Tambaya (51)❓
Shin abin da ke faruwa a
Palestine yana da alaƙa da alamomin tashin alqiyama ?
AMSA❗
Tabbas ta'addanci da zaluncin da yahudawa suke ga yan uwanmu musulmai mazauna Zirin Gaza dake kasar Palestine yana da alaƙa da alamomin tashin alqiyama
Kafin hujjoji su biyo bayan
bayanina yakamata mu san tarihin Isra'ela
Kisan gillar da sukewa yan uwanmu Musulmai abin dubawa ne wanda a satin da ya wuce sun kashe majinyata da
likitoci da injiniyoyi dake aiki a asibitin "al-Ahli Baptist
Hospital" harin da suka kai yayi sanadin salwantar rayukan musulmai sama
da 500, to ammanfa dukda haka wannan zaluncin da suke a wannan zamanin bai kai
kaso 1% cikin 100% na abin da sukayi a zamanin baya ba
Ko ka san cewar Yahudawa
Sun taba kashe Annabawa 43 a rana
daya, da yammacin ranar kuma suka kashe musulmai masu wa'azi 170
Haka kuma Abdullahi Ibn Mas'ud
(RA) ya ce: Banu Isra'ela sun taba kashe Annabawa guda 300 da hantsi suka koma
suka bude shagunansu suka ci gaba da sabgar kasuwancinsu kamar ma ba'ayi komai
ba
Hujjar wannan hadisi na cikin
Athari na al-Imamu Ibn Abi Hatim wanda ya rawaito a cikin Tafisirinsa
Kasar Palestine ita ce kasar da
akai tafiyar Isra'i daga Makka sannan kuma aka yi Mi'iraji a daidai masallachin
al-Aqsa, waje ne mai albarka kamar yanda Allah SWT ya fada;
( سُبْحَانَ الَّذِي أَسْرَىٰ بِعَبْدِهِ لَيْلًا مِّنَ الْمَسْجِدِ الْحَرَامِ إِلَى الْمَسْجِدِ الْأَقْصَى الَّذِي بَارَكْنَا حَوْلَهُ لِنُرِيَهُ مِنْ آيَاتِنَا ۚ
إِنَّهُ هُوَ السَّمِيعُ الْبَصِيرُ
)
الإسراء
(1) Al-Israa
Tsarki ya tabbata ga wanda Ya yi
tafiyar dare da bawanSa da dare daga Masallaci mai alfarma zuwa ga Masallaci
mafi nĩsa wanda Muka sanya albarka a gefensa dõmin Mu nũna masa daga ayõyinMu.
Lalle ne Shi shĩ ne Mai ji, Mai gani.
Nan ne garin da Annabi Musa AS
yasha gwagwarmaya da Banu Isra'ila
( وَآتَيْنَا مُوسَى الْكِتَابَ وَجَعَلْنَاهُ هُدًى لِّبَنِي إِسْرَائِيلَ أَلَّا تَتَّخِذُوا مِن دُونِي وَكِيلًا
)
الإسراء
(2) Al-Israa
Kuma Mun bai wa Mũsa littafi,
kuma Mun sanya shi shiriya ga Banĩ Isra'ila, cẽwa kada ku riƙi wani wakĩli baiciNa.
Duk da gatan da aka yi musu amman
sun kasance azzalumai
( وَقَضَيْنَا إِلَىٰ بَنِي إِسْرَائِيلَ فِي الْكِتَابِ لَتُفْسِدُنَّ
فِي الْأَرْضِ مَرَّتَيْنِ وَلَتَعْلُنَّ عُلُوًّا كَبِيرًا )
الإسراء
(4) Al-Israa
Kuma Mun hukunta zuwa ga Bani Isra'ĩla
a cikin Littafi, cewa lalle ne, kuna yin ɓarna
a cikin ƙasa
sau biyu, kuma lalle ne kuna
zalunci, zalunci mai girma.
Silar haka Allah SWT ya jarabcesu
da sharrin Bukhtanasar ya kashesu, da kuma Adolf Hitler wanda yayi ta babbakasu
da wuta a raye kamar a gidan biredi, silar gudun tsirar rai da sukai ne aka
basu matsuguni a Palestine amman wai yanzu sune suke kashe musulman yankin
alhalin an haramta musu wajen zama a duniyarnan
( فَإِذَا جَاءَ وَعْدُ أُولَاهُمَا بَعَثْنَا عَلَيْكُمْ عِبَادًا لَّنَا أُولِي بَأْسٍ شَدِيدٍ فَجَاسُوا خِلَالَ الدِّيَارِ ۚ وَكَانَ وَعْدًا
مَّفْعُولًا )
الإسراء
(5) Al-Israa
To idan wa'adin na farkonsu yajẽ, za
Mu aika, a kanku waɗansu
bayi Namu, ma'abũta yaƙi mafĩ
tsanani, har su yi yawo
a tsakanin gidajenku, kuma ya zama wa'adi abin aikatawa.
Allah ya basu ni'mah dayawa daya
daga ciki shi ne ya tseratar dasu daga fitinar fir'auna (Ramses II) da suka ga
mutuwarsa da al'ummarsa akan idanunsu;
( يَا بَنِي إِسْرَائِيلَ
اذْكُرُوا نِعْمَتِيَ الَّتِي أَنْعَمْتُ عَلَيْكُمْ وَأَنِّي فَضَّلْتُكُمْ عَلَى الْعَالَمِينَ )
البقرة
(47) Al-Baqara
Ya banĩ Isra'ĩla! Ku tuna
ni'imaTa, wadda Na ni'imta a kanku, kuma lalle ne Ni, na fĩfĩta ku a kan talikai.
( وَإِذْ نَجَّيْنَاكُم مِّنْ آلِ فِرْعَوْنَ يَسُومُونَكُمْ
سُوءَ الْعَذَابِ يُذَبِّحُونَ أَبْنَاءَكُمْ وَيَسْتَحْيُونَ نِسَاءَكُمْ ۚ وَفِي ذَٰلِكُم
بَلَاءٌ مِّن رَّبِّكُمْ عَظِيمٌ
)
البقرة
(49) Al-Baqara
Kuma a lõkacin da muka tsĩrar da
ku daga mutanen Fir'auna, su na taya muku muguntar azaba, su na yayyanke ɗiyanku maza su na rayar da
matanku. Kuma a cikin wancan akwai jarabawa mai girma daga Ubangijinku.
( وَإِذْ فَرَقْنَا بِكُمُ الْبَحْرَ فَأَنجَيْنَاكُمْ وَأَغْرَقْنَا آلَ فِرْعَوْنَ وَأَنتُمْ
تَنظُرُونَ )
البقرة
(50) Al-Baqara
Kuma a lõkacin da Muka raba tẽku
sabõda ku, sai Muka tsĩrar da ku kuma Muka nutsar da mutanen Fir'auna, alhali
kuwa kũ kuna kallo.
To amman dukda wannan sai suka
koma bautawa dan maraqi;
( وَإِذْ وَاعَدْنَا مُوسَىٰ أَرْبَعِينَ لَيْلَةً ثُمَّ اتَّخَذْتُمُ الْعِجْلَ مِن بَعْدِهِ وَأَنتُمْ
ظَالِمُونَ )
البقرة
(51) Al-Baqara
Kuma a lõkacin da muka yi wa'adi
ga Mũsa, dare arba'in, sa'an nan kuma kuka riƙi maraƙi daga bayansa, alhali
kũ, kuna masu zalunci (da bauta masa).
( وَإِذْ قَالَ مُوسَىٰ لِقَوْمِهِ يَا قَوْمِ إِنَّكُمْ
ظَلَمْتُمْ أَنفُسَكُم بِاتِّخَاذِكُمُ الْعِجْلَ فَتُوبُوا إِلَىٰ بَارِئِكُمْ فَاقْتُلُوا أَنفُسَكُمْ ذَٰلِكُمْ خَيْرٌ لَّكُمْ عِندَ بَارِئِكُمْ فَتَابَ عَلَيْكُمْ ۚ إِنَّهُ هُوَ
التَّوَّابُ الرَّحِيمُ )
البقرة
(54) Al-Baqara
Kuma a lõkacin da Mũsa ya ce ga
mutanensa: "Ya mutanena! Lalle ne ku, kun zalunci kanku game da riƙonku
maraƙin,
sai ku tũba zuwa ga
Mahaliccinku, sai ku kashe kawunanku.
Wancan ne mafii alheri a wajen mahaliccinku. Sa'an nan Ya karɓi tuba a kanku. lalle ne
Shi, Shi ne Mai karɓar
tũba, Mai jin ƙai.
A karshe suka ce sai sun ji
maganar Allah SWT sannan zasuyi imani kamar
dai yanda Annabi Musa AS (Kalamullah) yake jin maganarSa ba tareda
hijabi, bayan ya zabi mutane 70 a cikinsu sunje dutsen Dur Sina, sunji maganar
Allah SWT amman sai sukace sai mun ga Allah tukunna, sai aka saukarda tsawa ta
kashesu nan take;
( وَإِذْ قُلْتُمْ يَا مُوسَىٰ لَن
نُّؤْمِنَ لَكَ حَتَّىٰ نَرَى
اللَّهَ جَهْرَةً فَأَخَذَتْكُمُ الصَّاعِقَةُ وَأَنتُمْ تَنظُرُونَ )
البقرة
(55) Al-Baqara
Kuma a lõkacin da kuka ce:
"Ya Musa! Ba za mu yi ĩmani ba dõminka, sai munga Allah bayyane,"
sabada haka tsawar nan ta kamaku, alhali kuwa kuna kallo.
( ثُمَّ بَعَثْنَاكُم مِّن بَعْدِ مَوْتِكُمْ
لَعَلَّكُمْ تَشْكُرُونَ )
البقرة
(56) Al-Baqara
Sa'an nan kuma Muka tayar da ku
daga bayan mutuwarku, tsammaninku, kuna gõdẽwa.
Duk da an maido musu da
rayukannasu sai suka ce yanzu kuma suna son a saukar musu da girgije saboda
hasken rana yana takura musu kuma sukace su abinci daya ya ginshesu saidai a
saukar musu da naman salwa da darba (zuma) daga Aljannah;
( وَظَلَّلْنَا عَلَيْكُمُ الْغَمَامَ وَأَنزَلْنَا عَلَيْكُمُ الْمَنَّ وَالسَّلْوَىٰ ۖ كُلُوا مِن
طَيِّبَاتِ مَا رَزَقْنَاكُمْ ۖ
وَمَا ظَلَمُونَا وَلَٰكِن كَانُوا أَنفُسَهُمْ يَظْلِمُونَ )
البقرة
(57) Al-Baqara
Kuma Muka sanya girgije ya yi
inuwa a kanku, kuma Muka saukar da darɓa
da tantabaru a kanku; "Ku ci daga masu daɗin
abin da Muka azurta ku." kuma ba su zalunce Mu ba, kuma amma kansu suka
kasance suna zalunta.
Duk wannan falalar amman a karshe
sukace mun gaji da abinci kala daya, ka roka mana Ubangijinka ya bamu alkama,
albasa da sauransu;
( وَإِذْ قُلْتُمْ يَا مُوسَىٰ لَن
نَّصْبِرَ عَلَىٰ طَعَامٍ وَاحِدٍ فَادْعُ لَنَا رَبَّكَ يُخْرِجْ لَنَا مِمَّا تُنبِتُ الْأَرْضُ مِن بَقْلِهَا وَقِثَّائِهَا
وَفُومِهَا وَعَدَسِهَا وَبَصَلِهَا ۖ قَالَ أَتَسْتَبْدِلُونَ
الَّذِي هُوَ أَدْنَىٰ بِالَّذِي
هُوَ خَيْرٌ ۚ اهْبِطُوا مِصْرًا
فَإِنَّ لَكُم مَّا سَأَلْتُمْ ۗ
وَضُرِبَتْ عَلَيْهِمُ الذِّلَّةُ وَالْمَسْكَنَةُ وَبَاءُوا بِغَضَبٍ مِّنَ اللَّهِ ۗ ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمْ
كَانُوا يَكْفُرُونَ بِآيَاتِ اللَّهِ وَيَقْتُلُونَ النَّبِيِّينَ بِغَيْرِ الْحَقِّ ۗ ذَٰلِكَ بِمَا
عَصَوا وَّكَانُوا يَعْتَدُونَ )
البقرة
(61) Al-Baqara
Kuma a lõkacin da kuka ce:
"Ya Mũsa! Ba za mu yi haƙuri ba a kan abinci guda. Sai ka rõƙa mana Ubangijinka Ya
fitar mana daga abin da ƙasa take tsirarwa daga ganyenta, dumanta, da alkamarta da
albasarta. Ya ce: "Kuna nẽman musanya abin da yake mafi ƙasƙanci
da wanda yake mafi alhẽri? Ku sauka wani birni (daga cikin birane), lalle ne, kuna da
abin da kuka rõƙa. "Kuma Muka dõka
musu walaƙanci
da talauci. Kuma suka kõma
da wani fushi daga Allah. Wancan sabõda
lalle su, sun kasance suna kafirta
da ayõyin Allah, kuma suna kashe
Aannabawa, bada hakki ba. Wancan, sabõda saɓawarsu
ne, kuma sun kasance suna ƙẽtarewar haddi.
Kuma a cikin wadannan Yahudawanne
dai aka maida wasunsu birrai;
( وَلَقَدْ عَلِمْتُمُ الَّذِينَ اعْتَدَوْا مِنكُمْ فِي السَّبْتِ فَقُلْنَا
لَهُمْ كُونُوا قِرَدَةً خَاسِئِينَ )
البقرة
(65) Al-Baqara
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, kun san waɗanda suka ƙẽtare
haddi daga gare ku a cikin Asabar, sai muka ce musu: "ku kasance birai ƙasƙantattu."
Kai akwai watarana da suka cewa
Annabi Musa AS shi jahili ne;
( وَإِذْ قَالَ مُوسَىٰ لِقَوْمِهِ إِنَّ اللَّهَ يَأْمُرُكُمْ أَن تَذْبَحُوا بَقَرَةً
ۖ قَالُوا أَتَتَّخِذُنَا هُزُوًا ۖ قَالَ أَعُوذُ
بِاللَّهِ أَنْ أَكُونَ مِنَ
الْجَاهِلِينَ )
البقرة
(67) Al-Baqara
Kuma a lõkacin da Musa ya ce ga
mutanensa: "Lalle ne, Allah Yana umurtar ku da ku yanka wata saniya."
Suka ce: "Shin kana riƙon mu ne da izgili?" Ya ce: "Ina nẽman
tsari daga Allah da in kasance daga jahilai."
( قَالُوا ادْعُ لَنَا رَبَّكَ يُبَيِّن لَّنَا مَا هِيَ ۚ
قَالَ إِنَّهُ يَقُولُ إِنَّهَا بَقَرَةٌ لَّا فَارِضٌ وَلَا
بِكْرٌ عَوَانٌ بَيْنَ ذَٰلِكَ ۖ فَافْعَلُوا مَا
تُؤْمَرُونَ )
البقرة
(68) Al-Baqara
Suka ce: "Ka rõƙa mana
Ubangijinka, Ya bayyana mana, mecẽ ce ita?" Ya ce: "Lalle ne,
Shi, Yana cewa: "Lalle ne ita saniya ce; ba tsõfuwa ba, ba kuma budurwa
ba, tsakatsaki ce a tsakanin wancan,' sai ku aikata abin da ake
umurninku."
( أَفَتَطْمَعُونَ أَن يُؤْمِنُوا لَكُمْ
وَقَدْ كَانَ فَرِيقٌ مِّنْهُمْ يَسْمَعُونَ كَلَامَ اللَّهِ ثُمَّ يُحَرِّفُونَهُ مِن بَعْدِ مَا
عَقَلُوهُ وَهُمْ يَعْلَمُونَ )
البقرة (75) Al-Baqara
Shin fa kuna tsammanin za su yi
imani sabõda ku, alhali kuwa, haƙĩƙa,
wata ƙungiya
daga gare su sun kasance suna jin maganar Allah, sa'an nan kuma su karkatar da
ita daga bayan sun gane ta, alhali sũ, suna sane?
Su ne kuma sukace wutar Jahannama
basa ta qona su ba face na wasu kwanaki qididdigaggu;
( وَقَالُوا لَن تَمَسَّنَا النَّارُ
إِلَّا أَيَّامًا مَّعْدُودَةً ۚ قُلْ أَتَّخَذْتُمْ
عِندَ اللَّهِ عَهْدًا فَلَن يُخْلِفَ اللَّهُ عَهْدَهُ ۖ أَمْ تَقُولُونَ
عَلَى اللَّهِ مَا لَا تَعْلَمُونَ
)
البقرة (80) Al-Baqara
Kuma suka ce: "Wuta ba za ta
shafe mu ba, face, 'yan kwanuka ƙidayayyu."Ka
ce: "Ashe kun riƙi wani alkawari a wurin Allah, sa'an nan Allah ba zai saɓa wa alkawarinSa ba ko kuwa kuna faɗin abin da ba ku sani ba
bisa ga Allah?"
Sune masu kashe Annabawa ba adadi
kuma sun tsani Mala'ika Jibrilu;
( وَإِذَا قِيلَ لَهُمْ آمِنُوا بِمَا أَنزَلَ اللَّهُ قَالُوا نُؤْمِنُ بِمَا أُنزِلَ عَلَيْنَا وَيَكْفُرُونَ بِمَا وَرَاءَهُ وَهُوَ الْحَقُّ مُصَدِّقًا لِّمَا مَعَهُمْ ۗ قُلْ فَلِمَ
تَقْتُلُونَ أَنبِيَاءَ اللَّهِ مِن قَبْلُ إِن
كُنتُم مُّؤْمِنِينَ )
البقرة (91) Al-Baqara
Kuma idan aka ce musu: "Ku
yi ĩmani da abin da Allah Ya saukar." Sai su ce: "Muna ĩmani da abin
da aka saukar a gare mu," kuma suna kafircẽwa da abin da ke bayansa, alhali kuwa,
shi ne gaskiyar (da suka sani) mai gaskatawa ga abin da yake tare da su (na
Attaura) Ka ce: "To, don me kuke kashe annabawan Allah gabanin wannan,
idan kun kasance masu bayar da gaskiya?"
( قُلْ مَن كَانَ
عَدُوًّا لِّجِبْرِيلَ فَإِنَّهُ نَزَّلَهُ عَلَىٰ قَلْبِكَ بِإِذْنِ اللَّهِ مُصَدِّقًا لِّمَا بَيْنَ يَدَيْهِ وَهُدًى وَبُشْرَىٰ لِلْمُؤْمِنِينَ )
البقرة (97) Al-Baqara
Ka ce: Wanda ya kasance maƙiyi ga
Jibirilu, to, lalle ne shi ya saukar da shi a kan zũciyarka da izinin Allah, yana mai gaskatawa ga abin da yake gaba
gare shi, kuma da shiriya da bishara
ga mũminai.
Kuma sune wadanda suke bautar
gunkin Ba'al a zamanin Annabi Ilyas wanda a yanzu haka (a wani bincike da nayi)
sun dawo da wannan bautar tunaninsu ta hakanne zasuyi nasara akan musulman
Palestine;
( وَإِنَّ إِلْيَاسَ لَمِنَ الْمُرْسَلِينَ )
الصافات (123) As-Saaffaat
Kuma lalle Ilyas, haƙĩƙa, yana daga Manzanni.
( إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِ
أَلَا تَتَّقُونَ )
الصافات (124) As-Saaffaat
A lõkacin da yake ce wa mutanensa,
"Ashe, ba za ku yi taƙawa ba?"
( أَتَدْعُونَ بَعْلًا وَتَذَرُونَ أَحْسَنَ الْخَالِقِينَ )
الصافات (125) As-Saaffaat
"Shin, kuna bauta wa Ba'al
ne, kuma kuna barin Mafi kyautatawar masu halitta?"
( اللَّهَ رَبَّكُمْ وَرَبَّ آبَائِكُمُ الْأَوَّلِينَ )
الصافات (126) As-Saaffaat
"Allah Ubangijinku, kuma
Ubangijin ubanninku farko?"
Yakai mai karatu to Wannan fa shi
ne kadan daga cikin sharrin banu Isra'ela (wanda a kalla sun kashe musulmai yan
uwanmu kusan 3,000 ko sama da hakan a
cikin musulmai 2,300,000, mazauna Zirin Gaza). Saidai Alhamdulillah domin kuwa
suma an kashe musu sama da Yahudawa 5,000. Har yanzu sun rasa gano wai ya akai
sojojin Hamas suka samu manyan rokokin da sukai musu wannan babbar illa haka
Idan kuma muka koma tarihi, zamu
ga cewar shekaru 2,000 kafin zuwan Annabi Isah AS, akwai Kan'anawa da suka
zauna a wajen, suna jin yare 3, kananiyya (Can'an), araniyya (Aramaic), da
arabiyya (Arabic)
Hijirar Annabi Ibrahim AS daga
Oud ta kasar Iraqi zuwa Palestine, ya haifi Annabi Ismael da Ishaq AS, shekaru
3,000 kafin zuwan Annabi Isah AS, a zamanin Annabi Musa AS kuma Sarki Ramses II
(Firauna) ya kori Banu Israela su bar Misra zuwa Palestine, wanda hakan ya zama musabbanin halakarsa a cikin
kogin Nile (Ruwan maliya) lokacin da yabi biyansu
Kun tonu tarihin Jaluta da Daluta
?, harma Annabi Dawuda AS ya kashe Jaluta, silar hakan Sarki Daluta ya bashi
babban muqami, a karshe Allah SWT ya bashi sarauta da Annabta, ya haifi Annabi Sulaiman AS, shi ma ya gajeshi harma
ya mulki duniya, har suka hadu da Bilqisu ta musulunta
Sulaiman ya kafa daula 2, Yahuza
da Israela, Buktanasar ya yaqi Palestine, shekaru 600 kafin zuwan Annabi Isah
AS, yahudu suka riqe mulkin shekaru 400 kafin Annabi Isah AS. Kasar Japan, da
Rumawa sukai zamani da Annabi Isah AS,
da'awarsa ta tsone musu ido silar hakan suka kashe Annabi Yahya AS (A garin
Damascus) sunso kashe Annabi Isah AS amman sai akai sama dashi sai suka gicciye mai kama dashi, kuma tabbas
a karshen duniya zai dawo a matsayin Musulmi mai bin tafarkin Ahlus Sunnah
A shekarar 1917, General Alinbai,
baturen England yaci Palestine da yaqi, ta sake fadawa karkashin mulkin
mallakan turawan England kamar yanda Nigeria ta fada, har zuwa 1948, lokacin da
suka dauki matsalar suka kaita majalissar dinkin duniya, akaita munafurci a
karshe suka janye suka sa sharadin lallai sai an kafawa yahudawa daula a wajen
saboda yabudawa sun warwatse kamar yanda Allah SWT ya fada a cikin Suratul Isra
Su kansu turawa so suke su rabu
da sharrinsu shiyasa suka dauki tsarin maida angulu gidanta na tsamiya, aka
kafa musu daula aka bawa Palestine rabi wanda bai kai na yahudawa ba domin kuwa
yahudawan anbasu waje mai kyau
Aka kwacewa musulmai wajen da
suka mallaka wanda yakai eka miliyan 4, aka yiwa matansu fyade, aka fitardasu
daga garuruwansu sama da guda 400, inda aka basu shima aka kara rabashi gida 2
(West Bank da Gaza), a karkashin ikon Israela, komai idan zai shiga ya fita
saida izinin Israela
An dauke musu ruwa, wuta da
sauransu. Yankin West bank, Fatah suke mulki, Gaza kuma yan Hamas suke mulki
dukkansu Ahlus Sunnah na, amurka ke shawartar Israela su karya kowacce doka UN
ta saka, an basu manyan makamai wadanda suka ninninka na jaziratul arab
Kwanannan aka yi hira da wani
sojan Israela wanda ya ce yana shaawar yaga yaro dan Palestine yazo wucewa
makaranta ya samu bindiga ya kasheshi, akace mutane nawa ka harbe ya ce baisan
adadi ba amman kullum sai ya durawa bindigarsa harsashai 250 kuma baya dawowa
da ko guda 1, su HAMAS abbreviation ne na Harafatul Maqawana Islamiyya
Dan gwagwarmayar ba amurken nan
mai fashin baqi, Jackson Hinkle a yayinda yake dauko rahotannin musayar
fursunonin Israela (Nurit Cooper da Yochaved Lifshitz) ya ce: kafafan yada
labarai karya suke wa mutane la'akarida yanda ya ga Yahudawa suke shan shayi
(tea & cookies) tareda yin musabaha da sojojin Hamas cikin fara'a da kuma
kewar rabuwa
Sannan kuma a shafinsa na
Twitter, ranar 23 ga watan October, 2023 da misalin karfe 9:29pm, ya dora hoton
bomb (qirar amurka) wanda ya nuna cewar amurka ce take bawa Israela gudunmawa
wajen kashe musulman Gaza
Sahabban da suka rayu a Palestine
sun hada da; Ubadat bin Salih, Shaddad bin Aus, Usama bin Zayd, Wasilat bin
Asqa, Da'iya alkalby (wanda Jibril AS yake bayyana da siga irin tasa), Aus bin
Samit, Masud bin Aus, manyan malamai da suka bar tarihi Malik bin Dinar, Imam
ash-Shafi'i, Sufyan at-thauri, Muhammad bin Muslim bin Shabiz zuhri
Haka kuma Sayyadina Umar RA
tareda Abu Ubaidah RA sunje Palestine sun kwato Masjid al-Aqsa daga hannun
Yahudawa. Tarihi ya tabbatar da cewar Abdulaziz Bin Marwan shi ne ya gina
Qubbatus saqra (masallachin nan wanda ake saka hotonsa a jikin calendar, mai
kallon masjid al-Aqsa shekara ta 72 bayan hijira)
Nuruddan Zanki baturkennan, shima
ya bada gudunmawa a masallachin a zamanin Salahudden Ayyubi
A zamanin Annabi SAW saida aka
kwashe wata 17 ana kallon Palestine (al-Aqsa) kafin a dawo da alqibla zuwa ga
Ka'aba. Masjid al-Aqsa shi ne masallachi mafi daraja idan ka dauke Masallachin
Harami (Ka'aba) da kuma Masjid an-Nabwy
A yanzu haka mayaqan Hamas sun
kwacewa Banu Israela taswirarsu (Map) wanda yake a cikin wani Hard Disk mai
dauke da planning din mallake duk inda suke so a duniya, wanda suke kiran
taswirar da suna "Great Israel" wato Babbar Isar'ela wanda sunce har
Saudi Arabia sai ta dawo karkashinsu saboda idan bamu mantaba ai suna da tarihi
acan Madinar tun zamanin Annabi SAW, sunada alqaryu guda 3; Banu Nadir, Banu
Quraiza da Banu Qainuqa. Kwanannan sukayiwa kasar Misra magana akan idan zata
yarda ta karbi musulman Palestine ta basu wajen zama ita kuma zata yafe mata
duk wani bashi da take bin Misra din amman Egypt bata amshi tayin ba
Amurka (USA) sun kawo jiragen
ruwa manya guda 2 kowannensu a kalla akwai jiragen yaqi guda 70, kudin kowanne
jirgin ruwan yakai 12bn dollars (wato dollars biliyon 2). Prime minister
England yazo Israela ya ce muna taredaku shima Joe Biden ya ce yana goyon bayan
kisan da akewa musulmai. Hakama akwai masu jahilan Christians yan Nigeria da
suke jin dadi sabod ana kashe musulmai alhalin sun manta da cewar a satin da ya
wuce Israela ta wullo makami mai linzami cikin asibitin Al-ahli Baptist Hospital
wanda mallakin Christians ne, to anan yakamata kagane cewar su fa yahudawa
kamar yanda suka tsani musulmai to haka suka tsani Nasara (Christians) indai
kai ba nasu bane to karensu ma yafika a wajensu. Kuma baka isa ka shiga
addininsu ba, su kansu kadai suka sani, shiyasa zakaji bahaushe na cewa
"Yahudu tuba babu"
To ammanfa wai a haka zakaga
mutanenmu musulmai sunata kwaikwayonsu ta hanyar bata lokaci wajen
kallace-kallacen ball, wrestlings, fina-finansu na Hollywood da koyi da
al'adunsu irinsu gayyato masu kida yayin gudanarda bukukuwa (Dj) kuma wai ahaka
muke son Allah ya sa albarka a rayuwar zaman auren, ga kuma yin kwalliya (make
up) da mata suke wanda yake canza yanayin halittunsu (kuma nunsan dai haramunne
mutum ya canza halittar da Allah yayi masa) da kuma sauran abubuwa da yahudawa
suka tunkudo mana kuma muka riqesu hannu bibbiyu muna dabbaqawa, wanda daman
tuni Allah SWT ya gargademu da kada mu daukesu a matsayin majibinta;
( يَا أَيُّهَا الَّذِينَ
آمَنُوا لَا تَتَّخِذُوا الْيَهُودَ
وَالنَّصَارَىٰ أَوْلِيَاءَ ۘ بَعْضُهُمْ أَوْلِيَاءُ
بَعْضٍ ۚ وَمَن يَتَوَلَّهُم
مِّنكُمْ فَإِنَّهُ مِنْهُمْ ۗ إِنَّ اللَّهَ
لَا يَهْدِي الْقَوْمَ الظَّالِمِينَ )
المائدة
(51) Al-Maaida
Ya ku waɗanda suka yi ĩmani! Kada ku riƙi
Yahudu da Nasara majiɓinta. Sashensu majiɓinci ne ga sashe. Kuma
wanda ya jiɓince su
daga gare ku, to, lalle ne shĩ, yana daga gare su. Lalle Allah ba Ya shiryar da
mutane azzalumai.
( وَلَن تَرْضَىٰ عَنكَ الْيَهُودُ وَلَا النَّصَارَىٰ حَتَّىٰ تَتَّبِعَ مِلَّتَهُمْ ۗ قُلْ إِنَّ
هُدَى اللَّهِ هُوَ الْهُدَىٰ ۗ
وَلَئِنِ اتَّبَعْتَ أَهْوَاءَهُم بَعْدَ الَّذِي جَاءَكَ مِنَ الْعِلْمِ ۙ
مَا لَكَ مِنَ اللَّهِ
مِن وَلِيٍّ وَلَا نَصِيرٍ )
البقرة
(120) Al-Baqara
Kuma Yahũdu ba za su yarda da
kõme daga gare ka ba, kuma Nasara ba za su yarda ba, sai ka bi irin aƙidarsu.
Ka ce: "Lalle ne, shiriyar Allah ita ce shiriya." Kuma lalle ne idan
ka bi son zũciyõyinsu a bayan abin da ya zo maka na
ilmi, ba ka da, daga
Allah, wani majiɓinci,
kuma babu wani mataimaki.
Kuma Annabi SAW ya ce zamu bisu
sauda kafa gashi kuma din muna binsu wanda iya wannan kadai ya isa ya tabbatar
mana da cewar alqiyama ta kusa, me ya rage: bayyanar Muhammad Bin Abdullahi
(Imam Mahdi), bayyanar Dajjal sai kuma dawowar Annabi Isah AS wanda zai
hallakashi a daidai kofarnan mai suna Bab al-Lud daje Palestine, sai kuma
bayyanar Ya'juj da Ma'juj sai bayyanar Zi as-Suwaiqatan al-Afhaj wanda shi ne
zai zo daga kasar Yemen ya rusa Ka'aba, sai mutuwar salihan bayi masu imani sai
kuma aikata alfasha a bayyane (Wanda a yanzu haka 2023 dinnan, gwamnatin kasar
Mexico tace kowa ya aikata abin da yake so na alfasha a bayyane) sai a rasa
masu iya firta kalmar shahada, to akan wadannan fasiqanne Allah SWT zai tashi
alqiyama, za'a ji sautin busar kahon Mala'ika Israfil a yankin kasar Palestine
kuma anan dai Masjid al-Aqsa dinnan ne za'a tattara bayi ayi hisabi a wata
ranar Juma'a wadda Allah SWT ne ya barwa kansa sanin wacce ce
Don haka a karshe ina son nayi
amfani da wannan damar don janyo hankalin musulmai da mu koma ga Allah mu yawaita Istighafari,
domin kuwa naji yawancin malamai sunata cewa anya kuwa ba a kanmu za'ayi tashin
alqiyama ba ?, wallahu a'alamu, don haka mu taya yan uwanmu na Gaza addu'ar
Allah ya basu nasar akan wadannan azzaluman yahudawan. Allah ka karbi
shahadarsu. Allah ka yafe mana ka yafe musu sannan ka sakamu tare dasu baki
daya a Aljannatil Firdous
Ku turawa yan uwa da abokan
arziqi domin mu amfana da saqon baki daya
A DUBA: Littafin Albidaya wan
Nihaya wallafar Abubakar Alhafiz Ibn Khathir,
Hudubar Shaikh Professor Mansur Sokoto, Karatun Marigayi Shaikh Muhammad
Auwal Albany, Karatun Shaikh Professor Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo, Karatun
Shaikh Dr. Abdallah Gadon Kaya, Karatun Shaikh Sulaiman Mahmud, Karatun Shaikh
Musa Yusuf Asadussunnah, Karatun Shaikh Hamza Yusuf Hanson (President Zaytuna
College, California, USA), Karatun Shaikh Bilal Asad, Karatun Shaikh Sulaiman
Omar (Founder Yaqeen Institute, USA), mu daina kallon videos da BBC suke yadawa
domin kuwa duk mallakin Yahudawane saidai a shawarce mu dinga bibiyar shafin
Instagram na Motaz Azaiza (jajirtaccen musulmin dan jarida daga Palestine), ko
Plestia Alaƙad,
Ahmed Hijazi, Afaf Ahmed, Sara alsaqqa, Meera Adnan, da kuma YouTube channels
irinsu; Sense Islam, Quran and Islam, One Path Network, Rational Believer.
Sannan nayi amfani da Qur'ani tarjamar Hausa na marigayi Shaikh Abubakar Gumi
(Rahimahullah)
Amsawa;
Usman Danliti Mato
(Usmannoor_As-salafy
Subhanakallahumma wabi hamdika
ash hadu anla ilaha illa anta astaghfiruka wa'atubi ilayk
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.