𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam
Alaikum Wa Rahmatul Laah. Wai waɗanne
mata ne Allaah ya tsine musu bayan masu aske gashin gira (shaving)_ da masu ƙarin
gashi (attachment)?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah Wa
Barakaatuh._
Al-Imaam Al-Bukhaariy
(5934) ya riwaito daga A’ishah Ummul-Mu’mineen (Radiyal Laahu Anhaa) ta ce:
Wata budurwa ce daga cikin Ansaar ta yi aure, sai kuma ta yi rashin lafiya har
gashinta ya kakkaɓe,
sai suka yi nufin sada mata da wani, sai suka tambayi Annabi (Sallal Laahu
Alaihi Wa Alihi Wa Sallam), sai ya ce:
« لَعَنَ اللَّهُ الْوَاصِلَةَ وَالْمُسْتَوْصِلَةَ »
Abin da Allah
Ya sanya shi ganĩma ga ManzonSa dagamutãnen ƙauyukan nan, to, na Allah ne, kuma na
ManzonSa ne kuma na mãsu dangantaka da mãrayu da miskĩnai da ɗan hanya(1) ( matafiyi)
ne dõmin kada ya kasance abin shãwãgi a tsakãnin mawadãta daga cikinku kuma
abin da Manzo ya bã ku, to, ku kama shi, kuma abin da ya hane ku, to, ku bar
shi. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle, Allah, Mai tsananin uƙũba ne.
Allaah ya
tsine wa mai sadar da gashi, da mai neman a sada mata.
Al-Imaam
Muslim (5695) kuma ya riwaito daga Abdullaah Bn Mas’uud (Radiyal Laahu Anhu)
cewa, shi ya ce:
« لَعَنَ اللَّهُ الْوَاشِمَاتِ وَالْمُسْتَوْشِمَاتِ وَالنَّامِصَاتِ وَالْمُتَنَمِّصَاتِ وَالْمُتَفَلِّجَاتِ لِلْحُسْنِ الْمُغَيِّرَاتِ خَلْقَ اللَّهِ »
Allaah ya
tsine wa masu yin zane a fatar jiki, da masu neman a yi mata zanen; da masu
aikin aske gashin fuska da masu neman a aske musu; da masu yi wushirya domin ƙara
kyau, masu sauya halittar Allaah.
Da labarin ya
kai ga wata mace a cikin ƙabilar Banu-Asad mai suna Ummu-Ya’quub wacce makaranciyar
Alqur’ani ce, sai ta zo wurinsa ta ce: Wane labari ne nake ji wai kai ka tsine
wa masu yin zane a fatar jiki, da masu neman a yi masu zanen; da masu aikin aske
gashin fuska da masu neman a aske musu; da masu yi wushirya domin ƙara
kyau, masu sauya halittar Allaah.
Sai Abdullaah
ya ce: Me zai hana ni in tsine wa wadda Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa
Alihi Wa Sallam) ya tsine wa, alhali kuma yana cikin Littafin Allaah?
Sai matar ta
ce: Haƙiƙa!
Na karanta abin da ke tsakanin bango biyu na Alqur’anin amma ban gan shi ba!
Sai ya ce:
Idan dai har kin kasance kina karanta shi, to tabbas da kin same shi. Allaah
Mabuwayi Mai Girma ya ce:
ۚ
وَمَا آتَاكُمُ الرَّسُولُ فَخُذُوهُ وَمَا نَهَاكُمْ عَنْهُ فَانْتَهُوا ۚ
Kuma duk abin
da Manzon ya ba ku sai ku karɓe
shi, kuma duk abin da ya hane ku sai ku hanu. (Surah Al-Hashr: 7)
Sai matar ta
ce: Amma ai yanzun nan na ga matarka da wani abu irin wannan!
Ya ce: Tafi ki
duba dai.
Sai ta shiga
wurin matar Abdullaah amma ba ta ga komai ba, sai ta dawo ta ce: Ban ga komai
ba.
Abdullaah ya
ce:
أَمَا لَوْ كَانَ ذَلِكِ لَمْ نُجَامِعْهَا
Amma in da
akwai wannan abin ai da ba mu zauna da ita ba.
A taƙaice
dai waɗanda aka
tsine wa daga cikin waɗannan
hadisan su ne:
(i) Masu
sana’ar sadar da wani abu a gashin kai.
(ii) Masu nema
a sada musu wani abu a cikin gashin kansu.
(iii) Masu
sana’ar yin zane a fatar jiki (tattooing).
(iv) Masu
neman a yi musu zane a fatar jikinsu.
(v) Masu aikin
aske gashin fuska.
(vi) Masu
neman a aske musu gashin fuskarsu.
(vii) Masu
neman a yi musu wushirya.
MALAMAI SUKA
CE:
(i) Ma’anar
Tsinuwa ita ce: Nisanta daga samun Rahamar Ubangiji a duniya da Lahira. Wannan
kuma dalili ne a kan cewa wannan aikin haram ne, shi ya sa aka siffata mai aikatawa
da tsinuwar Allaah.
(ii) Daga
maganarsa cewa: ‘domin ƙara kyau’
ana fahimtar cewa abin ƙi kawai shi ne ga wadda ta aikata hakan saboda neman ƙarin
kyau. Amma idan ta buƙatu ga hakan ne, kamar domin magani misali, to ya halatta.
(iii) Kuma
maganarsa: ‘Masu sauya halittar Allaah’ wannan siffa ce ta dukkan masu aikata
kowanne ɗaya daga
cikin ayyukan: Sada gashi, zane a fatar jiki, aske gashin fuska. Ba wai masu
yin wushirya kaɗai
ba.
(iv) A cikin
As-Silsilah As-Saheehah (2792) ya kawo maganar Al-Imaam At-Tabariy (10/377)
cewa:
‘Bai halatta ga wata mace ta sauya duk wani
abu daga cikin halittar da Allaah ya halicce ta da shi ba, ta hanyar yin ƙari
ko ragi don neman ƙarin kyau, ko da domin miji ne ko kuma ma wanda ba miji ba.
Kamar wacce gashin giranta guda biyu suka haɗe,
sai ta yi ƙoƙarin
gusar da abin da ke a tsakaninsu. Ko wacce take da goyo a haƙoranta
ko take da haƙori mai tsawo, sai ta je ta cire shi. Ko mai gashin gemu ko
gashin baki ko gashin haɓa,
sai ta je ta tsittsige ko ta aske shi. Haka ko wacce take da gajeren gashi sai
ta je ta tsawaita shi, ko mai gashi mara kyau sai ta je ta sauya shi. Duk waɗannan sun shiga cikin
hanin da ya zo a cikin wannan hadisin, kuma sun shiga cikin masu sauya halittar
Allaah Ta’aala. Sai dai daga cikin wannan ɗin
an togace (watau an cire) duk abin da ke janyo cutarwa ko takurawa, kamar wadda
take da haƙori
mai goyo ko mai tsawo wanda kuma yake takura mata a wurin cin abinci.’
Duk wannan ya
nuna yadda musulunci ya damu da wannan al’amarin na kwalliyar mata, saɓanin yadda waɗansu musulmi a yau suke
yin sako-sako da shi, kuma suke ɗaukar
shi ba da muhimmancin da ya cancance shi ba.
Allaah ya ƙara
mana shiriya gaba-ɗaya.
WALLAHU A'ALAM
Sheikh
Muhammad Abdullaah Assalafiy
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.