Bayan wasu kwanaki ko na ce satuka, da zuwa lokacin sai na ce har na fara sabawa da halin mutanan cikin gidan Yaya Samir kam mutumin kirki ne shi ne abokin fira na idan yana falon idan bayanan zaman idan na ji zan takura sai na shige kitchen wajen Mai yi musu girki Baba Indo da tun farkon zuwa na take min wasa da dariya tana tsokanata da babbar jikarta kamata take take shaidamin, da matsalolin rayuwa ya sa take aikin a gidan amma ba wai zaman na mata da daɗi ba takan faɗa min su mutane ne kusan da ba ka taɓa iya musu ba su tausayin ta, su dai ta musu dai dai sukeso, abune kuma da ba zai yiyu ba, kai kanka ba ka cika goma ba bare kace za ayi ma dai dai ɗari bisa ɗari takan ba ni baki da lallashina idan suka ɓata min rai
Ina zaune falon duk da na takura
hanyar ficewa na kesonyi amma kallo kallo ya riƙeni, falon ya yi shiru sai ƙarar
Tv da hira ƙasa
ƙasa
na wasu daga cikin mutanan falon, wanda ni dai da ido nake bin Tv ina Kuma jin
daɗin kallon da muke
na film ɗin waris
"Yaya Abdulmalik ka san
mene?"
Naji Fatima na faɗin hakan
"Yaya Abdulmalik ya bata
amsa da
" sai kin faɗa”
Ta ci gaba da cewa
"Ka san me Yaya da zai yi
wai makarantarmu sai saka, wannan Sumayyah, ka jifa”
Tsaki ya yi jin maganarta ya Kuma
kalli gefena da na nuna masa kamar ban san suna yi ba
"Maine to shafuwarki da
hakan Fatima ki raba kanki dai kin san halin Yaya Samir baya san irin gulmar
nan, tun da ki ka ga har Abba bai isa da shi ba sai da ya kawota ke to Ina
ruwanki”
Yaya Abdulmalik ne yake ta sababi
duk da muryar ba da ƙarfi yake ba amma za ka gane sababi yake
Fatima ta ce
"Wallahi kawai dan yana nuna
ya fi ƙarfin
Abba ne shi ya sa ya kyalesa, yarinyar da suke talakawa ina suka cancanta da
zama damu, kaima kanka shaida ne Abba ya ce duk wanda ya zauna da su tsiya cewa
zai yi, kuma duk mamarsu ce gashi nan Abba Abdallah ko almajiri dake garari ya
fisa kyan gani akanme zama da muguwar mace mai ƙashin tsiya. .
Duk da Ummi na zaune bai hana
Fatima yin shiru daga cin zarafina ba, ko Kuma a ce ta kwaɓeta hawaye na ji sun soma
biyo kuncina da duminsu ya tabbatarmin da sune, gaskiya na yarda talaka yana
ganin garari 'yar uwata da nake tunanin za ta fi kowa sanin ciwona ita ce take
faɗin hakan a kaina,
ba ma akaina ba a gaban ido nama, lallai tabbas akwai wata ƙaddara
a zamana zuciyata tuƙiƙi take amma banaji zan iya hassala komai, ban iya faɗa ba ko cacar baki hasalima
rayuwata ni guda nake sai ko su Halima da rayuwarmu ta zo data idan na san ka
fini bana shiga rayuwarka gudun irin hakan
Muryar abid na ji kamar daga sama
yana cewa
"Haba Yaya Fatima ki bari
mana kin ga kuka take, Allah sarki ita bata da laifi dama mu duka za mu zama
kamarta”
Fatima ce ta ce
" Allah ya kyauta yaro ƙashin
tsiya ta yi gado fa”
Abid ya yi tsaki ya ce
"Kece kika sanshi amma ni
dai na san Yaya Sumayyah ta cancanta da zama da kowa kuma ta fiki kirki, ita
bata neman rigima”
Fatima ta miƙe ta
hayyako ta yi kan Abid za ta bigesa
Shigowar Abba ya dakatar da ita
ya daka mata tsawa hakan ya sa ta koma ta zauna tana turo baki sannu da zuwan
da ake masa bai amsa ba ya dubi Ummi
"Yanzu kina zaune za su yi
mana faɗa ba za ki
hanasu ba ko Sa'adatu?"
Ummi ta kallesa ta re da cewa
"Ai ka san halin Fatima baki
ya sa mata tana magana ka kosan ba za ta kyalesa ba, laifinsa ne”
Abba ya kalli Abid
"Kai maiyasa kasa mata baki
bana hanaku haka ba idan babba yana magana ba'asa baki”
Shiru ya yi Abid ɗin can ya ce
"Abba Yaya Sumayyah Yaya
Fatima ke ta nema da rigima Kuma kowa ya yi shiru ya kyaleta, shi ne na yi
magana, ni dai na san ba mu da banbanci da Yaya Sumayyah ko Abba”
Abban tsaki ya yi ba tare da ya
ce komai ba ya yi gaba kila ko maganata baya so ayi masa ko?, bare yaji ba'asi
maiya haɗa abun, jikina
ba kwari na bar musu falon ba tare da na kallesu ba da alkawarin ban ƙara
zama a falon gaba ɗaya
har na bar gidan, ina tafiya na fara jiyo maganar Ummi
"Fatima abin da kikai
gaskiya bai dace ba, karki ci gaba da biyewa Abbanku zai kaiku ya baro ku, ni
dai na faɗamiki cin
zarafi bai da wani alfanu"
Daga nan ban sake jiyo maganarsu
ba na kuma fasa shiga daki na yi hanyar kitchen
Baba Indo na samu da sallama baki
na na ƙarasa
inda take
Kallona ta yi bayan amsa
sallamarta tare Kuma da ajiye abin da take ta matso kusa da ni
"Sumayyah na san kina cikin
damuwa ko?"
Hawayen da suka ciko idona suka fara
zubowa na goge na kalli Baba Indo ba tare da ta ce min nabar zubar da hawaye ba
na soma magana domin dai iya shaƙuwa na shaƙu da Baba mukan tattauna al'amura da dama
na dangane da gidan harma ta ba ni shawarwari matar bata da surutu da yawan
magana dattijuwa ce mai sanin ya kamata hakan ya sa tare muke hira a gidan
Kamar muna da alaƙa da ita
"Baba babu mai sona a nan na
zo gurin da ban cancanta da zama ba gurin da arziƙi shi ne ƙimarka Yaya Samir kaɗai ke sona a bayan shi sai
Kuma ke duk da duk kulawata bata cancanta da ku ba amma wanda ya fi kusa dani
bai riƙeni
matsayin ɗiya ba Baba bana
son ci gaba da zama anan, na fiso naje inda na cancanta da zama na zauna da su
cikin so da ƙauna”
daganan na rushe da kuka
Baba ta dafani” Sumayyah ba zan
hanaki kuka ba danni ma na fara jiyo hayaniyar fatima, ban yi tsammanin Kuma
hakanba na ɗauka komai
wani abu da kake ji da shi ba za ka yiwa ɗan
uwanka ba, Amma abin takaicin kowa yana jinta aka goyamata baya kuma, Amma ki
sani baki cancanta da hakan ba kuma Allah zai miki sakayya ke ɗin yarinyar kirki ce mai ƙoƙarin
aikata abu mai kyau, na daɗe
ina kallo da nazarin 'yam mata kamarki kamarki amma ban sami ɗiya mai hankali nutsatsiya
ba a bayan ke, kin ga ko kece kika cancanta da kowa ya soki ma”
Shiru na yi na kalli Baba tare da
murmushi Mai ciwo jin ta kawo ƙarshen zancenta na ce.
"Baba ke nan haka mutane da
dama suka sha faɗi a
gareni amma har yau ban fahimci komai akai ba na kasa fahimtar ta ina Na
cancanta, Baba rayuwa ta abar tausayi ce tun da ga yarinya har zuwa girma na
sai kin zub da hawaye a lokacin da kikaga Abbana ki ka ga Abban Katsina kowa yaƙi
Abbana yaƙi
tallafa masa saboda Ummanmu sunce ko sun basa wani abun to a haka zai ƙare ba
zai arziƙi
ba sai dai idan sun rabu da Ummanmu, hakan ya sa kowa ya barsa cikin ƙunci, bayan
soma girmanmu mun ɗauka
ƙiyayyar
da sukewa Umma a iya ita kaɗai
za ta ƙare
ashe ta shafemu muma kanmu, mun zama kamar abin ƙyama a cikin danginmu, kowa hantararmu
yake, na rasa yaushe komai zai wuce”
Baba ta girgiza kanta ta ce
"Karki sare karki gaggawa
komai zai wuce ya zama tarihi kuma za ku zamo abin alfahari fiye da duk wanda
zai tunani za ku zama wasu abun insha Allah sai danginku sun fahimci ummanku
mai ƙashin
arziƙi
ce bana tsiya ba, kuma ma ki cire wa kanki tunanin akwai wani Mai ƙashin
tsiya kowa dai akwai iya arziƙinsa a rayuwa Kuma kowa zai tadda abunsa,
komai daran da ɗewa”
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.