𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam
Alaikum Wa Rahmatul Laah. Malam, wai menene hukuncin zaman aure tare da miji
mai yawan zargin matarsa?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus
Salaam Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.
(i) Me yiwuwa
tun kafin su yi aure ya san ta da hakan ne, ko kuma a hakan suka rayu kafin a ɗaura musu auren. In haka
ne, wajibin abin da yake a kansu yanzu shi ne gaggauta tuba da komawa ga Allaah
tare da neman gafararsa.
(ii) Dole ne
shi kuma ya hana kansa yin irin wannan tunanin, kuma ya ɗauki matakan da ba su ci-karo da koyarwar
shari’a ba, kamar ta hana ta fita daga gida sai tare da wani amintaccen
muharraninta.
(iii) A duk
lokacin da wannan tunanin ya taso masa, wajibi ne ya riƙa yin isti’aazah yana roƙon
Allaah Ta’aala ya
tsare shi daga sharrin shaiɗan,
kuma kar ya kuskura ya furta komai da bakinsa, ko ya rubuta shi.
(iv) Idan kuma
ya furta abin da ke cikin zuciyarsa a fili ko ya rubuta shi, har wani ya ji ko
ya gani, to hukuncin ƙazafi ya hau kansa ke nan.
(v) Dole ne
kuma wajibi ne ya kawo shaidu musulmi guda huɗu
adalai waɗanda za su
yi shaida a gaban alƙalin kotun musulunci cewa, sun ga matar tana aikata wannan al’amarin da yake zargin ta da
shi.
(vi) Idan kuma
shi kaɗai da idonsa
ne kawai ya gan ta tana aikata abin da yake zargin, bai iya samo shaidun guda
huɗu a kan hakan ba,
to ba abin da ya rage masa a nan sai dai ya yi haƙuri, ya rufe bakinsa kawai. In ya so yana
iya sakin ta shiru bakinsa-alaikum, ko kuma ya yi mata li’ani.
(vii) Idan
kuma ya kasa yin ko ɗaya
daga cikin abubuwan biyu, bayan kuma ya furta wannan maganar a fili, to babu
abin da ya rage sai ya kwanta a gaban alƙali a zuba masa buloli har guda tamanin
daidai.
Allaah Ta’aala
ya ce:
وَٱلَّذِینَ
یَرۡمُونَ ٱلۡمُحۡصَنَـٰتِ ثُمَّ لَمۡ یَأۡتُوا۟ بِأَرۡبَعَةِ شُهَدَاۤءَ فَٱجۡلِدُوهُمۡ ثَمَـٰنِینَ جَلۡدَةࣰ وَلَا تَقۡبَلُوا۟ لَهُمۡ شَهَـٰدَةً أَبَدࣰاۚ وَأُو۟لَـٰۤىِٕكَ هُمُ ٱلۡفَـٰسِقُونَ ٤ إِلَّا ٱلَّذِینَ
تَابُوا۟ مِنۢ بَعۡدِ ذَ ٰلِكَ وَأَصۡلَحُوا۟
فَإِنَّ ٱللَّهَ غَفُورࣱ رَّحِیمࣱ ٥
Kuma waɗanda suke jifar mata masu
kamun-kai, sannan kuma ba su iya kawo shaidu guda huɗu ba, to sai ku yi musu buloli guda tamanin,
kuma kar ku karɓi
wata shaida daga gare su har abada, kuma waɗannan
su ne cikakkun fasiƙai. Sai dai waɗanda
suka tuba daga bayan haka kuma suka gyara, to haƙiƙa! Allaah Mai Yawan Gafara ne, Mai Jin Ƙai.
(Surah An-Nuur: 4-5)
Sai kuma ya
ce:
وَٱلَّذِینَ
یَرۡمُونَ أَزۡوَ ٰجَهُمۡ وَلَمۡ یَكُن لَّهُمۡ شُهَدَاۤءُ إِلَّاۤ أَنفُسُهُمۡ فَشَهَـٰدَةُ أَحَدِهِمۡ أَرۡبَعُ شَهَـٰدَ ٰتِۭ بِٱللَّهِ إِنَّهُۥ لَمِنَ ٱلصَّـٰدِقِینَ ٦ وَٱلۡخَـٰمِسَةُ أَنَّ لَعۡنَتَ
ٱللَّهِ عَلَیۡهِ إِن كَانَ مِنَ ٱلۡكَـٰذِبِینَ ٧ وَیَدۡرَؤُا۟ عَنۡهَا
ٱلۡعَذَابَ أَن تَشۡهَدَ أَرۡبَعَ شَهَـٰدَ ٰتِۭ بِٱللَّهِ إِنَّهُۥ لَمِنَ ٱلۡكَـٰذِبِینَ ٨ وَٱلۡخَـٰمِسَةَ أَنَّ غَضَبَ
ٱللَّهِ عَلَیۡهَاۤ إِن كَانَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِینَ ٩
Kuma Waɗanda suke jifar matan
aurensu kuma bai kasance suna da waɗansu
shaidu ba sai dai su kansu kawai, to shaidar ɗayansu
ita ce: Rantsuwoyi har sau huɗu
da Allaah a kan cewa: Lallai ne shi yana daga cikin masu gaskiya. Kuma ta biyar
ita ce cewa: Tsinuwar Allaah ta sauka a kan shi, idan har ya kasance daga cikin
maƙaryata.
Kuma zai kawar mata da horon (jefewa) idan ta yi rantsuwa sau huɗu da Allaah a kan cewa:
Shi yana daga cikin maƙaryata. Kuma ta biyar ita ce: Fushin Allaah ya tabbata a gare
ta idan ya kasance daga cikin masu gaskiya. (Sura An-Nuur: 6-9)
WALLAHU A'ALAM
Sheikh Muhammad
Abdullaah Assalafiy
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.