Ticker

6/recent/ticker-posts

Falsafar Bahaushe Cikin Littafin Tatsuniyoyi Da Wasanni Na Ibrahim Yaro Yahaya

Binciken Da Aka Gudanar A Sashen Harsunan Nijeriya Da Kimiyyar Harshe Na Jami'ar Sule Lamiɗo Da Ke Garin Kafin Hausa, Jihar Jigawa, Domin Samun Takardar Shaidar Kammala Digiri Na Farko (B.A HAUSA), 2023

Falsafar Bahaushe Cikin Littafin Tatsuniyoyi Da Wasanni Na Ibrahim Yaro Yahaya 

NA

HABIBA ABUBAKAR IBRAHIM

09037084554

TABBATARWA

 Na tabbata cewa, ni na rubuta wannan kundin bincike da kaina, mai suna "Falsafar Bahaushe cikin littafin tatsuniyoyi da wasanni na Ibrahim Yaro Yahaya". A ƙarƙashin jagorancin Dr. ABDULƘADIR Ginsau. Kuma duk bayanan da aka samo daga wata madogara an ambato madogarar a cikin matani da kuma manazartar da aka ratayo. Babu wani sashe na wannan aiki da aka taɓa gabatarwa a wani wuri a matsayin kundin digiri ko diploma ko kuma maƙala a cikin mujallu wadda wannan bincike ya riska.

 

SHAFIN AMINCEWA

 Wannan kundi mai taken‚ "Falsafar Bahaushe cikin wasannin gargajiya" ya sami karantawa da dubawa da samin amincewa a matsayin wani ɓangare na cika sharuɗɗa da ƙaidar samun shaidar digiri na farko (B.A Hausa) a tsangayar Adamtaka, sashen Nazarin Harsunan Nijeriya da kimiyyar harshe ta Jami’ar Sule Lamiɗo da ke Kafin Hausa, Jihar Jigawa.

SADAUKARWA

 Na sadaukar da wannan bincike ga mahaifana Mal. Abubakar Nasalla, da Umma-kaltume Muhammad (Mama), da Mal. Harisu Babale, da kuma sashen harsunan NIjeriya, da sauran ƴan uwana, da ma ɗaukacin musulmi baki ɗaya.

 

GODIYA

 Ina godiya ga Ubangijin dukkan halittu, godiya ga Allah (S.W.T) da kowanne al'amari ke komawa gare shi, mai kowa, mai komai, mahaliccin sammai da ƙasai da abin da yake tsakaninsu, ya kuma daidaita a al’arshinsa. Godiya ga Allah (S.W.T.) wanda yake saukar da ruwan sama, kuma yake tsara al'amuran bayinsa yadda yaso. Godiya ga Allah (S.W.T.) da ya samar da ilimi, ya arzurtawa bayinsa , ya yi musu baiwar dawwamar da shi a ƙwaƙwalansu, sannan ya ba shi hikimar yin tunani a kowanne irin al'amari. Tsira da aminci su ƙara tabbata ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad (S.A.W.) da iyalansa da Sahabbansa da waɗanda suka bi tafarkinsu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

 Jagoran duba wannan kundi, Dr. ABDULƘADIR Ginsau, haƙiƙa ya cancanci godiya ta musamman, saboda jajircewarsa wajen ganin wannan kundi ya kai gaci, ya yi matuƙar ƙoƙarin nusarwa da ba da shawarwari masu matuƙar muhimmanci, Ina roƙon Allah (S.W.T.) ya ƙara masa lafiya da haƙuri da karamci, Allah ya ɗaukaka shi ya kuma ƙara masa ilimi, Allah ya kyautata rayuwarsa da ta iyalinsa, Allah ya biya masa duk buƙatunsa na alheri, Allah ya yi masa sakayya da gidan Aljanna.

Godiya ta musamman ga Jami’ar Sule lamiɗo ta Kafin Hausa, wadda ta ba ni gurbin gudanar da wannan karatu. Farfesa Aliyu Mhammad Bunza yana sahun farko a mutanen da suka ba ni ƙwarin gwiwar gudanar da wannan bincike . Ina miƙa godiyata a gareshi da kuma ɗumbin jama’a da suka taimaka yayin da nake tattaro bayanai da kuma rubuta wannan kundi. Gudummuwar da na samu a wurin jama’a ta taimaka wajen warware matsaloli masu yawa, kuma ta kawo mafita ga hanyoyin da aka bi aka tattaro bayanai .

 Wannan godiya ba ta manta da malamai na Sashen Harsunan Nijeriya ba na Jami’ar Sule Lamiɗo ta Kafin Hausa. Gudummuwar da Dr. Mu'azu Sa'adu kudan da Dr. Ɗahiru Abdulƙadir, Dr. Habibu Abdulƙadir, Dr. Abdulƙadir Ginsu, Mal. Muhammad Sani, da kuma sha kundum wanda ya ɗora mu bisa hanyar aiwatar da bincike, ya nusar damu ta hanya mai kyau Mal. Yusuf Nuhu Inuwa, haƙiƙa wannan bincike ba zai manta da irin gudummawarsa ba da jajircewa wajen ganin an iya kuma ya yi kyau, Allah ya biya su da kyakkawan sakamako.

 Haka kuma ina miƙa godiya ga manyan malamai masu ziyartar wannan sashe, Farfesa Bashir Aliyu Sallau, da Dr. Salisu Garba Kargi, saboda shawarwarinsu da haƙuri da suka yi wajen gabatar da tambayoyi da neman ƙarin bayani ga abubuwan da suka shiga duhu a wannan bincike. Allah ya haɗa mu a Aljanna baki ɗaya. Ba zan manta da Farfesa Ibrahim Garba satatima ba, shi ma ya bada gudummawa sosai a wasu ɓangarori na wannan binciken Allah ya biya su da gidan Aljanna..

 Masu iya magana sun ce, 'Hannu da yawa maganin ƙazamar miya.‛ Ina miƙa godiya ta musamman ga Farfesa Saidu Muhammad Gusau, haƙiƙa farfesa ya bada gudunmawa marar iyaka a wajen aiwatar da wannan bincike, tare da nusarwa da shawarwari harma da wasu guzuri duk da za su taimaka binciken ya kai ga kammaluwa cikin nasara, Allah ya biya shi da gidan Aljanna.

 Godiya ta musamman ga mahaifana, marigayi Malam Abubakar Nasalla, da kuma Ummakaltume Muhammad, saboda haihuwa da raino da kuma tarbiyya da suka ba ni har Allah ya kawo ni wannan matsayi, Allah ya saka musu da mafificin alheri, ya yi musu rahama ya kyautata ƙarshensu, shi da ya rasu Allah ya masa gafara, ita kuma Allah ka dawwamar dafarin ciki a rayuwarta ka sa aljanna ce gidanmu na ƙarshe baki ɗaya.

 Ina godiya ta musamman ga yayyena da kuma ƙannena saboda haɗin kai da goyon bya da nake samu a wurinsu. musamman babban yayana Yakubu Adamu da ya ɗauke duk wata ɗawainiyar karatuna tun daga matakin farko, Allah ubangiji ya saka da alheri ya kuma bamu ikon kyautata musu, Sauran ƴan uwana da suka ƙunshi: Maryam Abubakar, Asma'u da Khadija duka Allah ya haɗa mu a gidan aljanna.

 Godiya ta musamman ga Malam Harisu, Uba ne tamkar mahaifi a gurina ya bani gagarumar gudummawa a rayuwata da ta mahaifiya ta, Ubangiji ya saka masa da mafificin alheri yasa aljanna ce gidansa na ƙarshe. haka kuma ina godiya ga yayyena da ƙanne, Babannan, Faruq, Yahaya, Habu, Shu'aibu, Abdurrahman (marigayi), Sulaiman, Adamu ,Nura, Aishatu (babbar yaya), Rabi, Bilkisu, Fatima,Maryam, Rahama, Hauwa'u, Allah ya haɗa mu a gidan aljanna

Abokai sun taimaka min sosai a wannan aiki, musamman Malam Yusuf Mukhtar (Ɗawisu) Babban abokin karatu kuma mai bani shawarwari a fannoni daban-daban. Da kuma Maryam Aliyu Usman, Zainab tijjani, da sauran abokan karatu da abokan arziƙi na cikin makaranta da wurin kwana (hostel), Allah ya saka da alheri ya sa ilimin da muke yi mai amfani ne .

TSAKURE

 Wannan bincike mai suna Falsafar Bahaushe cikin littafin tatsuniyoyi da wasanni: Nazari ne daga Adabin Baka da ya nazarci tunanin Bahaushe da ke cikin Tatsuniyoyinsa da wasanni da ya riƙa aiwatarwa a rayuwarsa, binciken ya mayar da hankali a kan yadda Bahaushe yake sarrafa tunani da hikima da basira da kuma yadda ya ci moriyar kowannensu. Daga cikin tunanin da wannan bincike ya riska a waɗannan rassan na adabin Bahaushe akwai: Muhallin da yake gina su da kuma Taurarin da suke aiwatarwa da duk wasu al'amuran da suka jiɓanci rayuwarsa da zamantakewarsa. Binciken ya nazarci tunanin Bahaushe ne cikin waɗannan muhimman rassa na adabin baka (wasanni da tatsuniya ). Tunani wani abu ne da ɗan’adam yake amfani da shi mai matuƙar tasiri wajen gudanar da harkoki da suka shafi zamantakewa a cikinsa, yana kuma gudanar da al’amuran da suka shafi tattalin arziki da shugabanci da sauransu. Bincike ya yi magana a kan tunani yana nusar da mutum da abinda yake nufi a zuciyarsa. binciken ya ƙuduri aniyar cike giɓin da nazari a tunanin Bahaushe ya bari. ya kuma fito da dangantakar adabi da tunanin Bahaushe a ɓangarori daban-daban, sannan ya yi ƙoƙarin tabbatar da Bahaushe yana da nasa tunani a cikin wasanni da tatsuniyoyi . Binciken ya bi hanyoyi da dabaru iri daban-daban wajen tattaro bayanai da tantance su a wannan aiki. Binciken ya zaɓo nau’o’in adabin baka, kuma ya yi amfani da zaɓi na kusanci a lokacin da ya zaɓi wasanni da tatsuniyoyi wadda duka suke da makusanciyar alaƙa, a inda ya ziyarci manyan ɗakunan karatu a makarantu daban-daban na wannan yankin. ya kuma yi hira da manyan masana da tsofaffin masan harshe da adabi , ziyarce-ziyarce na cikin hanyar tattaro bayanai, binciken ya yi amfani da nazarin littafin tatsuniyoyi da wasanni gaba ɗayansu. A ƙarshe, binciken ya gano adabin baka na Hausa maƙunshin tunanin Bahaushe ne a kan al'amura da dama. Binciken ya gano akwai tasirin tunanin Bahaushe ga tarbiyyar ƴaƴansa, kuma alada tana da muhimmanci wajen gina waɗannan rassa na adabin baka na Hausa. Adabin baka na Hausa yana yin duba a kan da’irar rayayyun halittu wajen fito da idon zucin al’umma a kan zamantakewarsu a wurare daban-daban da suke rayuwa a cikinsa. Idon zucin Bahaushe a adabin baka yana kimanta rayuwa wajen suranta ta da yanayin da Bahaushe ke tafiyar da al'amuransa ta hanyar amfani da tunani a fuskoki daban-daban.

ƘUNSHIYA

TABBATARWA--..II

AMINCEWA-III

SADAUKARWA----.IV

GODIYA…-....V

TSAKURE-....IX

ƘUNSHIYA-.XI

BABI NA ƊAYA

GABATARWA

1.1- Shimfiɗa-..1

1.2 Manufar bincike----2

1.3- Dalilin bincike----.3

1.4- Hasashen bincike----.4

1.5- Muhimmancin bincike--...5

1.6- Farfajiyar bincike----.7

1.7 Naɗewa---8

BABI NA BIYU

BITAR AYYUKAN MAGABATA

2.1- Shimfiɗa-..9

2.2- Hausa da Hausawa da ƙasar Hausa--..10

2.3- Falsafar Bahaushe (Tuntuntuni)-.26

2.4- Wasanni-.43

2.5- Tatsuniya--....49

2.6- Naɗewa-..64

 

BABI NA UKU

HANYOYIN GUDANAR DA BINCIKE

3.1 Shimfiɗa-..65

3.2 Hanyoyin tattaro bayanai--..65

3.3 Babbar hanyar tattaro bayanai---67

3.4 Ƙaramar hanyar tattaro bayanai-...68

3.4.1Tattaunawa------68

3.4.2 Ziyartar Dakunan karatu--69

3.5 Naɗewa-...71

BABI NA HUƊU

FALSAFAR BAHAUSHE CIKIN LITTAFIN TATSUNIYOYI DA WASANNI

4.1 Shimfiɗa-..72

4.2 Dangantakar falsafa da adabin baka--..72

4.3 Falsafar Bahaushe cikin Tatsuniyoyi da Wasanni------...79

4.3.1 Muhalli-.81

4.3.2 Al’amuran Rayuwa--....82

4.3.3 Taurarin Tatsuniya--86

4.3.4 Waƙa-....90

4.4 Tatsuniyar Gizo da ɓaure--93

4.5 Tatsuniyar Dan Sarki ya zama maciji--98

4.6 Tatsuniya Na-goma--102

4.7 Wasannin Ka-cici-ka-cici...105

4.9 Wasanin Bata---------110

4.10 Naɗewa----113

 

BABI NA BIYA

NAƊEWA

5.1 Shimfiɗa-114

5. 2Taƙaitawa--....114

5.3 Sakamakon bincike--117

5.4 Shawarwari--.121

5.5 Kammalawa--125

Manazarta-....126

RATAYE NA1--.135

RATAYE NA 2--137

RATAYE NA 3--154

 

BABI NA ƊAYA

GABATARWA

1.1 SHINFIƊA

 Fannin adabi, fanni ne mai faɗin gaske wadda ya ƙunshi ɓangarori da dama da ake gudanar da nazari a cikinsu da suka haɗa da waƙoƙi, azancin magana, karin magana, tatsuniyoyi, labarai har ma da wasanni kwaikwayo iri-iri da kan zo a ƙarƙashin adabin Hausawa, ba ma iya waɗannan kaɗai ba, domin kuwa akwai wasanni daban da suke aiwatarwa waɗanda suka haɗa da wasannin yara na manya harma da ƴammata da kuma samari wadda har ta kai ga manazarta suna rubuta su da killacesu a littattafai. Haka kuma abu ne sananne cewa kowacce al'umma da yadda take kallon rayuwa, da kuma tafarkin da take bi wajan tabbatar da al'ummarta, ta yanda take son su yi riƙo da ita. Wannan ya nuna cewa kowace al'umma da yanda take gina mu'amalarta tsakanin al'ummarta, amma duk da yadda ake kallon abubuwan rayuwa, tushen ma'aunin ɗaya ne, wato Tunani. Tunani na ɗaya daga cikin darajojin da ya bambanta mutum da dabba da ma sauran halittu da ke doron ƙasa, da tunanin gane daidai da akasin haka ɗan Adam ya ƙara samun fifiko wajen yunƙurin kyautata rayuwarsa da kuma taimakawa ƴan uwansa bil'adam ta fuskoki daban-daban, domin su samu nutsuwa da jin daɗin rayuwa, hakan ne yasa galibi cikin hanyoyin da tunananin ɗan Adam (musamman al'ummar Hausawa) ke kai shi ga daɗaɗawa abokin zamansa akwai Wasa.

 Ba haka kawai Hausawa ke aiwatar da wasanninsu da kuma tatsuniyoyinsu ba da har ake iya gudanar da nazarce-nazarce game da su, akwai wasu dabaru da hikimomi har ma da fasahohi masu tarin yawa da suke cuɗanyawa cikinsu, wannan dalili yasa wannan aiki ya ƙudiri aniyar binciko irin hikimomi da falsafofin da ke cikin wasannin na gargajiya da kuma tatsuniyoyi, hakan ne ma kuwa ya sa aka zaɓi sanya wa binciken ko batun suna da "Falsafar Bahaushe cikin littafin tatsuniyoyi da wasanni na Ibrahim yaro yahaya". domin kuwa wasanni da tatsuniyoyi abubuwa ne da suke da matuƙar tasiri a wurin al'ummar Hausawa, kasancewarsu abubuwa ne da ke killace da harshenta da kuma al'adunta hakan yasa ba za a rasa wani ɓoyayyen tunani cikinsu ba, don haka binciken zai yi ƙoƙarin fito da falsaafar da ke cikinsu.

1.2 MANUFAR BINCIKE

 Babu wata al'umma a doron ƙasa da ba a aiwatar da bincike a cikinta ta hanyar amfani da dabaru domin adana duk wani tunaninta. Bisa ga wannan masaniyar yasa kowanne abu a duniya da za a aiwatar akan aiwatar da shi bisa manufa ta musammam. Wannan binciken na da manufofi kamar haka:

v   Fito da hikimomin da ke ƙunshe cikin wasannin Hausawa da kuma tatsuniyoyinsu na gargajiya.

v   Nuna yadda Bahaushe ke gudanar da al'amuransa cikin falsafa ta hanyar wasannin gargajiya.

v  Gwada yadda Hausawa ke amfani da wasanninsu da ma labarai na tatsuniya wajen ilimantar da ƴaƴansu da kuma nuna musu yadda ake tarbiyya da mu'amalolin rayuwa.

v  Fayyace yadda tunanin Bahaushe ya ke a cikin littafinin.

1.3- DALILIN BINCIKE

 Duk wani al'amari na duniya da ya faru ko kuma aka aiwatar da shi ba ya rasa wani dalilin da ya yi sanadiyyar faruwarsa ko aukuwarsa. Lura da wannan yasa kowanne bincike ake ɗora shi bisa tarin dalilai da ya haddasa gudanar da shi, to haka abin ya kasance ga wannan binciken, domin kuwa ba haka kawai aka tarki gudanar da shi ba akwai wasu tarin dalilai da suka haddasa gudanar da shi da suka haɗa da:

v  Da farko an zaɓo littafin wasanni da tatsuniyoyi ne saboda kasancewarsu sanannu a wurin al'ummar Hausawa, bayan saninsu da aka yi kuma har ila yau akan koyar da su takanas a ƙananan makarantu domin kuwa sune kan gaba wajan samuwar adabin Bahaushe.

v  Dalilin da ya sa aka zaɓi amfani da adabin baka na Hausa a ɓangaren tatsuniyoyi da wasanni domin fito da hikimominsu shi ne, duk wasu al'amuran Bahaushe na taskace a cikin adabinsa. ita kuma hikima tamkar jagora ce cikin al'amuran Bahaushe, wadda yake amfani da ita wajen bayyana al’adunsa da kuma kyautata al'amuran rayuwarsa. Domin haka ne aka zaɓi yin nazarin falsafar cikinsu.

v  Domin ɗaga darajar wasannin musamman na gargajiya da ke neman ɓacewa gaba ɗaya, saboda rashin ire-iren waɗannan ayyuka da za su ke ɗaga darajojinsu da fito da saƙonninsu.

v  Daga cikin manyan dalilan aiwatar da wannan bincken shi ne ido bai kai ga wani aiki da aka gabatar game da falsafar Bahaushe akan wasannin gargajiya ko tatsuniyoyinsu ba, bisa nazari da wannan bincike ya yi a ɗakunan karatu na wannan jami'a da ma sauran jami'o'i daban-daban da sauran fannonin ilimi . Aikin ya samu bayanai akan wasannin gargajiya da dama cikin littattafai da kundaye da mujallu, amma babu wani da aka riska wanda ya taɓo falsafar Bahaushe cikin littafin tatsuniyoyi da wasannin.

 Wannan su ne manyan dalilai da suka tunzura mai gudanar da wannan binciken zaɓar wannan batu.

1.4 HASASHEN BINCIKE

Akwai hasashe da dama da aka gina game da wannan binciken da suka daɗa da:

v  wannan binciken na hasashen cewa akwai wani dalili da ya sa Hausawa suke gina falsafa a cikin tatsuniyoyinsu da wasanninsu.

v  Tatsuniyoyi da Wasannin gargajiya a wurin Bahaushe na daga cikin hanyoyin da ya ke bi wurin gyaran zamantakewa da kuma kyakkyawar mu'amala, wannan yasa ba za a rasa hikimomi ƙunshe cikinsu ba.

v  Binciken na hasashen cewa ba iya cikin saƙon wasa ko tatsuniya Bahaushe ke sanya hikimarsa ba, galibi akan samu wasu hikimomin ga abubuwan da aka gina tatsuniyar da su, kamar wurare, taurari da sauransu. wasu kuwa sai an yi nazari mai zurfi ake gane hikimar da ke cikinsa.

v  A Ƙoƙarin gano irin yadda falsafa ta kutsa cikin adabin baka na Hausa, duk da cewa suna da dangantaka ta jini. Ana hasashen cewa idan manazarta suka dubi wannan aiki, lalle za su fahimci cewa falsafa na matuƙar bayar da gudummawa wajen haɓakar adabi.

v  A wannan aiki, ana hasashen cewa irin waɗannan hikimomi da Bahaushe ke sakawa cikin adabinsa babu su a wasannin wannan zamanin, Tabbas wannan ya kawo koma-baya ga tarbiyyar yaranmu da kuma samun kyakkyawar mu'amala.

1.5 MUHIMMANCIN BINCIKE

 Wannan binciken na da matuƙar muhimmanci ƙwarai da gaske, kasancewarsa wani yanki daga cikin katafaren fagen adabin Hausawa wanda ke tafiya da zamaninsa na dauri, saboda haka binciken zai amfanar da masu gudanar da nazarce-nazarce kan harkar adabin gargajiya a fannoni daban-daban.

v  Binciken zai ƙara ƙaimi da kuma sha'awar cigaba da aiwatar da ire-irensa a yanzu, domin ƙara samun wasu darrusa da hikimomi da ke cikinsa musamman ga yara da kuma matasa.

v  Binciken zai taimaka wajan sanar da al'umma irin gudunmawar da wasannin gargajiya ke bayarwa a harkar tafiyar da zamantakewar al'umma da kuma irin tasirin da yake da shi a rayuwarsu.

v  Binciken na da muhimmanci sosai a ɓangaren adabin Hausa, domin kuwa an yi ayyuka da dama da suka shafi Harshe wanda shi ne makwafin nahawu a larabci, haka kuma abin yake a fannin Aruli da balaga, amma ita falsafa an ɗan taƙaita mata nazari wajan shigar da ita sosai domin a yi nazarinta.

v  Haka kuma binciken na da muhimmanci sosai ga abinda ya shafi al'ada, domin kuwa wasu hikimomin da Hausawa ke sanyawa a cikin wasannin da tatsuniyoyi ba sa wuce al'adunsu da suka shafi zamantakewarsu ta yau da kullum don haka ake ganin a ɓangaren al'ada ma binciken zai taka muhimmiyar rawa.

v  A ɓangaren harshe ma binciken na da muhimmanci, domin kuwa Hausawa na amfani da salo iri daban-daban wajan sarrafa harsensu yayin aiwatar da labaransu na tatsuniya da kuma wasanni domin su ƙayatar da kuma ƙara musu ƙima. Wannan ma abu ne mai muhimmanci ga masu nazari akan harshe harma da dabarun sarrafa shi.

v  Bugu da ƙari binciken zai taimakawa ɗalibai musamman na sashen nazarin Harshen Hausa a manya da ƙananan makarantu wajen yin nazari musamman kan abinda ya shafi falsafa, da wasanni ko labaran tatsuniyar da kuma shi kansa Bahaushen.

1.6 FARFAJIYAR BINCIKE

 Hausawa na cewa "Daidai ruwa daidai tsaki" to haka abin yake a harkar gudanar da bincke, domin kuwa a duniyar ilimi duk wani aiki da aka tarki yinsa dole a samu iyakarsa kamar yadda aka farar da da shi.

 Farfajiyar wannan binciken ta taƙaita ne ga fannin adabin Hausawa, fannin adabin ma kuma ɓangaren labarun zube da kuma wasannin na gargajiya. Wasanni da tatsuniyoyin gargajiya suna da yawan gaske don haka binciken ya iyakance kansa ga wasu Tatsunioyi da wasanni guda biyar da suke rubutce cikin littafin Tatsuniyoyi da wasanni na Ibrahim yaro yahaya a littattafai na ɗaya zuwa na shida, saboda su ne suke da kamantacceniya wajen aiwatarwa da kuma irin muhimmancin da suke da shi a rayuwa, za a yi nazarinsu wajen fito irin falsafar da Hausawa ke sanyawa cikinsu, saboda haka wannan aikin zai yi ƙoƙarin binciko hikimomin na Hausawa cikin waɗannan Taatsuniyoyin da wasannin guda biyar kacal, tatsuniyoyi uku, wasanni biyu saboda masu nazari a gaba su ɗora daga inda aka tsaya.

1.7 NAƊEWA

 Bisa lura na tsanaki game da bayanan da suka gabata a wannan babin za a ga cewa kamar yadda batun binciken ya nuna an yi fiɗar biri har wustiyarsa, domin kuwa an fayyace rukunin da wannan aikin ya shafa a fagen ilimi wato "adabi" an kuma kawo asalinsa da kuma bayyana yadda shi kansa adabin ya kasu tare da bayyana kowanne daga cikinsu har ma da fayyace ɓangaren da tatsuniyoyin da wasannin gargajiyar suka karkata, wanda suka zo ƙarƙashin gabatarwar babin. Bugu da ƙari babin ya tattare duk wasu bayanai da binciken ya ƙunsa ta ɓangaren yadda za a aiwatar da shi, domin kuwa an zayyano manufofi, da kuma dalili da suka haddasa aiwatar da binciken, daga bisani kuma an nuna ko kuma fito da hasashen da aka hasko game da makomar binciken da ma irin muhimmancin da binciken ke tattare da shi, sannan kuma aka toge haɗe da katange iyakacin inda aikin zai taka birki domin gudun ko ta kwana da kuma kaucewa shiga shirgin da bai shafi binciken ba, a wannan babin ne aka tattare tsaki da tsakuwar duk wani abu muhimmi da yazo a ɓangaren mai gudanar da bincike da kuma binciken kansa.

 

BABI NA BIYU

BITAR AYYUKAN MAGABATA

2.1 SHINFIƊA

 A Harshen Hausa an bayyana kalmar bita da himmatuwa wajan nemo ayyukan magabata a kuma zauna a nazarce su, wanda kuma nazarin ke tattare da kiyaye dokoki da dalilai da aka sarrafa a wani binciken da wani marubucin ke son ya tabbatar, ko ya ƙago, ko ya kare, ko ya ƙara masa tsawo ko ya yi tankaɗe da rairaya (Bunza,2020).

 Wannan babin cikin kowanne bincike shi ake yiwa laƙabi da "Waiwaye" domin kuwa a babin ne mai gudanar da bincke ke bayyana ayyukan da ya bibiya masu alaƙa da bincikensa kama daga littattafai ,Mujallu, Muƙalu, Kundayen bincike da sauransu kamar yadda Bahaushe kan ce "daga na gaba ake ganin zurfin ruwa", haka shi ma wannan binciken zai bibiyi irin rubuce-rubucen da magabata su ka yi masu alaƙa da wannnan binciken a matakan ilimi daban-daban domin fahimtar inda suka ɗauko da kuma ɗorawa daga inda suka tsaya. wannan yasa binciken zai bibiyi ayyukan da aka gabatar game da Hausawa da tunaninsa da kuma falsafarsu, har ila yau binciken zai waiwayi nazarce-nazarcen da aka yi a ɓangaren adabin baka musamman ɓangaren wasannin gargajiya da tatsuniya domin gujewa nanata aiki iri ɗaya cikin fagen nazari ɗaya. Don haka babin na biyu zai tattaro duk wasu bayanai cikin nazarce-nazarcen magabata wanda ya shafi Hausawa da Harshensu, Ƙasarsu da falsafarsu tastuniyoyinsu da kuma wasanninsu na gargajiya a ƙarshe kuma a ƙarƙare babin tare da bayyana duk wani abinda aka tattauna cikinsa a taƙaice.

2.2 HAUSA DA HAUSAWA DA ƘASAR HAUSA

 Ma'anar Hausa a idon Hausawa da manazarta tana da yawa, akan danganta ma’anarta da harshen Hausa ko ƙasar Hausa ko al’umma da suke zaune a ƙasar Hausa da kuma azanci da Hausa ta ƙunsa. Bahaushe shi ne wanda ya gaji Hausa ta wurin mahaifinsa ko mazaunin ƙasar Hausa da ba shi da wani harshe sai Hausa. Ana iya samun Bahaushe ya danganta kansa da wata ƙabila, domin akwai ƙabilu masu yawa a ƙasar Hausa kuma wasu al’umman na kusa da nesa sun yi wa Hausa tasiri. Hausa ta yaɗu a wurare daban-daban saboda addini da zamantakewa da kuma tattalin arziki da siyasa. Hausawa suna da tsarin zamantakewarsu a gida da waje, suna zayyana muhallinsu daidai da sauyin zamani, kamar yadda cuɗanyarsu da Fulani da Barebari da Larabawa da sauransu ta haifar da sauye-sauyen rayuwa da bigiren da suke rayuwa a cikinsa. Kusan maganar Hausa a yau ta wuce a ce Hausa Bakwai da Banza Bakwai, domin Hausa ta mamaye ɗaukacin waɗannan wurare ta tsallaka cikin wasu yankunan da ba ƙasar Hausa ta asali ba. Harshen Hausa yana cikin rukin manyan harsuna a duniya idan ana maganar yawan masu amfani da shi a rayuwa ta kafafe daban-daban.

 Skinner, (1989). ya ce asalin kalmar ta samu ne daga mutanen Sangai (Songhai). Sanyawa sukan kira duk al’ummar da suke gabas da su da sunan HAUSA ko AUSSA, wanda daga nan ne sai Hausawa suka riƙa yi wa kansu laƙabi da suna Hausawa. Sai dai Zarruk da wasu (1982) tambaya suka yi shin Hausawa ƙabila ce? To amma duk wanda ya tsaya ya bayyana ma’anar ƙabila sosai, sai ya ga Hausawa sun shiga ciki, misali, bisa ga bayanin marubuta ƙabila mutane ne masu asali da harshe ɗaya da al’adun gargajiya da kamanni ɗaya. Ita kuma kalmar Hausa a gun Bahaushe tana nufin harshe ne, ta yadda har ma akan ji ya ce ban ji wannan Hausar ba, wato bai ganSe wannan harshen ba ko yaren ba, ko kuma ya ce "Na ji ana wata Hausa‛" wato ya ji ana magana da wani harshe.

 Amma a fahimtar Gusau (2008) ga Hausa, kalma ce mai ma’anoni da dama kuma mabambamta, wadda akan danganta ta da muhalli ko harshe, misali idan mutum ya ce ni a Hausa, wato ni a harshena ko nufina ko ma’anata. Ta fuskar muhalli kuma Kalmar Hausa takan ɗauki ma’anar wuri ko farfajiya ko yanki, wato kamar a ce ƙasar Hausa, maana yankin ƙasar Hausa ko farfajiyar ƙasar Hausa.

A tunanin Magaji,(1986:2).kalmar Hausa daga mutane masu hawa Sa take. Wannan ya faru ne sakamakon Hausawa masu kiwo Shanu ne, wai daga ƙarshe sai ake kiran mutanen da Hau+Sa = Hausa, wato daga hawan Sa.

Kabo, (2016). cewa ya yi an samo asalin kalmar Hausa ne daga kalmar Habasha kafin daga baya ta koma Habsa sannan ta zama Hausa. Goyon baya a kan wannan ra’ayi shi ne maganar Mahammadu (2006), wanda ya ce asalin Hausawa daga Habasha su ke, domin idan aka duba salon bautar Bahaushe ta gargajiya wadda yake bautawa rana, za a ga cewa lallai al’amarin ya yi daidai da bautar rana da al’umar Habasha suke yi, domin suna bautawa ubangijinsu mai suna 'Ra‛ shi ne suke cewa Ra Na (Ra+na) wato ubangijina. Zamu rufe da raayin Bello (2015) da ya bayyana cewa kalmar Hausa ta samo asali ne daga Buzaye, saboda ita ce kalmar da suke kiran mutanen da suke zaune a Arewacin kogin Kwara, wato Hausa. A taqaice dai kalmar Hausa tana nufin harshe kuma tana nufin mutanen da suke magana da harshen Hausa a matsayin harshen uwa, kamar yadda take nufin ƙasa ko muhalli ko farfajiya ko wurin da wannan mutane suke zaune.

 Umar, (1977). kalmar Hausa tana nufin masu yin magana da harshen, ko a ce al’ummar da suke amfani da harshen a matsayin harshen sadarwa, waɗanda ake kiransu da Hausawa. Kenan Hausawa al’umma ce ko rukunin mutane ne da suke gudanar da furuci ko magana da harshen Hausa. Haka kuma, su ne jama’ar da ƙasar Hausa ita ce muhallinsu tun daga iyaye da kakanni, kuma Hausa ce yarensu na asali ta yadda a sakamako haka ne ma ake kira mutanen da suka shaƙu ta fuskar al’ada ko suka taso cikin halaye iri ɗaya da suna Hausawa. Duk da cewa ana samun ɗimbin Hausawa da masu magana da harshen Hausa a ciki da wajen Afirka, musammman a yankin Afirka ta Yamma, amma an fi yin amfani da harshen Hausa a Arewacin Najeriya da Yammacin Jamhuriyar Nijar.

 kalmar Hausa na iya ɗaukar matsayin harshe, wanda shi ne yaren da Hausawa da waɗanda su ke iyaka da su su ke yin amfani da shi wajen sadarwa a zantukansu na yau da kullum. A taƙaice dai Hausa shi ne Hausanci wato yaren da Hausawa suke sadarwa da shi a matsayin harshen da suke fara koya ko tashi da shi tun daga ƙuruciya har zuwa ƙarshen rayuwarsu. Har ila yau, Hausa takan zamo harshe na biyu ko na uku ga wasu mutane waɗanda ba Hausawa ba ne.

 Gusau,(1982) cewa ya yi Hausa ita ce ta tuntuntuni da ake ginin tasirinsa cikin azanci na zantukan Hausawa, wanda yake ɗamfare a cikin harshen nasu. Tuntuntuni na nufin falsafa, wato gudanar da zuzzarfan tunani domin warware matsala ko kuma kyautata magana, wato ƙayata zance. Amma azanci ta fuskar maana shi ake kira da hikima, wato dabarun sarrrafa harshe a cikin magana da ma a rayuwa gaba ɗaya, wanda harshen Hausa yana ɗauke da dabaru na sarrafa harshe (Gusau 1982).

 Abdullahi,(1987).Wata ma’anar da kalmar Hausa ta ƙunsa ita ce wadda ake jingina ta ga yankin ƙasar Hausa. Abin nufi a nan shi ne muhallin da aka tabbatar a nan Hausawa suka zauna tun tali-tali a cikin garuruwa da birane da suka kewaye yankin. “ƙasar Hausa ita ce farfajiyar da Hausawa suka zauna a cikinta, wadda take cike da manyan garuruwa da fitattun birane. ƙasar Hausa a ƙarnukan baya kafin zuwan Turawan mulkin mallaka a dunƙule take wuri ɗaya, duk da cewa kowacce ƙasa tana ƙarƙashin babban sarki mai ‘yancin kansa amma sakamakon mulkin mallaka da ya cinye Hausawa da yaƙi, sai ƙasar Hausa ta rabu zuwa gida biyu, inda aka samu Hausawa da suka tsinci kansu a Nijar ƙarƙashin ikon faranshi, yayin da wasu kuma suka tsinci kansu a Nijeriya ƙarƙashin mulkin Ingilishi.

 Yayin da ake maganar kalmar Hausa ta fuskar nazari, to ana batu ne a kan karantar Hausa a matakin ilimi daban-daban a duniyar yau, wato koyar da Hausa tun daga matakin firamare har zuwa jami’a (Abubakar, 2015). Wannan bayani ya ja hankalin Junaidu (2011) ga bayanin Hausa a matsayin wani ɓangare na nazari da ake karantawa kuma ake karantar da harshe da adabi da al’adar Hausawa a sassa daban-daban na nazarin harsunan Najeriya a jami’o’i da manyan kwalejojin ilimi da jami’o’in Afirka da ƙasar Amurka da ƙasashen Turai da jamioin Asiya.

 Shi kuwa Adamu,(1978). ya fayyace ƙasar Hausa musamman inda yace "akasarin Hausawa suna zaune a farfajiyar da suke rayuwa har sai da sahara ta sabbaba gobirawa suka yi ƙaura zuwa kudu". Hausawa da al'adun Hausawa suna walwalarsu a ƙaƙashin gobir da kabi, da daura da katsina da zamfara da kano da rano da garun gabas ko biram. Haka Muhammad Bello ya bayyana Hausawa da ƙasar su a imfaƙhul-maisur.

Moughtin, (1964). ya ce ƙasar Hausa tana da ingantaccen tsarin kasuwanci da mulki da fasahar ƙere-ƙere, tun kafin zuwan turawa. Masanin ya ce zai yi wuya ya yi wa Hausawa da ƙasarsu kuɗin goro, amma a zariya daga an fito ganuwa sai tudun wada, wato mazaunin baƙi musulmi, kuma yawancin mazauna tudun wada gine-ginensu iri ɗaya ne da na gargajiya.

Smith,(1961 a). ya ce, taswirar ƙasar Hausa tana shimfiɗe a kan digiri na 10½º da 13½º a Arewa da kuma digiri na 4º da 10º. Amfani (2012) ya ƙara da cewa, ƙasar Hausa ta fara daga Azbin har zuwa Arewa-maso-Gabas na tsaunukan ƙasar Jos, ta Yamma kuma ta dangana da Kogin Kaduna, ta Arewa-maso-Yamma kuma ita ce har Kogin Kabi, sannan ta dangana da Arewa-maso-Gabas ta yi Azbin. Masanin ya ci gaba da cewa, ƙasar Hausa tana cikin arewacin Nijeriya da kudancin Jumhuriyar Nijar, kuma Hausawa sun zauni wannan wuri sama da shekara dubu ashirin. Inda Hausa ta laƙume wasu ƙabilu da asali ba Hausa ba ne. Masanin ya ce, Hausa ta gawurta a wuraren ƙarni na sha biyar zuwa na sha bakwai. Amfani (2012) da Adamu (1978) sun ce, Hausa harshe ne a cikin harsunan iyalin Chadi wanda ya tsira daga rukunin Afro-asiatic. Amfani (2012) ya ƙara da cewa, tarihi ya adana bayanin ƙeƙashewar Tafkin Chadi, wanda ya sabbaba yin ƙaura, kuma ƙaurar da mutane suka yi ta dangana da Gulbin Kebbi a Yamma, wasu mutanen da suka yi ƙaurar iyakacin su tsaunukan ƙasar Barno. Masanin ya ce, Hausawa da Bolawa da Ngizim da Manga da Margi da Kotoko su ne manyan ƙabilun da suka yi wanna ƙaura. Kuma sun daɗe a wannan farfajiya, amma an san su sosai ne a wurin ƙarni na sha biyar. Masanin ya ce, Hausawa sun fi sauran ƙabilun yawa, kuma sun fi su watsuwa.

Amfani, (2012). da Adamu (1978) sun yi tarayya wajen fayyace ƙasar Hausa, musamman inda Adamu (1978) ya ƙara da cewa, akasarin Hausawa suna zaune a farfajiyar da suke rayuwa har sai da sahara ta sabbaba Gobirawa suka yi ƙaura zuwa kudu. Hausa da al’adun Hausawa suna walwalarsu a ƙasashen Gobir da Kabi da Daura da Katsina da Zamfara da Kano da Rano da Garun Gabas ko Biram. Muhammadu Bello ya bayyana ƙasar Hausa a Infaƙul-Maisur kamar yadda Yusuf(2013), ya fassara. Mafassarin ya ce, Infaƙul-Maisur jigo ne wajen adana tarihin ƙasar Hausa da jihadin Shehu Ɗanfodiyo.

 Smith (1961 a) ya ce, ƙasar Hausa ta tsinci kanta a tsakanin Daular Barno da ta Songhai, waɗanda suka yi mata kyakkyawan tasiri; musamman inda Songhai ta ƙarfafa siyasa da sadaukantaka da addini da kuma tattalin arziki. A zamanin Muhammadu Rumfa (1465-99) aka kafa wata kasuwa baya ga wadda Usman Kalmana ya assasa, sannan Sarkin Kano ya ci gaba da gina ganuwa, ya gina sabuwar fada tare da samar da tara ta Kano da sauransu.

 Smith,(1961). ya ce, an sami sauyi a zamanin Rumfa sosai, inda Musulunci ya yi ƙarfi, aka ari wasu al’adun Barebari da sauransu. Masanin ya ci gaba da cewa, ƙasar Hausa ta sauya, domin ƙananan garuruwa sun bunƙasa, sarakuna sun ɗaukaka, sarauta ta koma gadon tsatso, darajar Hausa ta gusa daga ƙabila zuwa al’umma.

Usman, (1981). kuma ya ce, mazauna Durɓi-ta-kusheyi na farko wasu mafarauta ne kamar yadda mazauna Kwatarkwashi na farko suka kasance mafarauta. Masanin ya ce, ana kiran waɗannan mafaruta da suka zauni Durɓi-ta-kusheyi da suna Adawa, wato mutane ne masu girman gaske. Masanin ya ƙara da cewa, irin waɗannan mutane su ne suka zauni tarin jigawar da ke kewaye da Bugaje da Muduru. Masanin ya ce, tarihihi ya nuna cewa an ji ƙuriyar zaman irin waɗannan mutane a ƙasar Zazzau da Zamfara da Kano da kuma Barno.

 Haka kuma akwai irin wannan tarihihi da yake nuna wanzuwar irin waɗannan mutane a sassa daban-daban na duniya. Masanin ya ce, Durɓi-ta-kusheyi kufan mutanen farko ne kamar yadda Dala da Gaya a Kano suka kasance kufayin mutane da kuma cibiyoyin noma da haƙar tama da ƙere-ƙere.

Ƙaraye,(2003). ya yi bayanin irin zamantakewar Hausawa da iyalansu wanda ya ƙunshi, maigida, matar gida, ƴaƴa. Maigida ya kan ware sashensa, haka ma mata da ƴaƴansu.

 C.H.N.H,(1971). sun bayyana yanayin cuɗanyar Hausawa da wasu al'ummomi a sanadiyyar yaƙe-yaƙe, da ƙaurace-ƙaurace, har ma da kasuwanci, littafin dai ya karkata ne ɗungurungum ga yadda Hausawa suka yi rayuwa da sauran al'ummomi.

Adamu,(1964). shi kuma cewa ya yi Bahaushe kan tsara hanyoyinsa wanda galibi sukan ɓille zuwa makarantunsu, ko masallatansu da kasuwanninsu ko kuma dandalin hira, wasu hanyoyin ma har jaki kan iya wucewa.

 N.N.P.C, (1982). sun kawo bayanai game da yadda Bahause ya ke aiwatar da al'amuransa na zamantakewar rayuwar kamar abinsa na gargajiya suturunsa da dai sauransu.

HAUSAWA

 Ƙamusun Hausa na jami,ar bayero(2006) an bayyana cewa Bahaushe shi ne haifeffen mai magana da harshen Hausa da rayuwa irin ta Hausawa.

 Abdullahi smith, (1987) ya bada ra'ayin cewa " Bahaushe" mutum ne da ke zaune a ƙasar Hausa a ƙarshen ƙarni na sha biyar 15 a lokaci mai tsawo wanda ba a iya tantancewa ba. Ko da yake karkasuwarsu cikin wani yanki babu shakka ta sauya saboda tashe-tashen da ake yi cikin ƙasar Hausa da kuma daga wajen ƙasar Hausa.

Masanin ya ƙara da cewa, kusan ba ya yiyuwa a ba da sassauƙan bayani a kan wa za a ƙira Bahaushe ? saboda koyaushe mutane daban-daban a wurare da lokuta daban-daban suna amfani da ma'auni daban-daban wajen tantance wane ne Bahaushe, Haka kuma dangane da abinda ya shafi muhallin Hausawa shahararren Malamin nan mai suna Malam Abdullahi Usman Ɗanfodiyo a cikin Algaita journal ya nuna cewa duk wani mazaunin ƙasar Hausa, kamar shi kansa ya cancanci a karɓe shi a matsayin Bahaushe saboda ba zai iya kuɓuce wa harkar al'adunsu ba.

 Haka kuma akwai masana da suka tofa albarkacin bakinsu wajan kawo ra'ayoyi game da wanda ya dace a kira Bahaushe kamar haka:

v  Wasu na ganin cewa Bahaushe wanda yake da al'ada da addini irin na Hausawa.

v  Wasu kuwa sun ce Bahaushe shi ne duk wanda bai da wani harshe sai harshen Hausa. Masu wannan ra'ayin na nufin duk wanda ya taso a ƙasar Hausa, kuma ba shi da wani harshe sai Hausa to shi ne za a kira "Bahaushe" ko da kuwa iyayensa ba Hausawa ba ne.

 Abdullahi.U(1994) cewa ya yi Bahaushe shi ne wanda iyayensa asalinsu Hausawa ne, ya ke yin magana da Harsen Hausa, kuma al'adunsu na Hausawa ne, kuma addimin musulunci ya yi cikakken tasiri a kansa".

 Adamu,(2011) ya siffanta Bahaushe da cewa ba shi da dogon gashi kai irin na mutanen songai, amma ƙirar jikinsa da kamanninsa daidai yake da na al'ummar arniyyawa (Aryan), waɗanda a da suke zaune a tsakanin ƙasashen turai da Asiya kafin su yi hijira su warwatsu a gurare daban-daban na duniya. Ya ƙara da cewa Bahaushe manomi ne mai ƙwazon noma da tara abinci, sannan a fagen yaƙi jarumi ne mai juriya. sa'annan sananne ne a matsayin mai sana'a da sauran ayyukan ƙodago

 Adamu,(1997).ya ƙara da cewa kusan galibi adon Bahaushe namiji ba ya wuce riga da wando,musamman fanjama da takalmi faɗe ko sau-ciki da hula kube ko dankwara ko zita ko haɓar kada, idan kuwa saraki ne ko malami ko dattijo ya kan sa rawani. Adon mata kuwa, zani ne da riga da gyauton yafawa ko gyale da kallabi da ɗan tofi ko mukuru da ƴan kunne da dutsen wuya wato tsakiya ko murjani da warwaro a da can suna ɗan hanci amma yanzu wannan adon ya kau.

 Al’umar Hausawa dai al’umma ce da take zaune a Arewacin Najeriya da yammacin Jamhuriyar Nijar. Al’umma ce mai ɗimbin yawa, waɗanda suka bazu a cikin ƙasashen Afirka da yankunan Larabawa. A al’adance Hausawa mutane ne masu matuƙar hazaƙa, sai dai ta ɓangaren zubi baƙaƙe ne da wankan tarwaɗa da kuma farare jifa-jifa sannan suna da gajerun gashi. Hausawa sun sami kafa daularsu ne tun daga shekaru 1300, sa’ad da suka sami nasara a kan dauloli kamar Mali da Sanwai (Songhai) da Barno da Fulani. A farkon shekara ta 1900 lokacin da Hausawa suke ƙoƙarin kawar da mulkin aringizo na Fulani, sai Turawan mulkin mallaka na Burtaniya suka mamaye Arewacin Najeriya.

 Ta fuskar sana’a kuwa, noma shi ne babbar sana’ar Hausawa, ta yadda har ma suke yi masa kirari da cewa "Na duƙe tsohon ciniki kowa ya zo duniya kai ya tarar". Akwai wasu sanaoin kamar jima da rini da saqa da sassaƙa da farauta da sauran sana’o’i da dama. Ginshiƙin al’adun Hausawa sun haɗa da matuƙar jarumta da ƙwarewa ta fuskar ƙere-ƙere da sanayya ta fuskar kasuwanci fiye da sauran alummar da suke kewaye da su.

Mafi yawan abincin Bahaushe kuwa ana yin sa da gero ko dawa ko maiwa, sai kuma sauran abubuwan haɗawa kamar su gishiri da barkono da daddawa da albasa da kuka da kuɓewa da tumatur da kalkashi da lalo, da tafasa da ɗata, da kuma kayan marmari, su wake da shinkafa da acca da ibiro da kuma kayan rafi da saransu.

 Yawancin Hausawa Musulmai ne kuma suna amfani da Hausa a matsayin harshen sadarwa. A taƙaice dai Hausawa alumma ce da suka ɗauki harshen Hausa a matsayin harshen uwa kuma suke zaune a ƙasar Hausa da aladu irin na Hausawa masu matuƙar muhimmanci da daɗaɗɗen tarihi mai cike da jarumta da kuma gwaninta. Asalin Hausawa abu ne da masana suka sha kai-komo a kansa, sai dai abin takaici har yanzu ba a samu cikakkiyar amsa mai gamsarwa ba, kowa-da-kowa ra’ayinsa yake bayarwa gwargwadon fahimtarsa game da lamarin. Bari mu duba ra’ayoyi kamar haka dangane da asalin Hausawa:

 Mahammadu,(2006).a wata ƙasida ya nuna cewa akwai wata ƙaura da ta auku daga gabas zuwa ƙasar Tukururu, wadda ta yi sanadiyar samuwar Hausawa da harshensu, kuma ƙaurar ta faru ne a tsakanin 900-1000 miladiya. Dalilin ƙaurar kuwa shi ne Larabawa ne suka yaƙi mutanen da suke Arewacin Afirka, sai suka baro wannan waje zuwa ƙasar Hausa.

 Amma Adamu,(2011). ya tafi a kan cewar akwai dangantaka tsakanin al’ummar Hausa da mutanen Cadi, amma sun raba hanya a shekaru 1000 da suka wuce, kuma akwai Tukururu da suke zagaye da tafkin Cadi har zuwa inda ake kira da Sahara, saboda suna Arewa maso gabas wato inda Hausawa suke. Wannan ra’ayi na nuna cewa akwai alaƙa tsakanin harshen Hausa da harsuna iyalan Cadi.

 Usman,(2008) ya yi bayanin taƙaitaccen tarihin Hausawa inda yace " ƙasar Hausa tana shimfiɗe a Arewacin Nijar a can afrika ta yamma, daga gabas ta yi iyaka da ƙasar Barno daga yamma ta yi iyaka da ƙabilun Gwari, ƙasar Hausa tana da girman ƙwarai da gaske, daga kudu ,ƙasar ta fara daga Azbin har zuwa kusurwar Arewa maso gabas ta tsaunukan ƙasar jos. Daga nan sai ta kwasa ta yi yamma har zuwa inda kogin kaduna ya yi babban doro. Daga nan kuma sai ta buga ta yi arewa maso yamma sai da ta dangana da wani ƙaton kwari na gulbin kebbi. Daga wannan wuri sai ta karkata ta nufi Arewa maso gabas har azbin. Wannan zagaye shi ya nuna iyakokin ƙasar Hausa a gabas da yamma kudu da Arewa wadda kuma har zuwa yau su ne iyakokin ƙasar Hausa, wannan ƙasar Hausa ita ce ƙasar da Hausawa suke zaune fiye da shekaru (20,000).

 Akwai wata ƙasida da wani Malami ya buga a jaridar gaskiya tafi kobo ta ranar 22 ga watan 10 a shekara ta 1985 mai suna " Asalin Hausawa da harshensu‛. Inda Malamin ya tafi a kan cewa asalin Hausawa daga Masar suke, kuma sun fito ne daga sashen ƙibɗawa, mutanen Fir'auna; har ma ya ƙara da cewa daga cikin Firaunonin Masar da aka yi akwai baƙaƙe a cikinsu har lokacin sarautar gida na 24. Mutanen Masar su ne suka yi ƙaura zuwa Afirka ta yamma, sun fara zama a bakin tafkin Cadi wanda a wannan lokaci cike yake da ruwa. Farar fata na Hamada sukan kawo musu hari, wannan ta sa suka sake wurin zama kuma suna ɗauke da harshensu na Masaranci wanda daga baya ya sauya ya zamo Hausa.

 Kabo, (2016). ya nuna cewa asalin Hausawa daga Habasha suke sannan kalmar Bahaushe daga Bahabshe take, misali Bahabashe zuwa Bahabshe zuwa Bahaushe. Goyon bayan wannan ra’ayi shi ne maganar Maitama-Sule (2007), har ma ya tafi a kan cewa asalin Hausawa daga Habasha suke, domin an samo tarihin da ya nuna cewa Habasha tsohuwar ƙasar baƙaƙen fata ce kuma sarakunansu baqar fata ne, kuma sun bazu ne sakamakon fari da yaqi. Manazarcin ya cigaba da cewa ‘ya’yan sarki ne (maguzawa) su uku suka yi ƙaura daga ƙasar Masar zuwa ƙasar Hausa, a cikinsu akwai ‘Kano’ wanda ya sari Kano, sai 'Gayya' wanda ya sari Gaya, sannan sai 'Ranau' wanda ya sari Rano.

 Jinju,(1985). ya yi bayanin inda Huasawa suka samo asali a inda ya kawa ra'ayoyin masana daban-daban da suka yi tsokaci game da asalin nasu ,da kuma bibiyar labaru da tarihi masu alaƙa da asalinnsu.

 Khalid,(1999). cewa ya yi Hausawa da Harshensu sun yaɗu ne a duniya ta hanyar shige da fice da suka riƙa yi wurare daban-daban na nahiyar Afirika,da yadda suka riƙa mu'amalantar al'ummomi daban-daban a duniya.

 Amfani,(2011). ya fayyace yanayin Huasawan da da na yanzu ta hanyar kawo ire-iren halayyar Bahaushen da kuma Hausawan yanzu har ma da hasashen yadda Hausawa wani lokacin mai zuwa za su iya tsintar kansu, ta hanyar bayyana dalilai da kuma misalai masu kama hankali.

 Adamu,(2000). ya gabatar da takarda mai taken "Tarbiyyar Bahaushe" mutumin kirki and Hausa prose fiction: towards an analytical framework" a taron samina na tsangayar nazarin yaren turanci, jami'ar Bayero kano.

Ita ma wannan takardar ta yi bayani ne game da irin kyawawan halayya da Bahaushe ke da shi, da kuma irin yadda yake da ƙarfin tarbibiyyar da ahalinsa, da kuma ƙoƙarinsa na ganin ya girmama na samansa da kuma shuwagabanninsu.

 

 

2.3 FALSAFAR BAHAUSHE (TUNTUNTUNI)

 Kalmar falsafa an aro ta ne daga yaren Larabci, duk da yake wannan ba zai sanya a ce Hausawa sun rasa hikima ba, domin sukan ce‚ Magana jari ce, Kuma hikima da azanci tubala ne da ake gina karin magana ta Hausa da su. Falsafa hanyar tunani ce wadda take ƙoƙarin tattaro bayanin kusan dukkan al’amuran da suka shafi duniya da ɗan’adam da inda mutum ya sanya gaba. Haka ya sanya manazarcin ya tsakuro ma’anonin falsafa daga cikin Encyclopedia of Religion and Ethics, (1953, shf. 844) inda aka ce "falsafa ta samo asali daga Girkanci wato ‘Philo’ - ƙauna da 'sophy‛ hikima, watau gwari-gwari ƙaunar hikima ke nan. Maana ƙoƙarin zurfafa tunani tare da nazarin dukkan abin da yake kai komo a sararin Subuhana tare da hikimar bayinsa‛ (Amin, 2004, shf. 209).

 Bergery,(1933) ya bayyana ma'anar falasa da kawo abinda ya gabata wato mayar da saura ta wani abu da ya wuce , ko kuma hasashe na abin da ya gabata ko wanda zai zo" ya kuma ƙara da cewa wannan kalma ta falsafa wata manufa ce da ake auna abu bayan zurfafa bincike ta hanyar amfani da ƙwaƙwalwa yanda kuma hankali zai ɗauka.

Nasir,(1982) ya dubi kalmar falsafa a musulunci don haka ya ce: falsafa na nufin hikima tare da ƙoƙarin nazartar dukkan al'amari a bisa kyakkyawar shimfiɗar tauhidi.

 Popkin da Stroll,(1993). sun ce, falsafa fagen nazari ne da ya ɗara sauran fagagen ilmin wahala, saboda nazari ne da yake tu’ammali da zuzzurfan tunani. Mafalsafan sun ce, wasu sukan danganta falsafa da tunani a zantukansu, duk da yake batu ne da ya shafi ƙaunar hikima. A yau, kusan akan kalli falsafa ta fuskoki masu yawa. Misali idan wani bai aminta da manufar wani ba, yakan ce masa bai gamsu da tsarin da yake bi ya gudanar da kasuwancinsa ba. Idan kuma wani ya aminta da tsarin wata hukuma, yakan ce ya gamsu da manufofin wannan gwamnati. Yin tunani abu ne da ya shafi falsafa, musamman idan al’amura suka bijiro ko matsala ta auku da mutum, akan ba shi shawara ya tsaya tsaf ya yi tunani mai zurfi game da abin da ya fi zama masa alheri. Falsafa iya tantancewa ne da kuma ƙalailaice alamuran rayuwa domin a samo mafita. Domin falsafa tana tattare da manyan tambayoyi masu caza ƙwaƙwalwa.

 Mafalsafan sun ƙara da cewa, mafalsafi yakan zauna ya tsara wasu tambayoyi masu faida ga rayuwa, waɗannan tambayoyi sukan ƙalubalanci matsalolin da alumma take fuskanta kai tsaye ko a kaikaice. A kan tsinkayi alherin abu da sharrinsa yayin da ake yin tunani a kansa. Mafalsafan sun ƙara da cewa, tunanin mafalsafi yakan sabunta na al’umma, al’umma ta da]a fahimtar kanta da tadodinta, duk da yake ba kasafai ake aiwatar da ra’o’in da mafalsafi ya gina ba saboda tsaurinsu. Wannan bai kore fa’idar hangen nesar mafalsafi (game da duniya da mutum da sauransu) ta amfani al’umma ba.

 Abubakar,( 1994).ya kawo ma'anar falsafa da cewa kalma ce da za a iya bata ma'anoni da yawa waɗanda duka idan an haɗa su za su bada cikakkiyar ma'ana guda ɗaya, haka kuma falsafa na iya zama ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa guda ukun:

v  Wani abu a zuciyar mutum , wanda ya dame shi kuma har ya sanya shi baƙin ciki ko farin ciki.

v  Mutum ya riƙa saƙa wani abu a ransa wanda zai aikata ko zai samu a gaba mai kyau ne ko maras kyau.

v  Haka kuma falsafa na iya zama hikimar ɗan Adam wato tunani.

Aminu Alan waƙa, a cikin waƙarsa ta "Uwar iyaye" Aisha, ya nuna cewa tunani wata hidima ce da aka tarawa ƙwaƙwalwa har ta haifar da shi a zuciya:

Abinda ƙauna za ta bayar,

Shi biyayya za ta haifar.

Abinda ƙwaƙwalwa ta bayar,

Shi tunani za ya haifa

Dr A. Nassar,(1982).cewa ya yi mai da hankali da mutum kan yi wajen tunani akansa, wanda ya koru ga hankali ya sawwara kansa ya gano haƙiƙanin mutum da mafarin rayuwa, sai dai kawai a samar da wani nishaɗi a ƙwaƙwalwa. A dunƙule a iya cewa: falsafa ta ƙunshi wasu hikimomi da kowacce al'umma take aiwatarwa, Irin waɗannan hikimomi suna nuna hoton rayuwar al'ummar musamman ta fuskar zamantakewa da addini da tattalin arziƙi da duk wata hanya ta rayuwa. Wamnnan shi ne falsafar al'umma , yin nazari mai zurfi irin waɗannan abubuwan da aka lissafa shi ne falsafa.

Gusau, (2001). ya kawo ma'anar fasafa da cewa: falsafa wani fanni ne da ake nazarin tsarin rayuwar al'umma da yadda suka suke wanzuwa da dalilin faruwarsu, da matsayinsa a zangon nazari mai zurfi. sh- 68.

 Momoh, (2000).ya bayyana falsafa ce tushen duk wata wayewa, ita ce ƙoƙuwar rufin wayewar alumma a kusan komai. Mafalsafin ya ƙara da cewa, falsafa tana haska rayuwar alumma, idan ta yi ƙamfa kuma, akwai duhu kewaye da komai na alumma. Saboda falsafa hikama ce ta ƙoli. Mafalsafin ya ƙara da cewa, tunanin al’ummar da ba ta da falsafa yana ƙuƙumce da sarar bauta, haka kuma zurfin tunanin falsafa yana gaba da na sauran sassan ilmi

 Oxford, Dictionary,(2008) an bayyana ma'anar falsafa da cewa wata manufa ce ko ra'ayi da ke samowa daga ƙwaƙwalwar ɗan Adam. Sannan kuma an cigaba da cewa falsafa hanya ce ta sarrafa abubuwa da za a yi nazarin su ta yin amfani da ƙwaƙwalwa.

 Gusau, (2022). ya bayyana falsafa da cewa hanya ce ta aikata wani abu ta hanyar harshen da mutum yake magana da shi na tunani ko tafakkuri cikin hikima da azanci ta furuci ko rubutu, ya ƙara da cewa falsafa tunani ce ta hanyar samo wani abu ko gano ko kuma hango ko tabbatarwa cikin hikima ta yin hange ko hasashe ko ƙagowa ko sauwarawa ko kimantawa ko kwaikwayo dangane da muhimman manufofi a rayuwar mutum.

 Spirkin, (1983). ya ce, falsafa tana nazarin al’adu da kimiyya da fasaha da siyasa da addini da nagarta da sauransu. Waɗannan rassa na falsafa sun sanya ana danganta ta da hikima, wadda ta ƙunshi kusan kowane fage na rayuwa. Hakan ya sanya Descartes ya fasalta falsafa da bishiya, wadda ilmin zahiranci ya tsirarar da na gaibiyya, kuma sauran sassan ilmi suka zama rassanta; musamman likitanci da fasaha da nagarta. Falsafa hanyar nazarin tunani ce ko ra’ayi ko wani al’amari da yake wanzuwa a sararin duniya. Falsafa fagen nazarin duniya ne da halittun cikinta. Falsafa, tunani ne game da rayuwa da fa’idarta ga mutum, kuma ta karaɗe fagagen ilmin kimiyya da na fasaha. Falsafa tana ankarar da mutum game da muhallinsa. Falsafa tana ci gaba da ɗora mutane a kan turbar da za su ƙara fahimtar kansu, da yadda ya kamata su rayu. Irin namijin ƙoƙari da ake yi a falsafance wajen amsa waɗannan tambayoyi: Ya ya duniya take? Mene ne asalin mutum? Ya ya aka a yana gaba da na sauran sassan ilmi.

 Gusau,(1999) ya rawaito wata ma'ana daga Farfesa Ibrahim Yaro Yahaya a muƙaddimar littafinsa HANYA ƊAYA, cewa "ita falsafa wani ƙasaitaccen tunani ce taƙaitacce da ke koyar da hikima da kujiba-kujibar rayuwa, domin ita falsafa tana bayyana yadda al'amura suke a tsarin rayuwa, da fasalin aukuwar al'amura ta dalilin faruwarsa ga al'umma, wato tana samar da makamar rayuwa da hanyoyin da ake bi wajen gudanar da ita".

 Ogungbemi, (2007). ya ce, falsafa nazari ne da yake fafitikar gano amsoshin wasu manyan tambayoyi da suke da muhimmanci a rayuwa. Falsafatana haska alƙiblar rayuwa, a fahimci alamura a bisa hujjoji. Falsafa takan sanya wa mutum idon zucin alamura a zuciyarsa, kuma takan sanya masa tunani da ƙaimin tantancewa da rarrabewa a tsakanin al’amura. Mafalsafin ya ci gaba da cewa, falsafa ba ta zura wa al’amari ido kurum sai ta yi tambayoyi a kansa; tambayar takan bukaci amsar da ta shafi alherin abu da sharrinsa. Hangen falsafa a kan al’amura ya sa a da yadda mutane suke tunaninsu na yau da kullum, domin falsafa fagen nazari ne, kuma ilmi ne da yake tarke rayuwa ya sake gina ta a kan ƙwararan hujjoji.

 Wasu daga cikin manazarta musamman turawa suna taraddadin cewa ko al'ummar afrika suna da falsafa?, masanan irin su parinder (1961) da Finnegan (1970) da Bodunri (1981) da Hounrtoudji (1983) da Appiah (1992) duk sun haɗe kan fau-fau al'ummar da ba su naƙalci rubutu da karatu sosai ba. Hausawa dai sun ce aka taru aka zama ɗaya ba dan haka wasu masana musamman ƴan Afrika irin su Mbiti (1980)da Gyeke (1995) da Onyeweenyi (1993-1995 duk sun mayar da martani ga waɗannan Turawa cewa lallai Afrikawan suna da falsafa suka ƙara da cewa shirgici-bagiji ne ma a ce wai don kawai al'ummar Afrika ba ta daɗe da fara rubuta harshen ta ba don haka a ce ba ta da falsafa. waɗannan masana sun ce a nazarci adabin baka na al'ummar Afrika idan bana ga falsafa ba. Don haka ne ma gyeka ya ce la shakka da za a nazarci karin magana da guntattakin zantukan hikima da tatsuniyoyi da hikayoyi da tarihi na mutanan Afrika to kuwa da za a iske falsafa maƙale cikinsu, ya ƙara da cewa " ba a raba ɗaya biyu idan aka nazarci waɗannan ɓangarori na adabin baka lallai za a iske falsafar al'ummar Afrika gameda ma'anar da ita. Haka kuma a daɗa naƙaltar ɗan Adam da inda ya sa gaba , kai har ma da makoma bayan fakuwa duk da za a same su a waɗannan ɓangarori na adbin baka na mutanen afrika.

 Dangane da bunƙasar falsafa kuwa, Gusau, (2022) ya bayyana cewa duk lokacin da ake son gane yadda ilimin falsafa ya faro yana da muhimmanci a faro bincike tun daga lokacin da ɗan Adam ya fara tunani da kansa, wato ilimin sanin mutum kansa. Shi kuma sunan falsafa suna ne da ya samo daga yonanawa da girkawa mutane ne da masu son bincike , da gwaje-gwaje da zurfafa tunani, wajen tabbatar da duk abin da suka sa gaba tun farkonsu zuwa yau (Muhammad, 19-15 7).

Bincike ya nuna cewa sun fara tunani shin mene ne a cikin wannan duniya kafin samuwarta da kuma abinda ya samar da ita, yin bincike akan "samuwa", Haƙiƙa sun zurfafa bincike akai don haka suka sanyawa kansu wasu tambayoyi guda uku , wanda suka shafi kowanne mutum ko ya kan tambayi kansa:

= Daga ina ?--...nake.

= Ina zuwa ?--...ina za ni

= Domin me?

 Da waɗannan tambayoyi ne aka ɗora nazarin fannin falsafa tun asali, daga al'ummar yonanawa . Haƙiƙa mutum an samar da shi da wasu ɗabi'u wanda suka bambanta shi da waninsa, kamar dabbobi da tsirrai, da duwatsu. Babban abinda ya bambanta su shi ne :

v  Tunani : Nazari da bincike da neman dalili

v  Hankali : ƙwaƙwalwa

v  Harshe : furucin magana

            Domin haka sai mutum tun farko ya fara tunanin ya aka yi ya sami kansa a wannan fili, kuma me ya samar da shi ? kuma don me, ta yaya ake yin rayuwa?, masana suka haƙiƙance cewa masomin tunani a fannin falsafa. da wannan dalilin wasu masana suke ganin cewa ba yunanawa ko faransawa ne asalin ilimin falsafa ba. Suna ganin cewa wannan tunani ne da kowa daga cikin ɗan Adam zai iya yi, don haka matuƙar akwai tunani a wani ɓangaren to akwai falsafa a wurin. Amma idan ana magana akan wanzuwar ilimin da taskance shi to babu ja su ne sama da kowa

 Saffar, (1982) (sh 1), Faruwar tunani ga mutum daɗaɗɗe ne kamar yadda mutum ya daɗe , kuma ya zama abin da ba a ce ga daga wurin da tunani ya soma, shi tunani baiwace ta Allah ta jikin ko ta yin amfani da tunani shi ya bambanta, shi tunani nishaɗi ne na ƙwaƙwalwa ". ya ƙara da cewa idan kuma muka koma izuwa bunƙasar falsafa to muna iya cewa wannan ilimi ya ƙunshi wasu matakai guda huɗu a farkonsa kamar haka :

Alhawani,(1962) ya yi bayanin yadda falsafa take a tsarin addinin musulunci cikin littafinsa mai suna " Falsafa al-islamyya" an bayyana faruwar tunani ga mutum daɗaɗɗe ne kamar yadda mutum ya daɗe , kuma ya zama abinda ba za a ce ga daga wurin da tunani ya soma ba, shi tunani baiwa ce daga Allah ta jikin kowanne ɗan Adam yin amfani da tunani ne ya bambanta su, shi tunani nishaɗi ne na ƙwaƙwalwa".

A ɓangaren rabe-raben falsafa kuwa Gusau, (2021) ya kasa falsafa zuwa gida uku muhimmai, wanda suka haɗa da falsafar Harshe, falsafar kwatance, da kuma falsafar Rayuwa.

Guya,(2001).ya fito da tunanin Bahaushe a littafin gasa ta farko (1993) ya fito da tunanin Bahaushe dangane da kyawawan ɗabi'u da halaye waɗanda Hausawa ke kira ayi koyi da su, kamar jarumta,haƙuri da tunani da gaskiya da kara da kunya.

Edger,(2010). wanda ya yi managarcin sharhi akan tunani , inda yace , kalmar tunani na da alaƙa ta ƙut-da-ƙut da ƙoƙarin yin imani ko yarda musamman akan abin da ba a da tabbaci akan sa . Har ila yau ya ƙara da cewa tunani nasa hankalta akan wani abu musamman wanda ya ke kusa da mutum. Edger bai tsaya a nan ba sai da ya kawo alaƙar da ke tsakanin ilimi da tunani da fagen ilimin mutuntaka. Haka zalika masanin ya bayyana cewa masana ilimin ɗabi'a irin su Skinner (1971 sun bayyana cewa mutane na tunani ne da dukkannin jikinsu ba da kwakwalwa kaɗai bax wato tunani ɗabi'a ce a maganance ba a aiwace. Bugaje,(2014) yana da ra'ayin cewa tunani hanya ce ta warware matsala a wajen lissafi ko ƙirƙira ko a wasanni musamman irin na dara.

Bunza,(2015). ya ce kowanne al'amari falsafa na kallon mafari ko sanadinsa da dalilin samuwarsa tare da hujjoji da za su tabbatar da hasashen. A fagen nazari falsafa kimiyyar kanta ce, Hangen falsafar Bahaushe bai saɓa da ta Bature da Balarabe da Bagirke da Balatine ba, tattare da sanin cewa ƙamusoshin Hausa ba su kula da kalmar ba a hangensu, za mu iya cewa:

A wajen Bahaushe falsafa ita ce ƙololuwar basirar ƙyallaro dalilan faruwar abubuwa da hasashen fassarorinsu na kusa da nesa, bisa ga dalilan hankalin tuwo domin su yi cancaras da al'adun mutanensu. Falsafar kimiyyar hasashe ce, mai tafiya da al'adun mai hasashe da al'adar rayuwa da aka saba da ita. Falsafa kuratun mutanen jiya ne, da ya gagari mutanen yau saukewa, ya zama maganaɗisun rayuwar mutanen gobe. Ya ƙara da cewa: Idan za a yi hasashen falsafar Bahaushe, dole a dubi adabinsa na baka, da nau'o'in bautarsa, da warkarwarsa, da tattalin arziƙinsa,bda tsarin siyasar zamantakewarsa. Sanin cewa rayuwarsa ta gargajiya gaba ɗaya akan falsafarsa yake tafiyar da su, na ga ya dace in yi garkuwa da falsafa ɗaya in tunkari muradina, gundun ka da a yi kwasan karan mahaukaciya.

Gusau,(2022). ya yi bayani dalla-dalla game da asali da kuma shi kansa ilimin falsafar,har ila yau kuma an yi ƙoƙari matuƙa wajen bayyana tarihin masu ruwa da tsaki a ɓangaren binciken falsafa tare da zayyano manyan mafalsafan duniya kama daga ƙasashen ƙetare da ma duk wani sauran fannonin rayuwar ɗan Adam.

Marubucin bai tsaya iya nan ba, domin kuwa ya fito da yanayin falsafa a zamantakewar Hausawa ta farko a ƙasar Hausa, da kuma ayyana tsarin rubutun boko a matsayin tsari na gabatar da wasu ayyukan falsafa a rayuwar Hausawa. Tabbas ko ba a ce komai ba wannan muhimmin littafi na da makusanciyar alaƙa da wannan binciken, domin kuwa ya taɓo fannin falsafa ne tun daga samuwarta har yadda Hausawa suka riƙa ta'ammali da ita cikin lamuransu, duk da kuwa wasu na ganin cewa Hausawa dama suna da falsafarsu tuntuni, sai dai du da haka ba zai hana gudanar da wannan binciken ba domin kuwa ba a ware wani ɓangare na daban an fito da falsafar Bahaushe cikinta ba, kamar yadda wannan binciken zai fito da falsafar Bahaushe cikin wasannin gargajiya.

Yakasai,(1988 ). ya yi nazari a kan rayuwa da falsafa cikin al'ummar sinawa, inda ya fito da keɓaɓɓun kalmomin fannu da kuma maganganun azanci da hikima, waɗanda suka yi tasiri a rayuwar falsafa cikin al'ummar sinawa, sa'annan ya zaɓo tare da fassara irin kalmomi da wasu manyan masana suka yi bayani a kansu.

Marubucin ya yi ƙoƙari matuƙar gaske domin kuwa aikin zai bunƙasa ilimi dangane da falsafar al'ummar sinawa da tarihi da kuma aikin fassara da fahimtar falsafar sinawan game da rayuwarsu.

Muhammad,(1977).ya yi amfani da wani baitin waƙa na siyasar jam'iyyar NEFU mai suna ƴar fulani ya kawo misalin zalunci da ake yi ta hanyar ƙarya da makirci da yake cewa:

 "waƙa na fulani yimre,

mun ji ƙara sun ce masa yombe

ƙarfi sun ka ƙira shi da samba,

kai kasabubu abokin camba,

ƴar ƙarya da yawan makirci.

Ya yi amfani da wannan baiti ne domin nuna tunanin Bahaushe akan ƙarya da zalunci da kuma nuna cewa dukkan waɗannan abubuwa ne da bai kamata ana yinsu ba.

Maryam, (1998). ta bayyana mawaƙi a matsayin mafalsafi, a inda ta kawo matsayin mawaƙi a idon jama'a da kuma matsayinsa a addini da kuma matsayin mafalsafi da yadda falsafa take a ƙasar Hausa. Har wa yau ta kawo falsafa na marubuta waƙoƙi da yawa kamar "falsafar waƙar malam Muhammadu na Birnin gwari" ta kawo wasu baitoci masu nuni da halin duniya in da malamin ke cewa:

Komi na duniya mai ƙarewa,

Ni ban ga wanda zai shi ɗore ba,

 Na dubi duniyar har babinta,

 Ni ban ga tattali ya ibada ba,

Da ku da duniya kwa ƙare duk,

Da dukiyarku har da sarautarku.

Haƙiƙa wannan zancen na Muhammadu Birnin gwari ya yi gaskiya domin ya yi wannan waƙa ne da daɗewa, amma ga shi yanzu kamar yau ne ya yi ta, saboda a wannan lokacin mafi yawan jama'ar duniya suka sa a gaba sun mance da lahira. Haka ma idan muka dubi waƙar sa'adu zungur ta AREWA JAMHURIYA KO MULUKIYYA ya nuna falsafa sosai a waƙar inda yake cewa.

In kun dage kun shantako,

Bisa al'adu na mazan jiya,

Za ku rera faɗar da-na-sani,

Da na bi jawabin gaskiya.

 Saboda haka shima wannan bincike na da alaƙa da wannan aikin, domin kuwa duk suna magana ne akan falsafa.

Shi kuwa sankalawa,(1994).ya nazarci rayuwar Sani Sabulu da falsafar waƙoƙinsa a inda ya fito da yanaye-yanayen waƙoƙinsa ta fuskar jigo da zubi da tsari da salon sarrafa harshe a waƙoƙin.

Bello,(1993). ya yi bajakolin tunanin Bahaushe a harshen Hausa, inda ya zurfafa tunani wajen zaƙulo hikimomin Bahaushe game da Harshensa da kuma rayuwarsa a da da yanzu.

Adamu,(1994). ya gudanar da nazari akan tunanin Bahaushe game da duniya inda ya yi bayanin yadda Bahaushe ke kallon duniya da kuma hikimominsa game da zamantakewar rayuwar duniya, da ma yadda ya riƙa kwatanta duniya da sanyata cikin adabinsa ta ko ina da suka haɗa da zantukansa na hikima, karurrukan maganganunsa, azanci, da dai duk wani abu da ya shafi adabinsa da kuma zamantakewarsa.

Amin,(2004).ya binciko falsafar Bahaushe game da rayuwar ɗan Adam in da ya fito da irin tunane-tunanen Malam Bahaushe da hikimarsa har ma da dabarun rayuwarsa ta yau da kullum, ba ma iya tasa rayuwar ba har ma da yadda ya riƙa sanya daburu cikun zamantakewarsa da bakin al'ummomi da suka yi tarayya da su. Don haka shima wannan binciken na da alaƙa da wannan domin duka dai falsafar Bahaushen za su gano sai dai kuma kowa da inda ya karkata binciken nasa, wato shi ya yi game da rayuwar ɗan Adam wannan kuma akan wasannin gargajiya. Yayin da Amin, (2010) shi kuma ya fito da gudunmawar Mamman shata katsina wajen bunƙasar falsafar Bahaushe, ya bayyana irin ƙoƙarinsa wajan sanya hikimomin Bahaushe cikin waƙoƙinsa masu alaƙa da fannonin rayuwa iri daban-daban harma da harshensa. Shi kuwa Gobir 2012), ya fito da falsafar Bahaushe ne game da cututtukan iskoki ya yinda ya fayyace yadda Bahaushe ke kallon iskoki da kuma tunaninsa game da cututtukan da ɗan Adam ke samu a sanadiyyarsu da kuma yadda suke ta'ammali da iskoki cikin harkokinsu na yau da kullum.

Shi kuwa Musa,(2013). ya fito da falsafar Bahaushe a kan waƙar tsuntsaye ta malam Amadu ɗan matawallen Haɗeja, marubucin ya kawo irin hikimomin da ke tsuntsaye ke da shi inda mawaƙin ya yi bajakolinsu cikin waƙar tasa, haka kuma ya bayyana falsafofin ne ta hanyar zaƙulo nau' o'in falsafa da aka gina a waƙar dalla-dalla tare da tabbatar da wuraren da suka zo cikin waƙar ta hanyar kyakkyawan bayani, har ma da yanayin falsafar. Don haka nake ganin wannan binciken ma na da makusanciyar alaƙa da wannan, domin kuwa shi ma dai ɗungurungum falsafar ya binciko ta tsuntsaye, sai dai shi ya dubi waƙa ne, wannan kuma ya shafi wasanni ne. don haka ba zai hana a cigaba da wannan binciken ba.

Bunza,(2017). ya yi na zari game da falsafar al'ada a makamin democraɗiyya, ya yi namijin ƙoƙari ƙwarai da gaske wajen fito da yadda Bahaushe ya tsara hikimominsa a cikin al'adar shugabacinsa, wadda ƙarara suka bambanta da sabon tsarin da muke ciki. Shi kuwa Sani (2012 ) ya nazarci yadda ƙabilu suke a tunanin Bahaushe, aikin ya fito da irin ƙabilun da Hausawa suka riƙa tarayya da su da kuma irin fitattun labarai game da waɗannan ƙabilu da kuma ɗora su bisa tunanin Bahaushe na " da wayo ake faɗawa wawa gaskiya " tare da amfani da faɗakarwa da nishaɗantarwa".

Abubakar (2018), ya yi nazari game da bigire a tunanin Bahaushe, aikin na abubakar ya fitoda duk wani abu da ya danganci bigre (muhalli) na Bahaushe, da suka hada da gida, kasuwa, da dai sauran wurare daban-daban da suka shafi bigeren da kuma irin muhimmancinsa a wurinsu.

Dumfawa,(1988 ). ya fito da tnanin Bahaushe ne cikin littafin ruwan bagaja inda ya hasko irin tunanin Bahaushe na rayuwar yau da kullum wadda ta danganci ɗan Adam, ya yi bayanin tunin Bahaushe da ya danganci neman abu ga masu shi, da matsayin sarki ga Bahaushe, da imani da aljanu, da muhimmancin naciya ga mai nema, har ma da muhallin tsofaffi a cikin al'umma waɗannan su ne abinda marubucin ya karkata wajen fito da ma'anar da suke ɗauka a tunanin Bahaushe game da rayuwa.

Yusuf, (1988 ).ya gudanar da bincikensa kan falsafar malanta cikin littafin ruwan bagaja, shi ma wannan aikin ya taɓo falsafa ne ta Bahaushe game da al'amarin malanta (koyarwa) a inda aka fito da hikimomin da ke cikin koyarwar malam Bahaushe da kuma irn dabarun da yake da shi a fannin har ma da binciko irin matsalolin da ake samu a tsakanin malamai na hassada, da kushen juna da son ɗaukaka wanda wasu lokutan kan haifar da fito-na-fito .

Haƙiƙa wannan binciken ba zai hana cigaba da gudanar da wannan bincikenba,domin kuwa, shi ya karkata ne ga abinda ya shafi falsafar malanta.

Alala, (2021).ya nazari game da waƙoƙin Haruna Uji a inda ya fito da tunanin Bahaushe cikinsu, wato irin hikimomin malam Bahaushe da ya riƙa sanyo wa cikin waƙoƙin, Shi kuwa Ibrahim, (2021) ya yi nazarin falsafane cikin waƙoƙin sadi sidi sharifai, aikin ya yi matuƙar ƙoƙari, domin kuwa ya fito da irin falsafofi ko hikimomin mawaƙin da ya ke sawa cikin waƙoƙinsa.

Duka waɗannan nazarce-nazarce da aka bibiya game da falsafa, daga ayyukan magabata ba za su dagatar da wannan aikin ba, domin kuwa dukansu akalarsu ta karkata zuawa ɓangarori daban-daban da ake binciken falsafar a kansu, kamar waƙoƙi, bigire, malanta da saurnsu. Ko ba komai dai aikin falsafa ma ba baƙo ba ne a wurin masu nazarin, domin kuwa mun ga irin yadda masana suka gudanar da aikace-aikace na falsafa a fannoni daban-daban.

2.4 WASANNI

Kalmar wasanni jam'i ne na wasa a Harshen Hausa, wadda a yaren Ingilishi aka fi saninsa da (play/plays). Wasa wani motsi ne da gaɓoɓin jiki tare da magana ko ishara don washewa da nuna nishaɗi ko dan a kau da baƙin ciki ko a nuna gwanintaka, ko bajinta ko ƙwazo ko kuma akan yi wasa domin a kwaikwayi wani abu na musamman.

 Ɗangambo, (1984). an bayyana kalmar wasa da duk wani abu da ya shafi raha ko nishaɗi da akan aiwatar da su ta mabambanta hanyoyi da kuma sigogi daban-daban.

Yahaya, (1981) ya ce Wasa abu ne da yake nufin ba'a ko raha, ko wani abu da ake yinsa amma ba dagaske ba. shi kuwa Umar (2000) ya bayyana da Wasa hanya ce ta bayyana halaye ko ɗabi'u da buƙatu ta hanyarmotsa jiki da fasahar baka da hannu da hannu wadda ke ɗauke da hoton rayuwar al'umma.

 Ƙamusun Hausa CNHN, (2006), aka bayyana ma'anar wasa da abu wani abu da aka yi cikin raha da nishaɗi.

 Tukur, (1994/1999).ya fassara wasa da abu ne da yake nufin ba'a ko raha ko wani abin da aka yi shi amma ba da gaske ba". yayin da Gusau (2013) shi kuma ya kawo ma'anar wasannin yara da wasu hanyoyi ne da dabaru waɗanda yara maza da mata suke amfani da su na tsinka jininsu da motsa jki tare da cinye lokaci da samun walwala da naƙaltar dabarun zaman rayuwa cikin nishaɗi.

 Idris, (2019).ya kawo muhimmancin wasa da dama da suka haɗa da ƙulla dangantaka da zumunta tsakanin yara ko samari saboda ta sanadiyyar wasa yara kan taso tamkar ƴan Uwa., da kuma yadda yake da tasiri wajan hana yawace-yawacen yara ko kuma ƙar musu ƙaimi cikin duk wasu ayyuka da za su tunkare shi.

 Duba da yadda masana suka bada ma'anonin wasa za mu iya fahimtar cewa, "Wasa wani motsi ne da gaɓoɓin jiki tare da magana ko ishara don washewa da nuna nishaɗi ko dan a kau da baƙin ciki ko a nuna gwanintaka, ko bajinta ko ƙwazo ko kuma akan yi wasa domin a kwaikwayi wani abu na musamman.

 Yahaya, (1972), ya kawo ire-iren wasannin gargajiya da dama da kuma yadda ake aiwatar dasu cikin tsari da kuma abin burgewa.shi kuwa Umar, (1977), ya kawo ire-iren wasannin tashe ne da dama wadda ake da su a ƙasar hausa,da suka haɗa da tashen mai magani, mairama da Daudu, da dai sauran wasannin tashe da kan aiwatar a ƙasar Hausa musamman a lokutan azumi. Shi ma Lawan, (1977) ya yi bayanin wasannin yara na gargjiya da yadda ake yinsu , ya kuma bayyana amfaninin wasannin na yara a rayuwasu, sa'annan kuma ya yi bayanai sosai akan dandali.

 Wannan binciken na Umar ba zai hana gudanar da wannan binciken ba, domin kuwa shi ya kalli wasannin tashe ne kurum wannan kuma zai yi nazari ne game da falsafar da ke cikin wasannin gargajiya ta Bahaushe.

 Dembo, (2007), ya yi bayanin wasu wasannin gargajiya na yara sosai da suka haɗa da wasan langa, wasan ƴar kurciya, wasan kangal-kangal da sauransu.Wannan marubucin ya yi matuƙar ƙoƙari da burgewa, domin kuwa ya gudanar da aikin ne a sigar wasan kwaikwayo, amma cikin hikima ya riƙa sanyo wasannin yara daban-daban, tare da bayaninsu a taƙaice ta yadda wanda bai san wasannin ba kai tsaye ba lallai ya iya fahimtar yadda ake gudanar da shi ba akan bayaninsa. Don haka wannan binciken ya ƙudiri aniyar fito da duk wata falsafa ta Bahaushe a cikin wasanninsu tare da kuma faɗaɗa bayanai sosai domin fito da yadda tunaninsa ya cika wasannin nasa.

Daura, (1982). ya yi bayani game da wasu daga cikin wasannin gargajiya,sai dai a iya cewa su wasannin da ya yi magana akan su sun ta'allaƙa ne da wasannin manya kurum,irin su kokuwa,dambe, bori,ƴan hoto da sauransu. Marubucin ya yi ƙoƙari sosai sai dai bai zo da wani bayani game da wasannin gargajiya ba musamman yara da kuma matasa,don haka nke ganin ya dace a fito da hikimarsu a sarari domin ƙarin haske.

Sani da Gobir, (2020) sun fasalta wasanin ƙasar Hausa bakin gwargwado ta fuskar jinsi da shekaru da kuma yanayin aiwatarwa har ma da lokutan aiwatar da wasannin, hakan kuwa tabbas ya nuna jajircewa da kuma nuna bambanci da sauran takwarorin littattafan wasannin da suka shafi ƙasar Hausa, domin kuwa littafin na kammale da nau'ikan wasannin gargajiya da ma sauran wasanni har guda ɗari biyu da goma sha huɗu 214 waje guda.

Muhammadd, (1984) ya kawo fa'idoji da illoli da kuma matsayin ma'abota sana'o'i a idon jama'a, ƙarƙashin haka ya kawo wasannin masu yawa da yadda ake gudanar dasu awasu sana'o'in gargajiyar Bahaushe . A cikin wasannin ya ɗan taɓo wasu daga cikin wasannin yara . wannan aikin ma na da alaƙa da wannan binciken domin kuwa ya taɓo abinda ya shafi wasanni.

Ado,R. (1987) sun fito da irin alaƙar da ke tsakanin wasannin kwaikwayo da rayuwar al'ummar Hausawa musamman na yanzu, d kuma wasannn kwaikwayon da ake aiwatarwab yanzu, inda ya fito da irin halaye da kuma ɗabi'u da suka mamaye rayuwar Hausawa wadda kuma akan tsinto su ne daga daga cikin nau'ikan wasannin kwaikwayon da ake aiwatarwa.Saboda haka nake ganin ko kaɗan wannan kundi ba zai hana gudanar da wannan aiki ba.

Bunza da koko, (1988) sun bayyana yadda ake aiwatar da wasannin yara a ƙasar gwandu wanda suka ƙunshi wasannn maza da mata na gargajiya. wannan bincikenma ba zai hana aiwatar da wannan binciken ba. su kuwa Safiyanu,Hassan da Hassana(2017) sun gudanar da bincikensu game da dusashewar wasannin gargajiya a ƙasar yabo yayin da suka bayyana ire-iren wasannin da ake aiwatarwa a ƙasar yabo da kuma bayyana tsirinsusa annan suka bayyana yadda wasannin suka ɓace/dusashe a ƙasar yabo , har ma da dalilan da suka jawo dusashewarsu. yayin da Kaduna, (1988) ya binciko irin tasirin da zamani ya yi akan wasannin yara ƙasar Hausa da kuma hanyoyin da za a bi wajan farfaɗo da su. Aikin nasa na da dangantaka kwarai da gaske da wannan binciken, dalil kuwa shi ne dukkannisu biyu za su yi tsokaci ne game da wasanni, sai dai kuma aikin na Kaduna ba zai tsayar da wannan binciken ba saboda shi hikimomin cikinsu zai dubo.

Sakkwato, (1982) ya binciko ire-iren wasannin yara masu ɗauke da wake-waƙe sa'annan kuma ya karkata akalar bincinken nasa ne ga garin sakkwato. ya yin da aikin Mai rukubta,(1994) ta fayyace tawai a matsayin dabarun reno a ƙasar Hausa, a wannan binciken ta fito da waƙoƙi kala-kala waɗanda mata musamman ƴanmata ke yi wa yara lokacin raino.Irin waɗannan waƙoƙi na ɗauke da zambo, habaici, da ba'a da kuma kurarawa da gwarzantawa.

 Dangantakar wannan binciken da wannan shi ne kasancewar wasannin Hausa da dama suna ɗauke da waƙoƙi sannan yayin rainon kansu waƙa ake musu.

Abdu,yahaya bichi, (2002) ya yi bayanin tsofaffin Wasannin Hausawa da tsare-tsarensu da kuma yanayinsu. Yayin da Shehu (2002) shi kuma yayi nazari game da tashe dabire-irensa a garin kano, bayannan ya zayyano wasannin tashen da suka ƙunshi na mata da na maza.

Hadiza,S. (2009) ta yi nazari game da haƙuri a tunanin Bahaushe ainda ta yi duba cikin wasannin jatau na kyallu da wasan tabarmar kunya da wasan matar mutum kabarinsa da uwar gulma, a inda ita kuwa Garba.R (2009) ya yi nazari akan mace cikin rubutattun wasannin kwaikwayo, misali cikin Uwar gulma da kulɓa na ɓarna.

Badamasi, (2013) ya fito da yadda wasannin Hausawa suke wajan bunƙasa lafiyar al'umma , ya kawo wasu daga cikin wasannin yara tare da nuna yadda suke gudanarwa cikin ƙiriniya da doke-doke da sauransu. aikin nasa na da alaƙa matuƙa da wannan binciken amma duk da haka ba zai hana gudanar da shi ba.

Autatuwa ,(2021) ya yi bincike game da taɓarɓarewar wasannin gaɗa a garin haɗeja, a inda manazarcin ya fito da tasirinsu da kuma dalilan ɓacewarsu har ma da ci bayan da aka samu game da ɓacewar tasu.

Shi kuwa Malumfashi, (1984) ya yi bayanin akan bori addini ne ko kuma wasan kwaikwayo, binciken ya ƙunshi dukkanin bayanai game da yadda Hausawa ke kallon tare da gudanar da al'adar bori.ya kuma fayyace matsayinsa a rayuwar Hausawa. aikin ya na da alaƙa da na Malumfashi, domin kuwa shi ya fayyace Bori a matsayin wasan kwaikwayon kansa.

2.3 TATSUNIYA

 kalmar tatsuniyar nan tana ɗauke da sunaye mabambanta, ta la'akari da muhalli ko yankin ƙasar Hausa. Kamar yadda Bergery (1934/51:37) da kuma Gusau, (2013:1) suka bayyana, Tatsuniya ana kiranta da sunan “Gatana” a yankunan Sakkwato (da ya haɗa Kebbi da Zamfara a yau) da Katsina wanda suka yi hasashen samuwarta daga tsarin kalmomin da ake fara buɗe tatsuniyar dasu na “gata nan gata nan ku”. Sa'annan suka ci gaba da bayyana yadda ake kiranta a sauran yankunan Kano da Zariya da suke kiranta da suna tatsuniya

 masana da manazarta da dama irin su Bergery (1934/15: 1005) sun bayyana tatsuniya ko gatana a matsayin “Labari ko Almara”.

 Shi ko Skinner (1965:62) ya fassara kalmar “Fable” da “tatsuniya ko almara ko labari”. Shi ma Newman (1997:93/102) ya bayyana ta da kalmomi masu dangantaka da tatsuniya wato fable a matsayin hikaya da kuma folktale a matsayin tatsuniya wacce ta shafi tauraro Gizo”.

 Idan muka yi nazarin ma'anonin da suka gabata, dukkaninsu suna magana kan tatsuniya inda suka siffanta ta da labarun da suka dangance ta wato almara da hikaya da kuma ita kanta tatsuniya. Sai dai kuma dukkanin ma'anonin an bayar da su a dunƙule, ba tare da bayyana tatsuniyar ta yadda wanda bai santa ba zai iya gane ta.

 Ta fuskar ma'anar tatsuniya a sarari kuwa, masana da dama sun samu tofa albarkacin bakinsu kamar: Umar (1980:11) ya bayyana tatsuniya a matsayin:

 “ƙagaggen labari ne wanda magabata kan shirya don bayar da tarbiyya kan tafarki na gargajiya”.

 Shi kuwa Zarruk da wasu (1987:7) suna kallonta a matsayin “Labarin da aka shirya domin gizo da waninsa, mai tattare da hikima da fasaha”. Sai Yahya da wasu (1992:7) Sun kuma bayyana ma'anar ta tatsuniya a matsayin: “Tsararren labari na hikima mai an tsawo da nuna ƙwarewa wanda ya ƙunshi shiryawa kan nuni zuiwa ga kyawawan halaye da koyar da ilimin zaman duniya, tare da saka nishaɗi da kuma cinye lokaci”.

Su ma Junaidu da ƴar'aduwa (2007:75) sun daɗa zancen ta bayyana cewa “ƙagaggen labari ne na ƙarya marar ƙamshin gaskiya a cikinsa, wanda Hausawa kan shirya don sanya annashuwa da raha”. Ɗangambo (2008:30) shi ma ya bayar da tasa gudummuwa da cewa: “Tatsuniyoyi da labarai su ne makarantar farko ta ƴaƴan Hausawa, a zamanin da, lokacin da ba a samu ilimin karatu da rubutu ba, inda ake koyar da su tarbiyya da hani da horo da dabarun fafutukar tafiyar da rayuwa. Sai Koko, (2009:2) ita ma ta ce: “Tatsuniya labari ne da mutane ke ƙirƙirawa cikin azanci don tarbiyantar da ƴaƴansu da kuma cimma wasu buƙatoci dangane da alumma.

Gusau, (2013:5) ya bayar da nasa agaji wajen samar da ma'anar tatsuniya da cewa: Tatsuniya wani tsararren labari ne shiryayye wanda ake shiryawa cikin hikima da nuna ƙwarewa da naƙaltar harshe domin koyar dabarun zaman duniya daban-daban.

 Rabi'u (2018:65) a nasa kundi ya ƙara da cewa : Aiki ne da mai ba da labari ke tsarawa domin ya saita tunanin yara masu sauraro ta amfani da taurarinsa a lokacin da yake warware zaren tatsuniyarsa.

 Idan muka yi la'akari da ra'ayoyin masana da suka gabata dangane da ma'anar tatsuniya, za mu ga cewa dukkaninsu sun tafi kan abubuwan da yawa da su ne suka haɗu suka bayar da tatsuniya kamar “ƙagaggen labari ne da ake tsarawa kenan bayan an ƙaga, sai kuma an tsara don ya dace da manufar da ake so a isar, da kuma tunanin masu sauraro. Sa'annan kuma dole ne ya kasance yana “koyar da gyaran hali ta fuskar cusa tarbiyya da hani daga abubuwa marar kyau.” Sa'annan ya samar da nishaɗi. Idan har labarin ya kasance ya tsallake waɗannan dokoki to ya tashi daga zama tatsuniya, sai dai labari ko hikaya ko almara da sauransu

 Labarun tatsuniya an tsara su ne ta yadda suka dace da aladun Hausawa da tunanin yaro. Saannan suna da matuƙar muhimmanci, domin ana koyar da halayya mai kyau da tarbiya a cikinsu. Labaran suna da daɗin sauraro, kuma ba su saurin gundurar da waɗanda ake baiwa labarin, musamman waɗanda ake tsara labarin domin su, wato ƙananan yara.

 Kasancewar salon ba da labari da ake amfani da shi tare da riƙa jefa gajerun baituka na waƙa akai-akai wadda take jawo hankalin mai sauraro. Tatsuniya tana ɗauke da wasu muhimman abubuwa da suke ɗauke dabarun koyar da iya zaman duniya, da taskace al'adun al'umma da koyar da tarbiyya da saka nishaɗi. Duk da cewa wasu rukuni namalaman addinin musulunci suna kallonta a matsayin hululu, saboda kasancewarta ƙirƙira, amma tana da tasiri a zukatan masu saurare da saurin isar da saƙo da daidaita tunanin ƙananan yara masu tasowa.

 Dangane da tatsuniya a idon ƴan kallo, Su kuwa masu bayar da tatsuniya suna ganin tatsuniya a matsayin labari mai armashi wanda yake tarbiyantar da ƙananan yara da cusa musu wani zance tunani cikin sauƙi, su fahimta ba tare da ɓata lokaci ba.

 Kasancewar yaran yanzu ba su sauraren tatsuniya, amma an samu zantawa da wasu magidanta masu shekaru 50-55, inda suka bayyana cewa tatsuniya abu ce mai matukar amfani ga rayuwar Bahaushe wacce take ɗauke tsantsar al'adunmu na gargajiya da suke koyar da ɗa'a da zamantakewar rayuwa. Sun ƙara bayyana cewa rashin tatsuniya ya taimaka wajen samar da baƙin al'adu a cikin ƴaƴan Hausawa. (Hira da Malam Sama'ila ).

 A ƙarƙashin wannan rukuni na labarun Hausa, wanda aka fi sani da tatsuniya, masana sun karkasa shi ta la'akari da kayan cikin tatsuniya kamar Ruth (1970) da Skinner (1969) da Yahaya (1992) da Koko (2009). Sai dai za a bi fasalin Koko (2009) domin samun gabatar da su a bisa faifan nazari tare da yin sharhin ra'ayoyin masana kan yadda suka fahimci kashe-kashen tatsuniyar.

Tatsuniya sha kundum ce, domin ta ƙunshi labaru da suka haɗa da na mutane (na zamanin da ake ciki da tarihin abin da ya gabata) da labarun dabbobi (na nau'o'in dabbobin da ake samu a cikin muhallin Bahaushe na gida da na daji) da labarin aljannu (domin kuwa imanin Bahaushe bai kammala sai an samar ma aljannu matsugunni) da labarin gamin-gambiza (labari ne ya haɗa taurari na jinsi daban-daban) da Labarin tsuntsaye da kwari da tsiraruwa da labarin tarihi (Ahmad da malumfashi, 2019).

 Dangane da asalin samuwar tatsuniya kuwa masana irin su Gusau (2017), Yahaya (1987), Ɗangambo (1996), sun bayyana cewa Tatsuniya na ɗaya daga cikin ƙananan rukunnan adabin baka daɗaɗɗu da ba a iya cewa ga lokacin da aka faro su, ko kuma ga yadda suka samu, saboda tsawon lokaci da suka ɗauka cikin al'umma. Hasali ma ka ana iya cewa tana daga cikin hikimomin harshe na farko da Bahaushe ya samu bayan ya samu wurin zamansa na dindindin. A wajen neman asali ko samuwa ana duban tushe ko salsala don sanin lokacin abin ya faro da yadda ya faro, wannan ya sa a cikin fannin ilimi daban-daban ake neman sanin faruwar abubuwa da dama da suka wanzu lokaci mai nisa. Ma'ana a nan shi ne ana ƙoƙarin danganta wasu abubuwa ko al'amurra da samuwarsu, wanda lokacin da abin nan ya faro babu hanyar karatu da rubutu na taskace shi, Waɗanda suka faro shi ba su raye, waanda suke da labarin su ma sun kau. Ya kasance lokaci ya yi nisa da za a iya samun bayanan abin da ake nema

 Yahaya da wasu (1992:7) sun bayyana cewa tatsuniya tana daga cikin labarun Hausawa na farko waɗanda su suka ƙirƙiro su da kansu domin saka nishaɗi da koyar da yara tarbiyya. Sun yi riƙo da wannan hanya ta gado da suka gada daga kakanni da daɗewa kafin su samu cuɗanya da baƙin al'ummu. Tsintsar al'adun Hausawa, su ne harsashen ginin tatsuniya.

 Wannan ra'ayi na Yahaya da wasu (1992:7) ya ƙara tabbatar da bayanan da suka gabata na cewa Hausawa su da kansu suka ƙirƙira labarunsu ta hanyar amfani da fasaha da ƙwarewa da harshe don tsara labarunsu da za su taimaka wajen cusa tarbiyya a cikin zuƙatan ƙananan yara tare da koyar da su tsari da dokokin da ke yi wa al'ummarsu jagorancin rayuwa. Idan muka yi nazarin tatsuniya da idon basira za mu ga cewa babu wani ɓangare na rayuwar Bahaushe da ba ta taɓo ba, wanda ya shafi horo da hani a kan rayuwar yau da kullum.

 Haka ma Gusau, (2013:5) ya bayyana cewa tun asali Hausawa suna da daɗaɗɗun labaransu da suka tashi da su tun kafin cu]anya da wasu al'ummu wanda tatsuniya na ɗaya cikin waɗannan labarun. Waɗannan labarin da jimawa suka ƙirƙirarsu ta hanyar amfani da azancin da suke da shi a matsayinsu na alumma.

 A cewar Harward (1910:vii) ya bayyana cewa dukkanin yara suna sha'awar labarai. Duk da cewa akwai labarun da ake samu a cikin kowace al'umma da ke kowace nahiya ko yanki. Akwai wanda sun shafi keɓantacciyar al'umma wanda kowane yaro yana tashi da nau'in labarin ya shafi al'umma da muhallin da yake rayuwa a cikinsa. Shi ma Herskovits, (1961:169) ya bayyana cewa a cikin tatsuniyoyi da yanayin tsarin gabatar da su wata hanya ce ta gano abin da al'umma ke aiwatarwa da yanayin imaninsu, da tsarin zamantakewarsu, wanda shi zai bayar da haske kan yanayin al'adarsu.

 Haka ma Koko (2009:5-6) ta ƙara da cewa tatsuniya na daga cikin fannonin adabin baka da suka game duniya baki ɗaya. Domin kuwa a kowane harshe da ke cikin faɗin duniyar nan ana samun tatsuniya, kome ƙanƙantarsa, kome ƙarancin mutanen da ke amfani da shi, kenan tatsuniyar ta zama ruwan dare. Saannan ta ƙara da cewa jigogin tatsuniyoyi na harsuna daban-daban suna nuna cewa akwai dangantaka ta ƙut-da-ƙut tsakanin harsunan tsawon shekaru da dama daga wani yanki zuwa wani. Wannan ya sanya suke kamance ta fuskar salo da manufa da yanayin da ake amfani da shi. Shi ma Usman (2018: 44) a nasa bayani ya bayyana cewa a kowace al'umma ta birni da ƙauye suna da labarun gargajiya da suka gada daga magabata. Waɗannan labarun ko da ace suna raye har yanzu a cikin al'umma ko sun mutu, amma dai rubutaccen adabin da ke rayuwa a yanzu, dole ya samu asali ne da daga tsohon adabin baka na gargajiya na kowace al'umma.

A cikin al'ummar Hausawa kuwa babu inda ba a san da zaman tatsuniya ba. Idan muka duba yanayin ƙasar Hausa akwai ɓangaren mutanen Arewacin Nijeriya da suka haɗa da yankin Bauchi da jigawa da Zariya, Kano. Inda ake kiranta da suna tatsuniya Sai kuma Yammacin Arewacin Nijeriya da suka haɗa da Katsina da Sokoto da Kebbi da Zamfara har zuwa cikin garuruwan ƙasar Nijar suna kiranta dad a suna Gatana, ta la'akari da ra'ayin Bergery (1934/51:37) Wannan ya tabbatar da cewa dukkanin waɗannan yankuna suna riƙo da tatsuniyar. Sai dai nisan da ke tsakanin waɗannan garuruwa na ƙasar Hausa, yana sanya a samu ƴan bambance-bambance na karin harshen mazauna wurare daban-daban ta fuskar sautuka kalmomi da kuma musanyar kalmomi da suka dangance kowane yanki. Wannan ya sanya wasu yankuna ake kiranta a matsayin "tatsuniya", inda a wasu yankuna kuma "gatana" suke kiranta.

Har wayau Alidou (2002) ta ci gaba da bayyana cewa a cikin adabin baka ana la'akari wasu dokoki wajen bayar da labari da suka danganci jinsi da shekaru na masu sauraren labari. Inda ta bayyana cewa tatsuniya mafi yawa mata ne, musamman tsoffafi aka fi sani da aiwatar da ita a al'adance. A al'ummar Hausawa Dattijuwa (daga cikin Kakanni) a cikin gida ko a maƙwabta ke da alhakin tara yara tana ba su labarun tatsuniya, domin ita ce take da ilimin zamantakewa, kuma ta ga jiya ta ga yau, ta iya tsara labari da adana shi, da kuma sadar da shi ga masu saurare.

Koko (2009: 16-17) ta bayyana cewa, bayan an tsara tatsuniya akan sami mutane da suka shahara wajen bayar da labaru da hikayoyi da almara su riƙa bayar da tatsuniya a cikin al'umma. Wasunsu ma sukan yi tafiya daga wannan guri zuwa wani, musamman a tsakanin ƙauyuka, wanda wasunsu ma na ɗaukan shi a matsayin sana'a don samun wani ihsani. Ta bayyana ana samun waɗannan mutanen tsakanin ƙabilu irin na Hausa da Tamne da Yaroba da Yao da wasu ƙabilu masu yawa na Afirika. Hakama ta ƙara da cewa ko bayan manya da aka sani da bayar da labarun akwai ƙananan yara da suke bayar da labarun tsakanin junansu irin na kacici-kacici don wasa ƙwaƙwalwa. Hakama samari ko matasa a wajen hirarsu suka haɗu ko bukukuwa sukan ɗan taɓa labarun tatsuniya.

Shi kuwa Bichi (2014:1) ya tabbatar da cewa maza magidanta da matasa na daga cikin masu bayar da tatsuniya a ƙauyuka. Mafi yawa a lokutansu na aiki irin na gona da sauransu. Ya ƙara da cewa daga cikin waɗanda suka ba shi labaran tatsuniya akwai namiji ɗan shakara talatin da huɗu (34). Wannan ya nuna cewa masu tsara tatsuniya mutane ne masu zurfin tunani da azanci a cikin al'ummar Hausawa. Sai dai har wayau Bichi, (2014) ya ambato tsofaffin mata da sababbin amare a matsayin waɗanda suka fi bayar da labarun tatsuniya a cikin al'ummar Hausawa.

Shi ma Gusau, (2013:8-18) ya kalli masu bayar da tatsuniya ta fuskar zamunna da suka shuɗe, inda ya bayyana cewa, kafin zuwan musulunci a wuraren ƙarni na sha ɗaya (11). Manyan mutane maza da mata su neke aiwatar da tatsuniya, a bisa tunanin cewa tatsuniya wata hanya ce ta koyar da matakan zaman rayuwa a rukunonin jama'a. Wataƙila hakan ya sa aka bunƙasata don ta dace da wasu sassa na ɓangarorin zamantakewar rayuwar. Bayan zuwan musulunci, sai malamai suka ɗauki tatsuniya a matsayin ƙarya da hukunci wanda ya yi ƙarya, ya aikata zunubi. Wannan ya sanya ta ɗauki fasaha daban idan an gama gabatar da ita, inda ake cewa, “ƙurungus kan ɓera, ba don gizo ba da na yi ƙarya... Sa'annan kuma aka barwa mata da ƙananan yara jan ragamar tafiyar da tatsuniya.

Dukkannin masana da suka yi rubuce-rubuce kan tatsuniya da suka haɗa da Bichi (2014) da Koko (2009) da Yahaya (1996) da Umar (1980) da Gusau (2013), sun tabbatar da ƙananan yara ne suka fi saurare tatsuniya, domin kuwa ko yanayin labarin an tsara shi ne ta yadda zai dace da tunaninsu.

A cewar Alidou (2002) masu sauraren tatsuniya sun haɗa da yara maza da mata a gaban tsohuwa wadda itace za ta yi ta koyar da su darussa har lokacin da za su girma, inda tarbiyyar yara maza za ta koma hannun iyayensu maza, su riƙa yin labarunsu na maza, mata kuwa su ɗore da nasu labarai na mata.

Masana irin su Yahaya (1992:8) sun bayyana cewa, yawanci an fi yin tatsuniya da dare, bayan an ƙare cin abincin dare, kafin yara su shiga bacci. Ita ma Giwa (2012: 25) ta goyi bayan Yahaya (1992) a cikin kudin bincikenta inda ta ƙara da cewa, kamar yadda aka ruwaito a gabani, al'ummar Hausawa suna aiwatar da tatsuniya da rana, wanda da rana ɗin nan na iya yiwuwa da sanyin safiya ko kuma idan rana ta yi, idan har an tabbatar da cewa za a aiwatar da dokar da al'ada ta tanada kafin gabatar da tatsuniya. Sa'annan kuma da dare wanda a wannan lokacin aka fi aiwatar da ita.

Ana aiwatar da tatsuniya da dare saboda dalilai na rage tsawon lokaci kafin a yi bacci da hana yara yawon dare. Da kuma nishaɗantar da su cikin hikima, tare da koyar da su nau'ukkan ilimi da ake so su tashi da shi tun suna cikin ƙuruciya. Crowley da wasu (1954:3) sun ƙara jaddada cewa a zamanin da ya gabata ana bayar da labarun tatsuniya da dare a cikin babban gida na taro ko kuma idan aka taru a wata lalura ta abokai ko aka kai ziyara a wani gida da rana . Da farko, ƙananan yara za su fara gabatar da tatsuniyoyin, sai manya matasa su shigo ciki, wanda ana cikin yi, yara za su yi bacci, matasan su ci gaba da baje-kolin tunaninsu, wanda ya fi ƙarfin fahimtar ƙananan yaran.

 Umar (1980: 11) ya bayyana cewa ita dai tatsuniya galibi an fi aiwatar da ita da dare, idan kuwa har za a yi ta da rana, dole ne a gabatar da wata al'ada ta ɗaure gizo, maganin yin makuwa. Shi kuwa Ahmad (1997:8) ya nuna cewa ana aiwatar da tatsuniya da yamma a wasu yankunan ƙasar Hausa bayan an gama hadar-hadar yini, inda a wasu yankuna suna aiwatar da ita da dare, bayan an ci abinci kafin a yi bacci.

Bichi (2014:1-2)ya bayyana muna cewa a al'ummar Hausawa waɗanda suke sauraron tatsuniya su ne ƙananan yara. Zaman yana kasancewa da rana ko da dare, kuma mafi yawa a gidajen kakanni da maƙwabta idan akwai wata dattijuwa a nan. Su suke nishaɗantar da yaran da labarai a ɗaya ɓangaren suna ƙura zare da saƙa da ɓarar gyaɗa da sauransu. Idan akwai sabuwar amarya a gida, yaran suukan taru a wajenta da dare don su yi wasa, saannan su saurari labaru.

 Su ma Yahaya da wasu (1992:7) su ma sun bayyana labarun tatsuniya kamar yadda al'ada ta bayyana, hirar yara ce. Ashe kenan abar yara ce, sai dai mata tsofaffi da amare sukan yi ruwa da tsaki wajen gudanar da ita, wajen yi wa yaran ita, inda su kuma za su riƙa sauraro. Wannan haka yake, domin kuwa Gusau (2013:11), ya goyi bayan wannan zance, inda ya tabbatar har wayau yara ne jagororin tafiya na tatsuniya, tsofaffi da amare suna yada musu hanya ne kawai.

Daga cikin masana da suka yi ayyuka kan tatsuniya sun bayyana irin muhimmancin da take da shi da suka haɗa da Umar, (1980:12) inda ya bayyana cewa tatsuniya tana da matuƙar amfani wajen gina kyawawan ɗabiu tare da rusa munana, haka zalika tana taimakawa wajen koyar da yara harshensu na uwa, tana ɗauke kyawawan al'adunmu tare da bai wa yara nishaɗi.

 Shi ma Yahaya, (1974:1) ya ƙara da cewa duk da cewa gaskiya ne labarun tatsuniya ba su taɓa aukuwa ba, amma idan aka yi nazarinsu abin da ke ƙunshe cikinsu, za mu ga cewa suna nuni ga halayen zaman duniya ne. Saannan tana da kama da wasan kwaikwayo inda ake amfani da mutane da dabbobi da tsuntsaye da ma wasu ƙirƙirarrun halittu irin su gizo wajen nuna halayen kirki da kuma sakayya ga wanda ya munana daga ƙarshe. A cikinta ne ake cin karo da kyawawan al'adun Bahaushe irin sana'o'i da kunya da zumunta da tarbiyya da sauransu. A wata faɗa ta Yahaya,(1992:8) ya }ara fito muna da wani amfani da tatsuniya take dashi na katange yara a wuri ɗaya a hana su yawace-yawacen banza, sa'annan suna taya sabuwar amarya hira ta manta da kewar da take da ita na barin gidansu zuwa sabon wuri, su ma su kasance cikin nishaɗi. Sa'annan ga irin darussa daban-daban da suke ƙaruwa da su ta hanyar sauraren labarun na tatsuniya. Ita ma Koko, (2009:31-36), ta bayyana cewa muhimmancin tatsuniya ya fi gaban a bayyana shi duka sai dai a tsakura, domin ilmantar da take da koyar da zamantakewa da koyar da tarihin abubuwa, sadar da rayuwar al'umma daga wani zamani zuwa wani da kasancewarta ma'adanin al'adu, da koyar da matakan tsaro da madubin rayuwa na sanin sirrin al'umma da sauransu.

Rabi'u, (2018) ya gudanar da nazari mai taken habarcen tatsuniya a, nazarin ya bayyana cewa, Al’ummar Hausawa suna da nau’o’in habarcen tatsuniyoyi da dama, waɗanda suka haɗa da labari da tarihih da hikaya da almara da sauransu. Nazarin ya yi amfani da ra’in kwatantan adabi wanda ake amfani da shi wajen kwatanta adabin al’ummomi waɗanda ake ganin suna da wata dangantaka ko kuma wasu kamanni a wasu ɓangarori na adabi ko al’adu domin a tabbatar da alaƙarsu. An kwatanta tatsuniyoyin al’ummomin Hausa a ɓangaren arewacin Nijeriya da kuma Jumhuriyar Nijer. Bincike ya kwatanta yanayin tatsuniyoyin da jigo da salo da kuma adon harshen ta hanya kwatanci. Nazarin ya gano abubuwa masu kama da juna da kuma waɗanda suka bambanta da juna a duka tatsuniyoyin al’ummomin biyu. Misali kamar jigo a tsarin sarautar gargajiya, musamman dangantakar sarki da talaka inda suka bambanta.

Shi kuwa ahmad, (2017) ya yi nazari ne kan kwatancin taurarin waniƙiƙi a tatsuniyoyin Hausa da fulatanci, nazarin ya fayyaci irin abubuwan da suke da alaƙa ta kusa cikin tatsuniyoyin waɗannan al'ummomi biyu, wato Hausa da fulani, tare da ƙawata nazarin da misalai dgga kowanne ɓangare.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

2.5 NAƊEWA

 Ko ba a ce komai ba an ga yadda babi na biyu ya bibiyi ayyukan magabata waɗanda su ka yi kusanci da wannan binciken kamar yadda aka labarta a shinfiɗar babin. Haƙiƙa wannan babin ya waiwayi ayyuka daban-daban da aka yi akan Bahaushe da Hausawa, a inda aka kutsa cikin littattafai da aka wallafa masu magana kan Hausa da Hausawa har ma da Harshensu da ƙasarsu, haka ma kundaye da muƙalu da mujallu da sauran fannonin ilimi. Idan an koma kan falsafa ma haka abin yake domin kuwa an bibiyi ayyuka da dama da aka yi kan falsafar Bahaushe, wanda shi ma aka bincika littattafai da muƙalu da mujallu. A ɓangaren wasanni da tatsuniyoyi ma haka abin ya kasance domin manazarta da dama sun yi nazarce-nazarce haɗe da wallafa littattafai game da wasannin gargajiya, wasu kuma sun gudanar da nazarin ne a kundayensu na kammala karatu, haka ma cikin mujallu duk dai kowa da inda ya kalla a ɓangaren.

 A ƙarshe kuma an tabbatar da cewa dukkannin ayyukan da aka bibiya babu wanda zai hana gudanar da wannan binciken domin kuwa kowa da inda ya karkata akalar binciken nasa.

 

 

 

 

 

 

 

 BABI NA UKU

HANYOYIN TATTARO BAYANAI

 

3.1 SHINFIƊA

 Kamar yadda sunan babin ya nuna wannan ɓangare ne na musamman da ake bayyana irin hanyoyin da aka da aka yi amfani da su wajan samo dukkanin bayanan da aka kawo a cikin bincike a inda wannan binciken ya bibiya hanyoyi da dama yayin gudanar da wannan binciken da aka bibiye su domin tattaro duk wani Sbayani da aka gabatar ko za a gabatar a cikin binciken tun daga farkonsa har zuwa ƙarshensa, don haka a wannan babin za a bayyanawa yadda aka yi ƙoƙarin bibiyar muhimman hanyoyi da za su taimaka wajan cimma nasaran fito da abinda ake ƙulafacin ganowa, a ƙarshen babin kuwa a nannaɗe ko tattare duk wani abin da aka tattauna a cikinsa domin ƙara fito da abin fili yadda ya kamata.

3.2 HANYOYIN TATTARO BAYANAI

 Binciken sanin rayuwar al’umma yana gudana ta hanyoyi daban-daban, wannan ya sanya Osuala (2013) ya ce "dole ne ma’abocin sanin rayuwar al’umma ya tattaro ingantattun bayanai da aka adana". Ana kuma so bayanan su dace da aukuwar al’amuran da ake bukatar ganowa. Ana bukatar mai gudanar da irin wannan bincike ya san gwarazan mutane da suka wanzu a wannan zamani da yake ƙoƙarin tattaro bayanai a kansa. Idan ya yi haka, zai sanya ya sami sauƙin ƙulla bayani a lokacin da yake ƙwanƙwance bayanai da ya tattaro. Masanin ya ce, yana da kyau maabucin sanin rayuwar al’umma ya lura da yanayin yadda al’amura suke, domin lurar za ta sanya ya san tambayoyin da ya kamata ya yi idan ya fita fagen bincike. Ana so mai gudanar da irin wannan bincike ya san yadda zai ɓullo wa al’amura daban-daban da suka shafi al’ummar da yake yin nazari a kanta. (Abubakar, 2019)

 Wannan binciken ya tattaro bayanai ta hanya biyu; Babbar hanya da kuma sauran hanyoyi. Lura da yanayin littafin tatsuniyoyi da kuma wasanni su ne ginshiƙin hanyar da wannan bincike ya dogara a kansu ya sa tun a ranar 30/3/2022 wannan bincike ya fara tattaro bayanai a kan tunanin Bahaushe game da su. Binciken ya kai ziyara wasu sassan jami'o' da nufin ya samo bayanai game da yanayin tatsuniyoyi da wasannin Bahaushe da tunane-tunanen Bahaushen a kan wasannin da kuma tatsuniyoyin da suke ƙirƙira a zamantakewar rayuwarsu . Binciken ya nemi sanin tarihin wasu alamura game da faruwar tatsuniyoyi da wasanni a ƙasar Hausa ta hanyar tattaunawa da mutane daban-daban. Haka kuma binciken ya zagaya wurare daban-daban domin ya yi hira da mutane, kamar yadda ya ƙudurta a ransa yana so ya fahimci falsafar Bahaushe game da tatsuniyoyi da wasanni.

 Bincike kuma ya nemi izini daga Sashen Harsunan najeriya na Jami’ar Sule lamiɗo da ke kafin Hausa. Yayin da bincike ya samu takardar gabatarwa zuwa wurare da ya ziyarta daga sashe, mai bincike ya tuntuɓi wasu mutane mazauna garuruwan da ya ziyarta. Wasu garuruwan kuma kai tsaye mai binciken ya tafi, ya gana da masu ruwa da tsaki a ɓangaren da sauran wurare da bincike ya ziyarta.

3.3 BABBAR HANYAR TATTARA BAYANAI

 Babbar hanyar da aka yi amfani da ita wajan tattaro wannan bayanai ita ce nazartar littafin tatsuniyoyi da wasanni. Litttafin tatsuniyoyi da wasanni, littafi ne da ya yi ficea a duka zagiyar Arewacin ƙasar Hausa wannan bincike ya nazarci wannan tun daga na ɗaya zuwa na shida a tsakanin ranar 03/12/2022 zuwa 11/01/2023, domin kuwa an tattaaro duka littattafan daga na ɗaya zuwa na shida wadda ke ɗauke da wasanni guda 31 , a inda aka fara nazartar littafi na farko wadda yake ɗauke da darrusa guda uku, kuwa wasa ne na karya harshe wadda malami ke koyawa yara yadda ake kakkarya harshe cikin hikima, darasi na ukun kuwa shi ma tatsuniya ce aka kawo ta gizo da budurwar danƙo duka waɗannan wasanni an kawo su ne cikin shafuka daban-daban. A haka dai aka cigaba da nazartar littattafan ɗaya bayan ɗaya har zuwa na shida, wato na ƙarshe.

 Hikimar Bahaushe shi ne dalilin da ya sanya bincike ya tsayar da ƙafa a waɗannan sashe. Waɗannan tatsuniyoyi da wasanni da aka nazarta samfuri ne wajen nazarin tunanin Bahaushe. Wannan ya sa bincike ya tsaya ya lura da irin hikimomi da Bahaushe ya riƙa sanya su cikin wasanninsu da kuma tatsuniyoyinsu, waɗannan tatsuniyoyi da wasanni suna taimakawa matuƙa wajen adana al’adu da suka ƙunshi zamantakewar Hausawa, inda duk suka zama abu guda wajan isar da saƙonninsu a wannan lokacin, sai dai yan bambance-bambance kurum. Bincike ya lura akwai hikimomi a cikin wasannin Hausawan da tatsuniyoyinsu.

 Wannan nazari na waɗannan littattafai, ya ba binciken damar gano wasu bayanai game hikimomin Bahaushen, kuma binciken ya ga wasu wurare daban-daban da Bahaushen ya riƙa sanya tunaninsa cikin wasannin da kuma tatsuniyoyin, musamman wajen zaɓar taurarin da yanayin gudanarwa da tsare-tsarensu da sauransu. Bincike ya riƙa lura da yanayin kowacce hikima da aka sa, ya kuma lura da tsarin gininsu, da yadda suke da tasiri a rayuwa. Bincike ya lura da amfanin sanya waɗannan hikimomi cikin rassan na adabi musamman waɗannan ɓangarori.

3.3 ƘARAMAR HANYAR TATTARO BAYANAI

Daga cikin ƙana nan hanyoyin da aka bi wajan tattaro wannan bayanai akwai:

3.3.1 TATTAUNAWA

 Wannan Bincike ya gana da manya masana ilmi a fannin adabi. Haka cikin rukunin masanan da aka tttauna da su akwai manyan malamai masu digirin ƙoli da kuma shehunnan malamai; da ma sauran malmai maza da mata. Wasu daga cikin mutanen da aka yi hira da su ɗalibai ne masu neman digirin farko a sashen harsunan najeriya da ke da ke jami'ar Sule Lamiɗo ta K/Hausa. Wasu daga cikin ɗaliban sun sada wannan bincike da mutane daban-daban, musamman tsofaffi, kuma sun yi wa bincike jagora zuwa wurin waɗannan mutane. Wasu malamai na ciki da wajen Jami’ar Jami'ar Sule Lamiɗo ta Kafin Hausa sun yi ƙoƙarin bada gudunmawa a wajen binciken, yayin da aka yi magana da su baka-da-baka a kan abin da bincike yake bukata. Waɗannan malamai sun bayar da shawarwari kuma sun sanar da mai bincike wasu littafai da ya kamata ya tuntuɓa domin a kai gaci. Binciken ya kai ga wasu mutane saboda sanayyar da take tsakaninsu da mai bincike, kuma bincike ya yi iyakar ƙoƙarin adana sunan mutane da aka gana da su da wurin da aka yi hira da su, da kuma matsayin kusan duk wanda aka tattauna da shi. Rataye yana ɗauke da jadawalin sunan akasarin mutanen da aka yi hira da su da ranar da aka yi hirar da kuma wurin da hirar ta gudana. Bincike ya sami adadin shekarun wasu daga cikin mutanen da aka yi hira da su, wasu kuma ba a samu ba saboda dalilai da suka sha ƙarfin bincike.

3.3.2 ZIYARAR ƊAKUNAN KARATU

 Ɗakin karatu yana cikin muhimmin wuri da wannan bincike ya taro wasu bayanai daga cikinsa, wato, mai bincike ya shiga ɗakin karatu a Jami’ar Sule Lamiɗo ta Kafin Hausa da Jami’ar Bayero ta Kano da kuma kwalejin ilimi ta garin Gumel. Binciken ya samo littafai da kundayen digiri da maƙalu a waɗannan ɗakunan karatu. Yayin da binciken ya sami kundaye da littafai da maƙalu a waɗannan ɗakunan karatu, ya nazarce su, kuma ya amfana da su. ɗakin karatun ya ba da gudunmawa sosai ga wannnan bincike, musamman a fagen adabin baka ɓangaren wasanni da tasuniyoyi da kuma falsafar da ma shi kansa Bahaushen da kuma abinda ya shafi ƙasarsa da harshensa da sauransu.

 Wata hanyar da ta ƙara taimakawa wannan bincike ita ce Intanet, wannan kafa ta taimaka wa binciken ya samu bayanai ko ƙarin haske a fagagen da suka shafi falsafa da wasannin gargajiya da tatsuniya da sauransu. Binciken ya karɓi saƙuna daban-daban ta intanet (email) da dandalin sada zumunta, musamman wazof daga mutane na kusa da nesa. Binciken ya yi hira da mutane ta waɗannan kafafe, inda yawanci suka aiko da gudunmawarsu a rubuce. An yi musayar saƙonni tsakanin mutane da mai bincike ta wannan kafa, kuma binciken ya adana wasu saƙonnin a waya domin tabbatarwa masu nazari bayanai game da inda aka bincika da kuma waɗanda aka bincika . tare da taƙataccen bayani da zai taimakawa wannan binciken.

 

 

 

 

 

 

 

3.4 NAƊEWA

 Wannan babin dai ya bayyana yadda aka gudanar da aikin ne, ta hanyar kawo wurare da abubuwan da aka bibya ko aka tattaro da suka taimaka wajen tsayuwar wannan binciken, waɗanda suka haɗa manyan hanyoyi da kuma ƙanana , manyan hanyoyin sun ƙunshi nazartar littafin da aka yi tsokaci akansa gabaki ɗaya, sa'annan kuma an bibiyi ɗakunan karatu a mabambanta makarantun ilimi na cikin gida, bugu da ƙarin ƙoƙarin nemo ƙarshen zaren ikin ya haddasa tattaunawa da jama'a iri-iri , kama daga malamai mazauna makarantar da ake gudanar da aikin ƙarƙashinta, da kuma sauran manyan malamai fitattu a wuurare daban-daban, al'amarin bai tsaya iya nan ba, domin kuwa tattaunawar ta kasance harda wasu daga cikin ƴan uwa abokan karatu, dama makusanta abokai da dai sauransu. ba ma iya nan abin ya tsaya ba domin kuwa an binciko bayanai da dama ta hanyar kafar sadarwa ta internet, wasu kai tsaye aka riƙa binciko su, wasu kuwa an same su ne ta hanyar neman shawara daga gurin wasu inda suka bada bayanan ta kafar sadarwar wazof, da sauransu.waɗannan duk su ne ƙananan hayoyin da aka tattaro bayanan.

 

 

 

 

 BABI NA HUƊU

FALSAFAR BAHAUSHE CIKIN LITTAFIN TATSUNIYOYI DA WASANNI

 

4.1 SHINFIƊA

Babi na huɗu a kowanne bincike shi ne ƙashin bayan aikin, ma'ana a shi ne gundarin aikin yake, kasancewar aikin ya shafi binciko falsafar Bahaushe ne cikin tatsuniyoyi da wasanni, don haka wannan babin zai yi bayani dalla-dalla tare da fiddo da falsafar da ke cikin wasannin da tatsuniyoyin da farfajiyar binciken ta iyakance ɗaya bayan ɗaya , da suka haɗa da tatsuniyar gizo da ɓaure, ɗan sarki ya zama miciji, tatsuniyar na-goma, da kuma wasannin ka-cici-ka-cici, wasannin ɓata da sauransu, haka kuma a babin ne za a bayyana yadda fannin falsafa yake da mukusanciyar alaƙa da da fannin adabi ta ɓangarori da dama da suka jiɓancesu, kamar ma'anarsu, ire-irensu, bunƙasarsu, da ma sauran ɓangarori duk babin zai fayyace irin dangantakarsu ta waɗannan fuskoki, a ƙarshe kuma a tattauna duk wasu muhimman abubuwa da suka zo a cikin babin.

4.2 DANGANTAKAR FALSAFA DA ADABIN BAKA

 Wannan ɓangare zai dubi dangantakar dake tsakanin falsafa da adabin baka ne na Hausa, saboda haka kafin a je ga dangantakar ta su kai tsaye ya dace a yi waiwaye baya a dubi irin wanzuwarta tare da ma'anar falsafar da adabin da kuma rabe-rabensu, daga nan ne za a ga irin dangantakar da ke tsakanin adabin da kuma falsafar.

 Kamar yadda bayanai suka gabata dangane da ma'anar falsafa, kai tsaye ana iya taƙaicewa a ce :

 " Ita falsafa wani ƙasaitaccen tunani ce mai koyar da hikima da kujiba -kujibar rayuwa", ko mu ce amfani hikima da kuma iya sarrafa mu'amala." (Gusau 2022).

 Ta fuskar bunƙasa kuwa muna iya cewa : falsafa ta samo asali ne tun daga zaman farko na al'ummar duniya haka ta yi ta samun cigaba har izuwa yau, kuma duk hikimomin da ake isarwa a falsafa duk da harshe ake isar da shi, abubuwa ne da suka shafi rayuwa kai tsaye ba tare da wahalarwa ba , haka kuma idan muka kalli irin rabe-raben falsafa kamar yadda masana suka bayyana ta kasu kashi uku, wadda ya haɗa da, falsafar harshe, falsafar kintace/kwatance,falsafar rayuwa. (Gusau, 2022).

 A ɓangaren adabi kuwa shi dai adabi kamar yadda masana suka bayyana wani sarrafaffen harshe ne mai ɗauke da fasaha ta musamman mai ayyana basirori da hikimomin al'ummar Hausawa. Sannan kuma kai tsaye ana iya kallon adabi ta fuskoki guda uku, wato Waƙa, zube da kuma wasan kwaikwayo.

 To a wannan gaɓar farko abinda za mu fara dubawa shi ne dangantakar falsafa da adabin baka ta fuskar ma'anoninsu. da farko ita falsafar kanta tunani ce game da abin da ya shafi rayuwa yayinda adabi kuma yake bayyana mana hotunan rayuwar al'ummar masu ɗauke da hikimominsu . to anan ita falsafa dai ita ce tunane-tunanen da suke sanya wa cikin al'amuransu, waɗannan al'amuran da suke aiwatarwa masu ɗauke da tunanin kuma su ne adabin.

 Don haka wannan wata dangantaka ce mai ƙarfi game da falsafa da adabi.

 DANGANTAKAR FALSAFA DA ADABI TA FUSKAR RABE-RABENSU:

v  Falsafa na amfani da kwatance haka kuma ana amfani da kwatance a fannin adabi.

v  Falsafa na amfani da harshe a wani muhimmin kaso daga cikin kashe-kashenta, harshe shi ne abin da ya bambanta mutum da dabbobi, kuma shi harshe yana mazaunin linzami na tunani a hannun ɗan Adam, ta hanyar linzamin nasa ne zai iya karkata tunaninsa duk yadda yake so.

v  haka kuma abin ya ke ta fannin adabi , domin shi ma adabi ƙashin bayansa shi ne harshe. domin kuwa mutum kan yi amfani da harshe a matsayin kyautatwa ko yabo ko zuga, sai kaga wadda ya zuga yana tsuma har ya tuɓe rigarsa ya bashi ko matarsa ko duk wani abu da ya mallaka. Kuma mutum ne kawai ke gwada fasaharsa da nishaɗi ta hanyar harshe misali irin, karin magana, waƙa, Azanci, habaici, zambo, sakaya zance, taƙaitaa zance da sauransu.

v  Adabi na bincike ko tattaunawa game da rayuwa da zamantakewar al'umma, haka kuma falsafar rayuwa na ɗaya daga cikin jiga-jigan falsafa.

v   Falsafa kan nuna tsarin mulki da waɗanda za a mulka haka shima adabi kan fito mana da irin tsare-tsaren da ake tafiyar da mulki a rayuwa.

DANGANTAKAR FALSAFA DA ADABI TA FUSKAR ILIMI

 * Adabi a harshen Hausa ya samu shigar zamani a cikinsa kuma ya kai matuƙa wajen ɓaci har al'umma na yin alawadarai da irin abin da yake faruwa musamman in mun dubi wasannin kwaikwayo na Hausa na zamanin yau.

 haka abin yake in mun dubi falsafa domin ita ma ta samu canje-canje na musayar tunani, inda aka sami irin su (Kalmus) a falsafance suna ganin addinin mutane da al'adunsu masu kyau, sa'annan kuma ana faɗin ra'ayin falsafar ga ɗalibai da baka ba a rubuce ba.

DANGANTAKAR FALSAFA DA ADABI TA FUSKAR WANZUWA DA BUNƘASARSU:

v  Adabi ya bunƙasa ne kamar yadda tarihi ya nuna bunkasar falsafa ta hanyar samun wasu gwaraza da suka shafe lokutansu da yin tunani don samar da wani abu mai amfani.

v  Adabi Adabi ya biyo wasu matakai kafin fara rubuta shi, har ya zama rubutacce haka sha'anin yake a bunkasar falsafa.

v  Falsafa ta bunƙasa ne har ta kai ga an samu falsafar musulunci, kamar yadda Adabi ya samu bunƙasa zuwa adabin bayan zuwan musulunci, da kuma na gargajiya shi ne adabin da Hausawa suke tun kaka da kakanni, kuma ana kiransu da adabin baka, domin asalinsa ba a zube yake ba kuma shi ne adabin da ya ƙunshi makaɗa da kayan kiɗansu, da tatsuniyoyi da labarai da almara da sauransu.

DANGANTAKAR FALSAFA DA ADABI TA FUSKAR FARUWARSU:

v  Shi adabi babu wani takamaimai lokaci da za a ce ga ranar da aka fara shi, haka ita ma falsafa babu wanda zai ce ga ranar da ɗan adam ya fara tunani akan kaza ba.

v  Adabin Hausa ya fara da adabin baka kamar yadda falsafa ta samo asali daga tunani da ka.

DANGANTAKAR ADABI DA FALSAFA TA FUSKAR BA DA GUDUMMAWA GA RAYUWA:

v  Keɓe tarihin Bahaushe adabi da falsafa za su taimaka wajen taskance tarihi domin sanin jiya da yau, da kuma yadda za a fuskanci gobe.

v  Adabi da falsafa suna tabbatar tare da nuna martabar Bahaushe, kuma suna cusa alfahari da kai da kuma sanin ciwon kai, da kishin zuci, da kuma kishin ƙasa, da girmama abubuwan da aka gada tun daga kakanni.

v  Falsafa da adabi suna bunƙasa ilimi da wayar da kai.

v  Sa'annan falsafa da adabi suna koya dabarun zaman duniya.

v  Adabi da falsafa na wasa ƙwaƙwalwa, ta bayyana abubuwan fasaha da lugga da sauransu.

 Duk waɗannan abubuwa ne da suka haɗu wajen dangantakar falsafa da adabi.

 Wani babban abin sha'awa shi ne dukkanin masana falsafa a ƙarnukan da suka gabata za ka same su masana ne ƙwararru a fagen ilimn manɗiƙ, dan haka sai dangantakarsu da masana adabi ta yi ƙarfi, kuma da wuya ka sami masanin adabi da yake da jahilcin falsafa, domin ita ce matakin da ake takawa wajen sarƙafa tunani har a furta abinda zai zama adabi ga al'umma.

 Idan muka ɗauki ilimin (manɗik) shi ilimi ne da ke bin diddigin sirrikan harsuna, da kuma gano ma'ana mai zurfi cikin maganganun jama'a har ma da masu adabin. Masan adabi suna zurfafa tunani wajen yin hange dan su kwatanta abubuwa domin kyautata adabi, kamar yadda masana falsafa kan zurfafa tunani don gano wata matsala, kuma mafi yawa matsalolin sun yi tarayya da malaman adabi, wajen yin wani abu da zai taimakawa rayuwar al'umma.

 Kuma mafi yawan taƙaitattun jawaban da masana falsafa kan yi su na da dangantaka da wani abu mai kama da karin magana da salon magana ko kuma ɗan waƙa mai ƙunshe da wani saƙo mai muhimmanci misalima maganganun su (BROTAJOROS) da sauransu.

 Misali:

 = Mutum magwaji ne na duk wani abu.

 = Abinda ya yi kyau na wajen ka to muni na ga wani.da suransu.

Haka kuma idan muka kalli ɓangaren adabin gargajiyar Hausawa akwai jigo mai nauyi ta fuskar magungunan gargajiya, wanda in mun waiga baya masana falsafa su ne likitoci da binciken cuta da maganinta misali: Irin su IBN SINA da IBN NAFIS da can ma baya irin su "ALATO" in da ya bada gagarumar gudunmawa wajen fannin lafiya da riga-kafi wanda Hausawa kan ce " ya fi magani" a wani littafi mai suna Tafhatul- Arus shafi na 129, ya kamo irin gudunmawar "Plato" ta fuskar wasu abubuwa biyar da su kan iya kawo matsala akan lafiya:

1. Tsoron talauci

2. Rabuwa da masoya

3. Tunanin abubuwa na ɓacin rai

4.Ƙin karɓar nasiha

5. Biyan da damuwa game da dariyar jahili.

Don haka in muka dubi adabi ta fuskar magani to akwai falsafa cikin harkokin lafiya da magani,

Akwai dangantaka ta amfani da harshe ne ake koyar da yara tun suna ƙanana, domin su, bunƙasa tunaninsu da kyau, in mun dubi misalan kacici-kacici da maganganun karya harshe, da wasa ƙwaƙwalwa, ta yadda za su rike sunayen abubuwa da siffofinsu. dukkannin waɗannan hanyoyin suna da dangantaka da falsafa.

Kuma akwai dangantaka ta fuskar manufar adabin Hausa, ya sa a gaba da kuma masana falsafa suka sanya a gaba idn muka koma baya irin ƙoarin da platon ya yi wajen sabunta tunanin al'umma ta fuskar zamantakewarsu. Haka abin yake a adabi Gusau (2002), SALIHU JAN KIƊI a shafi na 68 a sakin layi na ƙarshe malam ya ce" Makadi mai falsafa wato masanin tsari kan hanyoyin zaman jama'a ya kan yi ƙoƙari wajen bayyana halayyar wanda yake yi wa waƙa da kuma tsarin da ya ɗauka yake tafiyar da rayuwarsa a kansa. Irin wannan makaɗi za a tarar da shi mai hangen nesa ne mai gargaɗi, mai faɗakarwa mai wayewa, kuma mai ilimantarwa kuma kullum yake ƙoarin ya ga al'ummar da ya ke a cikinta ta zama tagari".

Anan ana ganin cewa akwai dangantaka mai ƙarfi tsakanin falsafa da masanin adabi ko mai aiwatar da adabi makaranci mai karin magana" Mai fashin baƙi , da sauransu. A wani ɓangare za ka samu adabin Hausa na taɓo harkokin ilimi mai zurfi na hisabi wanda asalinsa daga falsafa yake , in mun dubi mawaƙi na rubutacciyar waƙa kan yi amfani da ramzi wajen rubuta shekarar waƙarsu ko kwanan watan da suka yi waƙa.

4.3 TUNANIN BAHAUSHE CIKIN TATSUNIYOYI DA WASANNI:

Kowace al'umma tana da nata tunanin na rayuwa, sa'annan kuma duk wani tunani da za ta yi dole ya dace da tata rayuwar. shi yasa Hausawa kan ce “ƙafar wani ba ta yi wa wani tafiya”. Sai dai duk da bambance-bambancen tunani da ake samu tsakanin alummomi daban-daban akwai wasu keɓantattun abubuwa da suka zama gama-gari ne, ana samunsu a cikin kowace al'umma.

 Haƙiƙa Bahaushe na sanya tunaninsa da falsafarsa cikin abinda ya shafi adabinsa, wanda ya jiɓanci rayuwarsa da zamantakewarsa ta yau da kullum, don haka ana iya kallon wannan falsafar cikin rabe-raben falsafa da falsafar rayuwa kasancewar al'amuran da yake gina tatsuniyar da kuma wasan duka kan gyaran tarbiyya ne da fatan samun kyakkyawar mu'amala.

 Irin wannan falsafa ta ƙunshi ciki da wajen waɗannan ɓangarori, domin kuwa abubuwa da dama ke wakana a wasu keɓantattun wurare da aka tsara bisa ga tunanin Bahaushe wanda ba haka lamarin yake a cikin rayuwarmu ta yau da kullum ba, domin kuwa magabata sun ɓata lokaci wajen yin tunani da yin ƙirƙirar abubuwan da suke son tsarawa a cikin al'ummarsu wanda zai dace da tsarin addininsu da al'adarsu da tunanin al'ummarsu da yanayin wurin zamansu da duk wani abu da ya jiɓinci rayuwarsu ta yau da kullum.

 Akwai abubuwa da dama da ake samu a cikin tatsuniyoyin kowace al'umma da kuma wasanninsu, sai ɗan bambance-bambancen da ba a rasa ba, wanda ya shafi yadda kowace al'umma ke gudanar da rayuwarta.

 A wajen al'ummar Hausawa, suna da nasu keɓantaccen tunani da suka tanadarwa tatsuniyoyi da wasanni a matsayin bayyana yanda al'amuranta ke wakana, ta hanyar amfani da wasu hikimomi da ake sanya wa wadda suka dace da su, kama daga taurarin da ke rayuwa a cikinta, da irin bidirin da ake aiwatarwa ba tare da takura ko rashin walawa ba. irin waɗannan wurare da ake riskar hikimar Bahaushe sun haɗa da muhallin da ake aiwatarwa, abubuwan da ake tsarawa, da kuma taurarin cikinsu.

4.3.1 MUHALLI

Ba kowanne al'amari ne yake gaskiya ba a al'amuran tatsuniya da kuma wasanni kamar yadda yake zahiri bisa sararin duniyar da muke rayuwa. Ba a iya cewa ga wani wuri takamaimai da wani al'amari daga cikin al'amurran tatsuniya ke gudana. To idan hakan ne, haƙiƙa an yi haka ne da ta hanyar amfani da ɗumbin tunani, domin kuwa a karon farko idan aka fara kallon duniyar da aka jingina tatsuniyar da ita, duniya ce da ta samu wahalawa ta yi yabanya take cin karenta ba babbaka, ba tare da tsangwama ba, haka kuma babu ita a zahiri sai dai mutum ya riƙa ƙiyasta ta a birnin zuciyarsa tare da tunani da imani ko kuma yarda. Wasu duniyoyin da ake gina tatsuniya a cikinsu a saman iska suke rayuwa, ko kuma a cikin tunani da imani wanda suna rayuwa a cikin duniyarmu ta yau da kullum, suna cin kasuwarsu daidai gwargwado. Kuma tatsuniyar ta yi tsawon lokaci na wani zango ba tare da tsangwama ba, kuma ta samu karɓuwa a zukatan al'umma manya da ƙanana.

 Haƙiƙa wannan ɓangaren na ɗauke da muhimmin tunani, wajen zaɓar muhallin gina tatsuniyar na musamman wanda babu shi a duniyarmu ta gaskiya, sai dai keɓantacciyar duniyar ta ƙunshi wurare mabambanta kama daga waɗanda muke dasu a cikin duniyar mu da suka haɗa da kogon itace, da kogon dutse, da ƙunƙuwa ko suri, da ruƙuƙin daji, da sararin samaniya, da gona, da fadar sarki, da cikin ruwa da faɗo, gidan azurfa ko zinare da sauransu. Haka ma da wasu da muke riya akwaisu a tunanin tunaninmu, amma ba mu ganinsu, waɗanda da yawansu ƙirƙarsu aka yi, aka cusa su a cikin tunanin mai sauraro don ya riƙa riyawa a ransa akwaisu, alhali kuwa babu su a cikin rayuwarmu ta yau da kullum, kamar kasuwar sama, da birnin aljannu, da wani gari da ake yawan ambatowa (ba a bayyana inda yake), da duk wasu wurare na musamman (Koko 2009:4).

 Idan aka yi nazarin abin da masanan suka bayyana da kuma amfani da ilimin da muke da shi, na mun wayi gari cikin al'ummarmu mun tarar da cewa ana aiwatar da wannan tatsuniyar. Mun san da cewa duk waɗannan abubuwa da aka ambata a sama ana riya cewa akwai su ko kuma suna wakana ne a wata duniya ta daban, a inda mu kuma muna karanta labarin wannan duniya ne kai tsaye, tare da imanin cewa ko shakka babu hakan abin ke faruwa. Sai daga baya idan hankali ya shiga ake rarrabewa tsakanin aya da tsakuwa, wato tsakanin zahirin gaskiya da kuma tatsuniya.wannan wata babbar hikima ce ta bahaushe.

4.3.2 AL'AMURAN RAYUWA

 Haka kuwa akwai abubuwa da dama da ke a cikin tatsuniya. Kamar yadda aka sani ne, a cikin rayuwarmu ta yau da kullum akwai ayyuka da aka al'adanta aiwatar da su, waɗanda su ne rayuwar. Duk wanda yake kan wannan turbar a cikin al'umma ana yi masa kallon yana kwantanta rayuwarsa bisa tsarin da al'umma ta aminta da shi. Wannan ma haka yake a cikin rayuwar tatsuniya, domin kuwa akwai tunane-tunane da dama da aka tsara game da al'amuran da suke aukuwa a cikin duniyar nan. Kuma waɗannan al'amurran ana tsara su bisa tsani na tunanin al'umma da tarbiyya da yanayin zamantakewar rayuwa. Misali, a tatsuniyar Maraya da saniya mai magana, tatsuniya ce da ke ɗauke kishi da ƙiyayya tsakanin ɗa da kuma matar ubansa, ta fifita soyayyar ƴaƴanta da ta haifa a kansa, saboda shi mahaifiyarsa ta rasu, amma kuma duk irin muguntar da take shirya masa sai saniyar da mahaifiyarsa ta bar masa gado ta ke sanar da shi tare da faɗa masa hanyar da zai bi ya kare kansa, har dai Allah ya kuɓutar da shi ita kuma ya nuna ishara a kanta, misali inda ta ke rera waƙa ta ke cewa:

 Janniya janniya jannati

kishiyar uwa, jannaiya jannati,

Ba uwa ba ce janniya jannati

za ta baka tuwo janniya jannati

Tuwo da magani janniya jannati

Idan ta baka janniya jannati

Ka zo nan guna janniya jannati

Ka haƙa ka rufe janniya jannati.

 A cikin tatsuniyar Mutuwa da Sa kuwa ana iya tsintar wayo tsakanin Gizo da Mutuwa, inda ta yi kiyon Santa sai da ya girma ta riƙa yawo da shi, tana neman wanda za ta baiwa ya ci soye bayan shekara ɗaya za ta zagayo ya taɓo kololuwar kanta, kowa yaƙi karɓa sai Gizo. Sai da shekara ta zagayo ta zo da niyyar a taɓo saman kanta. Sai ya yi mata dabara ya haye saman jimƙar ɗakinsa, da ta zo ta umurci ya fito, sai ya ce ta dakance shi yana ɗinke ginin ɗakinsa da ya tsage, sai ta yi nufin ta leƙa don ta ga yadda ake wannan ɗinkin. Sai kuwa ya yi sauri ya taɓo ƙololuwar kanta, alhali mutane suna biye da su da su ga yadda za su warware. Shi kenan sai ya tsira da rayuwarsa ta hanyar yi mata dabara. (Hira da Mama Amarya, mai shekara 59).

 Akwai kuma tatsuniyoyi irin su, Ɗan sarkin agadas, Musa ɗan Sarki, Fifi dallo, da sauransu, duka ire-iren waɗannan al'amura ne da suka shafi zamantakewar al'umma ta yau da kullum a mabanbanta abubuwa da Bahaushe ke hikimar amfani da da su cikin tatsuniyoyi domin fito da illar wani abu ko muninsa, wadda kusan kowacce tatsuniya ko wasa sai ka samu wani muhimmnin al'amari cikinta ko da babu a fili kuwa to matuƙar an zurfafa tunani sai an riske shi, kamar irinsu, wasannin ka-cici-ka-cici, ɗan ƙashin gwiwa, daskin da riɗi, da dai sauransu..

 Bugu da ƙari Bahaushe kan yi amfani da hikima wajen zaɓar yanayin cima a cikin wasa ko tatsuniya, misali a ɓangaren abinda yake mai muni ko fito da illarsa da rashin kyautuwarsa ana amfani da nau'ikan abinci munana waɗanda suka saɓa da cimar da al'ada ta yarda da su, kamar ɓera, kwaɗi dusa, dss. misali a tatsuniyar na-goma, an nuna irin abincin da dodanniya ke ci su ne, ɓeraye, ƙudaje dss. Ga ɓangaren abinda yake mi kyau kuwa ko mai muhimmanci za ka iske cewa an bayyana irin abincin da nama, ko zuma fura da nono alkaki da dai duk wsu dangogin abinci masu daraja da alfarma a ƙasar Hausa.

 Su kuwa Wasanni galibi akan gina su ne ɗauke da al'adun Hausawa iri-iri da ke zayyana hotonsu da suka haɗa da abinda ya shafi harkokin Aure, kama daga yadda ake neman auren har zuwa yadda ake gudanar da zamantakewar auren, da duk wasu abubuwa da suka jiɓance shi, ta wannan hanya ce al'ummar Hausawa kan riski abubuwa da dama da kuma samun haɓakar al'adunsu, da nusar da yaransu musamman ƴanmata ga fahimtarsa sosai ba tare da shan wahalar zaunawa a koyar da su ba. haka kuma nishaɗi, Sana'a , ilimi, da sauransu.

 Bugu da ƙari wasu wasannin akan gina su da hikimar shimfiɗa tsarin mulki lko shugabanci ga al'umma wadda yau da gobe wannan abin zai zauna a zuciyar yaran ko matasan, su san daidai da kuma abinda ba daidai ba, su kuma horu da bin doka ko zartar da ita, kasancewar wata rana su ne a fagen. kusan babu wani wasa a cikin wasannin malam Bahaushe da ba ya ɗauke da wata hikima makamanciyar waɗannan .

4.3.3 TAURARIN TATSUNIYA

 Bahaushe kan gina tunaninsa matuka wajen zaben taurarin Tatsuniya, Galibi za a ga cewa abubuwa da yawa na dangin abubuwa masu rai da marasa rai da kuma ƙirƙirarrun abubuwa ne ke karaɗe cikin tatsuniyar Bahaushe, daga cikin ire-iren taurarin akwai mutane da Aljanu, Imanin da Bahaushe yake da shi game da aljannu da tunaninshi dangane da siffarsu, halayyarsu da ayyukan ban mamaki da suke da shi ake fitowa da su a zahiri. Haka kuma ga abinda ya shafi Dabbobi,da tsuntsaye da kwari, Wasu daga cikin taurarin tatsuniyar ma kuwa babu su, ƙirƙira su aka yi, irin su Gizo da ƙoƙi da Botorami da Dodo da sauran Daga cikinsu akwai waɗanda su aka fi ambato, akwai waɗanda sukan fito jefi-jefi. Misali ta ɓangaren mutane ana yawan ambaton sarakuna; da jarumai; da mata da miji; da kishiyoyi da yanayin zamantakewarsu ta yadda za a fito da darussan da ke aukuwa a cikin yanayin zamantakewarsu ta aure. Misalin wannan kuwa shi ya fi yawa a cikin tatsuniya. Sa'annan dukkanin dabbobin da tsuntsaye da ƙwarin da ke fitowa a cikin tatsuniya ana mutunta su a ba su halayyar mutane ta yadda suna iya magana. Kamar Sa a cikin tatsuniyar Maɗori, mai bai wa ubangidansa labarin yadda aka yi kiwonsa don mai shi ya san yadda zai yi ɗori. Waɗannan duka wani kasaitaccen tunani ne da Bahaushe yake gina wa wadda kuma sai an zurfafa tunani ake iya gano su.

 Tunanin Bahaushe ya karaɗe taurarin cikin tatsuniya, kamar yadda yake yawan ambato su, tare da ba su matsayi ko aiki a cikin tatsuniyoyin, wasu taurarin an kirkire si su ne domin su tare wani giɓi da su kaɗai suka dace da shi. Domin kuwa dukkanin rayuwar da ake laƙabawa taurarin, rayuwar mutanenmu ake so a yi gyara. Don haka akwai halayyar da dole a nemo wasu taurari da ba waɗannan ba don su dace da saƙon da ake son a isar. Misalin halayyar tsoro da ake so a cusa a cikin zuƙatan ƴaƴan Hausawa, sai aka nemo Dodo aka ba shi wannan ragamar. Dabara da iya yi da yaudara da sauran halaye aka jingina su ga Gizo, sa'annan aka samar masa a murya ta musamman da ta yi daidai da tunanin yara, aka mutunta shi ta hanyar samar masa matarsa ƙoƙi, wacce take da haƙuri da shi kuma halayyarsa ya sha bamban da nata. Shi kuwa gizo-gizo ƙwaro da muke da shi a nan ƙasar Hausa, bai taɓa fitowa a cikin kowane labari na tatsuniya ko da sau ɗaya kamar yadda sauran dabbobi suke fitowa ba (Labura 2008:263). Gizo da muke da shi a cikin tatsuniya ya bambanta da gizo-gizo, haka ma matarsa ƙoƙi ba ita ce ƙoƙi-ƙoƙi ba. Gizo fitaccen tauraro wanda aka fi sani da mijin ƙoƙi yana da wasu keɓantattun halaye da babu tauraron da yake da su kamar wayo da haɗama da yaudara da ƙarya da wuce iyaka da sauransu. Dalilin da ya sa mutane suke ɗaukar Gizo a matsayin gizo-gizo, shi ne wasu daga cikin marubutan littattafan tatsuniya kamar Yahaya (1971) da Gusau (2013) idan aka zo wajen zana gizo sai a zana shi da surar gizo-gizon da aka sani, (Rabi'u, 2018).

Dukkanin waɗannan wasu abubuwa ne da Bahaushe yake shimfiɗa tunaninsa wajen zaɓarsu, da su ke haɗuwa wuri ɗaya don samar da gangar jikin tatsuniya. Haka kuma rashin ɗaya daga cikin waɗannan ababen, yana hana kammalar tatsuniya na kasancewarta mai inganci.

Ga ƙwari da tsuntsaye kuwa tunanin Bhaushe ya fi karkata ga Tsuntsuwa da maciji, haƙiƙa tsuntsuwa sha kundum ce a a tatsuniyar Bahaushe duba da cewa waɗanda tatsuniyar da shafa yara ne, shi kuwa miciji a har kullum ɗabi'arsa ita ce mugunta don haka dole ya zama abin tsoro ga al'umma.

Sa'annan kuma haka abin yake ga ɓangaren wasanni ma, sai dai shi wannan fannin ya ɗan sha bamban da tatsuniya domin kuwa shi wasa akan tsinkayi tunanin da ya gina ne cikin gundarin wasan, haka kuma wasu wasannin sun bambanta da jinsin masu aiwatarwa, ma'ana akwai waɗanda ake tarayya maza da mata, da kuma wadda maza ne kawai zalla ko mata zalla. ma'ana dai babu wata ƙirƙirarriyar halitta ko wani sauyi game da al'amarin kayan cikin wasa ko masu aiwatarwa. misali akan tsara wasa musamman a shiryashi ta hanyar zayyano ko lissafo duk wasu kyawawan ɗabi'u da ake son matashi ya siffantu da shi, ko kuma a ambato halaye abin ƙyama ga samari, amma sai ka iske cewa wasannin ƴammata ne masu aiwatar da shi ba su samarin ba. Ko a tsara wasan ta hanyar kwatance da siffanta yadda mata suke zaman aure da kula da miji da abinda ya shafi reno da tarbiyyar ƴaƴa, kuma duka ƴammata ne kawai masu aiwatar da irin waɗannan wasannin. Su kuwa Maza galibi wasanninsu sun fi karkata ne ga abinda ya shafi faɗa, ko yaƙi, a ciki za ka iske yadda shugaba ke aiwatar da doka ga mabiyansa da kuma da ƙoƙarin nuna jarumta don kada a ga gazawar mutum, kamar irinsu wasannin ɗan Akuya na da sauransu.

Akwai kuma wasannin da ake haɗuwa maza da mata wajen aiwatar da su, kamar irin su wasannin ɓuya, ko wasannin tattaɓa gwiwa, ko wasannin tambayoyi da amsoshi daban-daban. waɗannan wasannin duka jinsi biyun maza da mata sukan haɗu wajen aiwatar da shi. Babban abin lura anan shi ne Bahaushe ya zuba falsafa a wannan muhallin, domin kuwa duka nau'ikan waɗannan wasannin ana yinsu ne domin nishaɗi kawai, ko kuma akwai ilimi da ya jiɓanci harshen nasu, babban abin birgewa anan shi ne yaran duka babu matasa ko kuma ƴammata sai dai a iske ƙananan yara ne kawai.

Don haka kuwa kenan ba ma iya cikin wasannin ba hatta da da tsarinsu ma akwai hikima da tunani.

4.3.4 WAƘA

 Waƙa sha kundum ce a fagen hikimar Bahaushe cikin tatsuniyoyi da wasanni, domin kuwa mafi yawan kaso na tunanin Bahaushe cikin waɗannan rassa guda biyu waƙa ke taka rarwar gani wajen bayyanarsu.

Bahaushe na amfani da hikimar sanya waƙa cikin waɗannan ɓangarori da nufin jawo hankalin masu sauraro, kasancewar kuma mafiya sauraron ko aiwatarwar yara ne wannan zai yi tasiri matuƙa wajen saurin ɗaukar abin ta hanyar bibyar waƙar, ya yin da suka haddace ta a hankali saƙon zai riƙa shiga ƙwaƙwalwarsu, ba sai an maimaita kullum ba wannan ya sa galibi wasannin Bahaushe na gargajiya ake aiwatar da shi da waƙa, sa'annan kuma tatsuniyoyi ma kaɗan ne babu waƙa cikinsu kuma waƙoƙin su ke ɗauki da wani muhimmin kaso na saƙon da ke ciki misali tatsuniyar musa ɗan sarki a baitin da budurwar ke rerawa kamar haka:

 Kai wane, Kai wane wannen gayya,

 wane ɗan makaranta,

wane ɗan sarakai,

ka ƙaunaci Allh wane bani zane na,

ka ƙaunaci Allah wane ban riga ta,

ka ƙaunaci Allah wane ban bantena.

 Wasu waƙoƙin kuma cikinsu ne ake warware wata matsala da ta faru a cikin tatsuniyar .alal misali idan aka ɗauki waƙar cikin tatsuniyar Gizo da ɓaure inda tsuntsuwa ke cewa:

 Kai Gizo, kai Gizo,

a can ka ci ɓaurenka,

har ka kuskure bakinka,

har ka manto jallonka.

 

Haka kuma idan aka kalli waƙoƙin wasanni ma inda anan kuma gaba ɗaya cikin waƙen ne ma ake aiwatar da wasan, ma'ana a cikin waƙar manufar wasan ta ke misali, wasannin gaɗa:

jagora: Ina da ƴata da ba za na bai wa fulani ba,

ƴ/amshi: maye dalilin da ba za ki bai wa fulani ba,

jagora: yini a daji kwana a daji kamar kura

ƴan/Amshi:sai tumoro ala bamu kairin masoya.

jagora : ina da ƴata da ba za na baiwa barebari ba

ƴ/amshi: maye dalilin da ba za ki bai wa barebari ba

jagora: ƴa da tsagu uba da tsagu kamar ƙwaya

ƴ/amshi: sai tumoro ala bamu kairin masoya

 A wata waƙar da ake cewa:

jagora: Tama yaro tama galadima wasa ba faɗa ba

 ƴ/amshi: Arerere

 jagora: Ni nawa ɗan maharbi

 ƴ/amshi: ya harbe ki, kuci harbi ku kwana harbi

 gadon gidanku ne, bulala ɗari da hamsin

 ta shafeki, gaba tsudum, baya tsundum

a aljanna,

jagora : wasa ba faɗa ba

ƴ/amshi: arerere.

 

kai tsaye mai sauraron wannan waƙar zai fuskanci cewa ana so ne a bayyana nau'ikan al'adun wasu al'ummomi daban, wato yadda suke gudanar da al'adunsu da kuma al'amuran rayuwarsu. sa'annan kuma ɗaya waƙar na nuna irin saurayin da al'adar Bahaushe ta yarda da aurensa, wato mai sana'a, wannan aka tsara wasan ta wannan sigar.

Wani babban abin lura game da wannan gaɓa shi ne ba ma iya al'amuran da suka shafi wasannin yara kurum ba, hatta da wasannin da manya ke aiwatarwa akan yi su cikin sigar waƙa, yau da kullum kan sa ya riƙa tasiri a zuƙata, don haka wannan ma wani muhimmin tunani ne na Bahaushe a wannan ɓangare.

Bugu da ƙari duka waɗannan abubawa da Bahaushe kan yi game da wannan ɓangare na adabi (Tatsuniyoyi da wasanni) masu ɗauke da hikimomi iri daban-daban yana aiwatar da su ne bisa tunanin fito da wani muhimman al'amari da zai kyautata rayuwarsa da kuma zamantakewarsa ta yau da kullum.

Dan haka yasa aka zaɓo wasu fitattun misalai daga waɗannan rassa domin binciko ire-iren falsafar, wato tunanin, domin ganinsu a zahiri dan a nazarce su tare da gano dalilan sanya su da irin muhimmancinsu a rayuwa. kamar yadda za mu gani a ƙasa.

4.4 TATSUNIYAR GIZO DA ƁAURE

 Tatsuniyar gizo da ɓaure tatsuniya ce ta farko cikin littafi na ɗaya a jerin littattafan guda shida, sa'annan kuma ƙirƙirarriyar tatsuniya ce wadda ta ƙunshi rayuwa da zamantakewar al'umma guri ɗaya, da kuma abinda ya shafi shugabanci a tsakanin al'ummar, haka kuma tana ƙunshe da al'adu daban -daban.

 Babban maƙasudin zaɓar wannan tatsuniya a wannan binciken shi ne a gano irin hikmomi da tunani da Bahaushe ya gina a cikinta wadda a taƙaice akan iya kiranta da falsafa.

 Da farko dai Bahaushe ya gina tunaninsa a wurare daban-daban cikin wannan tatsuniyar wadda kai tsaye ba za a iya gano su ba sai ta hanyar zurfaffan nazari, ire-iren wuraren kuwa sun haɗa da zaɓen taurari da sauran abubuwan cikin tatsuniyar misali:

 Idan aka yi duba na tsanaki game da tatsuniyar za a ga cewa tun a farko Bahaushe ya gina tunaninsa wajen zaɓar sarki a matsayin wanda ya mallaki gonar ɓauren. A kowacce al'umma sarki mutum ne mai girma da matsayi har ma kuwa al'ummar Hausawa, baya da haka a bisa al'adar Bahaushe duk wani shugaba akan same shi mutum ne da ba a ƙetare umarninsa ko a yi watsi da hukuncinsa. ba kuma hakan yana nufin isa ba, sai dan ɗaukaka da daraji al'amarin gabaci, dake taka muhimmiyar rawa a al'adunsa.

 Tabbas Bahaushe ya zuba hikimarsa a nan domin bai zaɓo wani mutum daban daga cikin gari ya sanya shi matsayin mamallakin gonar ba, sai ya zaɓi sarki ya sanya domin girman al'amarin da yake son fiddowa.

 Haka kuma idan aka koma aka yi duba ga bishiyar ɓauren ma akwai babbar hikima wajen zaɓarta da Bahaushe ya yi, dalili kuwa shi ne bishiyar ɓaure dai bishiya ce mai daraja sa'annan kuma ba kowa ne zai ga bishiyar ɓaure ya kau da kansa ba, ko da kuwa ace ba aikin tsinkarta zai yi ba, saboda ɓaure abu ne mai zaƙi da ƙamshi da kuma garɗi, kamar yadda aka bayyana a tatsuniayar. Saboda haka wannan ma tunani ne na Bahaushe me kyau, domin kamar yadda tarihi ya nuna ƙasar hausa ƙasa ce mai tarin bishiyoyi da za a iya lissafa nau'ikansu ba, sa'annan akwai kayayyakiin amfanin gona kamar hatsi da sauransu, duka kowanne ana iya gina tatsuniyar a kansa, amma duka bai yi amfani da waɗannan ba sai ya ɗauko bishiyar ɓaure, saboda zaƙinta da ƙamshi, da kuma darajarta a idon al'umma Musamman yara.

A ɗaya ɓangaren kuma idan aka duba alƙawarin da sarki ya yi ga wanda ya amince da buƙatarsa da ya zo da ita , tabbas a nan ma ya yi amfani da tunani da hikima, domin kuwa idan aka duba a tarihin rayuwa da zamntakewar Bahaushe da yadda ya ƙarfafi al'amuransa za mu ga cewa a koyaushe sarki mai iya bada umarni ne ga kownne irin abu ba tare da ya biya lada ba , kai tsaye yana iya sawa a yi wannan aikin tare da gindaya irin wannan sharaɗin (babu wanda zai sha har ya gama) saboda girman shugabancinsa da kuma matsayinsa a wurin waɗanda yake mulka. kenan wannan gaɓar ma Bahaushe ya yi amfani da tunanin yin alƙawarin lada game da aikin da za a gabatar .

Haka kuma a wajen da sarki ya tara mutanen gari domin isar ga buƙatarsa, babu wanda ya amshi wannan buƙatar sai Gizo, kuma kaf cikin mutanen garin Gizo ne kaɗai wanda za a iya iya siffanta shi da wanda ba mutum ba, kamar yadda aka gani a hoton da aka zana ƙirƙirarriyar halitta ce . A nan tunanin Bahaushe ya fito kan cewa al'ummar Hausawa mutane ne masu tsananin tsoron amana, domin al'ada ce mai ƙarfi cikin kyawawan halayen Bahaushe, wannan ya sa kowa ya ƙi karɓa sai shi gizon a yayin da muka ga gizo dai ba za a kirashi da mutum kai tsaye ba. Don haka wannan ma wata hikima ce da Bahaushe ya yi amfani da ita cikin tatsuniyar.

Da gizo ya gama tsinke ɓauren aka kwashe, sa'annan aka cika masa alƙawarinsa (Bashi amarya da gararta) kafin a kai ga tafiya tsuntsuwa ta zo ta fallasa asirin gizo tahanyar bayyana abinda ya yi da waƙa.

To a wannan gaɓar kowa ya san cewa dai babu wani tsuntsu a duniya da yake magana bare har ya fahimci wani abu ya rera shi cikin waƙa ya kuma furta, kamar yadda masana suka bayyana ɗaya daga cikin abubuwan da suka bambanta ɗan Adam da dabbobi shi ne hankali da tunani, kuma abinda tsuntsuwa ta yi a wannan muhalli aiki ne na mai hankali da kuma tunani.

Bahaushe ya gina tunaninsa mai kyau a nan, wajen tabbatar da cewa duk abinda mutum ke aikatawa a ɓoye ko a fili ko da babu kowa to Allah mahalicci yana kallonka, kuma duk abinda aka aikata cikin rashin gaskiya abu ne da ba ya tasiri domin komai daren daɗewa sai gaskiya ta yi halinta ( kamar yadda sarki ya janye alƙawarin da ya yi wa gizo ya tashi a biyu babu , gashi dai ya sha wahalar tsinkewa ɓauren amma kuma buƙatarsa bata biya ba sakamaomakon cin amanar da ya yi ). Wannan ne ya sa Bahaushe yayi amfani da tsuntsuwa a wannan gaɓar domin nusarwa da tarbiyyayntarwa zuwa ga tsarkake zuciya da yin gaskiya tare da yarda da kasantuwar mahalicci tattre da bawa a duk inda ya kasance.

Haka kuma ya yi hikimar zaɓar tsuntsuwa a wannan muhallin ne saboda galibi waɗanda ake bawa labarin tatsuniya yara ne maso tasowa kuma mafi akasarin yara suna da wata ɗabi'a ta son tsuntsaye da ƙaunar su, sa'annan kuma tsuntsu halitta ce da masana suka siffanta shi da ɗabi'ar wayo. Don haka kai tsaye wannan abun zai fi yin tasiri a ƙwaƙwalwarsu.

Baya da waɗannan hikimomi na Bahaushe da aka fito da su a wasu wurare na cikin wannan tatsuniyar, akan iya gano wani wani muhimmin tunanin wadda ya gauraye tun daga farko har ƙarshen tatsuniyar. Tunanin kuwa shi ne ya yi hikimar ƙirƙirar tatsuniyar ne domin nuna illar CIN AMANA, Hakan kuma hikima ce ta koyar da ƴaƴansa ta irin waɗannan hanyoyi kamar yadda aka bayyana a baya cewa "Tatsuniya ita ce makarantar farko da Bahaushe ya ke ilimantar da ƴaƴansa ".

Don haka kai tsaye ana iya cewa babban tunani/hikima da Bahaushe ya gina cikin wannan tatsuniyar shi ne nusar da yara su guji CIN AMANA , a falsafance wadda idan kuma aka koma a fannin adabi, manazarta da masana adabi a fagen nazari za su kira wannan tunani da Jigo/manufa, wato saƙon da tatsuniyar ke ɗauke shi.

4.5 TATSUNIYAR ƊAN SARKI YA ZAMA MACIJI

 Wannan tatsuniyar na ƙunshe da abubuwa daban-daban na zamantakewar rayuwa, domin kuwa an gina tatsuniyar ne akan zuri'ar wani mutum da yake neman haihuwa saboda ba shida ɗa ko ɗaya, sa'annan kuma matansa guda uku ne, wadda kuma kowacce a cikinsu tana buƙatar haihuwar.

 Haƙiƙa wannan tatsuniyar akwai hikimomi a wurare da dama da Bahaushe ya gina, wadda idan ba a zurfafa tunani ba za a kalle su a matsayin tunani ne mai kyau a wannan gaɓar ba, misali:

 An nuna cewa mutumin na da mata har guda uku, sai dai kaf cikinsu akwai guda ɗaya wadda ita ba ya sonta, hasali ma da ya karɓo maganin haihuwar iya matan da yake so ya bawa, amma banda ita.

 Ba za a fahimci cewa hikima ce mai kyau a wannan gaɓar ba, sai an waiwaya zuwa ga ire-iren waɗannan tatsuniyoyi, wadda ƙarara ake bayyana fifikon soyayyar mace ɗaya ita kuma ɗayar a nuna ƙiyayya a kanta ƙarara. Kamar tarsuniyar Ruwan bagaja, Daskin- da- riɗi, da sauransu. Bahaushe na da tunnnin yin amfani wannan gaɓar domin nuna illar wani abu, ko kuma muhimmancinsa, domin idan aka duba al'ada ce mai ƙarfi da ya riƙe, akan sami Bahaushe mai matuƙar kula da iyalansa yadda ya dace ko dan gudun yin abin kunya da zubar da murunci, ko rage martaba a idon mutanen gari. Wannan yasa ko a tarihi ba a fiya samun ire-iren waɗannan halaye ba bisa ga rayuwar Bahaushe ta zahiri, sai dai ya ƙirƙire su cikin adabinsa, da nufiin fito da wani abu fili ko kuma nusarwa zuwa ga wani abu muhimmi ,misali; Tatsuniyar Daskin- da- riɗi, da ta ɗan sarkin agadas, da kuma tatsuniyar ruwan bagaja da sauransu.

 Haka kuma an bayyana cewa bayan da aka samo magani dukkansu suka sha suka samu ciki suka haihu, har da wadda ba a so wato (bora) sanadiyyar ɗiban ɗan guntun da aka zubar ta sha har aka haifi ƴaƴa duka mata, lokacin aurar da su ya yi, dukansu ya bada su ga waɗanda yake so, ita kuma gwi-da-yara (ɗiyar bora) ya kaita jeji saboda ƙiayayyar da yake wa mahaifiyarta ta shafe ta, ya haɗa da maciji a matsayin wadda za ta yi rayuwa da shi, haka kuma tayi biyayya, daga ƙarshe miciji da mutum ne kuma ɗan sarki, da aka bayyana cewa sai ya zama maciji da ya samu matar aure.

 Awannan gaɓar kai tsaye za a iya kallon wannan a matsayin hikima ce mai kyau, domin kuwa ɗan sarki mutum ne mai ƙima wadda kuma ya kasance abin so ga kowacce yarinya, amma sai aka nuna cewa ya rasa matar aure . An yi hikimar amfani da ɗan sarki a wannan gaɓar domin tatsuniyar ta karɓu sosai, ma'ana abinda ake son bayyanawa ya karɓu a wurin masu sauraron tatsuniyar, wannan ya sa ba a zaɓo wani saurayin daban cikin tatsuniyar ya zama matsayin wanda ya nemi aure bai samu ba, sai aka ce ɗan sarki, kowa zai ji abin da mamaki, domin kuwa duk kalar matar da ɗan sarki yake son aura , kai tsaye zai samu ba tare da shan wahala ba ko da kuwa ba ta so, saboda girman matsayinsa.

Bugu da ƙari hikimar sanya ɗan sarki ya zama miciji shi ne, kusan dabbobin da aka san su a zahiri. Maciji na ɗaya daga cikin muhimman dabbobi da ake tsoransu, saboda hatsrinsu, wannan yasa Bahaushe ya yi tunanin zaɓar miciji, ta haka ne za a fito da jarumtar yarinyar fili, aka sanya shi matsayin wadda za ta zauna da shi duk da kuwa ire-iren abubuwan tsoratarwa da aka nuna micijin ya yiwa yarinyar ba ta nuna ta tsorata ba.

A ɗaya ɓangaren kuma wata hikimar Bahuashe ta sanya miciji a wannan gaɓar za ta yi tasiri matuƙa ga masu sauraron tatsuniyar, musamman yara da galibi su ake yiwa tatsuniyar, sanya miciji (abin tsoro da firgici) a wannan muhallin zai taimaka wajen kiyaye abinda yake son nusarwa da saurin yin tasiri a zuciyoyinsu.

 Bayan da uban yaran ya shirya kai ziyara gidajen ƴaƴansa domin gano irin halin da kowacce ke ciki, an nuna cewa gidan ta farko da ya je ya samu abinci da miyar ɓera, a nan Bahaushe ya yi amfani da ɓera a matsayin abinci bisa tunanin fasalta irin munin abincin da kuma ƙasƙancinsa, domin kuwa ɓera ba abin arziƙi ba ne, kuma al'ada ba ta ɗauki ɓera a matsayin abu mai daraja da za a ci ba, hasali ma a rayuwar Bahaushe ɓera abu ne da ake ƙyama saboda mummanar ɗabi'arsa ta ɓarna. Haka ɗaya gidan ƴar da ya je ya tarar da tuwon dusa miyar ɗata, duk dai hikimr ɗaya ce a nan da muhallin da aka sanya ɓera, domin ita ma dusa kowa ya san ba cimar mutane ba ce sai dabbobi, amma sai aka gina tunani da yin amfani da dusa a muhallin da kai tsaye zai fito da ƙasƙancin abin da ɗumbin muninsa.

Bayan da uban ya samu labarin gidan gwida- yara a wurin ƴan matan har ta bada umarnin a kai shi jikin tagar gidan, ta wullo masa kaya masu kyau ya saka. A wannan gaɓar an yi amfani da tunani domin an nuna cewa wullo kayan da tayi maimakon ta ba shi a gidan, amma saboda kar mahaifinta ya ƙasƙanta sai ba a nuna ya shiga gidan ba sakamon yanayin matsayin gidan da kuma irin shigar da ke jikinsa.

Haka kuma bayan ya koma gida ya ba wa kowacce tsarabar ƴarta ta bayar an nuna da aka aikawa ƴaƴan su zo an sake nuna ɗaya daga ciki ta kawo babbakakkun ɓeraye duka waɗannan abubuwa ne da Bahaushe ya sanya tunanisa wajen saka su a cikin wannan tatsuniyar. A ɗaya ɓangaren kuma idan aka kalli tatsuniyar gaba ɗaya a tsanaki, akwai manyan hikimomi da suka game tatsuniyar ta fuskar saƙon da take ɗauke da shi ; kamar muahallin da ake ƙuntatawa uwar gwi-da-yara, har ta kai da an raba ta da ƴarta, Bahaushe ya kan yi amfani da irin wannan gaɓar domin nusarwa zuwa ga yin haƙuri a duka al'amuran rayuwa, da kuma biyayya ga aure, kuma haƙurin ya kan zama riba nan gaba (kamar yadda gwi-da-yara da mahaifiyarta suka ci nasara kan haƙurin da suka yi). Har ila yau ya yi amfani da tunani wajen nusarwa ga yiwa iyaye biyayya, wannaan ya sa aka yi amfani da gwi-da -yara, ba ta wulaƙanta mahaifinta ba lokacin da ya iske muhallinta da ta ke ciki. Sannan akwai hikimar nusarwa ga cewa babu wani abu da zaka nun ka fi ƙarfinsa (girman kai) a duniya komai matsayinka musamman game da manyan al'adun Bahaushe kamar Aure, wadda kuma al'amari ne da babu mai iya yin san rai game da shi sai wanda ya halicce shi, wannan ne yasa Bahaushe ya yi hikimar sanya ɗansarki a wannan tatsuniyar a matsayin wanda ya rasa matar aure, saboda al'umma na kallon jinin sarauta ya fi ƙarfin komai saboda matsayin mahaifinsa.

 Waɗannan hikimomi su ne suka haɗu suka samar da muhimmin saƙon da ake nufin isarwa, su ake kira falsafa wato tunani, ta hanyar amfani da falsafa ne saƙon ya ke fitowa sosai da sosai, su kuma manazarta adabi a fagen nazari suke nazarin saƙon tatsuniyar kai tsaye , kamar yadda sauka kira shi da jigo, misali, a ɓangaren adabi wannan tatsuniyar za a bayyana cewa tana ɗauke da jigon Haƙuri ne, kamar yadda Bahaushe ke cewa "mai hauri yana tare da riba" akwai kuma ƙananan jigogi da suka haɗa da wahala, ƙiyayya, da na sani da sauransu.

4.6 TATSUNIYAR NA-GOMA

 Tatsuniyar na-goma tatsuniya ce da aka gina ta game da wani maharbi da ƴaƴansa guda goma, wadda kuma tunanin Bahaushe ya game ciki da wajen tatsuniyar.

 Idan aka lura da kyau za a ga cewa, an faɗi wani maharbi da kuma ƴaƴansa goma duk maza, kullum ya je farauta ya samo tsuntsu sai ya neme shi ya rasa, ashe ɗansa ne na ƙarshe ke ɗauke tsuntsun ya gasa ya cinye ba a sani ba , har ta kai ga uban ya gajiya ya yanke hukuncin a tafi kogin rantsuwa domin a gano wanda yake cinye tsuntsun.

 A wannan gaɓar tatsuniyar ana iya hango hikimar Bahaushe, dalili kuwa shi ne an nuna cewa ƴaƴan wannan maharbi duka maza ne ba mata kuma sannan kaf cikin ƴaƴan nan babu wanda yake aikata wannan laifin sai ɗan karaminsa (Ɗan auta), to a nan za a iya cewa me yasa ƙaramin ciki ne ya kasance mai laifin?, Amsar anan ita ce Bahaushe ya yi ƙoƙarin bayyana wata al'ada tasa, a bisa tsarin zamantakewarsa, soyayyar ƴaƴa ba ta ɗaya daga cikin abinda yake fifitawa a rayuwarsa musmman ƴaƴan fari (manyan ƴaƴa) duk wata walwala da iyaye ke yi da ƴaƴansu sai dai ka tarar ƴaƴan nan ba na fari ba ne, haka kuma duk abinda yaro ya aikata ba daidai ba a fasa yi masa hukunci komai ƙanƙntarsa domin gyaran gaba, kuma komai ƙanƙantar laifin (kamar laifin na goma na cinye tsuntsu a wannan tatsuniyar bai kai ga yin wannan hukuncin ba, domin kowa yasan in kogi ya cinye mutum zai yi wahala ya yi rai) amma Bahaushe ya yi amfani da wannan gaɓar domin cimma manufar saƙon da yake son isarwa, sa'annan kuma a wannan muhalin Bahaushe ya yi la'akari da cewa masu sauraron tatsuniyar duk yara ne ƙana ba manya ba, wannan yasa ya tsara hikimar sanya ɗan ƙaramin ciki ya kasance mai aikata laifi, domin ya kasance labarni tatsuniyar ya yi daidai da tunani da kuma matsayin masu sauraronta

 Haka kuma akwai wani muhimmin tunani na Bahaushe da ya yi wajen fito da tasirin wasu abubuwan halitta da suke alaƙanta su ko danganta su da da wata buƙata ta musamman zuwa gare su, (kamar rantsuwar da aka yi wa kogi). Sa'annan ya nuna cewa bakin kogi dai wuri ne na iskoki ke zaune (muhallin iskoki ne) kamar yadda ya nuna cewa da ruwa ya tafi da na -goma har ya kai shi bakin kogi anan ya haɗu da dodanniya ta nemi cinye shi bayan ya bayyana mata duk abinda ya yi sanadiyar zuwansa wannan wurin da a baya bai faɗa ba.

 A tsakanin zaman dodanniya da na-goma akwai hikima saboda a tarihi babu wata halitta wai ita dodo, Bunza (1986), ga waɗanda kuwa suka yarda da akwai shi suna nuna cewa dodo da mutum ba sa zama inuwa ɗaya, dan kuwa mutum abincin dodo ne, haka kuma duk wasu dangogin abincin mutane ba sa ci sai dai na su na daban, amma a tatsuniyar nan sai dodo bai cinye na-goma ba har ma ta kan fita gari domin nema masa na sa abincin ta kuma cigaba da yi masa abin siyarwa (ƙosai) yana shiga gari yana siyar mata amma bai taɓa neman gidansu domin ya gudu ba, har Allah ya sa ya haɗu da ƴan'uwansa, suka kuma yiwa dodanniya goma ta arziƙi suka fanshi ɗan uwansu. Wannan ya nuna cewa ana samun kyakkyawar alaƙa da fahimtar juna tsakanin waɗansu jinsin halittu da mutane, musamman ma iskokai kamar yadda zamantakewarsu ta maguzanci har bautarsu suke yi. wannan yasa Bahaushe ya yi hikimar tsara wannan, domin kuwa da ruwan ya tafi da na goma ya cinye shi za a iya iske shi a bakin kogi in dodanni suka gani su cinye shi. A ɗaya ɓangaren kuma an yi amfani da dodo ne domin tsoratarwa da nusarwa ga barin halin da bai dace ba ga yaro, wannan yasa ake horar da su tun da fari.

4.7 WASANNIN KA-CICI-KA-CICI

 A Ƙamusun Hausa Na Jami'ar Bayero, Kano (2006), an bayyana kacici-kacici da: “Zaɓi ko kintata” Amma dangane da asalin Kalmar ka -cici-ka-cici kuwa, Yahaya (1991: 27) ya bayyana cewa:

 “Kalmar ka-cici-ka-cici tana da ma'ana kashi biyu masu alaƙa da juna. Da fari ya nuna an samo asalinta ne daga kalmar 'cinta', wato kintaci faɗi. Ya fito da haka ta nuna yadda yara sukan yi wasa a inda ɗaya zai rufe wani abu a hannunsa ya buƙaci ɗayan ya cinta, wato ya yi kintaci-faɗin abun da yake a hannunsa. A kan haka, Almajir, (2013: 4) ya bayyana cewa, wannan wasa da yara suke yi tsakanin junansu shi ne ya gina wannan wasa ta kacici-kacici wanda ake yi da tunani da siffanta wasu abubuwa. Sannan akan yi ta ga yara cikin wata irin Hausa mai zuzzurfar ma'ana

 Wasan ka-cici-ka-cici wani ɓangare ne na adabin baka, wasa ne da ya shafi yara da Hausawa suka ƙirƙire shi wanda yake tafiyar da cigaban rayuwarsu da kuma inganta zamantakewarsu. Wasanni ne masu ɗauke da ɗumbin hikima da kuma tunani na malam Bahaushe, irin waɗannan tambayoyi sun ƙunshi siffantawa ne na wani abu, da za a juya kamanninsa na yadda aka san shi, ta yadda mutum zai gano shi ne ta hanyar ɗan gajeren tunani, kafin gano abinda ake nufi.misali:

v  Makaranta a dokar daji (gidan tururuwa)

v  Shanu na dubu maɗaurinsu ɗaya (Tsintsiya)

v  Fai-fai na ɗinkin marido (Zuma)

v  Ƴar baƙa jakar mata (kujera)

v  Samarin gidanmu masu fararen kawuna (Taɓare)

 Waɗannan misalan idan aka lura dukkansu an gina su ne ta hanyar siffanta kamanninsu ko abubuwan da suke yi, wato a nan Bahaushe ya yi tunanin sarrafa tambayar ta hanyar siffantawa dan a samar da amsar abin daidai yadda yake. Irin wannan ta kan zo ne kamar sauran zantuka ko bayanai waɗanda idan mutum ya yi zai iya gane ma'anarsu, amma maimakon a bar su haka a fili, sai a kan yi dabara a ɗan ɓoye su don ruɗa mutum. ko kuma a yin tunanin amfani da sauti ko aikin da abun yake wajen tambayar domin gano kaifin basirarsu wajen ba da amsar, misali:

v  Daga nesa na jiyo muryar ƙawata (Ganga)

v  Rub-rub kushewar bayi (ƙaiƙayi)

 A ƙasar Hausa an rungumi kacici-kacici a matsayin wata hanya ta sanya shaƙuwa tsakanin al'umma. Kacici-kacici na sanya kaifin basira da kuma iya fahimtar maganganun na gaba da shi. Sannan yana zama wani rumbu da ke adana kalmomin al'umma. Yana kuma sanya raha da annushuwa ga waɗanda suke yin sa.

 Haƙiƙa wannan nau'in wasan cike yake da ɗumbin hikima da tunani kan irin abubuwan da ake gina wasan, da su ka ƙunshi abubuwa na rayuwa iri daban-daban, Hausawa na cewa "idan yau kai ne, gobe ba kai ba ne sai wani" idan yau ka san duk wasu abubuwan rayuwa, sunayensu da siffofinsu gaba ba lallai masu tasowa su sansu ba, wannan ya sa Bahaushe ya yi tunanin sarrafa wannan hikima ta hanyar sassauya abubuwan rayuwarsu ta yau da kullum, ta sigar wasa, domin na baya su taso da ilimin saninsu, duk wanda ya san amsar sai ya faɗa wanda kuma bai sani ba ya kan ce ya ba da gari. Wannan kansa yana nuni ne zuwa ga babban abu na rayuwar ɗan Adam, wanda mutanen duniya gabaki ɗaya suka yi amanna da shi, shi ko wannan abu ba wani abu ba ne da ya wuce horo, shi mai gabatar da ka-cici-ka-cicin na yin horo ne, ta hanyar biɗar a bashi gari, wannan wani horo ne da tun mutum yana yaro yake amanna da shi.

 A ɓangaren Kalmomin da ake amfani da su airin waɗannan wasan, wata babbar hikima ce, domin ma'adana ce ta ajiye kalmomi waɗanda sai dai tatsuniyoyin kaɗai ko wasannin za a iske su, misali:

v  Ƙulun ƙulufita.

v  Shirin ba ci ba.

v  Ta ƙanda ba ƙashi ba.

v  Kurkucif kucif. Dss

            Duka waɗannan kalmomi ne da ba a riskar su cikin zantuka yau da kullum, domin ba kalmomi ne da ma'anarsu ta ke a fili ba galibi sai dai cikin tatsuniyoyin da kumma ire-iren waɗannan ake samun su domin ƙarawa harshe daraja da ƙaimi, sa'annan waɗannan kalmomi da ake yi wata hikima ce ta gyaran zance ya yi daɗi da kuma saurin fahimta da daɗaɗa zancen.

 Akwai kuma tunanin fito da hikima da baiwar ubangiji ga halittunsa masu ɗauke da abubuwan mamaki game da su. Bahaushe tun kafin ya karɓi musulunci ya yi imani da yarda da abubuwan da ya tarar a duniya kamar Rana, Wata,Taurari,Duwatsu, Itatuwa, Tsirrai, da kuma ƙwari, wannan dalili ya ba shi damar ɗaukarsu a matsayin ababen bautarsa domin neman biyan buƙatunsa na yau da kullum. A irin waɗannan abubuwa Bahaushe ya yi tunanin nusar da ƴaƴansa su san waɗannan abubuwa da kuma nuna irin hikimomin dake tattare da su, komai ƙanƙantarsu, kuma komai girmansu, da yadda suka kasance ababen amfani ga rayuwarsu. misali:

v  Gaya ɗaya dama duniya/ Farin wuri dama kogi (Farin wata)

v  Abu siriri abu sarara abu tufkar Allah. (Gashi)

v  Kututture uku gagara ɗauri (ƙwai)

v  Mace da miji sun haifi ƴaƴansu iyaka

            A nan ana nufin Rana da wata da kuma taurari, waɗannan abubuwa ne da ubangiji ya halitta, masu ban mamaki da muhimmanci ga rayuwar ɗan Adam. Idan aka kalli yadda farin wata ya ke,. ga shi dai abu ne ga yadda muke kallona a zahiri ɗan ƙarami, amma ya yin da dare ya yi shi kaɗai ya isa haska ko'ina a duniya baki ɗaya, wannan wani babban abin al'ajabi ne da hikima tattare da halittar wata, haka ma gashi, shi ma dai dubi yadda yake kusan babu wani bawa da ya isa ƙirga adadin zirin gashin da ke jikinsa, amma dubi yadda Allah ya halicce shi, siriri abin ban mamaki, haka sauran abubuwan da ba za ƙirgu ba cikin halittun ubangiji irin su ƙwai duk cike suke da abubuwan ban mamaki .

Bugu da ƙari wani tunanin na Bahaushe da yake cikin wannan wasan shi ne yadda ya riƙa gina muhimman al'adunsa da ya gada tun kaka da kakanni, da kuma kwatanta wasu manyan al'adun nasa da irin kusanci da kayakkawar alaƙa da suke da shi da addini, misali:

“Abu uku ya yi kama da abu uku, abu uku ya zo ya hana"

 Amsar wannan gaɓa ta ka-cici-ka-cici ita ce, na ɗaya -Aure ya yi kama da bauta, ƴanci ya zo ya hana. Na biyu barci ya yi kama da mutuwa, numfashi ya zo ya hana. Na uku zabuwa ta yi kama da saƙi amma tozo ya zo ya hana. Aure muhimmin abu ne da ɗan Adam ke aiwatarwa, bauta kuwa kowa ƙinta yake, ƴanci kuma abu ne da kowa ya ke son sa , shi kuwa barci abu ne da yai yi kama mutuwa amma kuma shi numfashi kan sanya ran mutum ya dawo yadda ya ke.

 Wani babban misalin a nan shi ne gaɓar da ake cewa:

* Yadda ɗillin ta kan yi ɗillin haka ma ɗillin ta kan yi ɗillin"

 A nan kai tsaye an saka mai bada amsa cikin ruɗu, domin zai kutsa ne tunanin gano wane abu ne wannan, yakan samar da abu sannan abun ya samar da shi, sai kuma ka gano cewa a ga kaza ai ita take yin ƙwai, haka kuma kwai ne yake zama kaza, to da zarar wannan tunnnin ya zo maka amsar ta hau daidai da tambayar, wadda bayan ita ma akan iya samun wasu abubuwan masu kama da hakan.

 Irin waɗannan dabarun da hikimomin su suka gauraye wannan wasan suna da yawan gaske

4.8 WASANNIN ƁATA

 Wasannin ɓata wasu nau'ikan wasanni ne da yara ke aiwatarwa alokuta daban-daban domin motsa jikinsu da kuma samar da nishaɗi. Irin waɗannan wasannin yara maza zalla ke yinsa, wasanni ne da ake da tsalle-tsalle da kuma guje-guje a tsakanin yaran ta hanyar rera waƙoƙi iri-iri.

 Haƙiƙa wasannin ɓata cike suke da hikimomi da tunanin Bahaushe, domin kuwa ba haka kurum suke rera waƙoƙinba akwai abubuwa da yakan tsara cikinsu bisa wani keɓantaccen tunani na musamman, haka kuma waje tsarin wasan nan ma wasu tarin hikimomi ne da da cusa domin fito da wata manufa ta musamman da ke da nufin fiddowa alal misali, idan aka ɗauki wasan Ɗan akuyana.

 Da farko idan aka yiwa wasan kallo na tsanaki za a ga cewa, wasa ne da ya ƙunshi doka da kuma hukunci game da wata ɓarna, Bahaushe na da tunanin nuna wa ƴaƴansa muni da kuma illar ɗaukar abin wani da kuma yadda al'adarsa ta yi tir da Allah wadai da irin wannan ɗabi'a, wannan yasa wasan ɗan akuya na ya siffanta duk yanayi da halin da mai irin wannan halin ke tsintar kansa a yayin da ya aikata irin ɓarnar, sai ya yi hikimar tsara wasan da tunanin juya al'amarin kan wata halittar da ba mutum ba wato dabba (Ɗan Akuya) kasancewar al'amarin ba abin so ba ne, Sa'annan kuma gurin da ya shiga rumbu ne, sai aka siffanta shi da haɗa hannaye da yaran suka yi wato ƙawanya, domin kowa ya san abincin dabba dai ba ya wace hatsi, kuma sannan duk abinda aka sanya shi bisa rumbu abu ne da aka killace shi wuri guda, don haka kai tsaye an san ba gurin ajiyar abincin dabbobi ba ne.

A ɗaya ɓangaren kuma cikin waƙar sai aka bayyana cewa waɗanda suka ritsa mai lefin dukkaninsu suna ɗauke da munanan makamai na illata shi, ya yinda shi kuwa yake ƙoƙarin samun wata ƴar hanya da zai gudu domin ya tseratar da kansa daga azabar da suke shirin yi masa.

 wannan wasa ne kai tsaye da aka yi hikimar tsara shi domin gujewa aikata ɓarna ta ɗaukar hakkin wani da kuma ƙyamatar wannan ɗabi'ar.

4.10 NAƊEWA

Tabbas in ka ga wane ba banza ba, haƙiƙa al'ummar Hausawa ba kanwar lasa ba ne a fagen tunani game da al'amuransu, domin tun kafin a haifi uwar mai sabulu balbela take da farin gashinta" tun kafin cuɗanyar Bahaushe da baƙin al'ummu yake da wayewarsa ta fuskar kyautata zamantakewa da amfani da kaifin tunani da basira ga duka lamuransa. haƙiƙa ko ba a ce komai ba wannan babin ya fayyace tsaki da tsakuwa, gama kuwa an binciko tare da zaƙulo wannan baiwa ta bahaushe wato falsafa, a cikin waɗannan muhimman ɓangarori, in da aka zayyane duk wani tunani da hikima da ke cikin littafin tatsuniyoyi da wasanni guda shida da aka ambata a farfajiyar binciken, tunanin bahaushe ya fito da abubuwa da dama da kusan za a iya cewa babu su a a yau , kamar wajen zaɓen taurari al'amuran da ke cikinsu,wurare da muhallin da ake gina su, har ma da irin dangantakar da ke a tsakanin adabi da kuma falsafa ta fuskoki daban-daban.

BABI NA BIYAR

NAƊEWA

5.1 SHIMFIƊA

 A kowanne irin al'amari dole a samu farko da kuma ƙarshe, wannan babin a kodayaushe shi ke tattare duk wasu bayanai da binciken ya ƙunsa waje guda, domin ya samu kammaluwa ta hanyar taƙaitawa da kuma irin muhimman shawarwari daga bakin mai gudanar da aikin da ma irin sakamakon tambayoyin da binciken ya ɗauko bashin amsasu tun a farkon babin, ko kuma gano gaskiyar hasashen da bincken yake ɗauke da dakonsa, a taaice dai a wannan babi ake tattare tsaki da tsakuwa tare da nannaɗe tabarmar nazarin wuri guda domin a kaucewa wuce gona da iri a aikin binciken, wannan dalili ya sa ake yiwa babin laƙabi da kammalwa ko naɗewa.

5.2 TAƘAITAWA

 Wannan bincike an gina shi bisa tsarin babi-babi har guda biyar. Babi na ɗaya ya yi ƙoƙarin fito da manufofi da kuma dalilan wannan bincike a kan tunanin Bahaushe game da tatsuniyoyi da wasannani, haka kuma ya amsa hasashen binciken ta hanyar lura da yadda binciken ya iyakance farfajiyarsa, sannan kuma a babin ne aka zayyano irin muhimmancin da binciken yake da shi, ya zo duk a babi na ɗaya.

Babi na biyu kuwa ya ƙunshi waiwayen ne kan ayyukan da suka gabata, kuma babin ya kasu gida-gida. Yayin da binciken ya zo yin bitar ayyukan da suka gabata, ya yi la’akari da muhimman kalmomi da suka shafi aikin baki ɗaya. Waiwayen ayyukan da suka gabata ya taɓo jiga-jigan kalmomin da suka haɗu suka samar da batun. Wato babin na biyu ya waiwayi wasu ayyuka da suka yi magana a kan Hausa da Hausawa da kuma ƙasar Hausa, baya da haka babin ya yi waiwayen ayyukan da aka gudanar akan falsafa da kuma tunani, babin na biyu ya yi bitar wasu ayyuka a kan Wasanni da Tatsuniyoyi. Bita a kan falsafa ta taɓo wasu batutuwa a kan adabi a Hausa, yayin da wasu ayyukan suka yi maganar falsafar a Musulunci. Waiwaye ya yi tsokaci a kan falsafar Afirka da na mafalsafa a Yammacin duniya.

 Shi kuwa babi na uku ya yi tsokaci a kan hanyoyin tattara bayanai, inda bayanai suka samu ta hanyar manya da kuma ƙananan hanyoyi. Babin ya yi tsokaci a kan ginshiƙin hanayar tattara bayani (babbar hanya) da kuma sauran hanyoyi tattara bayanai.

Binciken ya yi hira da mutane daban-daban a wurare da dama. Mutanen da binciken ya gana da su malamai na jami’a da na addini da maza da mata da matasa da tsofaffi. Bugaggun littafai da kundaye da maƙalu da intanet sun taimaka wajen samun bayanai.

 Babi na huɗu ya nazarci falsafar Bahaushe ne a littafin tatsuniyoyi da wasanni wato muhimman rassan adabin baka na Hausa. Babin ya gwama tunanin da yake cikin ɓangarorin na adabin baka na Hausa da wasu bayanai da bincike ya samo a wuraren da ya ziyarta. Lura da yanayin tunanin/falsafar da abin da wasu bayanai a rubuce suka ce sun taimaka wajen warware bayanai a babi na huɗu. Inda aka gano tunanin Bahaushe a cikin tatsuniyoyi da wasanni ya gauraye gurare da dama, amma hikimomi game da al'amuran rayuwa da zamantakewa shi ne abu na kusa-kusa da ya fi zuwa ran jama’a idan aka yi zancen tunanin nasu. Muhalli da lokaci da kuma taurari suna da alaƙa da irin abubuwan da ake gina tunani kansu cikin waɗannan ɓangarori. Wasu daga cikin rukunin Hausawa da aka yi hira da su sun ce, tunanin Bahaushe a wannan gaɓar yana tafiiya ne da fata da kuma burin zamantowar ƴaƴansa mutumen kirki masu tarbiyya.

Babi na huɗu ya ƙarfafa nazari cikin wasu tatsuniyoyi da wasannin na cikin littattafan, kuma ya kawo ingantattun bayanai masu ɗauke da misalai game da tunanin da yake cikinsu kama daga kan muhallin, taurarin da kuma sauran al'amuran da aka gina su akai.

Binciken ya yi nazari akan tunanin Bahaushe kamar yadda al’ummomi da yawa na Afirka da sauran sassan duniya suke da irin wannan tunani. Bahaushe yana harkokinsa na yau da kullum, kuma adabin baka na Hausa ya nuna tatsuniya tana da tasirin gaske ga al’amuran da suke gudana yau da kullum. Babi na huɗu ya yi tsokaci a kan yadda adabin baka na Hausa yake da dangantaka da tunani/falsafa.

Babin ya yi tsokaci a kan dangantakarsu ta fuskar ma'anarsu, rabe-rabensu, samuwarsu, har ma da bunƙasarsu, musamman yadda suke da muhimmanci a rayuwar Hausawa. Duk da haka babin bai tsaya nan ba sai da ya taɓo dangantakarsu da fuskar ilimi.

5.3 SAKAMAKON BINCIKE

Wannan bincike an gudanar da shi ne a kan adabin baka, ɓangaren ƙagaggun labaran zube da kuma wasanni, a inda aka nazarci falsafar Bahaushe da ke cikin waɗannan ɓangarori a littafin Tatsuniyoyi da Wasanni... na Ibrahim Yaro Yahaya. Tunani na da matuƙar tasiri ga rayuwar alumma musamman saboda sauƙin aiwatar da kyakkyawar rayuwa. Bahaushe na amfani da tunani a duka al'amuransa kama daga maganganu na yau da kullum da waƙa da ƙagaggen labari na zube da kuma wasanninsa, ta yadda za a iya sarrafa harshe a zaɓi kalmomi masu ma’ana da suka dace da saƙon da ake son a isar ga alumma.

 Binciken ya tallafi kansa da wasu misalai daga wasu tatsunitoyi domin dukkansu wasu ginshiƙai ne a wajen samun falsafar rayuwa, musamman dokoki da rayuwar iyali da ilmi da kuma zamantakewa baki ɗaya (Kirk-Greene, 1973:3). Waƙa ta agaza wa binciken da wasu misalai, kasancewar tana adana falsafar al’umma baya ga kasancewarta makarantar da ke koya nagarta da hikimomin rayuwa ga al’umma a gargajiyance (Ahmad, S.B. 1997:13). Dalilan da suka sa aka kawo misalai daga wasu tatsuniyoyin a wasu wurare cikin wannan bincike sun haɗa da: dukan su dai abu ɗaya ne dake ƙunshe da wasu saƙonni da Bahaushe ke da manufar isarwa ga al’umma kamar yadda (ƙaraye, 1995:184) ya tsakuro amfanin adabin baka daga (Malinowski, 1971:19) inda yake adana tunani da al’adu da kuma faɗakar da mutum game da rayuwa.

Wannan binciken ya tabbatar da akwai tunani da falsafa a cikin littafin Tatsuniyoyi da wasanni--domin kuwa an fito da irin hikimomin da Bahaushen ya yi amfani da shi, wato tunanin da ya sanya a wurare daba-daban.

 Binciken ya gano cewa an yi amfani da hikimar zaɓar taurari wajen gina labarin kowacce irin tatsuniya daidai yadda saƙon zai fito fili a fahimce shi. Wannan dalilin yasa tatsuniyar Bahaushe ko da yaushe ke gauraye da nau'ikan halittu daban-daban tun daga mutane, dabbobi a wajen abinda ya shafi tsoratarwa kamar micizai, dodanni, kura. Ko kuma ƙwari, har ma da halittun da ƙirƙirarsu yake bisa kyakkyawan tunani, don ya zama mai armashi da kuma sauƙin ganewa. Su kuwa wasanni na ɗauke da hikimar aiwatarwa ta hanyar amfani da jinsin da abin ya shafa, ko kuma adadin ƙimar shekarun masu aiwatarwa, wato dai a ɓangaren wasanni Bahaushe kan yi amfani da wannan karin maganar da ke cewa "kowacce ƙwarya da abokin burminta".

 Binciken ya gano cewa hikimar ba ta tsaya kan iya taurari ba, domin kuwa duk wasu al'amura da suka shafi rayuwarsa ya kan tsara hikima ta musamman ya juya ta ko ya gina ta hanyar amfani da yadda yake a zahiri da kuma amfani da muhallin da ya dace da tsarin tatsuniyar ko wasan, domin cimma manufar da burin da ya sa shi yin ta, kamar abinda ya shafi rayuwar aure, maƙwabtaka, amana, gaskiya, cima ta abinci da sutura da sauransu.

Wani babban al'amari da binciken ya gano shi ne Bahaushe na amfani da sanya waƙa cikin dukka waɗannan ɓangarori domin saurin karɓuwar abin, kasancewar masu sauraron tatsuniyar galibi yara ne, waƙa za ta yin tasiri wajen saurin jawo hankulansu zuwa ga fahimtar muhimmancin abin, haka kuma wasanninsa kaf na ɗauke da waƙe-waƙe da ke taimakawa masu aiwatarwa wajen sanya su nishaɗi a junansu da ƙara musu ƙaimi wajen ɗarsuwar saƙonnin da waƙar ke ɗauke da shi cikin zuƙatansu, idan an dubi duka tatsuniyoyin da wasannin da aka nazarta babu wadda babu waƙa a cikinta, wannan ita ma wata hikima ce cikin ɗumbin hikimomin malam Bahaushe a wannan ɓangaren.

Wani babban al'amari da binciken ya ƙara gano wa shi ne, Bahaushe na sanya waɗannan hikimomin ne da tunani domin inganta tarbiyyar yara da kyautata rayuwarsu, ta hanyar nusar da su abubwa masu kyau da kuma marasa kyau, wannan yasa ake kiran waɗannan ɓangarori da makararanta ce ta farko a gurin ƴaƴan Hausawa, domin duka suna aukuwa ne ta irin hanyar da ake aiwatar da makarantu a yanzu. Don haka tun kafin haɗuwarsa da baƙin al'ummu ya ke da tsarin karantarwarsa.

Wannan bincike ya kai ga fahimtar ko gano cewa Wasannin gargajiya da tatsuniyoyi suna da matuƙar amfani musamman ta ɓangaren motsa jiki da kuma kaifafa tunani, wannan yasa galibi ƴaƴan Hausawa ke tasowa da hazaƙa da kaifin basira, sannan kuma ga ƙarfafa danƙon zumunci a tsakanin yaran ta yadda akan samu shaƙuwa mai ƙarfi har akai ga matakin tsufa, wata shaƙuwar ma mutuwa kaɗai ke iya raba ta.

Binciken ya fahimci cewa falsafar da Bahaushe ya riƙa cusawa cikin adabinsa ta yi tasiri matuƙa da kuma kasancewa abar al'fahari ka duk wani Bahaushe, domin kuwa duk irin abubuwan da yake fata game da ƴaƴansa ya samu, a iya cewa kusan duk inda ake ambaton tarbiyya da kyakkaywar mu'amala da zamntakewar rayuwa to al'ummar Hausawa ce kan gaba, don haka wannan nasara ce babba.

Babban abinda binciken ya fahimta game wannan al'amari shi ne, Bahaushe na so da kuma fatan ganin ƴaƴansa sun zama na gari,Alhaji Ɗahiru Musa Jahun yana cewa:

"Yaro kamar makaho ne,

Shi babba ai majayi ne,

Don haka neyasa shi ƙirƙirar irin waɗannan muhimman hanyoyin domin fatan ganin al'ummarsa ta kasance ta gari.

5.4 SHAWARWARI

 A fage na shawarwari lallai ko shakka babu wannan binciken an samar da wasu muhimman bayanai da za su taimaka wa al’umma.

Wannan bincike na ƙalubalantar al’umma musamman a irin wannan zamani da ilimi ya yawaita, a da lokacin da ilimin bai yawaita ba, al’umma sun riƙa amfani da tatsuniya musamman ta kallon wasu halayen taurari, suka riƙa koyar da yayansu kuma aka sami nagartaciyar alumma, saɓanin yanzu. Saboda haka ya kamata waɗannan halaye na taurari a tatsuniya su zama darasi ga al’umma.

 Manazarta sun gudanar da bincike-bincike a Hausa a fagage daban-daban, an wallafa littafai da ƙamusoshi da kundayen digiri masu yawan gaske da Hausa ko a kan Hausa. Yawancin manazarta sun bibiyi Hausa ta fuskar nazarin harshe da adabi da kuma al’adu. A iya cewa har yanzu manazarta ba su yi barci ba, duk da yake wasu suna ƙorafin kamar an bar Hausa a baya. Domin an gudanar da bincike-bincike na falsafa da sauran sassan ilmi a wasu harsunan Nijeriya da Afirka, amma ba a gudanar da irinsu a Hausa ba. Wannan ba zai sanya a ce nazarin Hausa yana baya-baya ba, sai daɗa bunƙasa da yake yi a ƙarni na ashirin da ɗaya. Hausa tana gogayya da manyan harsunan duniya a fagage daban-daban, tana gaba a harsunan Afirka, tana sahun gaba idan ana batun harsuna da ake yaɗa labaru da rubutu a ciki da wajen Afirka. Hausawa da masu sha’awar Hausa suna ƙoƙarin ganin Hausa ta ci gaba da gwagwarmaya kamar yadda ta saba.

 Tabbas wannan bincike yana ba manazarta Hausa shawara su daɗa zage dantse wajen cigaba da nazartar rassan adabi, domin tantance ɗimbin basirar Hausawa. Idan ɗalibai da manazarta Hausa suka ƙara ƙaimi a wannan ƙarni, babu shakka za su daɗa faɗaɗa bincike a kan falsafa ta fuskoki daban-daban. Nan gaba kaɗan za su ƙara tabbatar da dangantakar da take tsakanin adabi da harshe da ta harshe da adabi ko ta adabi da duniya da ta duniya da adabi, ko dangantakar adabi da fasihi da ta fasihi da adabi, da ta adabi da makaranci da ta makaranci da adabi da kuma dangantakar adabi da sauran matanoni da ta sauran matanoni da adabi. Idan manazarta adabin Hausa za su ƙara jurewa a irin wannan bincike, babu makawa Ilmi zai ƙara inganta, basira za ta ƙara bunƙasa, kuma ana fata rayuwa za ta ƙara inganci.

 Irin waɗannan bincike-bincike da makamantansu za su ƙara ƙarfafa gwiwar ɗalibai da mahukunta, su ƙara kutsawa fagen tunanin alumma domin su gano yanayin harshe da adabi da kuma dangantakarsu da falsafa. Zuzzurfan tunani ruhin duk wani nazari ne ko rayuwa baki ɗaya, musamman idan aka ƙara lura da dangantakar falsafar da adabin da komai na rayuwa, baya ga martabar Hausa a Afirka ta Yamma da duniya baki ɗaya.Idan manazarta za su ƙara zage damtse a fagen tunani, da yadda yake da tasiri a cikin adabin Bahaushe. Ɗalibai da masu shaawar Hausa za su ƙara gane aladun Hausawa fiye da yadda aka fahimci Hausa a jiya da shekaranjiya. Idan manazarta suka karkato da nazari ta wannan fuska, za a ci gaba da sake sabunta fahimtar yadda za a nazarci adabin alumma domin tafiya da wannan zamani.

 Akwai buƙatar Idan jamioi da sassan nazarin harsuna da aladu za su ci gaba da ƙalubalantar ɗalibai su riƙa ɗaukar waɗansu kwasa-kwasai da suka shafi tunanin Bahaushe, wannan wata hanya ce da za ta ƙara ƙarfafa gwiwar ɗalibai da tunaninsu a kan rayuwar, da yadda za su kwatanta adabin (yin bincike) za su dubi tunanin ta fuskoki daban-daban. Wannan bincike yana ba masu sha’awar faɗaɗa bincike a kan falsafa shawara, suna iya yin nazarin falsafa dangane da rayuwar Bahaushe, ba tare da sun danganta aikinsu da adabin baka na Hausa ba ko rubutaccen adabin Hausa ba. Nazarin falsafar Bahaushe zai iya taƙaita kansa a aladunsu ko kuma a yi nazarin tunanin ta laakari da Harshensu na yau da kullum. Idan kuma ana da bukata za a iya ƙara yin nazarin daga wani ɓangare na adabi kamar yadda wannan bincike ya gudana.

 Haka kuma wannan bincike yana bayar da shawara ga manazarta da su yi nazari a kan tunanin Bahaushe game da rassan na adabi. Bincike yana bayar da shawara ga masu bincike na gaba su ɗora daga inda wannan ya tsaya, musamman abin da ya shafi sauran dangogin tatsunya, kamar su hikaya almara da sauransu. Bugu da ƙari masu bincike za su iya nazartar sauye-sauyen da tunanin Bahaushe ya samu a yau, game da tatsuniyoyi da kuma wasannin da ake ƙirira a aiwatar a wannan zamani.

5.5 KAMMALAWA

Wannan bincike ya yi ƙoƙarin amsa hasashen da binciken ya yi, kuma ya tabbatar da manufa da kuma dalilan bincike, inda adabi da al’ada suka yi wa binciken tasirin gaske. Saboda da yawan mutane suna ganin Hausawa ba su yi fice a falsafa irin yadda wasu al’ummomi suka sanu ba a duniya, sai dai hikimarsu da adabinsu na baka ya adana akwai falsafa mai yawa a ciki tun daga al’amuransu na gargajiya da kuma sauyin da baƙin al’adu suka haifar wa rayuwarsu. Adabin baka na Hausa ya zama tsanin hango tunanin Bahaushe a wannan bincike, kuma tatsuniya da sauran nau’o’in adabin baka na Hausa sun cancanci a kafa hujja da su yayin da aka nazarci tunanin al’umma. Dalilin da ya sanya haka kuwa shi ne, salon da adabi ya ƙunsa shi ne yake warware jigon adabi, jigo kuma tunani ne da fasihi ya yi game da yanayin kusan komai na al’ummarsa; a zamantakewarsa, ko wani abu da yake aukuwa a cikinta, Tunani na da yalwatattun ɓangarori a Hausa, wadda kan iya zama kan rayuwarsu da muhallinsu da kuma harshensu kamar yadda misali ya bayyana a babi na huɗu. Don haka wannan binciken ya zaƙulo ire-iren waɗannan hikimomi na Bahaush cikin waɗannan muhimman ɓangarori na adabin baka (Tatsuniyoyi da wasanni).

MANAZARTA

Abraham, R.C. (1977). Dictionary of the Hausa Language. London: Hodder and Stoughton.

Abdurrahman, M.S. (1983). Nazari a kan Tatsuniyoyin Hausa da na Nupanci. Kundin Neman Digiri na Farko. Sakkwato: Sashen Koyar Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Abdurrahman, M. (2006). Nazari a kan Sababbin ƙagaggun Labarun Almara na Hausa.Kundin Neman Digiri Na Farko. Zariya: Sashen Harsunan Nijeriya Da na Afirika, Jami’ar Ahmadu Bello.

Adamu, J.S. (2010). Hikayar Mafari da Ire-irenta a Al’ummar Hausawa. Kano: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Ahmad, R. (2010). Kwatancin Tatsuniyar Hausawa da ta Fulani. Kundin Neman Digiri Na Farko. Zariya: Sashen Harsuna Da Al’adun Afirka, Jami’ar Ahmadu Bello.

Ahmad, Sakina Adamu, (2016) Tunanin Bahaushe a wajen zaɓen ƙwari a matsayin Magani a cikin The Hausa people Language and History: past, present and future. Kaduna: DNLL, Kaduna State University and Garkuwa publishing.

 Ahmad, S.B. (1997). Narrator as Interpreter: Stability and Variation in Hausa Tales.Rudiger Koppe Verlag Koln.

Ahura, T. (2008). Egalitarian Ethos in Tiv Folktales. In G.G. Darah (ed.), Radical Essays on Nigerian Literatures. Abraka: Department of English and Literary Studies, Delta State University, MalthousePress Limited.

Alhassan, H. da wasu (1982). Zaman Hausawa (Bugu na biyu). Lagos: Islamic Publication Bureau.

Aliyu A. H. (1978). Abokin Hira 1. Zaria: Northern Nigerian Publishing Company.

Al-Ghazzali,(1095M) Tahfati al-falsafa. Baghdad .

Alhawani,(1962) Falsafatu al-islamiyya.

Ajayi, J.F A&Crowder, M.(1974&1976) History of west africa. Volume two.

Londo: longman Group limited.

Amin, N. (2010). Littattafan Tatsuniyoyi Na Hausa Na Frank Edg. Muhimmancinsa Wajen Adana Al’adun Hausawa. A cikin Dundaye No, 3, Vol 1. Sakkwato: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya Jami’ar Usmanu Xanfodiyo.

Aminu, M. (1977). Tatsuniyoyi Dominku. Kano: Mainasara Publisher.

Amin,M.L (2007) Gudunmawar Dr. Mamman Shata katsina.

Amin,M.L (2004) Falsafar Bahaushe a kan rayuwar Ɗan'adam cikin Algaita king Journal of Hausa Studies; No: 3 Vol. I Kano: Department of Nigerian Languages, Bayero University.

Ayuba, A. (2018) Bigire a tuananin Bahaushe. Kundin digiri na uku a jami'ar Ahmadu Bello, Zaria.

Balarabe, H. (2001). The Relevance of Teaching Folk-Narrative (Tatsuniya) In Modern Hausa Society. In Faki, A.U. (ed.), Huda-Huda, No. 1, Vol. I Kano: Federal College of Education.

Baro, T.J. (2003). Nazarin Tatsuniya, Kundin Neman Digiri na Farko, Sashen Harsunan Nijeriya Da na Afirika, Jami’ar Ahmadu Bello.

Bello, M. (2004). Jigogin Gargaɗi a Cikin Tatsuniyoyin Hausa. Kundin Neman Digiri na Farko. Sakkwato: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Xanfodiyo.

Bargery, G.P. (1934). A Hausa-English Dictionary and English-Hausa. and is Vocalary. London: Oxford University Press.

Bichi, A.Y. (1995). Hausa Folkgenres. In Rufa’I, et al (ed.), Harsunan Nijeriya, vol xvii, CSNL. Kano: Bayero University.

Bichi, A.Y. (1979). Cultural Reflection in Hausa Folklore. In Yahaya, I.Y. (ed.), Harsunan Nijeriya, Vol. ix, CSNL. Kano: Bayero University.

Dembo,U.(1971) Wasannin yara. zaria: Northan publishing company.

Dumfawa, (1986), Falsafar Malanta.

Ɗangambo, A. (2008) Rabe-raben Adabin Hausa da muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. kano: Amana publishers.

Bichi, A.Y. (2002/2003). A Brief History of Hausa Folklore Scholarship. In Bchi, A.Y.(ed.), Harsunan Nijeriya, Vol. xx, CSNL. Kano: Bayer University.

Bichi, A.Y. (2008). The Type and Motif-Index of Hausa Folktale. In Bichi, A.Y. (ed.), Harsunan Nijeriya, Vol xxi, CSNL. Kano: Bayero University. Narrative A Case Study of Hausa Tatsuniya. Unpublished M.A. Thesis. Kano: Bayero University.

Chamo, Y.I. (2008). Mataki da Hanyoyin Nazarin Tatsuniya. A cikin Gusau, S.M. (ed.), Algaita No.5 vol. i. Journal of Current Research in Hausa Studies. Kano: Jami’ar Bayero.

CNHN (2006). Ƙamusun Hausa Jami’ar Bayero. Kano: Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya.

Xangambo, A. (1978). Dangantakar Labarun Gargajiya da Al’umma, First International Conference on Hausa Language, Literature and Culture. Kano: Bayero University.

Xangambo, A. (1984). Rabe-raben Adabin Hausa da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Kano: Triumph Publication Company.

Xangambo, A. (2008). Rabe-Raben Adabin Hausa (Sabon Tasri). Zaria: Amana Publishers Limited.

Edgar, F. (1911). Littafin Tatsuniyoyin Hausa Littafi na Biyu. London: Frank Cass.

Fatima, Y. (2002). Tatsuniya: The Art of Story Telling in the Hausa Society. B.A in Literature. Zaria: Department of English, A.B.U.

Finnegan, R. (1970). Oral Literature in Africa. London: Oxford University.

Furniss, G. (1996). Prose, Poetry and Popular Culture in Hausa. London:Edingburg University Press

Garba, S.A. (2013). Media and Folklore: Hausa Folktale on the Radio. Kano: Bayero University. (Paper Presented at International Conference Kano).

Galadanci, M.K.M. da Wasu (1993). Hausa Don ƙananan Makarantun Sakandare, littafi Na 3. Lagos: Animo Press.

Gusau, S.M. (1986). Tatsuniya: Sigoginta da Muhimmancinta a Adabin Baka na Hausa. Sakkwato: Kwalejin Ilimi, Maru. (Muƙala wadda ba a buga ba).

Gusau, S.M. (2000). Tatsuniya a Rubuce: Nazarin Sigogi da Hikimomi da Tasirin Tatsuniya, Kano: Gidan Dabino.

Gusau, S.M. (2006). Tatsuniya (Gatana): Sigoginta da Hikimominta. A cikin Gusau, S.M. (ed.), Algaita No.4, vol. 1. Kano: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Hassan, S. (2014). Trickster in Folktale: a Comparative Analysis between Hausa Bura/Babur. Kano: Bayero University, (Paper Presented at Kano).

Hayward, W. F. (n.d). Folklore: Trickster Stories Across Time-From African Ancestors to African American Rappers.

Junaidu, I. da ‘Yar’aduwa, T.M. (2007). Harshe Da Adabin Hausa A Kammale. Ibadan: Spectrum Book Limited.

Ƙaraye, M. (1979). Structural Characteristic of the Gizo in Hausa Folktales, Unpublished M.A. Thesis. University of Khartoum.

Ƙaraye, M. (1982). The Structural Study of African Oral Narrative: Evidence from Hausa. In Yahaya, I.Y. (ed.), Harsunan Nijeriya, xii, CSNL. Kano, Bayero University

Ƙaraye, M. (1997). Trends and Issues in Development Theories and the Place of Folklore in National Development. In Rufa’i, A. (ed.), Harsuna Nijeriya xviii CSNL. Kano: Bayero University.

Ƙaraye, M. (2001). Gizo: A Structural Approach to the Interpretation of the Trickster in Hausa Folktales. In Bichi, A.Y. (ed.), Harsunan Nijeriya, xix, CSNL. Kano: Bayero University.

Ƙaraye, M. (n.d). The Trickster in Folklore and Folklore Scholarship. Kano: Bayero University (Paper Presented at Kano).

Labaran, S.M. (2005). Waƙoƙin Cikin Tatsuniya: Nazari Kan Muhallan Da Masu Rera su, Kundin Nemasn Digiri Na Farko. Sakkwato: Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Mukhtar, I. (2002). Jagoran Nazarin ƙagaggun Labarai (Tsari na Biyu). Kano: Benchmark Publisher Ltd.

Muhammad, M.S.C. (2008.) Hauka A Idon Bahaushe Unpublished M.AThesis. Sakkwato: Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usman Xanfodiyo.

N.I.N.L, (2011). Basic Linguistics for Nigerian Languages, Ore, Yusuf (ed.).

Aba: Shebiotimo Publications.

Nasir, I. (2009). Gabatar Da Katun Na Hausa a Kan Tatsuniyar Gizo da ɓaure, Unpublished M.A. Thesis. Kano: Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

NNPC (1968). Labaru Na Da Da Na Yanzu. Zariya: Northern Nigerian Publishing Company.Pinto, C.F. (n.d). The Animal Trickster-An Essential Character in African Tales. Portugal: School of Education Polytechnic Institute.

Rattray, R.S. (1969). Hausa Folk-lore, Customs, Proverbs, etc. Vol.1, & II London: Oxford University Press.

Rufa’i, A. (1982). Huce Haushin Talaka Kan Basarake Misalai Daga Wasu Tatsuniyoyi. A cikin Yahaya, I.Y. (ed.), Harsunan Nijeriya, xii, CSNL. Kano: Bayero University.

Serekoane, B.B. (1996). Trick, Trickster Characters and Trickster Tales in Tswana Folktales, Unpublished M.A. Degree Rand Afrikaans University.

S.N.E.R.D.C and H.S.A.N, (1990). Hausa Metalanguage D. Muhammed (ed.), vol. i. Ibadan: University Press.

Shimizu, K. and Agabi, B.A (1975). Jukun Oral Literature: An Introduction and a Tale.In Yahaya, I.Y. (ed.), Harsunan Nijeriya VoL.v, CSNL. Kano: Bayero Unive College.

Skinner, A.N. (1980). An Anthology of Hausa Literature. Zaria: Northern Nigerian Publishing Company.

Smith, J. (2005). African and Native American Trickster Folktale. Yahoo

Umar, M.B. (1987). Dangantakar Adabin Baka da Al’adun Gargajiya. Kano: Triumph, Tofa Commercial Press.

Usman A K. (2014). Symbol of Entertainment and Education: Appraising the Binary Function of Gizo, the Trickster in Selected Hausa Folktales Kano: Bayero University. (Paper Presented at Kano).

Usman, A.S. (2000). Women in Hausa Folktales. In Bunza A.M. (ed.), Hausa Studies vol. II No. 2. Sokoto: Usman Danfodiyo University. Usman, B. (2005). Taskar Tatsuniyoyi, Littafi Na (1-6). Kano: Gidan Dabino Publisher.

Usman, H. (2002). Tatsuniya a Matsayin Tubalin Wasan Kwaikwayo: Nazari Kan Wasannin Kwaikwayon Hausawa, Kundin Neman Digiri Na Farko. Zariya: Sashen Harsunan Nijeriya Da na Afirika, Jami’ar Ahmadu Bello.

Uthman, A. N. (1996). Representation of the Status and Role of Women in Hausa Folktales, Unpublished M.A. Thesis. Zaria: Department of English, A.B.U.

Wushishi, B.J. (1998). Adabin Baka: Sigoginsa Da Hikimominsa,

Unpublished M.A Thesis. Kano: Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Yahaya, I.Y. (1971). Tatsuniyoyi da Wasanni Na (1-6). Zariya: Oxford University, Press.

Yahaya, I.Y. (1972). The Style and Content of a Hausa Tale. In Muhd (ed.), HarsunanNijeriya, Vol. ii, CSNL. Kano: Abdullahi Bayero College, Ahmadu Bello University.

Yahaya, I.Y. (1974). Labaru Gargajiya Na (1-2). Ibadan: University Press.

Yahaya, I.Y (1979). Hausa Folklore as an Educational Tool. In Yahaya I.Y. (ed.),Harsunan Nijeriya No. ix, CSNL. Kano: Jami’ar Bayero.

Yahaya, I.Y. (1979). Oral Art and the Sociolization Process: A Socio-Folklore Perspective of Initiation from Childhood to Adult Hausa Community Life Ph.D Thesis, Vol. 1. Zaria: Ahmadu Bello University.

Yahaya, I.Y. (1991). Nazarin Tsari Da Hikimomin Kacici-kacicin Hausa. A cikin Harsunan Nijeriya Vol. xv, CSNL. Kano: Bayero University.

Yahaya, I.Y. da Wasu (2001). Darusan Hausa 1. Ibadan: University Pres.

Yahaya, I.Y. da Xangambo, A. (1986). Jagoran Nazarin Hausa. Zariya: Northern Nigerian Publishing Company.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

RATAYE (1)

JERIN WAƊANDA AKA TATTAUNA DA SU

Farfesa S'idu Muhammad Gusau

 Gidansa na rijiyar zaki da kano

 15/06/2022

23/06/2022

29/08/2022

12/02/2023

Da dare

Farfesa Bashir Aliyu Sallau

 A cikin jami'ar Sule Lamiɗo K/Hausa

 

03/04/2023

11:45 Am

Farfesa Abduladir Ɗangambo

Gidansa da ke rijiyar zaki kano

 

17/06/2022

 

7:30pm

Farfesa Aliyu Umar B/kudu

 A Gidansa

 

20/05/2023

 

8:00pm

Farfesa Ahmad Yusuf

 

09/12/2022

 

3:48pm

Dr. Mu'azu Sa'adu kudan

 A Jami'ar Sule Lamiɗo, ofishinsa

06/02/2023

 

1:13pm

Dr. Salisu Garba Karki

Tattaunawa ta yanar gizo

02/03/2023

4:37pm

Dr. Sani (Abu ubaida), BUK

Tattaunawa ta yanar gizo

23/01/2023

05/04/2023

7:00pm

10:19pm

Farfesa I.G Satatima

A ofishin H.O.D languages jami'ar Sule lamiɗo

08/03/2023

 

12:00pm

Hajiya Uwani

Tsangayar Damau B/kudu

07/05/2023

 

02:56pm

Mama Amarya

A Gidanta

22/04/2023

4:00pm

Yusuf Mukhtar

A Jami'ar Sule Lamiɗo K/Hausa

04/01/2022

25/6/2022

11/01/2023

03/04/2023

9:15Am

12:17pm

3:00pm

5:40pm

Rabi'u Arma

A Jami'ar Sule Lamiɗo K/Hausa

03/ 03/2023

17/04/2023

10:30Am

2:35pm

Malam Shehu

A gidansa Masaya

14/05/2023

6:04pm

Hauwa'u Asheer

gidansu B/kudu

04/05/2023

9:08Am

 

 

 

 RATAYE (2)

 JERIN TATSUNIYOYI DA WASANNIN DA AKA NAZARTA

TATSUNIYAR GIZO DA ƁAURE

Ga ta nan ga ta nan ku.

 Wata rana ne dai wani sarki yana zance a zuci, yana cewa, ‘Gonata ta ɓaure ta yi kyau. ɓauren yanzu duk ya nuna. Gara in sami wani ya je ya tsinke mini duk ɓauren, kar in bar shi ya ruɓe a banza. Amma fa wanda zai tsinke ɓauren ba zai sha ba ko da ɗaya ma. Idan ya gama bai sha ba, zan ba shi.’yata tare da gararta baki ɗaya’.Shi ke nan. Kashegari sai sarki ya sa duk a yi shela a gaya wa mutanen gari sarki yana kiransu a ƙofar fada. Mutane suka taru a qofar gidan sarki. Sai sarki ya ce, dama ba wani abu ya sa na yi kiran ku ba. Gonar ɓaurena ce nake so a tsinke min, amma ba za a sha ko ɓaure ɗaya ba. Sai dai zan ba wanda ya tsinke xin ladan tsinkewar. Watau zan ba shi ‘yata da gararta baki ɗaya’. Sai kowa ya ce ba zai iya ba, domin ɓauren ya cika kyau, ga kuma ƙanshi da zaqi.Ba wanda zai iya ba tare da ya sha ba. Can, sai Gizo ya zo ya ce wa sarki ‘Zan iya’. Shi ken an, sai sarki ya ce, ‘To. gobe ka yi shiri ka tafi’.

 Da gari ya waye, sai Gizo ya ɗura ruwa a jallo, ya ɗauki madubi da kuma tsinkensa na sakace. Ya je gonar sarki ya kama tsinkar ɓaure.In yana cikin yi mutane suka zo suka ce, ‘Gizo barka da aiki’; sai ya tsiri tofar da yau, yana cewa, ‘Tuf! Kai wannan vaure! Ko warinsa ba na so’.Idan sun wuce, sai ya ci gaba da tsinkar ɓauren, yana sha yana zubo wani a ƙasa. Shi ke nan, ashe bai sani ba, wata ‘yar tsuntsuwa tana kallon sa.

 Da ya gama tsinkar vauren tas. Ya sauko zai tafi gida, sai ya ɗauko jallon ruwansa ya kurkure bakinsa, ya ɗauko madubin nan da tsinken sakace, duk ya ciccire ɓauren da ya maƙale masa a haqorinsa. Bakinsa ya yi tas, kamar bai ci kome ba. Sai sarki ya aiko mutane don su debi ɓauren da Gizo ya tsinke. Suka zo suka sami Gizo suka ce, ‘Sannu da aiki Gizo’.Ya ce, ‘Yauwa’ Suka ce, ‘Har ka gama?’Sai ya ce, ’I. Amma da ƙyar na gama. Kamar na yi amai, saboda warin vauren nan. Warin duk ya cika mini ciki’.Sai suka zuzzuba ɓauren a buhunhuna suka tafi suka kai wa sarki.Da suka je gida, sarki ya tambaye su labarin Gizo da tsinkar ɓaure.Suka ce, ‘Ai, yallavai, Gizo bai sha ɓauren ba, domin mun ga muna zobawa a buhu yana tofad da yau. Kuma da muka ce da shi, ‘Me ya sa kake zubad da yau?’ Sai ya ce warin ɓauren ne ya cika masa ciki.’ Sun gama faɗin haka ke nan, sai ga Gizo ya zo gidan sarki.Sarki ya ce da shi, ‘To, Gizo Ka yi aiki mai kyau, Sai kuma ka je gida ka gyaggyara, za a kawo amarya da gararta’. Shi ke nan Gizo ya je gida ya gyaggyara sarai.

 Aka ɗauko amarya da gara aka zo da ita gidan Gizo.Kafin ‘yan ɗaukar amarya su tafi gida, sai suka ji tsuntsuwa tana waqa tana cewa:

‘Kai Gizo, kai Gizo,

A can ka ci ɓaurenka,

Har ka kurkure bakinka,

Har ka manto jallonka…’

 Tana ta faɗar haka har sai da mutanen suka ce, ‘kai, ku tsaya mu ji abin da tsuntsuwar can take faɗa.’Sai Gizo ya ce da su, ‘kai, ku rabu da ita don Allah, shirmenta take yi.’ Sai mutanen suka ce, ‘Wane irin a rabu da ita? Kai! Mu tsaya mu ji.’Shi ke nan, sai ‘yan kawo gara da amarya suka ji tana cewa:

‘Kai Gizo, kai Gizo,

A can ka ci ɓaurenka,

Har ka kurkure bakinka,

Har ka manto jallonka…’

Sai suka ce ‘La’ila! Ashe dama ka ci ɓaurenka ce ba ka ci ba?’ Sai suka yi ta surutu da hayaniya. Shi ke nan. Sai suka mayar da amarya da gararta gida suka gaya wa sarki abin da ya faru. Kurunƙus.

 An ciro wannan tatsuniya daga littafin Tatsuniyoyi Da Wasanni na ɗaya (Yahaya 1971:1).

 TATSUNIYAR ƊAN SARKI YA ZAMA MACIJI

 GA TA NAN GA TA NAN

wani mutum ne dai yana da matans uku, ya fi son biyu daga cikinsu, ɗaya ba ya son ta sosai, sai ta zamo bora a gidan.

 To shi dai wannan mutumin ba shi da da ɗa ko ɗaya, ya damu saboda rashin ƴaƴa. Ana nan ana nan, ran nan sai ya sayo wa matansa guda biyu maganin haihuwa. Sai bai sayo wa bora ba.sai bora ta bari sai da suka jiƙa suka sha suka bar saura har ya sane sannan suka kai juji suka zubar, sannan ta bi ta ɗebo ta wanke da ruwa ta jiƙa sannan ta sha. Allah da ikonsa sai matan mutuminnan sua samu ciki baki ɗaya har da borar.

 A kwana a tashi sai ran nan suka haihu rana ɗaya kuma duk matan suka haihu rana ɗaya kuma duk mata suka haifa, da aka kwana bakwai, watau ranar suna, sai mijinsu ya yi wa ƴaƴan matan da yake so suna amma ya ƙi yiwa ƴar bora suna. sai bora ta ɗinga bin sa a gindi a gindi don ya yi wa ƴarta suna amma ya ƙi, da ya fusata sai yasakawayarinyar suna gwi-da -yara.

 Shikenan yara suna nan suna girma tare, duk lokacin da ya tshi yiwa ƴaƴan ɗinki sai ya yi ban da ƴar bora, ga tsangwamar matan gida da suke yi mata ita da mahaifiyarta.

 A kwana a tashi yara suka girma har suka isa aure gaba ɗaya, da babansu ya ya tashi yi musu aure sai ya zaɓarwa ƴaƴan nana biyu mazaje kyawawa ya aura musu, ita kuwa gwi-da-yara ya tafi da ita jeji cikin surƙuƙin dokar daji ya haɗa tada wani miciji ya ce da ita "kinbi wannan micijin, in ki ka ƙi , Allah ya tsine miki". sai ta ce, "to ba zan ƙi binsa ba baba".

 Sai mutumin nan ya tafi gida yan cike da farin ciki, haka suka yi ta murna shi da matan nan guda biyu, ita kuwa bora ba ta ce komai ba ta kuma kula da abinda suke yi ba.

 A can daji kuwa yarinyar nan sai ta bi micijin nan duk inda ya shiga sai ta bishida macijin nan ya ga ta bi umarnin babanta sai ya ce " ba za ki ji tsorona ba" sa ta ce "A 'a ba zan ji tsoronka ba".

 Daga nan sai ya hau jikin yarinyar ya ƙadandane a jikinta , ya sauƙa ya kanannaɗe a ƙasa ya fasa kansa, amma duk abinda yake ba ta tsorata ba, da micijin nan ya ga haka, sai ya ɗauke ta ya haɗiye ta, ya mai da ita fara , ya fito da ita ya dube ta ya ce "kai ba haka nake son ki ba" sai ya ƙara haɗiyeta ya ƙara haɗiyeta, y mai da ta ja zur, kyakkyawa, ga kyan gashi, ta zama ta kai haka. " ita kuma yarinyar duk haɗiyar da micijin nan ya yi mata ba ta ji tsoransa ba ko kaɗan.

 Amma kuma al'amarin can gidan su yarinyar ya ɓaci. kishiyoyin uawarta suna ta tsangwamarta , ita kuwa ba ta cewa komai. ashe dai macijin nan ba mutum ba ne wani ɗan sarki ne wanda taɓa neman aure a garinsu ya rasa shine wani malami yace sai ya zama maciji ya shiga daji za haɗu da matar aure, shi dalilin da yasa ya dawo daji ya zama maciji.

 Bayan da macijin ya mai da yarinyar yadda yake so sai ya zama mutum , ta ba shi duk labarin abinda ya faru har aka kawota daji, da irin iyayyar da ake musu ita da uwarta a gidan," sai ya ce to ba komai rufe idonki" da ta rufe idon bayan ta buɗe sai gata a wata babbar alƙarya suna tafiya mtane na ta kallonsu suna cewa " la kunga ɗan sarki da wata kyakkyawar yarinya, wa ye kuma ya bashi ita?"

 Da suka je gida dgga isarsu wurin babansu yanyi murna sosai , ya kwashe duk labarin a ya faru ya bashi, sarke ya ce "to Allah ya bada zaman lafiya' daa nan ya sa aka gina gidan zinariya da benaye ɗan sarki ya zauna tare da matarsa bayan anyi ƙasaitaccen biki.

 A can gidan iyayenta kuwa ran nana mijinsu a shiraya domin kai wa ƴaƴansa ziyara gidajensu, da ya tashi sai ya fara zuaea gidan ɗaya daga cikinsu ya tarar tayi miya da ɓera a gidan aka zuba masa ya ci ya rage guntu ya ce ya kai gida aga irn abinda ta ke ci, haka ita ma gian ɗayar ya tarar ta girka tuwon dusa miyar ɗata nana ma ya ci ya rage guntu domin kai wa uwarta irin abincin da take ci.

 Bayan ya bar gidan ɗayan ya kama hanya ,yana cikin tafiya sai ya tarar da wata rijiya wasu ƴan mata na ɗiban ruwa sai ya ce musu sannunku ɗan mata suka cenyawwa sannu sai ya ce don Allah ƴam mata ba kwa sam min ruwan nan na sha ba, sai suka ce tab a kwanan gwi-da -yaran zamu baka ruwa ka sha dk bakinka gaje-gaje da shi, sai mutumin ya yi shitu, can kuma sai ya ce "ƴammata don Allah wa ce ce kuma gwi-da -yara", sai suka harare shi suka rabu da shi, ashe gwi-da yara na jin duk gardamar da suke yi sai gta leƙo ta taga sai ta gani ashe babanta ne, sai ta kirawo wata daga cikin yaran ta ta ce a kawo tshohon gindin tagar gidan. sai a ka kawo shi, garin kallon ginin gidan yau har jiƙa rigarsa ya yi bai sani ba. Da ta ga haka sai ta ji bai kamata ya shiga gidan surukansa a haka ba sai ta jefa masa malun-malun da babbar riga ta taga. da ganin rigar sai ya kama ta da kokawa kici-kici, sai ta ce da shi " baba gidan surukanka ne fa" danya sa kayan sai ta s aka shigar da shi gidan suka fashe da kuka baki ɗaya, ta kwashe duka labarin da ya faru tsakaninsa da macijinnan ta bashi, sai ya yi mamaki sosai, tasa aka shirya masa shifiɗa a soro aka kawo masa abinci ya ci, can sai mai mijin nata ya dawo ya wuce bai san wanene ba , sai da gwi-da-yara tanyi masa bayani ya sake komawa har ƙasa ya gaida shi,sai da ya kwana uku a gidanta kana aka haɗa masa tara taarziƙi ya taho gida akan doki.

D isarsa gida matansa suka taryeshi da murna ya ɗauko tsarabar kowacce da ya samo daga gidan arta ya basu, sa'annan ya sa aka kirawo bora itama aka bata tsarabar da ƴarta ta byar, mamaki duka ya rufe su, daga nana sai boranta fashe da kuka, su kuma sauran suka yi yaji.

 D a aka dawo da su sai suka ce su basu yarda ba, sai an aikawa ƴaƴansu sun zo dukansu. dukkannin ƴaƴan kowa ya zo har da gwi-da-yara da ka rakota akan dawakai, aka shiga da tsarabra da ta zo da ita gidan,sauranma duka suka zo da tsarabarsu, aka rarraba kayayyakin da suka kawo harda na gwi-da -yara. sai suka saki baki galala suna kallonta.

Daga ƙarshe gabaki ɗaya suka shiga jeji saboda baƙin ciki, su kuwa suka cigaba da zamansu lafiya.

 Ƙurunƙus.

 TATSUNIYAR NA-GOMA

 GA TA NAN GA TA NAN KU!

To !

 Wani mutum ne dai da ya ‘ya ‘yansa guda goma, kowane lokaci yana zuwa daji yana yin harbi yana kama tsuntsuye. Shi ke nan kullum ya je kamun tsuntsaye daji sai ya kama tsuntsu ɗaya, shi ke nan duk lokacin da ya dawo daga daji wajen harbi, idan ya ajiye tsuntsun sai a sami wani daga cikin yaran nan na mutumin sai ya ɗauke tsuntsunwar nan da babansu ya kamo daga harbi ya je yacinye shi ka]ai.

 Shi ke nan sai mutumin nan ya zo yana neman tsutsun sai ya tarar babu, shi ke snan sai mutumin ya zo yana neman tsutsuwar yana ta fa]a, babu wanda ya kula shi a cikin yaran, shi ke nan sai mutumin ya ce to shi ke nan ai na san maganin wanda ya cinye mini tsuntsu, idan gobe ta yi za mu je kogi kowa sai ya shiga ciki ya yi ranstuwa ba shi ne ya cinye tsuntsuwa ba.

 Shi ke nan sai ya kwashi ‘ya’yansa gaba ɗaya suka tafi bakin kogi, don ana so a gane wanda yake ɗauke tsuntsuwar baban. Shi ke nan suna zuwa bakin kogi sai aka ce na farko ya fara shiga, da ya shiga sai ya fara waƙa da cewa:

 Ni na fari, ni na fari,

 ni na ci tsuntsun Babaye,

Ruwa tafi da ni,

Kar ka dawo da ni.

 Shi ke nan sai ruwa ya kawo mishi zuwa tafin-ƙafa, shi ke nan sai aka ce ya fito ba shi ba ne. Shi ke nan sai aka ce na biyu shi kuma ya shiga, shi ma sai ya shiga ya fara waƙa :

 Ni na biyu, ni na biyu,

 In ni na ci tsuntsun Babaye,

 Ruwa tafi da ni,

 Kar ka dawo da ni.

 Shi ke nan sai ruwa ya kawo mishi iya idon-sawu , shi ma sai ka ce ya fito ba shi ba ne. shi ke nan sai aka ce na uku shi kuma ya shiga, sai shi ma ya shiga, sai ya fara waƙa :

 Ni na uku, ni na uku,

 In ni na ci tsuntsun Babaye,

 Ruwa tafi da ni,

 Kar ka dawo da ni.

 Shi ke nan sai ruwa ya kawo mishi daidai iya ƙwabri , shi ma sai ka ce ya fito ba shi ba ne. shi ke nan sai aka ce na huɗu shi kuma ya shiga, sai shi ma ya shiga, sai ya fara waƙa :

 Ni na huɗu, ni na huɗu,

 In ni na ci tsuntsun Babaye,

 Ruwa tafi da ni,

 Kar ka dawo da ni.

Shi ke nan sai ruwa ya kawo mishi daidai iya gwiwa , shi ma sai aka ce ya fito ba shi ba ne. Shi ke nan sai aka ce na biyar shi kuma ya shiga, sai shi ma ya shiga, sai ya fara waka,

 Ni na biyar, ni na biyar,

 In ni na ci tsuntsun Babaye,

 Ruwa tafi da ni,

 Kar ka dawo da ni.

Shi ke nan sai kogi ya kawo mishi daidai iya cinya , shi ma sai aka ce ya fito ba shi ba ne. Shi ke nan sai aka ce na shida shi kuma ya shiga, sai shi ma ya shiga, sai ya fara waƙa :

 Ni na shida, ni na shida,

 In ni na ci tsuntsun Babaye,

 Ruwa tafi da ni,

 Kar ka dawo da ni.

 Shi ke nan sai ruwa ya kawo mishi daidai iya kwankwaso , shi ma sai aka ce ya fito ba shi ba ne. Shi ke nan har aka zo kan na goma sai aka ce shi kuma ya shiga, sai shi ma ya shiga, sai ya fara waƙa :

 Ni Na-goma, ni Na-goma,

 In ni na ci tsuntsun Babaye,

 Ruwa tafi da ni,

 Kar ka dawo da ni.

 Shi ke nan sai ruwa ya haɗiye shi ya tafi da shi ‘yan uwan na kallo, sai suna ta kukan rashin an’uwansu ruwa ya tafi da shi.

 Shi ke nan ana cikin haka har sai Na-goma ya kawo gidan wata dodanniya a cikin ruwa, sai dodanniyar nan ta ɗauki Na-goma ta kai shi gidanta, shi ke nan ana nan ana nan sai bayan ya kwana biyu sai dodanniya ta ce to ba zan cinye ka ba, amma zan mai da kai ka zama yarona, shi ke nan sai Na-goma ya ce to shi ke nan kowace ranar kasuwa sai dodanniya ta riƙa ɗora ma Na-goma tallar ƙosai yana kai mata kasuwa yana talla.Shi ke nan rannan Na-goma ya kawo tallar ƙosai kasuwa sai kawai ‘yan ‘uwansa suka gamu, suna ganin Na-goma sai suka ce kana ina, shi ke nan sai ya ce ai yanzu dodanniya ce mamanshi, ita ce ma ta ɗora masa talla yanzu, ku zo mu je gidannmu, shi ke nan sai suka kama hanya har gidan dodanniya, shi ke nan sai dodanniya ta ce idan za ku tafi da Na-goma sai kun kawo mini abinci iri-iri. Shi ke nan sai suka koma gida suka kawo mata buhu na hatsi iri-irisai dodanniya ta ce haka cikin waƙa :

 Kai ! Na-goma

Kai ! Na-goma

Ba ci na ba !

Ba ci na ba !

Na goma

 Ba ci na ba !

 Shi ke nan sai suka koma gida suka sake shi, to a wannan karo sai suka ]auko kayan abinci irin wanda suka dace da dodanniya, sai suka taho da buhu-buhu na }udaje da kyankyasai da tsutsotsi da kwa]i da sauran duk wani abncin }azanta, sai da aka kawo ma dodanniya. Shi ke nan suna kawo mata kayan abincin sai ta mi}e ta na wa}a :

 Ga ci na nan !

Na-goma,

Ga ci na nan !

Ga sha na nan !

Na-goma,

Ga sha na nan !

Madalla dai !

Na-goma,

Madalla dai !

ɗau wandonka !

Na-goma,

ɗau wandonka !

Sa rigarka !

Na-goma !

Sa rigarka !

Na-goma.

Sai wata rana

Na-goma

 Sai wata rana.

Shi ke nan sai Na-goma ya biyo ‘yan uwansa suka dawo gida, daga ranna bai ƙara ƙaukar wani abu wanda ba nashi ba.

ƙurungus.

 WASANNIN KA-CICI-KA-CICI

 Wasan ne da yara kan taru da yawa, ɗaya yana sako tambaya sauran kuma na amsawa ɗaya bayan ɗaya, misali:

 Kande: Ƙulunƙulufita?

Garba: Gauta.

Kande: Shirin ba ci ba?

Sima: Baba.

Kande: Faifaina ɗinkin marido?

Dudu: zuma.

Kande: Kuntukurun ɓarin ɓas?

Garba: Gidan tururuwa.

Kande: Tshohuwar gidanmu kullum za su fita sai sun raba mana

 goro?

Dudu: Kashin awaki.

Kande: Kututture uku gagara ɗauri?

Garba: Ƙwai.

Kande: Shanuna dubu-dubu maɗaurinsu ɗaya?

Ziza: Tsintsiya.

Kande: Iya ta zaga, Baba ya zaga, ba su haɗu ba?

Ilu: Kunne.

Kande: Gya ɗaya dama duniya.

Sima: Farin wata.

Kande: Kogina ya kai ya kawo sai a gefe na ke wanka?

Garba: Fate-fate.

Kande: Kogina ya kai ya kawo babu maai tsallake shi sai

 Bello mai ɗan warki?

Dudu: Kwaɗo.

Kande: Na je jeji, jeji na yi mini dariya?

Ilu: Auduga.

Kande: Rub-rub kushewar bayi?

Ziza: Ƙaiƙayi.

Kande: Na wanke ƙwaryata tas tas na je maka da madina na

 dawo ba ta bushe ba ?

Sima: Hancin kare.

Kande: Ɗan baka a bayan suri?

Garba: Farce.

Kande: Abu ɗil ya sa mai gari kuka?

Dudu: Abu ɗil sauko da sarki daga kan doki?

Ziza: Fitsari.

Kande: Ke wannan shegiyar da kika tsefe kanki wa zai yi miki kitso?

Ilu: Bishiya.

Kande: Daga nesa na jiwo muryar ƙawata?

Sima: Ganga.

Kande: Abu siriri, abu zarara, abu tubkar Allah?

Garba: Gashi.

Kande: Tsumagiyar kan hanya fyaɗe yaro fyaɗe babba?

Ziza: Yunwa.

Kande: Ɗillin bar ɗillin, ɗillin , ɗillin na kallon ki?

Ilu: Kaza bari tono, shaho na kallon ki.

Kande: Yadda ɗillin ta kan yi ɗillin haka ma ɗillinbya kan yi

 ya kan yi ɗillin.

Sima: Yadda ta kan yi ƙwan nan, haka ma ƙwan nan ya kan yi

 kaza.

Kande: Ƴar baƙa jakar mata?

Garba: Kujera.

Kande: Samarin gidanmu masu fararen kawuna?

Ziza: Taɓare.

Kande: Kurkucif kucif?

Ilu: Kwanciyar kare.

Kande: Gwanda lili da liyo?

Sima: Gwanda noma da awo.

 

 

 

 WASANNIN ƁATA

 Wasanni ne da yara maza suke yi domin motsa jiki da sanya nishaɗi.

 Da farko yara su kan taru waje guda suyi ƙawanya su riƙa aiwatardawasanni iri-irita hanyar rera waƙa, misali.

Musa: Ɗan Akuyana.

Amshi: Damushere.

Musa: Ya shiga rumbu.

Amshi: Damushere.

Musa: Zasu kasheshi.

Amshi: Damushere.

Musa: Nan da wuƙaƙe

Amshi: Damushere.

Musa: Har da su Adda.

Amshi: Damushere.

Musa: Nan da takobi

Amshi: Damushere.

 Wubub! wubub na wuce nan.

 wubub! wubub na wuce nan

 

 RATAYE (3)

NAGODE ALLAH KALIƘI MAI DUNIYA,

MAI TSARA KOMAI KAN HALITTU BAI ƊAYA.

 

SHI YAN NUFE NI NA TSARA WAƘA KUN JIYA,

KAN IN TUNASAR ƳAN UWA DON SHIRRIYA.

 

DUK SAI KU TARO HAKULANKU WAJE GUDA

WANI ƊAN TUƘAICI ZA NA BAKU NA GASKIYA.

 

KAN ILLIMIN NAN DAI DA SHI MUKA SA GABA

GUN RAYUWA YA ZAMO KAMAR GISHIRIN MIYA.

 

SHI ILLIMI KULLUM GUDA NE ƊANUWA,

AMMA FA HANYOYINSA BASU DA ƘAFIYA

 

ZURFI GARE SHI DA BABU MAI IYA TANKIYA,

KA BIƊE SHI HAIƘAN HAR KA ZAMTO JAN WUYA.

 

KA GA DAI BAHAUSHE YADDA YAI TA GWAGWARMAYA,

DUK DON YA KYAUTATA RAYUWARSA TA BAI ƊAYA.

 

BISA HANKALI, HANGE, DA TARIN FALSAFA,

YA FA ƘIRƘIRO WASANSA HAR TATSUNIYA.

 

DUK RAYUWA DA MU'AMALARSA YA KILLACE,

TA CIKINSU NE AKA YIN SANI FA DA TARBIYA.

 

NI DAI HABIBA INA KIRA GUN YAN UWA,

DA KU ZAGE DANTSE KUI YI AIKIN GASKIYA.

 

IN DAI KARATUN ZA KU YO KU YI MAI YAWA,

KU ZUBAR DA SURUTU NA MASU KARABNIYA.

 

KU TSAYA KARATU WADDA BABU HAYANIYA,

MA'ANA KU SA NUTSUWA KU KAU DA HATSANIYA.

 

KU LAƘANCI YIN NAZARI GA DUK KAN DARRUSA

KADA SAM KA TOGE IN DA MALAM YAB BIYA.

 

IN DAI KANA NAZARI KA GANE ƊAN UWA

TUNI ZA KA ZAMTO MAI DABARA BAI ƊAYA.

 

JIN DARRASI A AJI DABAN YAKE KA JIYA,

KAR KAI ZATON WAI NAN KARATUN YATTSAYA.

 

MAZA JE KA DUBA ABINDA MALAM YABBIYA,

NAN ZAKA NINKA SANIN DA KAI DARASIN JIYA.

 

DUK WADDA BAI NAZZARI JIYO SIFFA TA SA,

SHI NE FA WADDA YA KE GUDUN YIN TAMBAYA.

 

SANNAN DA MALAM YA FAƊO AIKIN GIDA,

SHI NE NA FARI DA ZA YA ZAM YIN KARRAYA.

 

HAKA IN ANA MAGANAR ASSINGMENT KO GWAJI,

DUK SAI YA RUƊE NAN YA HAU YIN MAGIYA.

 

DAGA NAN YA JE CAN YAI TA NEMAN MAI MASA,

A GURIN ABOKAI WANDA SU SUKA BIBIYA.

 

SHI YA ƘI SAM WAI BA RUWANSA DA WAHHALA,

A BATU NA YIN ILIMI FA YA GAMA KARRAYA.

 

MAI NAZZARI KU SANI FA BA SHI DA KARRAYA,

KO BAI SANI BA KWA TO DA HIMMAR BIBIYA.

 

GUN MALAMAI KO ƊALIBAN DA SUKE SAMA,

YA BIƊA A NAN YAI CAN YA JE YA YI TAMBAYA.

 

KA ZAMO MUTUM MAI JURIYA GA BIƊAR SANI,

WATA RANA KA GA A GUNKA ZA A YI TAMBAYA.

 

IN HAR KA ZAM HAKA KA CI RIBA MAI YAWA,

KA ZARCE WANDA YA KASA HIMMAR YA IYA.

 

WATA RAN FA KAINE ZAKA ZAMTO MALAMI,

MA'ANA GURINKA AKE ZUWA YIN TAMBAYA.

 

NAN ZA NA SA AYA IN ƘARƘARE BAITUKA

BAITI TALATIN BA GUDA ƊAYA NAB BIYA.

 

NI CE HABIBA ABUBAKAR, BIRNIN KUDU,

DA NA KE NAZARTAR HAUSA YAREN TUTIYA.

 

NA ROƘI ALLAH MAI DARE MAI SAFIYA,

YA YI GAFARA GA KURA-KURENMU GABA ƊAYA.

www.amsoshi.com

Post a Comment

0 Comments