𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu
alaikum..Don Allah ina da tambaya ne. Shin Idan nace ma mijina ya sakeni saboda
ya yi aure ni kuma bazan iya zama da matar ba domin ni inada kishi. shin inada
laifi?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikis
salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Karin aure, wani
abu ne wanda Allah ya halastashi bisa bayinsa maza muminai, bisa sharuɗɗa guda biyu. Wato
mutukar mutum zai iya yin adalci atsakanin matansa, kuma mutukar zai iya daukar
dawainiyarsu ta ɓangaren
saduwa da kuma abin da rayuwar yau da kullum take bukata.
Kamar yadda
Allah ya yi isharah Qarara acikin Alqur'ani :
فَانْكِحُوا مَا طَابَ لَكُمْ مِنَ النِّسَاءِ مَثْنَىٰ وَثُلَاثَ وَرُبَاعَ ۖ فَإِنْ خِفْتُمْ
أَلَّا تَعْدِلُوا فَوَاحِدَةً أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُكُمْ ۚ ذَٰلِكَ أَدْنَىٰ
أَلَّا تَعُولُوا
ku auri abin
da ya yi muku dãɗi
daga mãtã; biyu-biyu, da uku-uku, da huɗu-huɗu. Sa'annan idan kun ji
tsõron bã zã ku yi ãdalci ba, to, (ku auri) guda ko kuwa abin da hannayenku na
dama suka mallaka. (Wato kuyangi) Wannan shi ne mafi kusantar zama ba ku wuce
haddi ba. (Suratun Nisa'i ayah ta 3).
Don haka
Manzon Allah ﷺ ya
Qara aure, Sahabbansa ma mafiya yawansu ba su zauna da mace guda kacal ba. Don
haka ki kwantar da hankalinki ki yi hakuri kibi mijinki yadda zaku samu zaman
lafiya da albarkar aure.
Abu ne sananne
cewa ku mata kuna da tsananin kishi akan abubuwa da dama, amma babu kamar akan
mazajenku. Wannan ba laifi bane tun da hali ne wanda yake gine azuciyar Ɗan
Adam. Kuma an riwaito halaye na kishi daga wasu da yawa daga Salihan mataye tun
daga kan matayen Fiyayyen Halitta ﷺ
har zuwa na Sahabbansa da tabi'ai. To amma wannan kishin bai kaisu zuwa ga
neman sakin aurensu ko neman hana faruwar abin da tun tuni Allah ya Qaddarashi
kuma ya halastashi ba.
Ya kamata kiji
tsoron Allah ki yi hakuri ki zauna da Maigidanki Kasancewar rabuwarki da shi za
ta iya janyo illoli ga rayuwarki ko rayuwar yaranku da kuka haifa dashi. Kuma
zama da kishiya tamkar taimakekeniya ne wajen aikata aikin alkhairi (wato shi
ne kulawa da maigida) kamar yadda Allah ya yi umurni :
...وَتَعَاوَنُوا عَلَى الْبِرِّ وَالتَّقْوَىٰ ۖ وَلَا تَعَاوَنُوا
عَلَى الْإِثْمِ وَالْعُدْوَانِ ۚ وَاتَّقُوا اللَّهَ
ۖ إِنَّ اللَّهَ شَدِيدُ الْعِقَابِ
Kuma ku
taimaki juna kan ayyukan alheri da ƙarin taqawa, kuma kar ku taimaki juna a
kan zunubi da ƙetare haddi, kuma ku ji tsoron Allaah; haƙiƙa
Allaah Mai Tsananin Uƙuba ne. (Suratul má’idah
aya ta 2)
Kuma maimakon
ki samu labarin cewa maigidanki yana neman matan banza, ai gara ki samu labarin
cewa zai Qara aure ɗin.
Kiyi hakuri ki
ba shi haɗin kai, ki
taimaka masa wajen kulawa da iyalansa har da ke aciki. Amma idan har kinga
cewar ba zaki iya yin hakuri ki jure ba, babu laifi ki nemi khul'i daga
gareshi. Wato ki ba shi sadaqin da zai isheshi ya auri wata matar, tare da
dukkan abin da ya kashe alokacin da ya aureki. (Amma wannan agaban alqali ake
warwarewa).
Amma dai ki
sani cewar hadisi ya inganta daga Sayyiduna Thawban (rta) baran Manzon Allah ﷺ yana cewa "Lallai
Manzon Allah ﷺ ya ce
"DUK MATAR DA TA NEMI SAKI DAGA GUN MIJINTA BA TARE DA WANI LAIFI BA,
(WATO BA TARE DA LAIFIN DA GIRMANSA YAKAI HAKAN BA) TO QAMSHIN ALJANNAH YA
HARAMTA GARETA"
(Imam Abu
Dawud ne ya ruwaitoshi).
Anan nake Qara
baki shawarar cewa ki yi hakuri ki zauna lafiya da mijinki da kuma abokiyar
zamanki. Hakika Allah yana tare da masu hakuri. Kuma yana bayar da lada mai
yawa ga duk wanda ya yi hakuri ya jure musiba dominsa. Amma tabbas idan har
kika matsa wa mijinki akan sai ya sakeki domin ba zaki iya zama da kishiya ba,
to fa Allah yana iya jarrabarki kuma bayan kin bar gidan.
Jarrabawar nan
tana iya zuwa miki ta kowanne ɓangare
(ba fata nakeyi miki ba, amma abu ne da yakan faru). Kodai Allah ya jarrabeki
da tsananin baqin jini, ki kasa samun wanda ma zaizo gidanku yakce yana sonki,
ko kuma duk wanda zaizo sai kiga bai kai koda rabin matsayin mijinki na baya
ba. Ko kuma duk wanda zaizo wajenki sai kiga shi ma yana da mata ɗaya ko biyu ko uku. Su ɗinma masu zafin kishi
irinki. Kinga idan hakan ta faru, keda kanki zaki gwammace gara ma gidan
mijinki gidan Uban 'ya'yanki. Shi kuma watakila sannan ya sake Qara wani auren,
kuma hankalinsa ya kwanta, zai ce ba ya bukatar ki dawo gidansa. Kinga daga nan
kuma rayuwarki za ta shiga wani sabon salo maras daɗi.
Kiyi hakuri ki
jure ki zauna ki riƙe yaranki. Kina da wasu darajoji agun mijinki wanda ita
amaryar ba ta dasu. Misali :
- Kin rigata
shiga gidan, kin rigata zama dashi. Kinfi ta sanin halayensa, don haka zaki fi
ta sanin yadda zaki zauna da shi lafiya. Kece uwargidansa kuma 'ya'yansa. Ita
kuwa ba ta da kowa agidan. Kin rigata aure. Don haka watakila kinfi ta iya
girke-girke kala-kala. Kinfi ta sanin 'yan uwan miji, da makobta da abokansa da
dukkan jama'arsa. Don haka ki yi kokari ki fita tsafta, kwalliya, hakuri,
kulawa da bukatun maigida, da sanin hanyoyin tattali da zama da shi lafiya.
WALLAHU
A'ALAM.
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.