Sallamar Abid ta katse min tunanin da nake yi sai da na amsa masa ya shigo daga cik gefena ya zauna ya miƙomin wayar dake hannunsa
"Yaya Sumayyah ki amsa waya Yaya ya ba ni ƙawarki na kiranki”
Ban tsammanin kiran kowa ba bayan
Halima Kuma ita ce dai ƙawar tawa da Yaya Samir ke da number ɗinta haka nan kuma na ji gabana yana faɗuwa haka dai na daure na
anshi wayar, wayar Yaya Samir babu password hakan ya sa na karɓa na danno number ɗin Halima na bi kiranta
Sallama na yi mata bayan ta ɗaga jin bata amsamin ba ya
sa na cire wayar a kunnena na duba wayar ba wai an katse ba ne haka na yi
tunanin ko ba service haka dai na sake maida wayar kunnena na sakeyin wata
sallamar kukan Halima na ji da shashshekarta tuni na ruɗe gabana ya ci gaba da faɗuwa na daure na fara tambayar
Haliman
"Halima lafiya maike damunki,
ba za kimin magana ba sai kuka mai yafaru dan Allah ki sanarmin kar ni ma ki
sani kuka”
Da wannan lallashin da nake yiwa
Halima ya sa ta yin shiru tana ajiyar zuciya zuwa can ta soma magana
"Sumayyah ƙaddara
ta riga fata duk ƙoƙarinmu ba xamu guje mata ba, kuma kowanne bawa da irin yadda ƙaddararsa
ke zuwar masa, haka dole kowa ya yi haƙuri da irinta sa, saboda cikar imaninka”
Shiru na yi Ina sauraren Haliman
Kuma bugun zuciyata na tsananta ƙaruwa na dai daure na ce
"Halima dogon jawabin nan ya
isheni duk na san da hakan, ki sanar dani abin da ke faruwa dan Allah, hankalina
ya kasa kwanciya”
Halima ta ɗanyi shiru kafin ta ce
"Exam din mu ta ƙualyfying
ta fito sai dai Sumayyah ajinmu mutum goma suka samu ciki. . . "
Gaba na ya ƙara faɗuwa na dakarta da Halima idona
yana zubar da hawaye masu zafi
"Babu ni a cikin waɗanda suka ci ko?"
Nayi mata tambayar saboda Ina da
yaƙinin
haka ne jikina kawai ya bani
Shiru ta yi na sake jefa mata tambaya
"Ban ci ba ko?"
Cikin ƙinƙina ta ce
"Eh. . ey"
Bata kuma sake cewa komai ba
Nice ma na sake ƙoƙarin
yin magana amma na ji ta yi shiru alamun ta katse wayar hakan ya sa na cire
wayar a kunne na na miƙawa Abid da hawaye suka cikamin idanuwa na
Abid ya soma magana
"Yaya Sumayyah mai yafaru ne
kike kuka”
Hawaye na na goge na ce
"Bakomai Abid"
Kallona ya yi ya ce
"A'a da komai fa Yaya
Sumayyah ki faɗamin
Dan Allah"
Na sake ce masa
"Bakomai Abid, kaje ka kaima
Yaya wayarsa”
Ya ce
"To shike nan zan kai masa
amma dai zan faɗamasa
kuka kike bayan kin gama wayar"
Haka Abid ya tashi ina kallansa
sau tari idan na gansa muna wata firar Ina tunawa da Ahmad da yake kusan
kamarsa, haka a halayyarsa nakan tuna Ahmad saboda yadda shi ma Abid ke da
kyawun hali sam ba ruwansa da sabgar 'yan gidansu, shi da Yaya Samir halayyarsu
ta banbanta da 'yan uwansu su akwaisu da tausayi da son zumun ci saɓanin sauran kowa halin
iyayensa ya biyo, batun ƙualyfying ɗinmu
ta faɗomin a raina na
rasa mai zan yi kuka zan yi ko me da zan ji sauƙi a zuciyata kaina na kife a ƙasan
carpet ɗin da nake kai
zaune ina wani irin kuka Mai ciwo shike nan karatun da na saka rai zanƙarasa ba
zai samu ba, karo na farko na faɗi
jarabawa, shin ta ina iyayena za su nemo kuɗin
da za a biyamin na kammala karatuna na sani babu mu ɗin da neman na yau da kullum muke ta yaya za
mu nemo kuɗin biyan
jarrabawa, duk da Ina da yaƙinin a cikin dangin mahaifina akwai waɗanda mutum dubu za su biyawa jarabawa ba tare
da arziƙinsu
ya girgiza ba amma inada yaƙinin ban da ni hakan ya sa ma ban saka rai ba, ya sa kuma na shiga
damuwa mai tsananin gaske
Sallamar da Abid ya sakeyi ta
dawo dani daga tunanina ta Kuma tsayarmin da kukan da nake amsa masa sallamar
na yi ya Kuma shigo ya maida kallensa gare ni
"Yaya Sumayyah kuka kike ko,
ina jiyowa tun daga kofar ɗaki
ki barwa Allah komai”
Na _daga masa kai
Da ga nan ya ce
", Yaya yana waje ya ce kije
yana compound"daga nan ya fice ni ma ba nida zaɓi illah na saka hijabi na bi bayansa
A tsaye na hangosa fuskarsa babu
wata walwala sallama na masa ya amsamin na gaishesa ba yabo ba fallasa ya amsa gaisuwar
tawa, wanda ban san dalilin hakan ba yana nuna min kujerun robar da ke kusa
dani yana ƙoƙarin
jan ɗaya daga ciki ya
ce
"Ki zauna ma na” hakan ya sa
na ja ni ma na zauna da Bismillah baki na
Kallon da Yaya Samir yake min da
na kasa jurewa na yi ƙasa da kaina
Shirun da ya ratsa tsakaninmu can
Yaya Samir na ji gyaran muryarsa ya fara magana
"Sumayyah dan Allah ki yi haƙuri da
duk yadda rayuwar za ta zo miki na sani hakan babu daɗi, na ji kamar ina ma nine ke, rayuwarki tana
ba ni tausayi duk da na sani jarabtace daga Allah, na san komai Sumayyah, ni
Haliman ta fara yiwa maganar ban san ta Ina zan tunkareki da zancen ba hakan ya
sa na ce ta sanarda ke da kanta, ko damuwar za ta zo da sauƙi a
gareni, Sumayyah ba ni da sauran nutsuwa duk da na san kin cancanta na miki
komai sai dai yadda zan riƙa kyautata miki ba tare da na ɓatawa
su Abba rai ba, ban san ta ina zan misalta boɗadden
halayyar Abba da Ummi ba dan Allah kiya haƙuri Sumayyah ki ɗauki komai na rayuwarki bisa kaddara kuma
komai zai wuce”
Kai kawai na ɗagawa Yaya Samir don ban
san irin amsar da zan basa ba don zan iya fashewa da kuka ina fara magana, magana
shi ma ya ci gaba dayi
"Yanzu ki kwantar da
hankalinki, zan yi magana da Abba zan biya miki kuɗi ki zana a private idan lokaci ya tashi”
Ban wani gasgata lamarin ba dan
na san abin Kamar da Kamar wuya shiga islamiyya ma sun hanani bare Kuma biyan
kuɗin zana exam, hawaye
suka cikamin idanuwa na don ina da tabbacin kawai lallashi ne kawai, na dai
daure na ce
"Yaya Samir ko ban zana na
ba na karɓi kaddarata,
amma Yaya Samir Halima da Batul nake so na ji sun samu, hankalina ya fi tashi
idan na tuna su ban san tasu makomarba”
Yaya Samir ya kalle ni
"Ki share hawayenki Dan
Allah, sai na faɗamiki
komai”
Ba nida zabi illah na goge
hawayen na fara saurarenshi
"Batul da Halima duk sun
samu, Sumayyah kece kawai Allah ya ƙaddaramiki hakan ba wai dan baki da ƙoƙari ba
illah kawai jarrabata ce daga Allah hakan Allah yaso, idan Allah yaso zai
jarrabci bawa saiya jarabceshi da abubuwa kala kala bawai dan bai sanshi ba, sai
dan yana nufin mutum da wani alkhairi”
Bana sauraran zancen Yaya Samir
sosai na kife kaina jikin gwiwa ta ina kuka da bana jin akwai mutumin da nake
buƙata
a yanzu bare jin muryar wani, a kusa da ni, ƙaddara ce na sani amma ban san kalar ta
wa ba a lokaci ƙanƙani komai ya sauya min, ni ka ɗai
na san ciwan da na ke ji da raɗaɗin da nake ji da babu mai
fahimtata.
Bayan wasu kwanaki da na ɗauki komai a bisa ƙaddarata
na Kuma amshi hakan, walwalata ta soma dawowa saboda yadda kullum na yi waya da
Umma a wayar Yaya Samir takan kwantarmin da hankalina
Yau da shirin zuwa aiken Ummi na
ta shi, dutsen safe za mu ni da Abid gidan ƙanwar Ummi Aunty Ramla ka sancewar
weekend be ƙarfe
goma muka fito bakin titi ni da Abid da nake sanye da doguwar rigar material
sai mayafina kalar brown kwalliyar fulawar jikin material ɗin muna tafe muna fira
cikin wasa da dariya mun yi matuƙar sabo da Abid matuƙa
kamar mun shekara da shekaru tare haka muka tsaida napep muka shige muna faɗamasa unguwar da zai kaimu
dutsen safe low-cost, babu laifi mun yi 'yar tafiya, kafin mu isa unguwar har ƙofar
gida aka ƙarasa
damu, muka miƙamasa kuɗi
muka fito ni da ma ban taɓa
zuwa gidan ba Abid ne yake jagorantar tafiyar sai da muka ƙwanƙwasa
gate ɗin gidan da
mintina kafin zuwa can muka ji alamun tafiya, hakan ya sa muka tsaida buga
gidan Aunty Ramla din ce ta buɗe
kofar da fuskarta ba yabo ba fallasa ta yi mana izinin mu shigo ciki bayanta
muka bi har zuwa ciki a babban falo muka zauna saman kujera muna gaishe da
Aunty Ramla din haka dai ta amsa tana ɗan
shan ƙamshi
har mamakin hakan na yi ganin da Abid na taho ya kamata a ce ta ɗan saki fuska ko danshi duk
da ban san halin Aunty Ramla din ba ƙila hakan take ba mu jima sosai gidan ba
muka fito Dan yaran Aunty Ramla biyu duk basa nan, suna gidan kakanninsu, ba mu
samu napep ba a nan ƙofar gidan ganin za mu daɗe
ya sa muka fara tafiya a ƙasa duk da saƙon da muka amso masu nauyi ne amma ba
muda zaɓi ban da muyi
kama kama muka riƙe hannun ledar nida Abid muka fara tafiya zuwa bakin titin
hankalinmu kwance muna fira da Abid yana ba ni labarin Aunty Ramla Wanda a
labarin na fahimci halayyarta ce shariyar data mana, amma duk da hakan har dama
wulaƙanci
na faɗa a raina
labaran Aunty Ramlan ya dinga ba ni na tun kafin ta yi aure har zuwa yanzu wani
abun har dariya take ba ni a raina Kuma "ina lallai su Abid tona asiri ne”
"Sumayyah!, Sumayyah!!, Sumayyah!!!"
Kin kiran ba ɗaya ba ba biyu ba ya sa ni
waigowa tare kuma da san tuno Mai muryar tsammanin da na yi ko hakan ne
Malam Hamid ne idan ba idona ne
suke min gizo ba, domin a sanina lokaci baiyi tsawon da zan manta da shi ba, kallon
mamaki nake masa, ni ma shi yake min a hakan har ya ƙaraso inda muka tsaya, gaishesa
na yi ya amsa da murmushi fuskarsa haka Abid ma ya gaishesa Malam Hamid ya miƙawa
Abid hannu suka gaisa yana tambayarsa sunansa Abid ya yi murmushi ya faɗa masa da alamu Malam Hamid
ya birgesa guri na ya juyo ya maida dubensa gareni
"Wato da ba za ki juyo ba
ko?, harna fara tunanin ƙila bake bace, dan muryarki kawai na ji harna ci gaba da
tafiya na yi tunanin ke ce”
Nayi murmushi nace
"Eh ni ce ni ma da farko ban
yi tsammanin kai ba ne, saboda ban yi tunanin sake ganin ka ba”
Murmushi yayi
"To saboda me, bayan kin san
nan garinmu ne”
Shiru na yi dan ba ni da tacewa
danni ganin mai kuɗi
nakewa Malam Hamid Ina zansa wa raina tunanin ganin sa, karo na biyu
Maganar Malam Hamid ta katse min
tunanina
"Kinyi shiru kullum na kira
Halima saina tambaye ta ya kike takan cemin lafiya lau, Kuma har lambarki na buƙata ta
ce baki da waya yanzu haka da ta yayanki na nan kuke gaisawa, ni kuma banwai
amsa ba saboda ban san mai zance masa ba idan na kira”
Na jinjina kai alamun na gamsu da
maganarsa
Ya ci gaba da cewa” na samu
labari jarrabawar ku batayi kyau ba Allah ya sa hakan ya yi sanadiyyar samun
nasararku a nan gaba, abun sam baimin daɗi
ba Sumayyah saina ji kamar ni abun ya faru dani”
Duk da bana son a tuno min abunda
ya faru amma haka nan na daure
"Nace Amin na gode”
Bai ƙyale maganar haka ba, ya
ce
"Yanzu kin ga rana ta farayi
kimin kwatancen gidanku na nan sai na samu lokaci na zo, mu ƙarasa
maganar da ba mu ƙarasa ba a baya”
Shiru na yi Ina tunanin maganar
da na san ta soyayya ce take nufi ba dan ina da buƙatar sa a rayuwata ba na
masa kwatancen gidan tare da jagorancin Abid a kwatancen kawai dai saboda
kirkinsa na yi masa kwatancen amma gaba ɗaya
a Raina kulllum ba ni yake Malam Hamid ba sa'ana ba ne a soyayya bare kuma aure
duk da ban san koshi waye ba
Haka muka yi sallama yana Mai min
alƙawarin
zaiso a satinnan insha Allah, daganan muka ci gaba da tafiyarmu Abid yana tambayata
waye shi wannan, na masa bayaninsa, a matsayinsa na malaminmu ya dube ni
"Gaskiya Yaya Sumayyah yana
da kirki sosai”
Nayi dariya na ce
"Kai Abid daga ganin mutum
haka ai ba’a shaidar mutum Karan farko"
Ya jinjina kai ya ce
"Haka ne”, daganan muka
sauya firar da wata” har muka ƙaraso bakin titi
Abun abun mamaki nan ɗinma babu motoci ga zafin
rana haka na ji Kamar nasa hannu ka na fashe da kuka dan tsabar takaici da
bakin ciki ga fangon kaya a hannu tsugunnawa mukayi muna roƙon
Allah ya kawo mana mafita, babu jimawa mota mai kyau sosai ta tsaya kusa da mu
da ni ba ma'abociyar sanin mota ba bare na san sunanta ko kuɗinta horn aka yi mana ganin
ba mu san mai ita ba mukayi shiru jin ƙarar buɗe
motar ya sa muka ɗago
kanmu, Abid na ga ya ƙarasa gurin mutumin da yafito daga motar da alamu Abid yasan
mutumin ni ma kallansu na yi
"Kawu"naji Abid ya faɗa
Saurayin da Saida ya kirasa kawun
na kallesa tabbas yana yanayi da Umminsu Abid
Tambayar Abid yayi
"Yana ganku a nan Abid"
Abid ya sosa kai
"Mota muka rasa”
"Ku shigo na kaiku gida yi
ma waccen da kuke tare magana” kawun ya faɗa
da ba musu ya ƙaraso guna Abid ɗin
niko tun kafin ya ƙaraso na miƙe dan gajiye nake dama, kayan muka kinkima
mu ka ƙarasa
wajen motar, Abid ya buɗe
min gidan baya na shiga a lokacin har kawun ya shiga mota abid ɗin ya shiga gidan gaba kusa
da Kawun nasa sai a lokacin na gaida Kawunsu Abid ɗin ya juyo ya amsa kafin ya juya ina jinsa
yana cewa
"Abid wannan wace ban gane
ta ba”
Abid na ji ya ce
"Yaya Sumayyah ce, 'yar ƙanin
Abbanmu ce Abba Abdullahi”
Naji yana ce wa
"Au ita ce rannan naje gidan
na ku, Ummin ku ke ba ni labarin zuwan nata”
Waigowa Kawun ya yi ya sake kallo
na na ji ya ce
"Yasu Asma'u ai sai yanzu na
ga Kamar ki da Asma'un"
Na ce masa
"Suna gida lafiya lau"
Da haka ya ja motar cikin mintina
ƙalilan
muka ƙarasa
gida parking ya yi muka fito harda Kawun su Abid ɗin
shi ne ya ɗauki ledar
saƙon
yana janmu da hira har muka ƙarasa cikin falon da ba kowa a falon sai
Yaya Samir ɗin, yn
danna wayar shi d Tv kunne Amma babu volume, sallamarmu ya amsa yana murmushi
fuskarsa kusa da shi kawun ya zauna ya bashi hannu
"A'a Malam Samir ana gida ke
nan"
Yace
"Eh wllh Kawu Mahmud, yanzu
da na ji shiru ba su dawo ba nake tunanin Kiran lambar Aunty Ramlah"
"Ayya wllh a hanya na haɗu dasu suna jiran abin hawa”
Ba muƙarasa jin zancen ba muka
wuce ciki, kitchen Ni na nufa, na kawo musu lemo zan tashi Yaya Samir ya ce
"Zauna mana firarki mu keyi
da kawu Mahmud, ya ce waya ya kamata na siya maki ya ce kin isa riƙewa”
Kallona na mayar ga Kawu Mahmud
ganin mun haɗa ido ya
sa ni cikin jin kunya na maida kaina ƙasa, Muryar Kawu Mahmud na ji ya na cewa
"Eh mana ki ɗago kanki mana Sumayya
aikin isa riƙewa
na san ƙawayenki
duk wasu na da ita kuma insha Allah na san ba ba za ki wani abu mara kyau da
ita ba” Har ya gama maganar ban ɗago
ba sai ma ci gaba da kallon carpet da nake yi
Kawu Mahmoud na ji ya ɗaura da cewa
"Tun kafin na gane ta na
daiga yanayi da Asma'u tunanina ma da ko ƙanwar Asma'u ce saina tuna Asma'u bata da
ƙanwa
ashe ƴar
tace, sosai tana da natsuwa Samir"
Muryar Yaya Samir na ji ya bashi
amsa da cewa
"Eh na yi tsammani za ka ganeta
tana yarinya a Gwarzo tana maƙalewa gurina Ummi tana cewa Sumayyahn
Samir"
Naji kawu cikin ƙosawa
ya ce
"Zaka fara surutun naka da
sai anfi awa ba a ƙare ba ke nan ko?dan Allah tashi muje yanzu a siyo mata wayar
nan tun ina da kuɗi a
jikina idan mun dawo sai ayi firar, in Kuma an kirani wani gurin shike nan"
Dariya ce take neman zuwarmin jin
tattaunawar da suke yi, saika ɗauka
abokaine ko na ce ƴan biyu ko cousin brothers sun burgeni sosai duk da inada yaƙini
Kawu Mahmud ma ya girmi Yaya Samir tun da har ta yi soyayyah da Aunty Asma'u duk
da cewa ban san a yana shekara nawa sukayi soyayyar ba, ƙila soyayyahr ƙuruciya
ce kawai, hakan sosai ya ƙara burgeni
"Taso muje ki zaɓa da kanki”
Maganar Kawu Mahmud ta katse min
tunanin da nake yi miƙewa na yi, hanyar komawa ciki na yi na kira Abid mu tafi tare
ya tayani zaɓar danni
ba wani zaɓen da zan
iya ba na sani
"Ina za ki kuma?"
Muryar Yaya Samir ta sani juyowar
na kuma tsaya da tafiyar da na fara idonsa na tsaye akaina yana kallona daurewa
na yi cire idona daga nashi sannan na ce
"Abid zan kira yaya”
Yaya Samir ne ya harareni kafin
ya ce
"A'a Malama dawo wuce mu tafi”
ya ƙara
sa maganar yana nuna min hanyar fita falon
"Toh Yaya” na iya faɗa na dawo da baya inda suke
da Kawu Mahmud har ya buɗe
ƙofar
falon yana ƙoƙarin
ficewa ni ma na bi bayansu
A motar Kawu Mahmud muka fita, Ba
muyi tafiya mai nisa ba muka ƙara sa inda za mu siya wayar Green House
parking Yaya Samir ya yi muka fito duk a tare muka shiga ciki
Nida ban san wayoyi ba bare na
iya zaɓar waya Yaya
Samir ya zaɓarmin
Iphone, da ƙarama
maxfone da Kawu Mahmud ya ce a ɗaukar
min acewarsa saboda iPhone bata riƙe caji sosai shi ne kuma ya biya kuɗin wayoyin, har layuka aka
siyamin akamin register Yaya Samir ya yi min register saboda shi ne mai
National ID Card sai ko Kawu Mahmud da ya ce ya bar nashi a gida, Murna sosai nake
yi da yin wayar tawa dan ban taɓa
kawowa raina ba na kuma dinga musu godiya kamar kujerar Makkah suka biyamin, dan
kam wayar babbace sosai wanda ya siyama wannan wayar ya samu dama da rabon ka
Makkah ɗin ma zai
biyama dan ina gani Kawu Mahmud ya ciro Atm ɗin
shi aka cire dubunnan kuɗin
wayar da sai lokacin na gasgata kuɗin
wayar dan dan ko da aka faɗa
da farko ban gasgataba
Naka sa Kuma fahimtar dalilin
hidimar Kawu Mahmud mai yawa haka wajena Nidai na san ba mu da wata alaƙa ban
da ka sancewarsa ƙanin Ummi Saidai tun da ya ambaci Aunty Asma'u na fara tunanin
ƙilashima
yana cikin samarin Aunty Asma'u tana budurwa ta yi samari babu laifi
"Hakanne ma ban da hakan ai ba zai miki hakan ba” zuciyata ce ta faɗa min hakan ta gasgastarmin,
Duk da a halayyar Aunty Asma'u ban yi tsammanin akwai wanda zai mata matukar so
hakan ba saidai ance so gamon jini ne
***********************************
Ban jira na caza ƙaramar
ba, Na kira layin, Halima, duk abin da zan yi bana manta Halima ita ce take
fara faɗomin a raina, inasan
Halima, fiye da tunani, ina jin wayarnan dama tana nan tare za a siyamana, Batul
kam ba tada wata matsala, ita dai biye mana take yi, aurenta ma, tana gama
makaranta za ayi nafi tunanin kirana duk da ban tabbatar ba
Har wayar ta gama ringing ta
katse Halima bata ɗaga
ba hakan ya sani tunanin ko tana wani guri ko takai wayar caji da wannan
tunanin na miƙe na maida ba wayar caji, na ci gaba da saƙa da
kwancewa wata damuwa ta fara ƙoƙarin ziyartata
Wayar na maida caji ina ci gaba
da tunanin Halimah Allah ya sa dai ba wata damuwa idan kaji shirun mai ƙaunarka
ya kamata ka shiga damuwa dan masoyi ɗaya
ya fi ma maƙiyinka
sau million
Tunanin nawane ya katse jin ƙarar
wayata daga cajin na ciro ta ina duba mai kiran nawa da bana raba ɗaya biyu Halima ce dan ita
ce zan iya cewa kaɗai
na kira a wannan lokacin
Da sallama bakina mai haɗe da zumuɗi na ɗaga wayar Halima ɗin
Ba tare da ta amsamin ba sai ƙarar
murnar ta da ta cika kunnena ta ɗaura
da cewa
"Sumayyah, ba dai kin yi waya
ba, "
Nayi murmushi mara sauti Halima ke
nan na yi maganar a zuciyata daganan na furta
"Oh Halima haka kike yi kuma
yanzu, kin cikamin dodon kunne da ƙara”
Tsaki Halima ta yi min ta ce
"Kiji 'yar rainin wayau dan
ina murna shi ne kike min wulaƙanci, bari na kashe wayata dama ba katin
gareni ba”
**** ****
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.