zamto
masu yawan godiya, shine wanda yafi dukkan halittu girman godiya ga
ubangijinsa, saboda haka yai umarni da kyautata sunaye Yace: ( ku kyautata
sunayenku) domin mai kyakkyawan suna yana iya rayuwa abisa dabi’unda suka dace
da kyakkyawan sunansa, sunansa kyakkyawa yana iya kaishi kyautata ayyukansa,
saboda haka nema zakaga mafiya yawa daka cikin magabata sunayensu sun dace
dasu, Mafi yawan daukakar dasuka samu tadace da sunayensu. " Tuhfatul
maulud ( 146-147).
Sunan ÃÃSIYA yanada ma’anoni masu yawa acikin
harshen larabci, daka ciki yana nufin magani, da tushen gini, Dukkan ma’noninsa
kyawawane.
Amma kwai (ASIYA) wanda shi kuma yake nufin mai saɓo, wanda shine manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam
yaji ana kiran wata dashi cikin sahabbai yacanja mata da (JAMILA).
Amma ZALIHA sunane na alam wanda za’a gane cewa
sunan watace, amma ma’anarsa tana nufin rauni. Shine bahaushe yake cewa,
ZALIHA, ko ZULAI, ya halatta sanyawa mutum shi batare da la’akari da hararo ma’anarsa,
lokacin sawa mutum shi.
WALLAHU A’ALAMU.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur’ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.