Ticker

6/recent/ticker-posts

Jinin Haila Yazo Min Lokacin Shan Ruwa (Buda Baki)

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Menene Hukuncin Wacce Tana Azumi Lokacin Shan Ruwa Sai Jini Yazo Mata?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Idan Haila tazowa mace tana cikin azumi, azuminta ya lalace, koda jinin yazo matane kafin magariba koda da second ɗaya ne, wajibine ta rama azumin idan na wajibi ne, haramunne taci gaba da azumi tana haila.

Imamun Nawawi yace: Al'umma ta haɗu akan haramcin azumi ga mai haila da jinin haihuwa, koda sunyi azumin bai yiba, Al'umma ta haɗu akan wajabcin rama azumin ramaān akansu, Turmuzi da ibnu Munzir da Ibnu jareer da Malamanmu sun ciro ijma'i akai.

Al-maj-mu'u (2/386).

Ibnu qudama yace: Malamai Sun haɗu akan mai haila da mai jinin biqi bai halatta musu suyi azumi ba, zasu sha azumi zasu rama, idan sukayi azumi baiyi ba, Aisha Allah yaqara yarda da ita tace: ( Mun kasance Muna Haila azamanin Annabi Sallallahu Alaihi wasallam, yana Umartarmu da Rama azumi, ba'a umartarmu da Rama Sallah.) Bukhari da Muslim.

Abu Sa'idin yace: Annabi Sallallahu Alaihi wasallam yace: ( shin idan dayanku tana haila bakuga bata sallah bata azumi ba, wannan shine tawayar addininta) Bukhari.

Haila da Biqi ɗaya suke, domin jinin biqi shine na haila, hukuncinsa shine hukuncinsa, duk lokacin da aka samu haila awani yanki na rana azumi ya lalace, a farkon rana ne ko aqarshen rana, idan mai haila ta qudurci niyyar azumi ta kame daka ci da sha tare da masaniyar haramcin hakan, ta aikata saɓo azuminta bayi ba. Kamar yanda Shaik Uthaimeen ya fada acikin littafinsa " Addima'ul dabi'iyyah lil nisa'i" shafi na (38).

Fatawa lajnah sukace: Idan haila tazowa mace kafin faduwar rana azuminta ya lalace, amma idan bayan rana ta faɗi, bata kai ga shan ruwa ko kiran Sallah ba, azuminta yayi, ba zata rama Shi ba.

idan kafin faduwar rana yazo mata, azumi ya ɓaci, zata rama shi, idan bayan rana ta faɗi ne, azuminta yayi bazata rama ba.

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments