Ticker

6/recent/ticker-posts

Zuga Tubalin Gina Siyasa: Tsokaci Daga Waƙoƙin Siyasar Zamani

Takardar da aka tura wa Biram Journal Of Contemporary Research In Hausa Studies, Sule Lamiɗo University, Kafin Hausa, Jigawa State, Nigeria.

www.amsoshi.com

ZUGA TUBALIN GINA SIYASA: TSOKACI DAGA WAƘOƘIN SIYASAR ZAMANI

Daga:

ALIYU RABI’U ƊANGULBI
JAMI’AR TARAYYA GUSAU
GSM NO. 07032567689 0R 07088233390
EMAIL: aliyurabiu83@gmail.com

TSAKURE

Waƙa aba ce mai muhimmancin gaske a fagen isar da saƙo cikin hanzari ga alumma. Ana amfani da ita wajen yaɗa manufofi na kowane fanni na rayuwar yau da kullum, cikinsu har da harkokin siyasa. Wannan maƙala mai take, ’ Zuga Tubalin Gina Siyasa: Tsokaci daga waƙokin siyasar zamani, za ta tattauna a kan gudummawar da zuga a cikin waƙokin siyasa yake takawa ga gina siyasa a Nijeriya. Mawaƙan siyasar zamani mutane ne da ke amfani da damarsu wajen yaɗa manufofin jam’iyyun siyasa da ‘yan takara domin faɗakar da al’umma a kan muhimmancin zaɓen shugabanni nagari. Zaɓen mutanen kirki shi ne tubalin gina siyasa a tsarin mulkin farar hula, wato siyasa. Salon zuga da mawaƙa ke amfani da shi cikin waƙoƙinsu, wata dabara ce ta jawo hankalin yan siyasa da sauran al’ummar ƙasa baki ɗaya, su fahimci irin tasirin da shugabanci nagari ke yi ga gina siyasa mai ɗorewa a ƙasa. Shugabanci nagari, wanda shi ne tushen samun zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki da adalci tsakanin masu mulki da waɗanda ake mulka. Wato, zuga dabara ce da mawaƙan siyasa ke amfani da ita domin su harzuka ‘yan siyasa su nemi tsayawa takarar kowace kujera ta siyasa; don a fafata da su ko da kuwa ba su cancanta ba. Saboda haka, wannan takarda za ta mai da hankali ne ga nazarin gudmmawar da zuga ke bayarwa wajen kambama ‘yan siyasa da shugabanci da jam’iyyun siyasa da ‘yan takara da hana maguɗin zaɓe da ha’inci ko cin hanci da rashawa da ke yi wa siyasar zamani barazana a Nijeriya. Wato, takardar za ta tattauna a kan muhimmanci kyawawan ɗabi’u da gaskiya da riƙon amana waɗanda ke haifar da samuwar mulkin adalci da gina siyasa ɗorarriya a ƙasa.

1. 0 Gabatarwa

Kyawawan ɗabi’u da nagarta su ne abubuwan da suke ƙoƙarin zama tarihi a siyasar Najeriya. Wannan dalili ne ya sa ‘yan siyasar zamani suke kutsa kansu a siyasa ba tare da sun kyautata halaye da ɗabi’unsu ba. Dangane da haka ne, sai mawaƙan siyasa suka sami damar yin amfani da salon zuga domin su kambama kowane ɗan siyasa da ya nuna ra’ayinsa ga tsayawa takara, ko da kuwa ba shi da ɗabi’u nagari; matumƙar dai yana da abin hannunsa, (Ɗangulbi: 2003). Yin haka ya saɓa wa tsarin siyasa ta gina ƙasa. Saboda haka matuƙar ana son siyasa ta gina ƙasa, dole mawaƙan siyasa su mai da hankali wajen Zuga mutane masu ɗabi’u nagari domin su tsaya takara don a sami kyakkyawan mulkin siyasa. Don haka, zuga wani salon kambamawa ne, ko ingiza ‘yan siyasa su yi gogayya da shahararrun ‘yan siyasa a fagen neman kowane muƙami na siyasa. Mawaƙan siyasar zamani suna amfani da shi domin su cusa wa matasan ‘yan siyasa son shugabanci. Mawaƙan siyasa suna amfani da zuga domin su jawo hankalin ‘yan siyasa da sauran al’umma su zaɓi mutanen da za su iya kawo wa ƙasa ci gaba a siyasance.

1. 1 Manufar Bincike

Gurin wannan maƙala shi ne ta faɗakar da al’umma game da gudummawar da zuga yake bayarwa wajen gina siyasa mai ɗorewa a Nijeriya. Manufar gudanar da wannan bincike ita ce, a nazarci yadda zuga da mawaƙan siyasar zamani ke amfani da shi cikin waƙoƙinsu yake da muhimmanci wajen wayar da kan al’umma. Saboda da haka ƙudurin wannan muƙala sun haɗa da :

a. Gudummawar da zuga ke bayarwa wajen jawo hankalin ‘yan siyasa su kasance masu gaskiya da riƙon amana.

b. Yadda zuga yake taimakawa wajen tallata manufofi da aƙidun kowane dan takara cikin waƙoƙin siyasar zamani.

c. Harzuƙa yan siyasa su jajirce wajen fuskantar kowane irin kalubalen siyasa da ka iya yi masu barazana ga siyasarsu.

d. Nazarin saƙon da zuga yake ɗauke da shi cikin waƙoƙin siyasar zamani da nufin fito da tasirinsa wajen gina siyasa mai ɗorewa.

1. 2 Tambayoyin Bincike

A tsarin gudanar da kowane irin bincike, ana tsara tambayoyi ne domin su zama jagora ga mai bincike wajen samar da ingatattun bayanai da suke da alaƙa da wannan binciken. Daga cikin tambayoyin wannan bincike akwai:

a. Wace gudummawa ce zuga yake bayarwa wajen gina kyakyawar siyasa. ?

b. Ko zuga ya taimaka wajen tallata kyawawan ɗabi’un ‘yan siyasa da manufofinsu?

c. Ko zuga ya taimaka wajen harzuƙa yan siyasa wajen tsayawa takara?

d. Wane muhimmin saƙo ne zuga yake ɗauke da shi zuwa ga al’umma dangane da gina siyasa mai ɗorewa?

1. 3 Ma’anar Zuga

Zuga wata magana ce, wadda mawaƙan Hausa na baka ko rubutacciya ke amfani da shi domin su ingiza ko harzuƙa wani mutum ya aikata wani abu wanda ba zai iya yin sa ba, idan yana cikin hankalinsa. Wani lokacin kuma, zuga yana nufin kambama wani mutum ya ji cewa ba wani mutum da ya kai shi ƙarfi ko hazaka ko dukiya ko daraja ko kyauta a duniya. Zuga ya samo asali daga zuga-zugi da makeran gargajiya ke amfani da su wajen hura wuta a maƙera, domin su gasa ƙarfe ya yi ja da laushi kafin a sarrafa shi zuwa wani abin amfani. Ana sarrafa baƙin ƙarfe zuwa wasu abubuwan amfani da suka haɗa da kwashe, da wuƙa da galma da sauran kayan amfanin gida da gona. Yadda ake amfani da zuga-zugi a hura wuta a maƙera har ruru ta gasa ƙarfe ya yi ja, haka zuga da ake yi wa mutum kan harzuƙa wanda aka yi wa, ya kumbura ya aikata wani abin bajinta ko akasin haka.

1. 4 Asalin Kalmar Zuga

Kalmar zuga ta samo asali daga zuga-zugi da maƙeran gargajiya suke amfani da su wajen hura wuta, su gasa karfe ya yi ja, kafin su sarrafa shi zuwa wani abin amfani kamar kwashe ko galma ko wuƙa da sauransu. An sami wannan bayani daga Salisu Zakari, (sarkin maƙera Bagega), ƙaramar hukumar mulki ta Anka, jihar Zamfara. Ya ƙara da cewa zuga-zugi wasu fatun awaki ne da ake jemewa a ɗinka su kamar jikuna da baki wanda ake liƙa masu kwarkwaron ƙarfe domin ya ba da iska kai tsaye ga ramin maƙera. Hausawa sun aro wannan kalma daga waɗannan fatun awaki da ake kira zuga-zugi, suka riƙa amfani da ita a cikin maganganunsu na yau da kullum. Haka kuma a cikin waƙoƙin Hausa ana amfani da kalmar domin a harzuƙa mutum ya aikata wani abin bajinta ko wani abin alheri ko akasin haka.

Mawakan Hausa, musamman na siyasa suna amfani da zuga a cikin wakokinsu domin su kambama ‘yan siyasa su ji cewa sun fi sauran mutane kwarjini. Wato, zuga wani salo ne da mawaƙan Hausa ke amfani da shi wajen jawo hankalin mutane su fahimci wani saƙon da ake son su sani game da wanda ake zugawa. Masana da manazarta sun tofa albarkacin bakinsu wajen bayyana ma’anar kalmar zuga. Bergery, (1934), da Oxford Dictionary (9th edition) da Bunza (2009), dukkansu sun yi ittifaƙi da cewa, zuga wata magana ce da ake furtaw domin a harzuƙa ko a kambama wani mutum ya aikata wani abu da ba zai iya aikatawa ba, idan yana cikin hayyacinsa. Bunza ya ƙara da cewa, zuga da kirari tamkar ɗan juma ne da ɗan jumai wajen taka muhimmiyar rawa a fagen isar da saƙo. Ya ƙara da cewa, idan zuga ya amshi sunansa, dole ne a ji amon kalmomin yabo a cikinsa, domin zuga wata dabara ce da mawaka ke amfani da ita a cikin waka ta hanyar ambaton wasu kyawawan ɗabi’u da ayyukan bajinta da iyaye da kakanni suka aikata domin su isar da saƙo ga masu sauraren waƙoƙinsu.

A taƙaice zuga wata magana ce, wadda ake furtawa zuwa ga wani mutum domin a harzuƙashi ya aikata wani abu da ba zai iya aikata shi ba, matuƙar yana cikin hankalinsa. Mawaƙan siyasa suna amfani da zuga a cikin waƙoƙinsu wajen kambama yan syasa su ji cewa suna iya fafatawa da kowane mutum a fagen neman muƙaami. Wato, zuga wata dabara ce ta harzuƙa yan siyasa su sadaukar da duk abin da suke da shi, don haɓɓaka jam’iyyunsu da tsayawa takarar muƙamai daban daban, ko da ba su dace da muƙaman da suke nema ba.

1. 5 Zuga Tubalin Gina Siyasa

A jamhuriyoyin da suka gabata, wato jamhuriya ta farko da ta biyu, mawaƙan siyasa sun taka muhimmiyar rawa wajen yin amfani da zuga don gina siyasa a Nijeriya. Misali, a jamhuriya ta farko mawaka sun yi amfani da zuga , inda suka kambama jam’iyyunsu da manyan ‘yan siyasa har suka samu karɓuwa ga jama’ar ƙasa. A jam’iyyar NEPU, mawaƙa irin su Mudi Sipikin da Lawal Maiturare da Saadu Zungur da Aƙilu Aliyu, sun yi amfani da zuga wajen kambama al’ummar Nijeriya su zama cikin shiri domin su ƙwato wa Arewa da sauran alummar ƙasa ‘yancinsu. Misali, Mudi Sipikin a cikin waƙarsa ta nasiha ga yan siyasa, yana cewa:

 ‘Yan siyasar gari gari,

 Duk ku zo kan batun shiri,

 Cikin nasiha da hanƙuri,

 Inda dai babu tunzuri,

 Sai batun masu gaskiya.

 (Mudi Sipikin: Waƙar nasiha ga yan siyasa).

Malamin ya yi kira ga jama’ar Nijeriya, musamman ‘yan siyasar Arewa da kudancin Nijeriya na kowane lungu, wato, gari gari da su zo ƙwansu da kwarkwatarsu domin a shirya yadda za a haɗa kai a ƙwato wa Nijeriya‘yanci daga hannun ‘yan mulkin mallaka. Mawaƙin ya zuga mutane da “su zo”, a zauna cikin kwanciyar hankali da haƙuri domin a tattauna ba tare da an tada jijijyar wuya ba, a fito da hanyar da za a ƙwato wa Nijeriya yancinta. Ya ƙara da kira ga jamaar ƙasa ta hanyar zuga su, su yi ƙoƙari tare da yin haƙuri domin ana buƙatar a haɗa kai cikin hanzari, a yi aiki na gaskiya domin a cimma biyan buƙatar samun ‘yancin kai. Malamin yana cewa:

Duk mu tayar da ƙoƙari,

A kasar nan a zam shiri,

Ana buƙatar fa hanzari,

Sai mu ƙara da hanƙuri,

Mu yi aiki gaba ɗaya.

(Mudi Sipikin: Nasiha ga ‘yan siyasa).

Saboda haka, mawaƙin ya yi kira ga yan siyasar gari gari da su haɗa kai su goya wa shirin siyasa baya don a kai ga nasarar samun ‘’yancin kai a Nijeriya.

Haka a jamhuriya ta biyu, mawaƙa irin su Garba Gashuwa da Muhammadu Auwalu Isah Bunguɗu, suna daga cikin mawaƙan da suka ba da gudummawa wajen amfani da zuga domin su harzuƙa yan siyasa da jamiyun siyasa; domin su jawo hankalinsu su jajirce wajen neman ‘yanci domin ganin siyasa ta kafu da gindinta a Nijeriya. A cikin waƙarsa ta P. R. P. . Auwalu Isah Bunguɗu yana cewa:

Talakawa kar a burge ku,

Wata naira kar ta ruɗa ku,

Ku tsare girman mutuncinku,

Ku tsaya ku fito da ‘yancinku,

Ku ba bayin mutum ne ba.

(Auwal Isah Bunguɗu: P. PP, maganin zamba ta ɗaya).

Mawaƙin ya yi amfani da kalmomin zuga da suka haɗa da ‘kar a burge ku’, da ‘ku tsare’ , ‘ku tsaya’ da ‘ku fito’ domin ya harzuƙa talakawa su dage ba tare jin tsoro ko karɓar kuɗi ba su sayar da mutuncinsu. Domin idan har za ruɗi mutane da kuɗi don a hana masu gudanar da ƙudurinsu na neman yanci, to babu shakka gwagwarmayar neman yanci ta sami matsala. Saboda haka ne mawaƙin ya zuga talakawa da tsaya su dage su kare mutuncinsu ta hanyar ƙin karɓar kuɗi, wanda yin haka shi zai sa ba za acimma nasarar abin da ake nufi ba.

Shi kuma Garba Gashuwa a cikin waƙarsa da ya yi wa malam Aminu Kano, mai take, Aminu Nurul zamani. Mawaƙin ya zuga mutane ‘ya’yan jam’iyyar P. R. P. su jajirce su rungumi jam’iyyar P. R. P wadda ya sifantata da mai ƙirjin ƙarfi. Wato ƙarfinta ya zarce na sauran jamiyyun P. P. P da G. N. P. P. , da sauransu. Malamin yana cewa:

Jama’a ku kamo P. R. P.     

Nasara ga mai ƙirjin ƙarfi,

Wadda ta buge ɗan P. P. P.            

Ko Borno ba G. N. P. P,

Sai shehu Nurul Zamani.

(Garba Gashuwa: Waƙar Aminu Kano).

1. 6. Zuga Jam’iyya

A wannan jamhuriya ta huɗu da muke ciki, mawaƙan siyasa sun taka muhimmiyar rawa wajen gina siyasa har aka sami nasara ta zauna da gindinta. Idan muka lura da yadda mawaƙan siyasar zamani suka tallata jamiyyunsu da yan siyasarsu, sai mu ga cewa, haƙa ta cimma ruwa wajen gina siyasa mai ɗorewa a wannan jamhuriya ta hudu. Misali, mawaƙan siyasa daban daban sun yi amfani da dabarar zuga domin su kambama yan takara da jamiyyun siyasa domin jawo hankalin alumma su zaɓi mutanen da suka cancanta su jagoranci al’umma. Waɗannan mawaƙa sun ba da gudummawa wajen harzuƙa yan siyasa na kowace jamiyya domin su tallata su ga jamaa su aminta da su.

Misali, a jamiyyar APP, mawaƙa sun taimaka wajen kambama jam’iyyar domin su ƙara ɗaga darajarta ga mutanen Nijeriya. A cikin waƙarsa Ibrahim Aminu Ɗandago ya kambama jam’iyyar inda yake cewa:

Hantar kura a gun kare ta fi ta lasuwa,

Ɓarin gari ba a yi a kwashe tsab ɗan’uwa,

Ba a dukan Uba a ce an yi da mantuwa,

Dashen Allah ba dashen mutum ba dashen kainuwa,

Hukuncin Alllah a bi shi, shi ya fi da hayaniya.

(Aminu Ɗandago: Waƙar A. P. P. ).

Mawaƙin ya kambama jamiyyar A. P. P. , inda ya kamanta darajarta da ta kura, wadda kowa ya san cewa kura dabba ce mai kwarjini da ke bai wa kare tsoro. Domin har shi kansa karen yana mugun tsoron haɗuwa da kura ga azaliya. Saboda haka, hantar kura ba ta lasuwa ga kare ko ta mutu, balle tana raye; domin ta fi ƙarfinsa. Don haka, duk wata jam’iyyar da ba A. P. P. ba, dole ta bi bayanta. Mawaƙin ya kamanta darajar A. P. P. da sauran jamiyyu, wadda ya ce ta fi sauran jamiyyu. Har wa yau ya nuna cewa, ita jam’iyyar A. P. P. Allah ne ya dasa ta ba wai mutum ba, abin nufi Allah ya ba ta kwarjin da kowa ke sha’awar ta. Saboda haka duk wanda Allah ya ɗaukaka, to a bi shi shi ne masalaha. Mawaƙin ya yi amfani da salon karin magana domin ya isar da saƙonsa cikin hikima da kuma samar da nishaɗi ga masu sauraro ta yadda za su fahimci saƙon cikin hamzari. Misali, ‘Hantar kura a gun kare ta fi ta lasuwa’. Wannan wata dabara ce ta isar da saƙo ga alumma cikin hikima tare da samar da nishaɗi.

Shi ma Garba Gashuwa ya yi irin wannan kambamawar ga jamiyyar A. P. P. , a cikin waƙarsa da ya raɗa wa suna, ‘Munafurcin Karen Ruwa’. yana cewa:

A. P. P. ta mamaye ƙasa,

Tun da ta ɗauke jiga-jigan ƙasa,

Ta ko gama da na nesa har kusa,

Kar ka shigo mana mai munaƙisa,

Ka hautsina al’umma gaba ɗaya.

(Garba Gashuwa: Waƙar A. P. P. )

Malamin ya nuna wa jama’a cewa jam’iyyar A. P. P. ta samu karɓuwa a duk faɗin Nijeriya, inda har ta ɗauke manya-mayan jiga-jigan ‘yan Nijeriya. Wato a siyasance, duk jam’iyyar da ta kama mayan masu kuɗin ƙasa, wani lokacin har da sarakuna da manyan maaikatan gwamnati, to babu shaka jayayya da ita sai an shirya. Wannan dalili ne ya ya sa mawaƙin ya kambama jamiyyar ta A. P. P. domin ya bai wa sauran jamiyyu tsoro. Wannan salon zuga da mawaƙin ya yi amfani da shi, ya ƙara jawo wa jamiyyar A. P. P. kwarjini ga alummar Nijeriya baki ɗaya.

Shi kuwa Shu’aibu ‘Yar Medi a waƙarsa ta jamiyyar P. D. P. ya nuna wa duniya cewa a Nijeriya, P. D. P, ba wata jam’iyyar da ta dace ta mulkin jama’a sai ita. Ya tallata jam’iyyar inda ya kambama ta, yadda har mai saurare zai zaci cewa P. DP. wata hamshaƙiyar mayaƙiya ce da ta gagari abokan gaba. Malamin yana cewa:

Ga jirgin zuwa bahrul Aswad Tekun gabas waccan,

Ba zan hau kwami ya kife ba da ni ‘yar ƙorama kui can,

P. D. P. nake so jam’iyya ba na cikin waccan,

Duk mai son ƙasa ya fito a yi P. D. P. mazanmu da mata.

(Shu’aibu: Waƙar P. D. P).

Da yake tofa albarkacin bakinsa dangane da kambama jam’iyyar P. D. P. , Kabiru Yahaya Kilasik yana cewa:

Ɗaukar rigimata sai party marinjayi,

Ko kare ya kai gwarzo ai ba ya cin tayi,

Lema ni ka so don ita kowa yake yayi,

Ban barin ɗiya in tahi don tambaɗa boya.

(Kabiru Kilasik: Waƙar Bello matawalle).

Kabiru Kilasik mawaƙi ne, kuma ɗan siyasa mai aƙida. Duk ɗan siyasa da ke da aƙida, ba zai taɓa yarda da yaudara da ruɗin masu siyasar, ‘duk inda ta fi maiƙo can muka mai da kayanmu’. Mawaƙin riƙaƙƙen ɗan jam’iyyar P. D. P. ne, wanda aƙidarsa ta kai shi ga nasarar tsayawa takarar kujerar ɗan majalisar wakilai ta ƙasa har ya samu nasarar lashe zaɓe a shekarar 2015. Saboda haka mawaƙin yana wayar wa jama’a kansu tare da faɗakar da dukkan al’umma game da amfanin siyasar aƙida; wadda da ita ake samun kafa mulikn siyasa na cigaban ƙasa. Saboda haka sai ya ƙara kambama jamiyyarsa ta P. D. P. domin ya nuna wa jamaa cewa idan kai ɗan aƙidar siyasa ne, to tarin dukiya ko matsayin wasu ‘yan siyasa ba zai ruɗe ka, ka bar jam’iyyar da ke da manufar gina ƙasa ba. Yana cewa:

 Komi za a yi man P. D. P. nake ƙauna,

 Babbar jam’iyata ita ma tana so na,

 Ko tana gudu na ita za ni sa kaina,

 Bello inda amana ɓota ba ta ƙin hauya.

 (Kabiru Kilasik: Waƙar Bello matawalle ta P. D. P. ).

1. 7. Zuga ɗan Takara

Mawaƙan siyasar zamani suna amfani da zuga domin su kambama ɗan takara ya ji ƙarfin karawa da kowane mutum da ya fito neman kujerar da yake takara a kanta. Wato, mawaƙan siyasa suna ingiza ko harzuƙa ɗan takara ta hanyar sa sabulu su wanke laifukansa ko ɗabi’unsa waɗanda ba su da kyau, sannan su rangaɗa masa kwalliya da wasu kyawawan halaye ko ɗabi’u domin su tallata shi ga al’umma. Wannan zuga da mawaƙan kan yi wa yan takara wata dabara ce ta jawo hankalin masu saurare tare da faɗakar da ‘yan siyasa game da muhimmancin kyawawan ɗabi’u ga duk mutumin da yake son mutane su so shi, kuma su zaɓe shi ga kowane matsayi na siyasa. Misali a cikin waƙarsa da ya yi wa Janar Muhammadu Buhari, Ibrahim Yala hayin banki, ya kambama ɗantakararsa da cewa:

Ka zama jinjirin wata kai ne ake jira,

Rana ta fito ta riga ta gagara,

Dutse ka wuce buhu koko tokara,

Har mai gatari Muhammad zai juriya.

(Ibrahim Yala: Yau Nijeriya riƙo sai mai gaskiya).

Wannan baiti yana ɗauke da saƙo ne na kambama darajar Buhari bisa ga sauran yan takara domin a nuna wa jamaa irin kwarjinin da Buhari yake da shi a cikin alummar Nijeriya. Mawaƙin ya yi amfani da salon kwalliya inda ya kira Buhari da dutse, wanda ya ce ya wuce a sa shi cikin buhu, ko ma a tokare shi. Wannan salon kwalliya da mawaƙin ya yi amfani da shi, wata dabara ce ta kambama ɗan takara domin ya fifita darajarsa da sauran ‘yan takara abokan adawarsa. Saboda haka, zugan da Yala ya yi wa Muhammadu Buhari ya taimaka matuƙa wajen kai Buhari ga nasarar lashe zaɓen shugaban ƙasa a shekarar 2015. Amfanin zuga cikin waƙoƙin siyasa da mawaƙa ke amfani da shi, shi ne domin su wayar wa jama’a kai da kuma cusa masu son ɗan takara a zukatansu.

Shi ma Yusuf Fasaha kano, ya yi amfani da salon zuga domin ya kambama ko ingaza ɗan takararsa ya jajirce wajen aikin alhairi da yake yi wa al’ummarsa. Yana cewa:

I Musa Iliyasu riƙe Allah,

Makiyanka ba za su kai ka ba,

I ka yi taka ka yi ta raggo,

Zaki mujin Amina mai ba da tallafi.

(Yusuf Fasaha: Mu bi A. P. C. , al’ummar ƙasa).

Shi ma ya yi amfani da salon kwalliya ko kinaya, inda kai tsaye ya kira gwarzonsa da suna ‘zaki’ don ya nuna wa jama’a irin ƙarfin da ɗan takararsa yake da shi a cikin harkokin siyasa. Ya kuma nuna wa jama’a cewa Musa Iliyau, ba wai ga matsalarsa kawai ya tsaya ba, a’a da zarar ya gama tasa, sai ya yi ta raggo, wato ta mai ɗanƙarfi ke nan.

1. 8. Zuga Hana maguɗin Zaɓe

Mulkin siyasa ba ya tabbata sai da gudanar da zaɓe, wanda ke halitta wa waɗanda aka zaɓa gudanar da harkokin mulki kamar yadda kundin tsarin mulki ya gindaya. Talakawa su ne ƙashin bayan gudanar da kowace irin tafiya ta siyasa, domin su ke zaɓen ‘yan takara, ta hanyar jefa ƙuriunsu su zaɓi mutumin da ya dace ya shugabance su. A sanadiyar haka ne, ya sa mawaƙan siyasar zamani suke amfani da salon zuga domin su harzuƙa yan siyasa da sauran talakawa su jajirce wajen tsayawa ga akwatunan zaɓe don su hana maguɗi a lokacin kaɗa ƙuria. Kowace jam’iyya tana ƙoƙarin tsayar da wani mutum (Agent), wanda zai sa ido ga zaɓen da ake gudanarwa domin su hana a yi maguɗin zaɓe. Kowace jam’iyya tana tsayar da mutum mai kwarjini, wato, ɗan takararta mai kwarjin da riƙon amana wanda zai ƙwato wa talakawa ‘yancinsu da haƙƙoƙansu. Saboda haka sai su nemi mawaƙan siyasa su yi amfani da salon zuga domin su jawo hankalin masu jefa ƙuria su aminta da wanda jam’iyyarsu ta tsayar takara. Waɗannan mawaƙa su za su fito fili su zuga ɗan takara da talakawa su sa ido ga yadda zaɓuɓɓuka ke gudana. Sannan, su ne, za su zuga talakawa su tashi tsaye su ga cewa ba a yi maguɗin zaɓe ba a lokacin kaɗa ko jefa ƙuria. Misali, Murtala Mamsa Jos ya zuga talakawa a lokacin zaɓen da aka gabatar a shekarar 2015, inda ya harzuƙa talakawa su sa ido, su kasa su tsare don gudun kada a yi masu maguɗin da ‘yan jam’iyya mai mulki suka saba yi a lokacin zaɓuɓɓukan da suka gabata. Ya ce a yanzu kai ya waye, tsoro ya ɗebe don haka ƙarya ne a sake tafka magudin zaɓe, a zaɓe mai zuwa. Saboda haka ko da tsiya ko da arziki sai sun hana a yi masu maguɗi domin ba su yarda da haka ba. Misali, yana cewa:

Janar Buhari ikon Allah ka zud da ƙwallon yan Nijeriya,

Kun ci zaɓe an murɗe mana, hayaniya za mui kai ka tsaya,

Kana hana mu mu ɗau doka a hannu al’ummar Nijeriya,

Lokaci in ya yi Uban kuturu kaɗan ya yi, yai mana fariya.

(Murtala Mamsa: Waƙar sabuwa ta zo, A. P. C. ).

Mawaƙin ya yi ƙoƙarin jawo hankalin talakawa su fahimci irin shirin da yayan jamiyya mai mulki suka yi na tafka maguɗin zaɓe domin su ga ko ta halin ƙaƙa sun koma ga mulkinsu, (Tazarce). Ta hanyar zuga talakawa da mawaƙin ya yi, ta faɗar cewa, ‘in lokaci ya yi Uban kuturu kaɗan yayi yai mana fariya’. Wato mawaƙin ya nuna wa yan Nijeriya cewa a shirye talakawa suke su nema wa kansu ‘yanci ta hanyar hana maguɗin zaɓe a zaɓe da ke tafe. Wannan harzuƙa talakawa da mawaƙin ya yi ya taimaka ainun wajen jawo hankalin masu jefa ƙuria su dage su ga sun hana maguɗin zaɓe; wanda haka ya sa zaɓen Muhammadu Buhari ya samu nasara a 2015.

Haka abin ya kasance a saƙon da Ibrahim Yala ya isar wa talakawa na su jajirce a lokacin jefa ƙuria su ga cewa ko ta halin ƙaƙa sun hana a yi maguɗin zaɓe, idan aka zo jefa ƙuria a 2015. Malamin yana cewa:

Ku zo mu ƙara faɗa masu dai,

Yau ƙasarmu A. P. C. muka yi,

In za ai zaɓe a yi gaskiya,

Ba za mu yarda da runto ba,

Nijeriya sai baba Buhari,

Gaskiya dokin ƙarfe.

(Ibrahim Yala: Waƙar A. P. C. 2015).

Shi kuma Mudassiru Ƙasimu, ba wai yana zuga talakawa kaɗai ba, su hana maguɗin zaɓe, a’a ko da za a ce sai talakawa sun biya kuɗi sannan su zaɓi Buhari, to a shirye suke su yi haka, muddin dai suna da damar yin haka ɗin. Yana cewa:

Ranar zaɓe mu zaɓi Buhari,

Koko da za a ce sai an biya kuɗi,

Za mu biya mu zaɓi Buhari            .

(Mudassiru : Mu amshi ruwa ma zaɓi Buhari).

A wannan baiti da ya gabata, mawaƙin ya zuga talakwa su tsaya tsayin daka, ko da sai an biya a zaɓi Buhari, to su shirya su ga an zaɓi Buhari ba tare da an yi maguɗi ba. Sannan ya nuna wa duniya cewa talakawan Nijeriya sun shiya tsaf su canza gwamnatin jam’iyyar P. D. P da suka jefa ƙasa cikin mawuyacin halin taɓarɓarewar tattalin arzikin ƙasa da rashin aikin yi ga matasa, wanda ya haifar da taɓarbarewar tsaro a Nijeriya.                                           

1. 9. Zuga don hana ha’inci da cin hanci

Ha’inci da cin hanci kusan ɗan juma ne da ɗan jumai domin dukkansu suna nufin tauye haƙƙin mai haƙƙi. Wasu suna fassara ha’inci da cin hanci da rashawa. Ko yaudara ta hanyar danne dukiyar talakawa da shugabanni ke yi. Ƙamusun Hausa (1934), ya bayyana cewa, ha’inci yana nufin yaudara ce ta kowane fanni na rayuwa da ya shafi rashin bai wa mai haƙƙi haƙƙinsa. Wannan bayani ya nuna cewa, a duk lokacin da aka hana mai haƙƙi haƙƙinsa to, wannan ne hainci domin akan yi amfani da ƙarfin iko ko kuɗi don a sauya akalar wani abu daga wani bagire zuwa wani wuri na daban. Ko a yi amfani da kuɗi ko wata kyauta don a saye wanda nauyin mutane ya rataya a kansa yayi abin da ya saɓa wa dokar ƙasa ko aladar alummar da yake tare da su. Mawaƙan siyasar zamani sukan yi amfani da zuga wajen wayar wa mutane kai, su jawo hankalinsu su fahimci duk wata badaƙala da shugabanni suke shiryawa domin su hainci alummarsu, wato talakawa. Misali, Ibrahim Yala, a cikin waƙarsa ta C. P. C 2011, ya zuga matasa su tashi tsaye su ƙwato yancinsu da shugabannin Nijeriya suka haince su. Ga abin da yake cewa:

Ina kuke rundanar matasan Nijeriya,

Mu tashi mu ƙwaci yanci Nijeriya,

Mata kar ku yarda yau a yi muku murɗiya,

Sai mu zage, mu kai Buhari mai gaskiya.

(Ibrahim Yala: Waƙar C. P. C 2011).

Mawaƙin ya zuga matasa maza da mata su jajirce su zaɓi Buhari don shi ne zai sa su ƙwato yancinsu. Ƙwatar yanci yana nufin su kauce wa karɓar kuɗi a lokacin zaɓe, su daure su zaɓi mutum nagari, wanda zai ba kowa haƙƙinsa ba tare da tauyewa ba. Wato, ba tare da an ha’ince su ba, ko tauye masu wani kaso da ya dace su samu.

Shi ma Dauda Kahutu Rarara ya yi irin wannan zuga ga Buhari, wanda ya ce shi mai gaskiya ne, ba ya sata, ba ya ha’inci. Saboda haka mulkin Nijeriya sai baba Buhari. Mawaƙin yana cewa:

Tattali za a yi ba cuwa-cuwa, sai kai baba,

Baba ka ƙara ƙwazo kana daɗa kauda cutawa.

(Dauda Rarara: Waƙar Buhari ta A. P. C. 2015).

Dauda ya yi amfani da salon kamance, inda ya kamanta Buhari da mutaen kirki masu gaskiya da riƙon amana. Yana nuna cewa ko da ganin ɗabi’un Buhari bai yi kama da mutanen banza waɗanda mawaƙin ya kira su da suna cutawa. Wato, duk mutumen da ya kasance mahainci to sunansa macuci ko maha’inci domin ba shi tausayin talakwan da ako ɗora masa alhakin jagorancinsu.

Irin waɗannan mutane ne Yusuf Fasaha yake gargaɗin ‘yan Nijeriya da su kauce wa zaɓen su domin ba nufinsu siyasar gina al’umma ba, sai dai aka kasa kowa ya kwashi rabonsa. Irin wannan ɗabi’a ta wasu ‘yan siyasar Nijeriya, ta a ci wawa, a watse, shi ke hana mulkin siyasa ya zama ɗorarre, sai dai wata masana’antar da mutum zai sai da mutuncinsa domin ya sami abin dukiya. Zancen gina siyasa mai ta gina ƙasa da alumma ta tashi a nan. Mawaƙin yana cewa:

Za mu kauda rashawa, cin hanci,

Har zamba ba ma ƙyale yin ta ba.

‘Yan ƙasarmu sai mun tashi tsaye,

A kudun Arewa sannan mu kai gaci.

Mu bi A. P. C. sak ba canji,

‘yan ƙasarmu mun samu lokaci.

(Yusuf Fasaha: Mu bi A. P. C. , al’ummar ƙasa).

Mawaƙin ya yi amfani da kalmomin zuga don ya jawo hankalin mutane su fahimci amfanin gwagwarmayar neman‘yanci ita kaɗai ce hanyar da za abi a samar da kyakkyawan mulkin dimokuraɗiya mai ɗorewa a Nijeriya. Ya yi amfani da kalmomin zuga da ke kiran mutane su tashi tsaye don ya harzuƙa su kamar haka;‘’yan ƙasarmu’, ‘tashi tsaye’, ‘kudun da arewa’ da sauransu. Wato tashi tsaye na nufin zuga ‘yan ƙasa su san yancinsu ta hanyar zaɓen Muhammadu Buhari, mutumin da aka shaide shi da gaskiya da riƙon amana. Mutum wanda ba ya hainci ba ya karɓar rashawa, balle ya tauye haƙƙin talakawa.

Shi kuwa Shu’aibu ‘Yar Medi yana ganin karɓar kuɗi ba ya hana a zaɓi wanda ya cancanta a waƙarsa ta jamiyyar P. D. P. Yana cewa:

Jam’iyya a kan manufa aka fara ba muƙami ba,

Zaɓen nan abin ra’ayi aka faro ba da naira ba,

In an ba ka naira hamsin sa hannu riƙe baba,

Sai ka je akwati ka ɗau inuwar lema a gyara ƙasata.

(Shu’aibu: Waƙar P. D. P).

1. 6 Kammalawa

Babu shakka zuga wata dabarar isar da saƙo ce da mawaƙan siyasar zamani suke amfani da shi domin su jawo hankalin masu sauraren wakoƙinsu su fahimci saƙon da suke isarwa gare su. Mawaƙan siyasa sun yi tasirin gaske ga rayuwar al’ummar Nijeriya musamman wajen wayar masu da kai a kan muhimmancin zaɓen mutane nagari a muƙamin siyasa. Ta hanyar lura da irin tasirin da siyasa take da shi a rayuwar al’umma ya sa, mawaƙan siyasa suke amfani da waƙoƙinsu domin su isar muhimman saƙonni dangane da yadda shugabanci yake tafiya. Mawaƙan suna amfani da zuga domin su harzuƙa yan siyasa su riƙa bunƙasa suna taka muhimmiyar rawa wajen aiwatar da abubuwan cigaban ƙasa da kuma alumma baki ɗaya. Yin amfani da dabarar zuga da mawaƙan siyasa ske yi, yana daga cikin hanyoyin faɗakarwa da siyasa take shauƙin cimma nasarar da kowace jamiyyar siyasa ke yi. Saboda haka zuga ya taimaka tuƙuru wajen haɓɓaka dimokuraɗiyya mai ɗorewa a wannan jamhuriya ta huɗu da muke ciki.

1. 7. Sakamakon Bincike

Gwanin rawa shi ne wanda ya burge masu kallo, inji Hausawa. Mawaƙan siyasar zamani su ne tsane da ‘yan siyasa suke takawa su hango wuraren da za su jefa ƙafafunsu. Don haka ne suke amfani da mawaƙan siyasa domin su cimma manufofinsu na gina siyasa a duk lokacin da aka buga gangumman siyasa. Wannan takarda ta gano irin tasirin da zuga ya ya yi wajen faɗakarwa da wayar da kan ‘yan siyasa dangane da alfanun zaɓen mutanen kirki a siyasance, waɗanda ke zama gimshiƙin samar da ko kafa mulkin siyasa mai ɗorewa.

Zuga da mawaƙan siyasa ke amfani da shi cikin waƙoƙinsu ya taka rawar gani wajen gyara ɗabi’un ‘yan siyasa, musamman waɗanda ke sha’awar tsayawa takara. Kyawawan halaye na gaskiya da eiƙon amana su ne gimshiƙin samar da shugabanci nagari a siyasance. Har wa yau, zuga ya taimaka waje tallata kyawawan aƙidun shugabanni masu gaskiya da riƙon amana, waɗanda cigaban ƙasa da bunƙasa tallalin arzikinta da zaman lafiya, shi ke a zukatansu.

A bangaren ‘yan siyasa su kansu, zuga ya taimaka masu wajen gyara ɗabi’unsu da cire masu shakkun tsayawa takara matuƙar ba su da wani mummunarn tsalmi a rayuwarsu. Hausawa suna cewa, ‘idan baka san asalinka ba, to shiga siyasa, yanzu za san kai kowane ne’. Wannan takarda ta gano cewa zuga ya taimaka wa ‘yan siyasa wajen fahimtar tasirin da aiwatar da ayyukan raya ƙasa suke da shi wajen gina siaysa mai ɗorewa a ƙasa. Saboda haka, wannan takarda ta gano cewa, zuga da mawaƙan siyasa suke amfani da shi ba waai ya tsaya ga ƙosar da nishaɗi ga masu sauraren waƙa kaɗai ba, a’a wani makami ne gyara tarbiya da ɗabi’un ‘yan siyasar zamani a yau. Dalilin amfani da zuga ya sa aka sami sauyin gwamnati a shekarar 2015, inda aka zaɓi Muhammadu Buhari da ake yi wa lakabi da, ’gaskiya dokin ƙarfe.

1. 8 Shawarwari

Gina siyasa ta cigaban ƙasa ba ta yiwuwa sai an sami mutane masu amana da kyawawan ɗabi’u da hazaƙa da ilimin sanin makamar aiki da ƙwarewa ga iya hulɗa da mutane. Waɗannan abubuwa da aka ambata su ne, za su samar da kyakkyawan mulkin siyasa a ƙasa, wanda zai kawo wa al’umma hanyoyin cigaban rayuwa. Saboda haka, domin a gina ƙasa har ta zama daidai da sauran ƙasashen da suka ci gaba ta fuskar siyasa, dole ne a sami mutane masu gaskiya da amana su shugabanci al’umma ga mulkin siyasa. Da wannan shawara ce, ake sa ran idan aka yi amfani da ita za a sami siyasa ta ginu bisa ga kyakkyawar turba ta gaskiya da adalci a Nijeriya.

MANAZARTA

Bergery, G. P. (1934), Hausa-english and english- Hausa Vocabulary. London ; Oxford University press.

Bunza A. M. (2009) Nanarambaɗa, Ibrash Islamic Publications Centre LTD.

Bunza A. M. (2013), Makamin Dimokuraɗiyya a Falsafar Al’ada. 1st National Conference in Languge, Literature, and Culture. Center for Study of Nigerian Languages, B. U. K. Kano.

Bagega S. (2023), Asalin Zuga- hira da sarkin m\ƙeran Bagega, Ƙaramar Hukumar Anka, ranar 24/03/2023.

Bunguɗu A. I. (2017), Tarken Rubutattun Waƙokin Siyasa Na Kabiru Yahaya Kilasik. Kundin digiri na biyu, Jamiar Bayero, Kano.

Ɗangulbi A. R. (2003), Siyasa A Nijeriya: Gudummawar marubuta waƙoƙin siyasa na Hausa ga kafa Dimokuraɗiyya a Jamhuriya ta huɗu, zango na farko. Kundin digiri na biyu. Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo , Sokoto.

Idris Y. (2016), Jigon Bijirewa A Rubutattun Waƙoƙin Siyasa A Ƙasar Hausa-(1903-2015). Kundin digiri na uku , Jamiar Ahmadu Bello Zariya.

Oxford Dictionary, 9th edition.

Yahya A. B (1997) Jigon Nazarin Waka, Kaduna: Fisbas Media Services.

Garba Gashuwa----Waƙar Aminu Kano P. R. P. 1978.

Garba Gashuwa-----Waƙar A. P. P. Munafuccin Karen Ruwa

Ibrahim Ɗandago-----Waƙar A. P. P. 1998.

Ibrahim Yala------Waƙar AP. P 2003,

Iibrahim Yala----Waƙar C. P. C. 2011

Ibrahim Yala ----Waƙar A. P. C. , 2015

Kabiru Yahaya Kilasik ---Waƙar Bello Matawalle, P. D. P.

Muhammad Auwalu Isah Bunguɗu----Waƙar P. R. P. 1978.

Mudi Sipikin-------Waƙar siyasa, nasiha ga yan siyasa 1956.

Murtala Mamsa Jos----Waƙar A. PC. , sabuwa ta zo.

Shu’aibu ‘Yar Medi-----Waƙar P. D. P. 1998.

Yusuf Fasaha ----Waƙar A. P. C. , Mu bi A. P. C al’ummar ƙasa

Dauda Kahutu Rarara---Waƙar A. P. C.

Yusuf Fasaha----Wakar A. P. C. , Mu bi A. P. C. sak ba canji.

Mudassiru Ƙasimu----Waƙar A. P. C. mu amshi ruwa mu zaɓi Buhari.


Post a Comment

0 Comments