𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Idan Mutum Baiyi Sallar Azahar Ba, Sai Ya zo Yatarar Ana La'asar Jam'i, Zai
Iya Binsu Da Niyyar Azahar Idan Aka Idar Sai ya yi La'asar Ɗinsa?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد لله.
Wajibine jerantawa wajan ramuwar sallar data wuce mutum amazhabar jamhur ɗin malamai.
Ibnu ƙudama Allah yajiknasa darahma acikin Almugniy ( 1/352) ya ce: Adunkule
wajibine jerantawa wajan ramuwar sallolin dasuka wuce mutum.
Imamu Ahmad yafaɗi
hakan agurare da dama, da naka'iy da zuhuriy da rabee'ah, da yahyal Ansary da
malik, da lais da Abu hanifah, da ishaƙ.
Imamu shafi'i ya ce: Bawajibi ba ne domin ramuwar sallar data wuce ba
wajibibane jerantasu, . . . . kamar azumi idan jerantawa yatabbata to wajibine
jeranta azumi ko da mai yawane, Ahmad yafaɗi haka awani wajan.
Abu hanifa da malik sukace: Badole ba ne jeranta sallolin ba idan wacce
takubecewa mutum sun haura sallar dare dawuni ɗaya, saboda lura dacewa abunda yakaru a
kan sallolin dare dawuni zaiwa mutum wahala, zaikuma ci gaba damaimaitawa, saboda
haka jerantawa tafaɗi
akansa, kamar jerantawa wajan rama azumi.
jerantawa wajibine awajan jamhur ɗin Hanafiyyah da malikiyyah dahanabila, saidai Abu
hanifa da malikiyyah basa wajabta jerantawa idan ramuwar sallar yakaru a kan sallolin
wuni da na dare.
Yanda ake jerantawar shi ne mutum ya zo da sallar ayanda jerangiyarsu take,
misali wanda azahar da la'asar suka kubuce masa, to inya zo ramasu zaifara yin
azaharne sannan sai ya yi la'asar.
Saidai wajabcin jerantawa yana faɗuwa a kan mutum abisa mantuwa ko rashin sani
kokuma tsoran fitar lokacin sallar da lokacinta yake bai fitaba, dakuma tsoran
kubucewar jam'i abisa Zance mafi rinjaye.
Misali idan ana binka salloli biyu, azahar da la'asar saikafara yin la'asar
kafin azahar abisa mantuwa korashin sani wajabcin jerantasu sallarka ta yi babu
komai akanka.
Ko kuma kanajin tsoran fitar lokacin sallar la'asar muktari zaifita kafin
kai azahar, zakai la'asar daka baya kai azahar ɗin.
Haka dazaka shiga masallaci katarar an tayarda jam'in sallar dalokacinta
yake.
shin za ka fara sallar ramuwane ko zakabi jam'in wacce akeyi?
Imamu Ahmad awata ruwaya daka gareshi wacce shaikul Islam ibnu taimiyyah
yazaba cewa jerantawa yafaɗi a
kan mutum idan yana tsoran rasa jam'i.
Saidai alokacin mutum zaibi, jam'i daniyyar rama sallar wacce ake binsa, kamar
wanda ake binsa sallar azahar saiyatarar ana jam'in la'asar zaibi jam'in
daniyyar azahar, ban-banci niyyarsa data limaminsa ba zai masa komaiba, idan
aka idar sai ya yi la'asar ɗin.
Sharhin mumti'i Ala zadul mustaƙni'i ( 2/138-144)
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu. . .
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp. com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www. facebook. com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t. me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.