Ticker

6/recent/ticker-posts

Ɓoye Aibu Kafin Kulla Aure

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Mutum ne ya auro mace mai fama da wani rashin lafiyar da ba a gaya masa ba, sai a bayan auren ne ya gano. To dole ne ya nema mata maganin wannan matsalar?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.

Haƙƙi ne a kan maaurata tun kafin a ƙulla aurensu su sanar da junansu duk wani aibu ko rashin lafiyar da zai iya zama tarnaƙi ko matsala a wurin jin daɗin zamantakewarsu a bayan aure, bai halatta su ɓoye shi sai a bayan auren a gano ba. Idan kuma suka yi sakacin haka, to ya halatta ga wanda aka yi masa wannan rufa-rufar ya warware auren a lokacin da ya gano hakan.

Sai dai kuma ba kowane irin rashin lafiya ne ake warware aure saboda shi ba. Malamai sun yi bayanin cewa hakan na tabbata ne kawai a kan cututtukan da samuwarsu ke hana jin daɗin zaman auren, kamar rashin ƙarfin ikon saduwa a wurin namiji, ko toshewar gaba a wurin mace, ko kuma kuturta a wurin ɗayansu.

A asali miji ya nema wa matarsa magani a kan duk wani rashin lafiyar da take fama da shi yana daga cikin haƙƙoƙinta a kansa, kamar yadda Allaah (Subhaanahu Wa Taaala) ya ce

وَعَاشِرُوهُنَّ بِٱلۡمَعۡرُوف

Kuma ku rayu da su a cikin alheri. (Surah An-Nisaa’: 19).

Kuma ba rayuwa a cikin alheri ba ce miji ya bar matarsa haka nan a cikin zogi da raɗaɗin ciwo ko rashin lafiya, ya nuna halin ko-a-jikinsa! In kuwa haka ya kasance, to ina ƙauna da tausayin juna da Allaah ke sanyawa a tsakaninsu kenan?!

Amma idan ya zama wani abu ne da aka ɓoye masa, aka yi masa rufa-rufa ba a sanar da shi tun kafin ƙullin auren ba, to yana da yancin ya mayar da ita ga waliyyanta don su yi mata maganin matsalar sannan ta dawo, kamar dai yadda yake da ikon warware auren, ya ce ya fasa, muddin dai wannan matsala ce da take hana jin daɗin zaman auren a tsakaninsu, kamar yadda ya gabata.

WALLAHU A'ALAM

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

08164363661

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments