𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu
Alaikum warahmatullahi Wabarkatuh. Shin Ya halatta takaita sallama dawasu
kalmomi, kamar ASLM ALKM ko SALAM ko WLSM? Shin Wanda ya takaita irin waɗannan kalmomi zai samu
lada sallama kamar wanda ya yi Cikakkiyar Sallama (Assalmu Alaikum
warahmatullahi Wabarkatuhu)?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus
Salam warahmatullahi Wabarkatuh.
الحمد لله والصلاة والسلام على محمد وعلى آله وصحبه وسلم.
Musulmi yana
da damar ya takaita sallama ga ɗan'uwansa
musulmi da sigogi guda uku, banda su babu wata shiga da mutum zai takaita
sallama da ita, mai amsa sallamar shi ma yana da damar takaitawa da
kwatankwacin Abun da maiyi masa sallamar yatakaita masa dashi, ya ce
"ASSALAMU ALAIKUM" ko "ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH"
wannan ya fi nafarko falala ko "ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH
WABARAKATUHU" wannan ya fi falala da kuma alkhairi.
Mai Amsawa
idan yakara akan abun da mai yi masa sallama yaimar da shi shiya fi saboda faɗin Allah madaukakin
sarki:
وَإِذَا حُيِّيتُمْ بِتَحِيَّةٍ فَحَيُّوا بِأَحْسَنَ مِنْهَا أَوْ رُدُّوهَا ۗ إ
Idan
Angaisheku da sallama to ku Amsa dawacce tafita alkhairi, ko kuma kumaida
dai-dai da wacce akai muku. (Suratul Nisá'i: 86)
Ankarbo daka
Abdullahi ɗan Abbas
Allah yakara yarda agaresu ya ce: umar bin khaddab yaje wajen manzon Allah ﷺ awani ɗaki nasa sai ya ce:
ASSALAMU ALAIKA ya manzan Allah ﷺ
ASSALAMU ALAIKUM, umar yashigo? Abu dauda (5204) Shaeik albany ya inganta shi
acikin sahihu Abu dauda.
Turmuzi ya
ruwaito ahadisi mai lamba (2721) Manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam ya ce:(
Idan mutum ya haɗu
da ɗan'uwansa
musulmi ya ce masa ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH WABARAKA TUHU) Albany ya
ingantashi acikin sahihul Turmuzy.
Ankarbo daka
imran bin husaini Allah yakara yarda dasu ya ce: wani mutum ya zo wajan manzan
Allah sallallahu Alaihi wasallam sai yai masa sallama ya ce: ASSALAMU ALAIKUM
sai Annabi ya Amsa masa sai yazauna, sai Annabi ya ce yasamu lada goma, sai
wani ya zo ya ce: ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH, sai Annabi ya amsa masa sai
ya ce: yasamu lada ashirin, sai wani ya zo ya ce :ASSALAMU ALAIKUM
WARAHMATULLAH WABARAKA TUHU, sai Annabi ya amsa masa sai ya zauna, sai Annabi
ya ce : yasamu lada talatin, Hadisine sahihi Abu dauda yaruwaitoshi (5195) da
turmuzi(2689) Albani ya ingantashi acikin sahihul turmuzi.
Daka A'isha
Allah yakara mata yarda tace: manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam ya ce:
wannan Jibrilu ne ya ce inkaranta miki sallama amadadin sa sai tace: sai nace:
WA'ALAIHISSALAM WARAHMATULLAH WABARAKA TUHU, Bukhary(3045) da muslim (2447).
Imamul nawawy
Rahimahullah ya ce: Ababin yanda ake sallama, Anso wanda zai fara yiwa wani
sallama ya ce "ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH WABARAKA TUHU" ya zo da
lamirin sunan dayake nuna mutane dayawa yake yiwa sallamar koda mutum ɗaya zai yiwa sallamar.
Shi kuma mai
amsawa ya ce: WA'ALAIKUMUSSALAMU WARAHMATULLAH WABARA KATUHU, ya zo da wawul
adaf wacce take nuna mutane dayawane awajan cewa "wa'alaikum" Riyazul
saliheen(446).
Amma karin WAL
"MAGFIRAH" tazone awasu hadisai na yin sallama dakuma amsawa, sai dai
cewa ba su ingantaba, daka hadisan da aka ruwaito akan haka akwai hadisin
Sahal ibn
mu'az bin Anas daka babansa daka Annabi sallallahu Alaihi wasallam, da ma'anar
hadisin imaran bin husain wanda yagabata, acikin sa akwai mutum na huɗu dayazo wajan manzan
Allah ﷺ ya ce:
"ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKA TUHU WA MAGFIRATUHU" sai
Annabi sallallahu Alaihi wasallam ya ce: yasamu lada arba'in, sai ya ce: haka
falala take kasancewa, Abu dauda yaruwaito wannan hadisin (5196). hakika wasu
malamai sun raunana wanan hadisin mai karin WAL "MAGAFIRATUHU" daka
cikinsu akwai ibnul Araby Almaliky, da ibnul qayyeem, da imamun nawawy, da ibnu
hajar asqalany, da Albany, Allah yajikansu.
Ibnul qayyeem
rahimahullah ya ce: wannan hadisin bai tabbata ba domin yana da illoli guda
uku.
1- ahadisin ya
zo daka ruwayar Aba marhuum, Abdurraheem bin maimuun, kuma ba a hujja dashi.
2- acikin
hadisin akwai sahal bin mu'az shi ma ba a hujja dashi.
3- Sa'idu ɗan Abah maryam ɗaya daka cikin ruwayoyin
sa baya tabbatar da ruwaya, saidai ya ce ina tsammanin na ji nafi'i bin yazeed
ya ce:
Zadul ma'ãd fi
hadyi khairul ibada (2/417- 418).
Da kuma silsila
za'ifa ta Albany (5433).
Dama sauran
hadisan dasuka zo akan haka, mafi kamalar sallama shi ne ka ce "ASSALAMU
ALAIKUM WARAHMATULLAH WABARAKA TUHU" mafi cikar amsawa shi ne ka ce WA'ALAIKUMUSSALAMU
WARAHMATULLAH WABARA KATUHU.
Amma SALAM da
ASLM ALKM waɗannan
duk ba sallama ba ce, kuma mutum bazai samu ladan sallama ba in ya yisu, haka
mai amsawa. komai yawan masu aikata hakan da kuma girman masu yi.
Masu kawo wata
shubuha cewa wai SALAM gaisuwar 'yan Aljannace danhaka yahalatta kacewa ɗan'uwanka SALAM, saboda
Allah yabada da labari cewa 'yan Alajannah idan sun shiga Aljannah sallamar su ita
ce "SALAM"
"تحيتهم فيها سلام"
Sallamar 'yan
aljannah ita ce salam.
Sai muce duk
da wannan Annabi sallallahu Alaihi wasallam ya san shi ɗan Aljannah ne, kuma sahabbansa duka 'yan
aljannah ne, amma duk da haka ba a samu Annabi yana yiwa sahabbansa irin wannan
sallamar ba, kuma ba a ruwaito sahabbai suna yiwa junan su, irin wannan sallamr
ba, haka magabata na kwarai, to ko iya wannan ya isa rusa waccan shubuhar, haka
kuma rayuwar duniya daban data aljannah, bazai iyu kadakko abun da Allah yabada
labarinsa cewa 'yan Aljanna zasuyi insun shigeta ba, kadabbaka anan rayuwar
duniya kuma ka ce addinine kake yi, duniya gidan Aikice dafata, aljannah kuma
gidan sakamako ce, kuma baka da wani nassi daya tabbatar maka kaidin ɗan Alajannar ne, Anan
duniya..
In shã Allahu za
mu zo da karin bayani akan ya halatta takaita sallama dawasu kalmomi, ko kuma
takaita rubuta salatin Annabi ﷺ
da wasu haruffa, ko rubuta kaɗaitar
Allah da wasu haruffa da maganganun malamai akai, Allah ta'ala muke roko Ya karɓi ayyaukan mu, yakuma
sanya mana Albarka arayuwar mu ta duniya da lahira.🤲
WALLAHU A'ALAM
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.