TAMBAYA (170)❓
Assalamualaikum, Malam dafatan antashi lafiya
barka da safiyar Juma a. Don Allah Malam menene maganin matsafa masu dauke
kuruwar amfanin gona. Agaskiya da anabani labarin cewa ana dauke kuruwar
amfanin gona bana yarda. To amma yanzu gona ta kullum abin sai ƙara raguwa yakeyi.
Dama makwabta na sun camfi wani mutum Wanda keda gona a tsakanin gonakin mu da cewa yakan iya dauke kuruwar amfanin gonar wani zuwa tasa gonar. Abinda na kula shi ne ,gonar shi ko Rabin tawa batayi ba Amma yakan dibi amfanin da ni Mai babban gona bana diba Kuma ba gyara gonna tashi yake yi fiye damu ba. Don Allah Malam in akwai wata addua ta musamman a taimaka mana don kare gonakin mu. Nagode 🙏
Ai ganin wannan labarin ne yasa na tuna da wannan
matsalar tawa Malam. Don baka fayyace mana irin addu,o in da kabashi ba. Shi
yasa nayi wannan tambayar kozan sami mafita. Don agaskiya abin Yana damu na,
har ma Ina tunanin hakura da noma gonar. Duk da cewa gona ce da na gada awajen
mahaifina.
ƁARAYIN GONA
AMSA❗
Waalaikumus Salam Warahmatullahi Wabarakatuhu
Lahaula wala ƙuwwata illa billah
Shi wancan mutumin indai ya tabbata Haka yake to
tabbasfa da akwai taimakon bokaye a lamarinnasa Kuma Duk Wanda ya je wajen Dan
duba to sallarsa ta Kwana 40 baa amsarta
Wanda Kuma ya yarda da Dan duba to haƙiƙa ya kafircewa abinda aka saukarwa da Annabi
Muhammad Sallallahu alaihi wasallam
A shawarce kayi masa tsayuwar dare ta hanyar miƙawa Allaah kokenka
sannan Kuma Abu na biyu shine kaje ka samu mutumin ka ƙulla alaƙar kasuwanci dashi
Ka biyo Masa ta inda yake da naƙasu (weakness point) ma’ana
tunda son abin duniyane a gabansa to ka bincika sana’arsa sannan ka ƙulla alaƙar business dashi ka
dinga yi masa ihsani idan kuma wannan abinda yake mara kyau shi ya maida sanaa
to dukda haka ka dinga yi masa ihsani
Idan ya gano cewar wannan gonarka ce to tabbas
bazai sake ƙoƙarin cutarka ba in Sha
Allaah
Kowacce mas’ala tanada mafita saboda dukkan
tsanani yana tareda sauƙi kamar yanda Allaah Subhanahu wataala ya fada a Ƙur’ani mai girma
Wallahu taala aalam
Subhanakallahumma wabi hamdika ash-hadu anla’ilaha
illa anta astaghfiruka wa’atubi ilayk
Amsawa:
Usman Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.