TAMBAYA (91)❓
Assalamualaikum warahmatullah MLM mene alaqar addini da dariqa, kamr kadiriyya tijjaniyya halissunnah shin yazama dole mutum seya kasance yna cikin Daya dga cikin wayennan NE ko y abin yake, sbd ni a iya sanina ban tabajin ance manzon Alalh Dan dariqa kaza ne Ko Dan dariqa kaza ba don Allah Karin bayani nke bukata ahuta lfia se naji amsa ta
AMSA❗
Alhamdulillah
Da farko dai, batu akan rarrabuwar kan al'umma abune wanda
yake dole, ba makawa sai anyi shi kamar yanda Annabi Sallallahu alaihi wasallam
ya fada
Annabi (SAW) yace: "Duk wanda a cikinku ya rayu, bayan
na rasu, to zai gai manyan fitintinu iri-iri"
Abu Dawud (4067), al-Albaani ya inganta hadisin a cikin
Sahih Abu Dawud
Kungiyoyi sun bayyana a bangaren siyasa da kuma aqida, a
bayan zamanin kalifofi shiryayyu wato Khulafa'ur Rashidun (Abubakar, Umar,
Uthman da Aliyu, Allah ya kara musu yarda baki daya), kamar irinsu kungiyar
Shi'ah, Murji'is da Khaawarij
Cikin rahamar Allah Azzawajallah, ya tsara cewar wadannan
kungoyoyi zasu bayyana ne yayinda musulmai suka qyale hanyar daidai, suka
kirkiro tsarinsu na son rai, kuma ana iya gane su ne ta hanyar sunan da suke
dauke dashi. Don haka aqidar Ahlus Sunnah Wal Jama'ah da kuma aqidar mafi yawan
musulmai babu wani kokwanto ko kuma shakku a cikinta sabanin sauran aqidun can
na bidi'ah da suke alaqanta kansu da sunan wanda ya fara kafa kungiyar. Zaka
gane haka a lokacin da ka kalli sunayen aqidojin kamar irinsu Shi'ah wanda su
gaba daya ma suna danganta kansu ne da Kungiya kuma Allah Azzawajallah yace
kada ku zamo Shi'an wato kada rarrabe ku zamo kungiya kungiya
Shahararren hadisin da yayi bayani akan rarrabuwar kungiya
shine hujja akan hakan
An karbo daga Mu'awiyah Bin Abu Sufyan, yace: Annabi
Sallallahu alaihi wasallam yace: "Wadanda suka gabaceku daga cikin mutanen
da aka bawa littafi sun rarrabu kaso 72, wannan al'ummar tawa kuma zata kasu
kaso 73, kaso 72 duk yan wuta ne, kaso 1 ne kadai yan Aljannah, wadannan sune
Jama'ah"
Abu Dawood (4597) da wasunsa; al-Haakim yace Sahih Hadith ne
da yake nuna muhimmancin aqidah (1/128), Ibn Hajar al-Asqalani yace Sahih
Hadith ne, a cikin Takhreej al-Kashshaaf (63). Ibn Taymiyah yace Sahih Hadith
ne a cikin Majmoo’ al-Fataawa dinsa (3/345), haka ma Imam al-Shaatibi a cikin
al-I’tisaam (1/430), da kuma al-‘Iraaqi a cikin Takhreej al-Ihya’ (9/133)
Malaman Ahlus Sunnah da yawa sun rawaito wannan hadisi,
hakama Sahabbai da isnadai dayawa, akan cewar al'ummar nan zata rabu kaso 73
Annabi Sallallahu alaihi wasallam ya kira su da
"Jama'ah" ma'ana "Ijma'in malaman musulunci" a wata riwayar
kuma "adadi masu yawa" kamar yanda yazo a cikin Hadisin Abu Umaamah
da wasunsa, wanda aka rawaito daga Ibn Abi ‘Aasim a cikin al-Sunnah dinsa
(1/34) da kuma al-Tabaraani a cikin al-Mu’jam al-Kabeer (8/321), da isnadi
hasan li ghayrihi (saboda tarin hujjojin hadtarin
Haka kuma Annabi Sallallahu alaihi wasallam yayi bayaninsu a
wani hadisin, yace: "Al'ummata zasu rabu kungiya 73, kowannensu zasu shiga
wuta face kungiya 1". Sai sahabbai (Radiyallahu anhum) suka ce: Su wanene
ya Rasulullah ?. Sai yace: "Sune masu bin abinda nake akai tare da
sahabbai na"
Kamar yanda aka rawaito daga ‘Abdallah ibn ‘Amr ibn al-As,
kamar yanda Imam al-Tirmidhi ya kawo shi (2641). al-‘Iraaqi yace Sahihi ne a
cikin Ahkaam al-Quran (3/432), da kuma Takhreej al-Ihya’ (3/284) sannan kuma
Imam al-Albaani ya hassana shi a cikin al-Tirmidhi.
Da wadannan hujjojinne musulmi zai gane hakikanin gaskiyar
hanyar da ya kamata ya bi, ta malaman hadisi wadanda aka yarda da iliminsu,
kuma hanyar Salaf-Us-Saleh wato mahangar Sahabbai, Tabi'ai da Tabi'ut'tabi'in,
da kuma limaman shiriya na mazhabobinnan guda 4 (Imam Ahmad Bin Hanbal, Imam
Malik, Imam ash-Shafi'i, Imam Abu Hanifa) da sauran magabata na kwarai tareda
taka tsantsan don gudun fadawa hanyar yan bidi'a
Shaykh al-Islam Ibn Taymiyah (Rahimahullah) yace:
"Alamun musulmi dan Bidi'ah shine zaka ga baya bin tafarkin Salaf"
Majmoo’ al-Fataawa (4/155)
Haka kuma yace (3/346): "Alamun wannan kungiyoyi guda
72 da suka barranta daga Ahlus Sunnah wal-Jama'ah sune zaka ga sun bar koyarwar
Qur'ani, Sunnah da Ijma'in malamai. Duk wanda yake bin Qur'ani da Sunnah da
Ijma'in malamai wannan shine wanda yake kan tafarkin Ahlus Sunnah wal-Jamaa'ah
Abune wanda bazai taba yiwuwa ba kace ai shiryayyu ko
zababbu a cikin 73 dinnan sune kungiyar Shi'ah, ko kuma kace sune karkatattun
Sufaye, ko Khawaarij ko Habashis. La, saidai su wadannan kungiyoyi ne na
bidi'ah wadanda basa kan hanyar daidai. Gaba dayansu basu yarda da Sayyadina
Abu Bakr, ‘Umar, ‘Uthmaan ko ‘Ali (Radiyallahu anhum) ba, ko kuma Imam Abu
Haneefah, Maalik, al-Shaafa’i ko Ahmad ibn Hanbal ba.
Shin akwai wani a cikin yan Adam mai hankalin da zai ce
wadannan bayin Allah din basa kan shiriya ?
Yi tunani da nazari akan wannan tambayar. Ko iya hujjojinnan
ma sun isa su tabbatar maka cewar akwai banbanci mai girma tsakanin Ahlus
Sunnah wal-Jama'ah da sauran kungiyoyin Bidi'ah
Ibn Taimiyya (Rahimahullah) yace
Ahlus Sunnah sal-Jama'ah sune kungiyar shiryayyu la'akari da
sune mafi yawa (ta bangaren fahimtar addini akan sunnah), sauran kungiyoyin
kuma suna bin zato ne da son zuciyoyinsu, kuma babu ko daya daga cikinsu wanda
ya kama kafar kusantar adadin yawan kungiyar shiryayyu (Ahlus Sunnah)
ballantana kuma yayi daidai dasu
Zaka gansu yan qalilan, kuma ana gane su ne ta hanyar yanda
suke watsi da hujjojin Qur'ani da Sunnah da Ijma'in malamai. Masu bin Qur'ani,
Sunnah da Ijma'i, wadannan sune Ahlus Sunnah wal-Jama'a
Majmoo’ al-Fataawa (3/346)
Imam Al-Shaatibi (Rahimahullah) ya zayyano sunayen wadannan
halakkakun kungiyoyin a cikin littafin al-I'tisaam (1/453-460)
Na biyu kuma;
Malaman Ahlus Sunnah wal-Jama'a sun yi bayani a cikin
littattafansu cewar sauran kungiyoyin sune karkatattun yan Bidi'a kuma sun
cancanta su shiga wuta saboda bidi'o'in da suka shigar a cikin addinin Allah
Azzawajallah. Saidai kuma duk da haka ba kafirai bane ba, musulmai ne wadanda
bazasu dawwama a cikin wuta ba
Shaykh al-Islam Ibn Taymiya (Rahimahullah) yace: "Haka
kuma, munafukan da suke a cikin kaso 72 din, wadannan Kafirai ne amman su
ragowar wadanda ba munafukan cikinsu ba su ba kafirai bane ba duk da yawan
zunubbansu. Wasun su suna da daya daga cikin rassan munafurci ko kuma ba su da
kalar munafurcin da zai kai zu cikin wuta
Duk wanda kuma yace, kowanne daya daga cikin kaso 72 dinnan
kafiri ne to maganarsa ta ci karo da Qur'ani, Sunnah da Ijma'in Sahabbai da
kuma Ijma'in malaman mazhabobi 4 da sauransu. Babu wanda yace dukkan kaso 72
din kafirai ne saidai wasu daga cikinsu ne kafiran
Majmoo’ al-Fataawa (7/218)
Hakan na nufin ba kowanne mutum wanda ya kira kansa musulmi
bane musulmi na gaskiya, a'a saidai zasu iya zama kafirai da kuma masu ridda
kamar irinsu Shi'ah Raafidis, da kuma Sufayen da suka wuce gona da iri, da kuma
kungiyar Baatiniyya kamar irinsu Druze, Nusayris da sauransu. Wadannan duk sun
fita daga musulunci kuma ba'a saka su a cikin kaso 72 dincan na Hadisi
Na uku;
Dalilin samun rabuwar kan al'ummah kamar yanda hadisin ya
tabbatar, yana da alaqa da addini da kuma aqeedah, bawai banbancin ra'ayi na
fiqhu ba
Al-Shaatibi (Rahimahullah) yace: "Wadannan kungiyoyi ne
saboda sun banbanta da shiryayyu ta bangaren addini da kuma shari'ah, bawai
akan kananan abubuwa ba saboda samun banbanci akan kananan abubuwa ba ya kaiwa
ga rabuwa, ana samun rarrabuwar kai ne silar banbance-banbancen da suka shafi
addinin musulunci"
Al-I’tisaam (1/439)
Idan har wata kungiya ta musulmai ta ware kanta daga wasu
saboda salon da'awah da kuma wasu ayyuka na addini, amman basu ci karo da
aqidar Ahlus Sunnah wal-Jama'ah ba, hakan bazai sa a kira su da dulmiyayyu ba,
saidai su shiryayyu ne, ma damar suna bin koyarwar Sahabbai da Tabi'ai a aqida
da kuma ayyuka
Dangane da kungiyoyin Tijjaniyya, Qadiriyya da sauransu,
wadannan suma suna bin abinda wadanda suka fitarda kungiyar suka tsara ne.
Tijjaniyya suna bin abinda Ahmad Tijjani ya kawo, suna amfani da littattafai
irinsu "Jawaahirul Ma'ani" da kuma "Jawaahirul Masa'id"
wanda Ibrahim Inyas ya rubuta, kuma littafin cike yake da shirka kala-kala
Idan kana son gane mecece dariqar Tijjaniyya, ka je ka
karanta littafin "ad-Dariqatut Tijjaniyya" da kuma "Shaikh Inyas
as-Singali" wallafar Prof. Dahiru Maigari (wanda shi Prof. a gidan kaulaha
ya taso, shine yayi project/thesis dinsa na PhD akan wannan dariqar)
Kungiyoyi 72 dincan sune suka fantsama suka kara fitarda
wasu sabbin kungiyoyin masu zaman kansu a yanzu, ma'ana, kungiyar Sufanci itace
ta haifi Tijjaniyya
Duk zaka ga sunan kungiyoyin yana komawa ga sunayen mutanen
da suka kirkirosu, kamar Qadiriyya, asalinta, Abdulqadir Jilani da dai sauransu
Haka kuma idan muka duba littattafai irinsu "Then I was
Guided" wallafar Muhammad al-Tijani, wanda da ya kasance dan Shi'ah ne
amman daga baya ya koma dariqar Tijjaniyya, shine ya rubuta wancan littafin
ma'anarsa shine: "Yanzu na shiryu", a tunaninsa shiriya tana cikin
dariqar Tijjaniyya ba Shi'ah ba, zamu gane cewar indai ba Ahlus Sunnah
wal-Jama'ah ka bi ba to dole zaka bi hanyar wadancan dariqun
Yakai dan uwa, mai tambaya, ina roqon Allah ya jikanmu da
rahama, cewar baka taba jin Annabi Sallallahu alaihi wasallam ya bi dariqa ba
wannan haka yake amman ya dora Sahabbansa akan tafarki madaidaici wato bin
sunnarsa
Ko dai mu bi sunnar sa ko kuma mu bi wata dariqar. Zabi ya
rage ni da kai da sauran musulmai
Kuma mu sani cewar Munkar da Nakir, ba zasu tambaye ka
Minhaj dinka a kabari ba, saidai za su tambaye ka: "Menene
addininka", idan ka ce musu Izala to wuta zaka je, Tijjaniyya wuta,
Qadiriyya, Shi'ah duk ba ruwansu da wannan amsar, saidai kace musu, addini na
shine musulunci
Kenan Ahlus Sunnah ko kuma Salaf minhaji ne ma'ana hanyace
ta neman ilimin addini ta yanda mutum bazai fada Bidi'ah ba
Duk da amsar zata ci karo da son zuciyar wasu to amman ita
gaskiya daci ne da ita kuma bulalar kan hanyace, fyadi yaro fyadi babba. Ya
kake tunani idan mai ciwo ko kurji yana son rabuwa da wannan gwalandon, idan
aka kaishi asibiti dole ya hakura a diddirje wannan gwalandon ko zaiyi kukan
jini kuwa, to kamar haka ne shi ma wannan rubutun, ana so a gyara aqidar mutane
ne, kuma zafin gyaran yafi zafin wanda akewa dorin karaya, kuma hujjojine
gasunan muraran a rubuce ga duk dalibin ilimi mai son gaskiya sai ya dubo su.
Ban bada amsar nan da son zuciyata ba, tunda magana ake ta aqidah, sannan idan
akwai gyara sai a sanar damu mu bi diddigi mu gyara
Ina fatan dan uwa ya gamsu da amsar tambayarsa
Allah ya tabbatar damu akan bin Sunnar Annabi Sallallahu
alaihi wasallam bisa minhajin Salaf (magabata na farko)
Wallahu ta'ala a'alam
Amsawa
Usman Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.