𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalam
alaikum malam ina gajiya ya aiki, malam na kasance shekararmu 4 da saurayina
muna biyewa san zuciya muna aikata saɓon
ALLAH watau (zina) acikin hakan har Takai ga munyi ciki yana wata 2 sai muka
zubar toh ahalin yanzu mun tuba har za muyi aure mallam yaya matsayin auren mu
yake? kuma ALLAH zai karɓi
tuban mu?? wlh mallam bada san raina hakan tadinga faruwa ba, duk sanda za muyi
nakoma gida sau naita kuka ina nadama.
Shin Ya Halatta Mace Ta Auri Wanda Ya Taɓa Yin Zina Da Ita?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikis
salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Hakika kun
aikata babban kuskure, domin zina ita ce laifi mafi girma acikin kaba'irori in
banda shirka da kisan kai babu wani laifin da ya kaita girman azaba awajen
Allah.
Amma
kasancewar kinyi nadama bisa abin da kika aikata, ba shike nan ba. Akwai wasu
abibuwan da suka wajabta gareki ki aikata domin cikar tubanki.
Misali wajibi
ne ki yi istibra'i (jini uku domin tabbatar da tsarkake mahaifarki) Kuma ku
nisanci juna sosai alokacin da kike cikin istibra'in kada ku kusanci juna
ballantana har Shaiɗan
ya sake ruɗarku.
Kada ku sake
aikata wata haramtacciyar mu'amala. Ku hakura da junanku har sai bayan an daura
muku aure. sannan daga cikin sharuddann tubanki akwai ɗaukar niyyar har abada ba zaki sake komawa
cikin laifin ba. Sannan ki kaurace wa duk dalilan da za su kaiki zuwa ga wannan
laifin.
Hakanan laifin
zubar da cikin nan da kukayi, shi ma babban laifi ne. Amma mutukar kun tuba
Allah zai yafe muku domin yana daga cikin siffofinsa tsarkaka cewa Shi mai
gafara ne kuma mai rahama ga bayinsa.
Kuma niyyarku
ta yin aure, abu ne mai kyau. Muna muku fatan Allah ya sa auren ya zama
sanadiyyar shiriya da rabauta gareku, sannan ya zama sanadiyyar shafe dukkan
kusakurenku na baya.
Sannan kuci
gaba da gyara rayuwarku ta hanyar yawaita sauraron wa'azin Maluma, da neman
ilimi da kokarin aiki dashi. Allah yana cewa :
لْ يَا عِبَادِيَ
الَّذِينَ أَسْرَفُوا عَلَىٰ أَنْفُسِهِمْ لَا تَقْنَطُوا مِنْ رَحْمَةِ اللَّهِ ۚ إِنَّ اللَّهَ
يَغْفِرُ الذُّنُوبَ جَمِيعًا ۚ إِنَّهُ هُوَ
الْغَفُورُ الرَّحِيمُ ٣٥
Ka ce: (Allah
Ya ce): "Yã bãyĩNa waɗanda
suka yi ɓarna a kan
rãyukansu! Kada ku yanke ƙauna daga rahamar Allah. Lalle Allah na gãfarta zunubai gabã ɗaya. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai gãfara, Mai jin ƙai."
(Suratuz Zumar ayah ta 53).
WALLAHU
A'ALAM.
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
TAMBAYA TA BIYU
SHIN MACE ZA TA IYA AURAR WANDA YA TAƁA AIKATA ZINA DA ITA?
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Shin aure ya halatta tsakanin wanda ya kusance ni ta ƙarfi a
lokacin da nake idda? Dan Allah ataimake ni da amsa amma fa a bisa tsautsayi ya
faru.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wanda yayi zina da mace acikin iddarta, daidai yake da wanda
yayi zina da matar aure. Tun da har yanzu akwai sauran ikon mijinta akanta. Don
haka idan har da amincewarta sukayi zinar, dukkaninsu mazinata ne. Hukuncinsu
shine jefewa (idan shi ma ya taɓa yin aure) mutukar dai shaidu sun tabbata
akansu, ko kuma sunyi furuci da laifin.
Daga cikin malamai (Musamman Mazhabin Hanbaliyyah) akwai
wadanda suke ganin cewa har abada aure ba ya halatta atsakanin mazinaci da
wacce ba mazinaciya ba. Sai dai idan ya tuba, cikakkiyar tuba. Idan kuma duk su
biyun mazinata ne, duk da hakan dai wajibcin tuban yana nan akansu.
Mace mai iddah idan ta aikata zina, ko kuma akayi mata fyaɗe,
to iddodin sun zama biyu ke nan akanta, wato iddar sakin da akayi mata, da kuma
iddar Istibra'i. Sai dai kuma iddah ta biyun tana shiga cikin ta farkon. Wato
idan har tayi haila (sau daya ko biyu) bayan zinar da tayi, to shi ke nan ta
kammala iddar sakin ke nan tare da istibra'in tabbatar da kubutar mahaifarta
daga komai.
Daga karshe idan har ya tuba tsakaninsa da Allah zaki iya
aurarsa in har kina sonshi ahakan.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin
wannan group domin Fadakarwa...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.