𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Menene
hukuncin sakin mace alhali tana cikin biƙi (jinin haihuwa)? Sannan ya ya lissafin iddarta zai kasance?
HUKUNCIN SAKIN MACE CIKIN JININ BIƘI (JININ HAIHUWA)?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah Wa
Barakaatuh.
Mai haila ce aka hana miji ya sake ta, saboda
maganar Allaah Ta’aala:
يَاأَيُّهَا النَّبِيُّ إِذَا طَلَّقْتُمُ النِّسَاءَ فَطَلِّقُوهُنَّ
لِعِدَّتِهِنَّ
Ya kai Annabi! Idan za ku saki mata, sai ku sake
su ga fuskantar iddarsu. (Surah At-Talaaƙ: 1).
Shiyasa lokacin da Ibn Umar (Radiyal Laahu
Anhumaa) ya saki matarsa a cikin haila, sai Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi
Wa Alihi Wa Sallam) ya sa shi ya mayar da ita, ya ƙyale ta har sai ta yi tsarki, ta sake yin wata
hailar, kuma ta sake yin tsarki, sannan inya ga daman sake sakin sai ya sake ta
a lokacin, kafin ya kusance ta. Ya ce:
«فَتِلْكَ العِدَّةُ الَّتِي أَمَرَ اللَّهُ أَنْ تُطَلَّقَ لَهَا
النِّسَاءُ»
Wannan ce iddar da Allaah ya yi umurnin a saki
mata a halin suna fuskantar ta. (Sahih Al-Bukhaariy: 5251, Sahih Muslim: 1471).
Amma mai ciki ko mai naƙuda ko mai jego ko mara lafiya da sauransu, ba a
hana sakin ta ba, matuƙar dai sharuɗɗan sakin sun
cika. Kamar na kasantuwar ita ɗin matar aurensa
ce a haƙiƙa, kuma shi ɗin mijinta ne
baligi mai hankali, kuma mai zaɓin rai, da
sauransu.
Haihuwar da matar ta yi dalili ne a kan cewa tana
cikin shekarun yin haila kenan. Kuma tsawon iddar irin wannan matar shi ne
haila uku, kamar yadda Ubangiji Ta’aala ya faɗa:
وَالْمُطَلَّقَاتُ يَتَرَبَّصْنَ بِأَنْفُسِهِنَّ ثَلَاثَةَ
قُرُوءٍ
Kuma matan da aka sake su sai su yi haƙuri da kawunansu har
tsawon ‘ƙur’u’ uku. (Surah
Al-Baƙara: 228).
Duk da kasantuwar malamai sun sha bamban a kan ma’anar
‘ƙur’u’ a nan, amma dai
maganar da ta fi ƙarfi in sha’al Laah, ita ce
ta waɗanda suka ce: Haila ake nufi. Saboda hadisin da Annabi
(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya faɗa wa wata mace cewa:
«دعِي الصَّلاةَ أَيَّامَ أَقْرَائِكِ»
Ki daina yin sallah a kwanakin ƙuru’inki. (Al-Arna’uut
ya sahhaha shi a cikin takhreejinsa ga Sharhus Sunnah: 9/207).
Kuma abu ne sananne cewa, mata suna barin yin
sallah ne kawai a ranakun da suke yin haila.
Wannan fassarar ta ƙur’u kuma ita ce aka riwaito daga Abubakar As-Siddeeƙ, da Umar, da Uthman, da
Aliyu, da Abud-Dardaa’i, da Ubaadah Bn As-Saamit, da Anas Bn Maalik, da Ibn Mas’ud,
da Mu’aaz, da Ubayy Bn Ka’ab. da Abu-Musa Al-Ash’ariy, da Ibn Abbaas (Radiyaal
Laahu Anhum). Sannan kuma daga: Sa’eed Bn Al-Musayyib, da Alƙamah, da Al-Aswad, da
Ibrahim, da Mujaahid, da Taawus, da Sa’eed Bn Jubair, da Ikrimah, da Muhammd Bn
Seereen, da Al-Hasan, da Ƙataadah, da As-Sha’abiy, da Ar-Rabee’, da Muƙaatil Bn Hayyaan, da As-Suddiy, da Mak-huul, da
Ad-Dahhaak, da Ataa’u Al-Khurassaniy (Rahimahumul Laah). (Haka Al-Hafiz Ibn
Katheer ya ambato a cikin Tafseerul Ƙur’anil Azeem: 1/608).
Don haka, sai wannan matar ta lissafa zuwan jinin
hailarta har sau uku bayan ta gama jinin biƙin. Idan ta yi wanka a bayan ta tsarkaka daga jini
na uku, to ta gama iddarta kenan. Sai ta yi aure, in tana buƙata.
Shi kuma mijin da ya sake ta lallai ya san cewa
akwai sauran nauye-nauyen aure a kansa matuƙar ba ta gama iddarta ba.
* Haƙƙin ciyarwa, da shayarwa, da magani, da mazauni a gare ta da abin ta haifa
duk suna wuyansa, ba su sauka ba.
* Idan kuma ɗayansu ya rasu
kafin cikar iddarta, to akwai gado a tsakaninsu.
* A cikin iddar kuma yana iya yin kome (wato ya
mayar da ita ga matsayinta na matarsa), ko da ita ko waninta bai yarda ba, matuƙar dai sakin ba na ƙarshe ba ne.
Wal Laahu A’lam.
Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy
+2348021117734
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur’ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.