Da sunan Allah mai Rahma mai jin kai. Allah kasa yanda na fara lafiya in kare shi lafiya. Wannan labarin ya faru da gaske dan kusan Book dina da nake yi true life ne sai dai in yi masa kwaskwarima dan abun ya fi ba da citta.
Ku biyo ni ku sha labari.
Ku daure ku yi comment dan in ji ra'ayoyin ku a kan Littafin nan......
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishaɗantarwa tare da faɗakarwa da jama'a bisa harshen hausa}_
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo
⚜️©J.A.W📚🖌️
Marubuciyar
* Amince Da Ni
* KAI KA JA WA KANKA
Yanzu kuma gani ɗauke da
ƘANWATA
Paid Book ne
Vip 300
Special 500
Acct No. 3115484026, First Bank, ko kuma Kati MTN (Ba na son VTU)
Idan kin biya ta bank kina iya turo shaidar biyar ki ta wannan 09069080725
🌟🌟 ƘANWATA Na Ikilima Adam [Kashi na 3]🌟🌟
4️⃣1️⃣
'' Ta fara ja
da baya baya'
Kallon ta yake banda haushin ta ba abun da
yakeji danma tasamu har yana neman tabata shi ne take raina masa wayau cijje
labban sa ya yi yana kara kusanto ta saida takai bangon daki Sannan tafara
kokarin rufe Idanun ta da hannayen ta kasa tsayuwar ta yi tana kokarin
durkushewa kasa.
Hannayen sa ya
sa ya ɗago ta tare da
Jan ta zuwa gadon '' cikin sanyi murya ya ce kwanta ina fatan kin samu Sallah
yanzu Ko ?
Girgiza kai ta
yi ta ce A'a nifa sai in yi wata ina jini be tsaya ba..
Dan jimm ya yi
yana nazarin kalaman ta shi a iya sanin sa besan hukunce hukunce da suka shafi
mata ba amma mamaki yake ya ce daman mata suna kai wata suna jini maganar zuci
yake yana ciza labbansa.
Ci gaba da
kallon ta yake sai fadi yake a zuciyar sa InshAllah saina cika Burin Mamy ''
gashi rannan nataba boob din ta a rashin sani gashi yazame mun kamar jaraba
kamata ya yi infita harkan yarinyar nan kada rainin ya yi yawa 'amma zan taba
koda na karshe yakarashe zancen yana me kokarin bude zip din rigar ta..
Saurin zare
hannun sa ya yi lokacin dayaga Rahma takoma masa kamar kunama wani ihu mai
karfi ya saki jikin sa na rawa.
tashi ta yi cikin razana ta ce Amjad me yake
damun ka ''..
Baya baya yake
ta yi yana fadin karki kusanto ni neman hanyar fita waje yake cikin sauri
sauri...
Rahama tsaye
ta yi tana mamakin ikon Allah ba ta kawo komai aranta.
Waigowar da
zeyi sai yaga Rahama ta koma masa normal ''.
Ajiyaar zuciya
yasoma sauke wa akai akai.
Kallon ta yake
ya ce mu je Ko tare da yin gaba dan yanzu ya fara tsoron ta..
Kiyi sauri ki
shirya mu je na ji kince suna Asibiti Ko ? ta gyada kai Alamun haka ne.
Good yafada tare
da yin gaba yana tafiya cikin tsananin damuwa a kan abun da yagani........
Yana saukowa
kasa ya iske su sun shirya cikin manyan kaya shadda ba ƙaramin kyau suka yi da
shigan ba da huluna duk a kan su babban rigar dake jikin su yasha aiki wajen
kwararren tela.
Kallon Yarima
suke sake da baki Faruk ya ce banga kashirya ba kasauko.
Uhmm kun san na
manta kuwa kallon yanayin shi suke ganin muryan sa ta canza sossai.
Faruk ya ce to
maza ka koma kashirya kai zamu raka..
OK ku dan jirani ya ce tare da komawa cikin
dakin sa..
Yana shiga ya iske Rahama har ta shirya tsaf
tana sanye cikin shadda lace mai dankaren tsada yasha adon Stone sossai dinki
ya zauna mata ajiki ka santuwa riga da siket ne ya fito mata da shap din boob
din ta kuwa cas cas suke a jikin rigar da yakamata a jikin ta sossai..
Kallon ta yake yanda ta yi masa kyau sossai
kamar ba ita ba simple makeup da ta yi ba ƙaramin tafiya da tunanin sa ya yi ba..
Azuciyar sa sai fadi yake wannan Yarinyar ta
yi min kama da wacce nake gani a mafarkina wata zuciyar ta ce ba ita ba ce kada
kai ya yi yana fatan yaci gaba dayin mafarkin nan nasa da tabbas wacce yake
mafarkin ta ita ce matar da yake da Burin aure bayan neman mahaifin sa zanen
hoton kamannin ta da ya yi da shi yake yawo.
Rahma ta juyo
ta kalle shi a tsaye jingine jikin Kofa.
Muryan cen
kasa ta ce dan matsa zan fita.
Kallon ta yake
kamar me tunanin wani abu hannun ta yake kallo ganin ta dauko babban gyale a
hannun ta.
Da mamaki yake
kallon ta yana kallon abun da ke hannun ta..
Cikin Daga
murya ya ce ina zakije ne ??
Ta ce bakace inshirya mu je ba..
Wani kallo yake bin ta da shi m'asu tsorata
wanda ake kallon sa..
Murya na rawa kaman za ta yi kuka ta ce kaine
kace inshirya mu je Asibiti..
Harara ya watsa mata ya ce eh kinyi abun da
nasaki ne ba kunama kika zama ba dan ki harbeni yakai karshen zancen cikin
takaicin abun da yagani ya san iska ne batasan an yi ba yanason yaga reactions
din ta..
Cikin rawar baki ta ce kunama kuma ya Allah
kaimana tsari da kunama..
Tsoro ne yabayyana a kan fuskar ta tana nanata
kunama sai Girgiza kai take yi.
Alamun tarin
damuwa a tattare da ita.
Inhar ki nason kije ki ajiye gyalen ki saka
hijab.
Komawa cikin dakin ta yi tabude akwatin nata tare
da dauko hijabin nata..
Tasaka hartakai bakin kofa ya ce daka ta.
Cak tatsaya ta ce wai Allah wannan mutumin ya
fi Salma matsala tafada a zuciyar ta....
Naam ta furta tare da waigowa..
Ki dawo ki saka nikaf da safa yafada cikin
bacin rai kinfison kina tafiya ahanya ki taraman jama'a ko
Ki bari
inkinbar kar kashin inuwar aure na.
Zakiyi abun da kika ga dama.
Rahama ta ji zafin kalaman nasa amma ta nuna
masa bakomai jiki asanyaye ta koma ta yi yanda ya ce din sannan tafita dakin..
Saukowa kasa ta yi ganin Su Faruk suna selfie
suna kyalyalewa da dariya.
Faruk yahau
kan matakalan step yaba Aminu wayar sa dan ya yi masa hoto.
Daukar shi hotuna Aminu ya yi tayi.
Rahama ta raba
gefen nasu ta ce sannun ku.
Yawwa Amarya sai yanzu cewar Faruk.
Wai ina mijin naki ne.
Tun dazu ya shanya mu.
Shiru ta yi ba ta basu Amsa ba ba ta fiya son
surutu Ko magana mara amfani ba.
Samun wuri ta yi ta zauna zaman j'ira..
Saida yakai minti Ashirin kafun ya fito Daga
dakin.
Aminu ya taba kafadar Faruk da hankalin sa
yake kan waya yana chatin ya ce kalli mutumin ka.
Wow suka Furta yayin da yake Saukowa cike da
takama da izza.
Yaci shadda geznar da babban riga kamar nasu ''
takalmin sa haf cover suke kallon yanda take walwali tana sheki..
Sanye yake da hula daidai da kalan shaddar
nasa hash kala..
Kallon shi suke ba ƙaramin kyau ya yi ba daya
shanya gilashi a Idanun sa.
Jajayen bakin sa Rahama take kallo dan tun
fitowar sa itama takasa sauke Idanun ta a kan sa.
Yana Saukowa ka san ya kalli Abokan sa ya ce
sai fa nadan ci abinci restaurant zanje yana kwabe baki.
Faruk ya ce Restaurant kuma abinci da matar ka
ta Dafa fa.
Dan Allah kaci koda kadan ne..
OK dan kun hadani da Allah ne kun san Ko a
gida bana cin Abincin yara yakarashe zancen yana kallon Rahama da ta dukar da
kanta kasa.
Tana maimaita kalmar yara daya fada Azuciyar
ta sai fadi take kada Allah ya sa kaci din cikina Ko naka.
Shiko dîner table yazauna ya bude food flask
din tare da zubo abinci a plate.
Kallon abinci yake yana kwabe fuska yanata Jero
adu'oi harda rufe fuskar sa dan ze zuba abinci a bakin sa.
Duk abun da yake ciki Rahama na kallon sa ta
gefen idanu.
Uhmm. Ta ce daman ina iya zuwa gaban sa dauke
abincina zanyi ya je restaurant din dayasaba sai kace yaga kashi.
Bismillah
yakaranto tare da saka loma daya a bakin sa wani dadi da gardi ne yaziryarci
harshen sa'' ware Idanun ya yi kodai be gani sossai ne.
Ganin eh lallai Abinci nata ne.
Ciki yake yana yana lumshe Idanun sa saida
yacinye abincin nan tas.
Ya ajiye kwanun badan ya ishe shi ba saidan
beson yaci abinci ya koshi sossai hakan yana Haifar masa da wani laluran...
Faruk ya ce mu
je to tun da ka gama wai da Madam za ka je ne yana kallon Rahma.
Samad ya ce eh yana iya ta ce wai yar uwar ta
tana Asibiti cen zamuje ma gaisa acen ya wadatar kallon Rahama yake ya ce tashi
mu je Ko.
Tashi ta yi tadau jakar ta tana gaba yana
bayan ta kallon ta yake yanda hijab dinta ya sauka har kasa.
Babu ba ta lokaci
duk suka shiga motar.
'' Samad bayan
motar yashiga itama Rahama nan tazauna..
Faruk ke
drever din su yana tambayar inda Asibitin yake.
SAMAD ya yi masa
kwatance da Asibitin da aka taba kwantar da shi ne.
*********************
KA SANCEWA
lasa'ar ta gabato sheik na kokarin fita dan yakoma ba da Sallah unguwar tasu.
Limamin Asibitin yasha gaban sa cike da
girmamawa da magiya ya ce Sheik Imam dan Allah ka taimaka kabamu Sallah hade da
dan tafsir.
Sheik kallon dattijon yake ya ce Baba Nike ba
da Sallah a babban masallaci.
Dattijon ya ce dan Allah kasa wani naka ya
wakilceka nayau kadai zakai mana pls.
Sheik ya ce to bara mugani kiran Abubakar
yashiga yi wanda Alwala yagama ya ce kaje cen kabasu Sallah la'asar ni anan
zanyi.
Abubakar cike da girmamawa yatafi dan cika
umarnin mahaifin nasa..
Nan da nan unguwar yadauka Sheik Abdurrazak
kabeer hizqeel makarfi ne zebada Sallah a wannan Masallaci dandazon mutane Daga
nesa da na kusa kankace me Asibitin yacika da dunbun jama'a.
Wasu unguwanni Daga nesa suka ringa tahowa
Daga an yi shela maganar ta bazu.
Cike da mamaki likitoci Asibitin suke kallon
cikar da akayi danyin Sallah a massalacin..
Dan za su iya rantsewa massalacin be taba cika
ba''
ba a taba wuce
sahu biyu ba bayan liman sai gashi Saboda sheik duk Asibitin babu hanyar wuce
wa...
Tun daga nesa
Samad yake hango cinkoson mutane a kofar massalacin.
Daga nesa suka faka motar dan babu hanya..
Kafun su fito saida suka yi Alwala hakan ya sa
basu yi wata wata ba sukabi Sahu...
Rahama dake zaune cikin mota Jin muryan
mahaifin ta ya sa ta ware Idanun ta tare da sauke nikaf din dake kanta.
Abba ta furta a fili waishi ke ba da Sallah
uhmm Allah ya saka wa Abba da Alkhairi.
Bayan An idar da sallah saida yadauki minti
talatin yana waazi
' kuma waazi
yake a kan Maza masu tauye hakkin matar su' da suji tsoron Allah ya yi Jan
kunne ne a kan Abun da akaiwa Salma.
SAMAD JIyake kamar dan shi sheik yake wa'azin
nan.
Jiki babu
kwari ya tashi bayan anfara watsewa ana ta tafiya
Masu daukar wa'azi a wayoyin su sun dauka..
Shiga suka yi a motar shida Shi da abokan sa
kai tsaye Asibitin suka nufa...
Suna parking motar a harabar Asibitin ya yi daidai
da fitowar sheik Daga massalacin..
Kallon su yake dan yanason yaga ne kamar mijin
Rahama ne.
Ganin Rahama ta fito Daga motar ta nufo inda
yake ya sashi sakin Murmushi yana musu sannu da zuwa..
SAMAD CIKE DA FARIN CIKI YADUKA YA GAISHE DA
SHEIK.
Suma Faruk gaishe shi suka yi nuna musu hanyar
dakin da Salma suke yayi.
Cike da fara'ar su suka shiga..
Rahama ganin anty aguje taje ta rungume ta gam
a jikin ta tana kukan farin ciki.
Mama cikin farin ciki ta ce yata baki ganni
bane.
Tashi Daga jikin Anty ta yi taje gaban Mama
tana gaishe ta cike da ladabi.
Su Abdul Samad kallon ta suke yanda duk tarude
ganin iyayen ta..
Karasowa dakin suka yi dukan su harda sheik.
Sheik ya nuna masu waje da su zauna.
Cike da ladabi suka gaida Mama da Anty
Mama sai kallon Abdul Samad take tana son tuno
inda ta taba ganin fuskar shi..
Zumbur ta Mike
tsaye kallon ta kowa yake a dakin.
Baki na rawa ta
ce wannan na taba ganin hoton sa a dakin Baba Salihu.
😳😳
Sheik ya ce
Baba Salihu kuma '' ta ce kwarai kuwa lokacin da za ai gyaran gidan namu.
Mukaje ajiye wasu kayayyakin mu anan naga
hoton me kama da wannan.
SAMAD AZABURE
YAMIKE TSAYE... YA CE WHAT...
4️⃣2️⃣
Ya ce What mai
kama dani a hoto a dakin Baba Salihu waye Baba Salihu ya tambaya cikin
kidima...
Mama ta ce yana iya zama kamanni ne amma
tabbas naga hoton nan.
Kuna yanayi
sossai.
Sheik ya ce hoton yana dakin nasa ne.
Mama ta ce kwarai kuwa.
Abdul Samad cikin kaduwa ya ce zanso naga
hoton nan mama.
Cikin kasa da murya ta ce babu matsala.
Rahama zuwa ta yi gaban Salma dake kallon su
cikin Mamakin ganin Yarima Samad din ganin shi take kamar cikin larabawa ya
fito yanda fatar jikin sa ke fresh '
Bakin sa take
kallon yanda leben sa yake jajir. '.
Rahama ta dawo da ita Daga tunanin ta tahanyar
shafa fuskar ta ta ce kanwaty ya jikin naki.
Salma ta ce na
ji sauki amma Idanun ta nakan Samad.
Rahama Kallon Anty take ta ce waimeke damun
Salma ne.
Ganin su Samad na wajen ya sa Abba fadin inaga
Maleria ce da taifot sai dai result ya fito zamu ji..
Sannu Rahama ke jero mata ta ce wai ina mijin
Salma ne.
Mama ta yi Jim ta ce ya je yadawo.
Cike da tausayawa Rahama ke kallon yanda Salma
ta rame sossai..
Samad ya ce Abba daman munzo da niyar zuwa
wajen naka sai mukaji kuna Asibiti..
Cikin Jin Dadi sheik ya ce au to nagane nanma
ya isa ya muka iya da kaddarar cuta sai hakuri..
Samad ahannun ya sa cikin Aljihun sa yazaro
bandir din dubu dari ya ajiye gaban Anty ya ce gashi babu yawa ayi hakuri..
Sheik ya ce an
yi haka kuwa ɗana yana
Murmushi ya ce amma kudin sunyi yawa ka rage su..
Fauk ya ce kar ka damu ya sheik imam '' kudin
Asibiti har ku gama zama yadauki nauyin sa.
Adu'arku yake nema dan shima yazama dan Ku.
Sossai Samad yaji Dadin bayanin Faruk.
Tashi suka yi da niyar za su fita.
Samad ya kalli Mama ya ce uwata zamu tafi Ko
zan iya zuwa gobe gidan naku dan inga hoton.
Sheik ya ce kar ka damu zanturo Abdul j'alil
yakawo maka.
Samad kallon Rahama yake yaga Alamun ba son
tafiya take ba.
Sheik na Lure da kallon Rahama da yake yi.
Haka ya sa ya
yi gyaran murya ya ce Rahama tashi kuje Ko tun da an yi ziyar hankali yakwanta.
Samad ya karbi
zancen da A'a ka barta akwai inda zamu je inmun dawo zamu biyo mu dauke ta
yakarashe zancen tare da fita dakin.
Abokan sa suka take masa baya.
Sheik godiya yashiga yi musu bisa kokarin sa
da kyautatawan su.
Sheik dawowa cikin dakin ya yi yazauna yana
kallon Rahama Sam bega Rama tattare da ita ba.
Yaga tadanyi
haske.
Cikin damuwa yake ba Rahama labarin abun da ya
samun Salma.
Salati ta fara tana kallon Salma ta ce Amma
Abba mijin ta beda imani yanzu yana ina haka.
Sheik ya ce inazan sani.
Sai dai Allah
yakyauta ya tsare gaba.
Salma cikin kuka ta ce ni dai ba zan koma
gidan shi dukana yake yi tare da nuna musu shaidan dukan.
Ganin jikin ta
da zanen bulala.
Mama ta ce subuhannalah harda duka ta ce
kwarai kuwa.
Sheik ya ce ai
ba zan raba auren ba koda zaki koma ba yanzu ba Salma sai kinyi watanni agida
InshAllah.
Salma ta ji dadin furucin Sheik har ta murmusa
Rahama ta ce Abba Ko zata dawo gidana da zama ne.
Dasauri anty ta katseta ta hanyar fadin A''a
bazata je ba a kan me zata zaune miki gidan miji..
Ran Mama da Salma ya yi mugun baci hakanan su
ka shanye abun da ta yi musu..
Sheik ya ce
Sa'adatu ai gaskiya kika fada da auren wani ba za ki je gidan wasu ba ki zaune
musu ba sai dai ziyara.
Rahama ta yi shiru tana sauraren su.
Sheik tashi ya yi ya ce to zanje sai bayan
isha'i zandawo Daga haka yabar dakin.
Sheik nafita Mama ta rinƙa
jifan Anty da kallon banza.
Ita Ko anty hakan bedamun ta inhar a kan gaskiyar
ta ne.
*************************
🇧🇯
Kwatano.
Karima ce
tasamu wani sirrintance waje tare da zama ta kunna wayar ta.
Nombar Samad
ta danna wa kira.
Tayi ring
kamar baza a Daga ba.
Jin an Daga ya
sa ta sakin ajiyar zuciya.
Cikin kasa da muryan ta ta ce ya shugaba na
Yarimar Gheuzo baiwar ka Karima ce..
Daga can ɓangaren
ya ce Karima sai yanzu kika samu damar kirana ta ce kayimun Afuwa tare da
risinawa kamar tana gaban sa.
Abdul Samad ya ce ina son ki samun idanu
sossai a kan Marwan.
Da shige da fitan sa.
Idan drever na yana nan ki masa sakon nan shi
ne zeringa bin sahun Marwan har fulani ɗa
Abba Marwan.
Ina fatan kin fahimta ta ce naam ya shugaba.
Ya ce ke cikin gida ne zaki min aiki taimako
ki shi ne zekai ni da nasarar gano baiwar nan data gudu Saratu.
Cike da
gamsuwa Karima ta ce InshAllah zanyi yanda kace.
Har ze katse sai jiya yi ta ce ya shugaba na.
Ya matar taka
take.
Shiru ya yi na wani lokaci kafun ya ce tana
lafiya Karima..
Karima ta ce Ranka ya dade kar ka zo garin nan
da ita harsai Allah ya azurtaku da haihuwa.
Cike da Mamaki yake nazarin kalaman ta ya ce
Karima banfahimce ki ba
Ki dan ban
haske.
Har ta yi tunanin bazata gaya masa ba sai ta
tuna irin kaunar da take masa.
Cikin raunin murya ta ba shi labarin abun da ya
faru a yan kwanakin nan..
Ya Girgiza matuka da Jin zancen nata.
Cikin dauriya ya ce kada ki damu Karima ni
wannan be dameni ba.
Matata kuma zanzo kwanan nan wajen wani
shari'a ba zan zo da ita ba.
Sossai Karima ta ji dadin bayanan sa.
Daga haka suka
yi Sallama.
************
****** *******
🇬🇦
Gabon
Hajiya Assana
ce zaune kan sallaya bayan ta idar da Sallah Daga hannayen ta sama ta yi tana
rokon Allah ya mallaka mata zuciyar baba Salihu kuka take iya karfin ta..
Diyar ta mai
suna hauwa ce ta shigo cike da mamaki take kallon uwar ta tana kuka ta durkushe
gaban ta ta ce Mama haryanzu baki daina kukan mutuwar baba bane.
Adua'a yake
bukata.
Girgiza kai ta
yi ta ce hauwa Ba wannan kukan nake ba yata.
Cikin tsananin damuwa hauwa ta tallabo fuskar
uwar ta tana goge mata hawaye jiki asanyaye ta ce mama Ko baki yarda dani bane.
Hajiya hassana dago jajayen Idanun ta ta yi tana
kallon yar ta ta ce niko nayarda dake hauwa ta'''...
Hauwa ta numfasa ta ce to dan Allah gayamin
damuwar ki inbada maganin ta intayaki da adua
Zaunar da hauwa ta yi ta ce akwai wani bawan
Allah mai suna Alh Salihu turaki wlh nakamu da son sa banajin zan iya rayuwa
babu shi.
Hauwa ta ce Alhaji Salihu turaki daya dai ɗana sani dan gidan Sarauta
ne fa tafada cike da zare idanu.
Mamar ta ta ce ya'akai kika san haka daughter tare
da share hawayen ta.
Numfashi hauwa ta fesar ta ce mama nasan shi
kiyarda wani dattijon yana gidan sa.
Agun jikokin sa nake samun labarin sa ance
Sarki ne a garin kwatano.
Amma wasu dalilai ya sa ya sauka kan karagan
mulki.
Hajiya Hassana tashi ta yi Daga zaune tana
ciza yatsar ta ta ce yanzu nagane dalilin dayasa yaki Amsar ta yi na.
. Hauwa ta ce mene
ne dalilin mama ''
ta tsareta da manyan
idanuwan ta.
Hajiya hassana ta ce inhar Salihu turaki ne
uhmmmmmmmm
4️⃣3️⃣
Hajiya Hassana
ta ce inhar Salihu Turaki ne uhmmmmm nasan sunan sa tun da dadewa '' Saboda
mummunar labarin daya karade a duniya a kan sa.
Hauwa ta zare Idanun ta ta ce mummunar labari
kuma wannan Salihin mutumin.
Hassana taku ta yi taje wajen Windows dakin
nata maida kallon ta ta yi a wajen ta ce ke ba zan iya gayamiki wannan labarin
ba harsai na binciko gaskiyar Al'amarin.
Hauwa kallon bayan uwar take fuskar ta dauke
da damuwa ta ce taya zaki gano abun da ke boye bayan kina nan shikuma garin su
kwatano ne.
Dariya mai sauti hassana ta yi tana buga
kafafun ta kasa tare da waigowa tadawo kusa da yar ido cikin ido take kallon ta
ta ce kwatanon zanje InshAllah indai bashida hannun a kan abun da na ji to
wallahi zan sama masa mafita.
Hauwa ta ce la'ila rike da baki ta ce mama ki
rufa mana asiri '' ki hakura da Salihun nan banjin dadin damuwa da wanda be
damu dake ba da kike yi akarshe yazo be aure ki ba.
Murmushi mama ta yi ta ce baby na zanyi ne Dan
Allah dakuma kaunar da nake masa '' kimun adua dan Allah karki fitar da sirrina
Ko kanin ki kada ki gayamasa ga inda zanje.
Kinji Ko !!
Gyada kai ta
yi Alamun gamsuwa Idanun ta cike da kwalla ta rungumi uwar ta cikin sanyin
murya ta ce Mama Allah ya sa kada kiyi zuwan banza nasan ke uwa tagari ce dan
Allah ki kara rike mana martabarki da mutunci ki ina Alfahari dake uwata.
Kuka ya kwace mata tana shafa kan hauwa ta ce
nagode daugheter tare da manna mata kiss 💋 a goshin ta..
*************************
Baba Salihu
zaune a dakin kamar yanda ya saba ya kunna wannan cctv camera yana kallon abun
da akai uhmm Samad yafada a zuciyar sa nasan ka bakada sauki fa tunanin mafita
yake y' hakan ya sa ya dauko babbar wayar dake gefen nasa ya danna kira gun mai
bashi labarin Samad..
Cikin damuwa ya ce dafatan kowa lfy.
Ya ba shi amsa da lafiya lau ne.
Dan numfasawa baba salihu ya yi yana taune lip
din shi.
Ya ce nalura kamar Rahama ba ta Jin dadin zama
da Samad '' Daga can ɓangaren
ya ce shima yaso ya fahimci haka amma zekara sa idanu yaga ne gaskiyar
Al'amarin.
Baba Salihu cikin damuwa ya ce bana son
mahaifina yabar duniya banyi tozali da shi ba..
Idanun sa cike da kwalla.
Kasa jure wayar da suke yi ya yi tare da katse
wayar y azauna yana kuka iya karfin sa.
Tuno abun da yasuka wuce shekara da shekaru
yake cikin kunan rai ya ce waze wanke ni a idon duniya..
Ya zanyi mahaifina yaga haske na..
Daga HANNAYEN SA SAMA ya yi cikin kuka yana
rokon sassauci a rayuwar sa....
Ita Ko hajiya
Hassana ta shirya tsaf har airpor yayan ta suka rako ta zata tafi kwatano.
Suna Airport
har jirgin nasu ya tashi sararin samaniya.
Hauwa da kanin
ta jiki asanyaye suka koma gida
.
🇳🇬
KANO
Sai bayan isha'i
suka koma asibitin dan dauko Rahama daidai da dawowar Abubakar da Abdul jalil
'cikin Jin dadin ganin Samad suka yi musabaha dashi'
Abubakar ya ce
mijin Rahama Ko ?
Murmushi ya yi
ya ce eh nine.
Ah yanzu kuka zone mu shiga Daga ciki mana.
Aminu ya ce Ranka ya dade ai munzo daukan
Rahama mu kazo yi yafada tare da yin gaba.
Abubakar ya ce bismillah mu je cike da dokin
son ganin Rahama yashiga dakin.
Yana shiga ya iske ta tana karatun Alkur'an.
Kallon ta yake yanda take karatu a natse ya ce
inkinkai Aya ki dakatar ga mijin ki yashigo...
Samad da suke bakin kofar shida a bokan sa
kallon ta suke hartakai Aya..
Rahama ta ce la la Yaya ABU ashe dai zamu hadu
daman ina takaicin tafiya ban ganka ba.
Abubakar cikin Jin dadi yakama hannun ta cikin
nashi yana matsama tare da dafata suna Face din juna.
SAMAD RANKA IN
ya yi DUBU YABACI ya saN YAYAN TANE UWA DAYA UBA DAYA..
Faruk ya lura ransa yabaci murya a tausashe ya
ce yaya ABU sauri muke yi dan Allah..
Abubakar ya ce babu matsala.
KE RAHAMA TASHI KU TAFI KINJI KO..
Kallon Anty take dake barcin Gajiya gashi Mama
taje gida ta dawo..
Rike hannun Salma ta yi ta ce my kanwaty mun
tafi Allah yakara lafiya.
Nikaf dinta ta sanya tare da nufar hanyar
fita.
Shiko Samad tuni suka bar dakin suna cikin
Mota suna jiran ta.
Sai cika yake yana batsewa wannan yarinyar yar
rainin hankali ce.
A rainin wayau ne tashanya mu 'mu yaran Tane
tana cen tana murza hannun namiji.
Kallon takun ta tana tahowa ya sa kallon sa
yakoma akanta.
Karasowa ta yi tare da bude murfin motar..
Ta shiga ta inda yake zaune.
Matsawa ya yi Daga gefe yana bubbuga kafa
Alamun zamu je gida zaki sani.
Faruk drever ɗinsu
ya yi har gidan nasu.
************************
England.
Adamsy ne yake
Chattin da Asiya ta whsap.
Cikin tsananin damuwa yayiwa Asiya voice ya ce
wallahi Asiya har gobe ina son Rahama da Yarima ze sakar min ita danafi kowa
farin ciki wallahi nakasa sukuni.
Asiya cike da nutsuwa ta ba shi Amsa ta ce
babu abun da ya fi karfin adua..
Ka yaki shaidan acikin zuciyar ka Rahama yanzu
Matar wani ce kasa m'a ranka hakuri.
Zan ba ka adu'oi da za su taimakeka...
Adu'oi dayawa ta yi masa audio tare da tura
masa.
Adamsy dake kwance saman gadon sa mai laushi ya
ce Asiya na ji bayananki InshAllah zan aiki dashi.
Asiya ta ce to yaushe za ka dawo ne munyi miss
dinka.
Murmushi ya yi ya ce ai garin babu dadi babu
Rahama daman Saboda ita nashiga koyarwa a wannan makarantar taku
Uhmm Asiya ta ce kenan mu ba mutane bane.
Yi hakuri Asiya ai kodan son da kike ma Rahama
zanzo
Wai ina bakar
munafukar kanwar Rahma take.
Asiya ta ce indakwai sunan da ya fi wannan
kana iya kiranta da shi Algunguma aitayi aure a ranar na tsani me bakar zuciya
ace yayar ki uwa daya uba daya.
Uhmm in'nice Rahma nida ita har Abada wlh saide
ita Rahama zuciyar yafiya gareta yanzu za a mata abu anjima zata ce ta yafe.
Adamsy ya ce dabi'un ta da hankalin ta suna
Daga cikin abun da yajawo hankalina akanta Ko banza nasan yaya na za su samu
tarbiyya.
Asiya ta ce haka ne wlh tamasu raino Daga uba
nagari uwar dakin ta mutumiyar Arziki da tawakali.
Ahakadai suka
cigaba da hira ita da Adamsy sun shagala sossai..
**************************
Yarima Samad a
gajiye suka karaso falon nasu.
Faruk ya fada
kan 3tsr ya ce Wash munsha yawo kuma babu nasara.
Aminu ya ce wlh babu nasara fa amma wataran
zamuyi nasara.
Yarima Samad kallon su yake yana kwabe baki ya
ce kudai an yi ragwaye wlh jibi yanda kuka baje kan kujera yakarashe zancen
yana hawa kan matakalan step.
Tuni Rahama ta shige dakin nasa.
Sauri sauri
take ta cire kayan jikin ta.
Turo kofar da akayi ne ya sa cikin hanzari
tamaida hijabin ta a jikin ta.
Zama ta yi akasa tana latsa wayar ta.
Da sallama bakin sa yakaraso falon kallon ta
yake yanda ta na de kafafun cikin hijab.
Wuce ta ya yi ya fara rage kayan jikin sa.
Haka kawai yaji kamar tana kallon sa.
Ya waiga yaga
hankalin ta nakan waya.
Uhmm ya ce wannan Yarinyar zan gyara mata zama
mu tasa Yawon da ba mu shirya ba.
Gyaran murya ya yi wanda yajawo hankalin ta a
kan sa.
Ke taso ki je ki hadamun ruwan wanka gaki kin
fito babban gida.
Amma Sam
bakida wayau.
Kallon shi take shima itake yake kallo yanajin
bugawar zuciyar sa yana tsananta duk sanda ya yi tozali da ita.
Ko karya nayi
miki ne ?
Banda son a
taba ki babu abun da ke burgeki.
Hararan ta yake tana tsaki.
Tashi ta yi Daga zaune tana ciza labbansa ta
suka bushe.
Azuciyar ta
sai fadi take uhmm shi kullum laifi ake masa babu rana ta banza da ba zai ce ga
wani abu ba.
Kai tsaye toilette din ta fada tana kokarin
hada masa ruwan wanka.
Taji taku a
bayan ta.
Bata kawo
komai aranta ba taci gaba da hada ruwan.
Dagowar da za ta yi taga abu gabanta tsaye
cikin bakaken kaya.
Idanun sa kwala kwala kamar kwai.
Soma ja da baya ta yi yana kusanto ta.
Ta kai karshen....
4️⃣4️⃣
Ta kai karshen
bangon dakin tafara adu'oi tana tofa masa tana adu'oi cikin aro jarumta ta ce
me kake nema dani ne ?
Nufo shi ta yi ta cire tsoro nan da nan ya
fara ja da baya batt ya ba ce Daga bandakin.
Ganin yaba ce be sa ta daina aduar da ke bakin
ta ba ta nayi cikin Daga murya.
Yarima Samad mamaki ne yacika shi Jin muryan
ta ita kadai a bandakin.
Daga shi sai dan gajeran wando jikin sa cikin
hanzarin sa ya shiga bandakin ganin gabadaya hankalin ta baya kansa adu'oi take
ta zubawa tana magana ta ce yakai mummunar halittar nan dawo nan ban gama da
kai ba yaka gudu.
Sai gashi ya bayyana gaban yanata susa jikin
sa na masa kaikayi.
Murya cen sama take jiyo wani murya mai amo hakan
ya sa ta Daga kanta sama.
Keee Rahama wlh inkika cutar da dan aikena
namiki Alkawarin nadama a rayuwar ki.
Samad dake tsaye yana kallon ikon Allah rike
take da kugun ta Idanun ta sun kada sunyi jajir 'bejin komai sai tashin muryan
ta.
Jin muryan ta ya yi tana Wani buga uban kara
hade da dariya ta ce bakuda abun da zaku yi maganina Ko mu gwada yanzu ne
suratul bakara tafara karantowa da karfin ta wannan Aljanin dake gaban barin
wajen yayi' '' Shiko me magana Daga Sama yana ihu fadi yake Rahama ki dakata Ko
kin hanani wucewa hanyar dazanbi nawuce wuta nake gani.
Rahama bako ta saurare shi ba cigaba da
karatun take tana kara sautin muryan nata.
Wani irin kara ya yi Daga cen Sama ya ce
Inkina yiwa darajar Manzon Allah SAW ki bar karatun nan wlh natuba najanye
kalamai na.
Tsai gaita karatun ta yi cikin fushi ta ce
gayamin me nayi muku kuke neman takura mun.
Daga can ɓangaren
ya ce wallahi turomu akai.
Rahama cikin zafin rai da batasan tanadashi ba
ta ce za ka gayamin gaskiya Ko sai nayi kasa kasa da kai.
Wani huci Sama Sama yake yi yana nishi ya ce
anturomu ne Daga baban Maryam.
Yana fadin haka yabar wajen cikin tsananin
wahala.
Nanata kalamin nasa take yi ta ce baban Maryam
kuma.
TA MANCE A BANDA KI TAKE.
JIN MURYAN ABDUL SAMAD YANA FADIN KE LFY
KIKE..tare da tsareta da idanu cikin damuwa.
Ajiyar zuciya tafara suke wa tana kallon sa.
Kamo hannun ta ya yi sukaje daki tare da
zaunar da ita bakin gado ya ce Rahama wai meke damun ki gayamin.
Kallon shi take ta ce anya gidan nan bana
Aljanu bane.
Kallon ta yake ya ce kamar ya fa gidan Aljanu.
Uhmm abubuwa ban tsoro nagani harda cemin wai
baban Maryam yaturo su.
Abdul Samad cikin tsananin tashin hankali
yashiga Jin zancen nata..
Ya Salam ya furta cikin Jin tausayin ta yakama
hannayen ta ya ce Rahama ba gidan Aljanu bane.
Shaidanun mutane ne da shaidanun Aljanu sune
suke takura mana.
Tunani yake cikin zuciyar shi ya ce karfa
Yarinyar mutane tasamu matsala Saboda ni.
A'a Rahama ba zan bari acutar mun dake ba.
Maganar zuci yake yana kallon yanda take ta
ajiyar zuciya.
Besan sanda ya jawo ta ya rungume ba.
Itako kasa fita Daga jikin nasa ta yi dan wani
dumi ta ji yana ratsata kamshin jikin sa take shaka hade da lumshe Idanun ta.
Tana tunanin to wannan abun shi mene ne shi
taya akai suka shigo rayuwar ta, tunani take tasan duk a ɗangin nata babu baban
Maryam.
Kara shigewa jikin sa ta yi wanda hakan ya
sakar masa da kasala.
Cikin dauriya ya
ce bara inje in yi wankar Ko ?
Sam tama mance shi ta runguma harda make
kafada za ta yi kukan shagwaba.
Kallon bakin
nata yake nan take Yaji wani yarrr.
A jikin sa.
Jin ya hade
bakin sa nata ya fara tsotso kamar ya samun lollipop firgit ta dawo hayyacin ta
tana kokarin kwacewa Yarima Samad yaki ba ta koda kofar kwacewa '' kuka tafara
tana tana kokarin kwacewa.
Hannun sa yana kan na shanun ta kokarin cire
mata brezia yake yaji karar buga kofa da karfi.
Jin muryan Faruk ya yi yana fadin zoka bude
mana kofa.
Ransa ya yi matukar
baci yaso ya samu sa'ar ta adaren nan duk yaga ta tsiya.
''
Sakin Rahama ya yi cikin Daga murya ya ce ina
zuwa.
Jallabiyar sa yazura cikin hanzari.
Itako Rahama
toilet ta koma dan yin wanka dan Allah ne ya cece ta hannun sa
inhar ya yi mata mugun kamu tofa sai dai Allah
shike kwatar ta.
Tuno abun da ya faru da Salma ta yi ta dalilin
jima'i hakan ya sa hankalin ta ya yi mugun tashi.
Ta ce ina wallahi nafi Salma son jikina banson
abun da ze taba lafiya ta.
Kuka take ta ce ya zanyi Rahama banson wannan
jima'in harda shesheka kuka haka kawai ya je ya sabatamun rayuwa ta.
Tuno kawar su da ta yi aure ta yi irin wahalar
datasha a hannun mijin nata...
Uhmm ni dai Allah ya sa yakyaleni inhuta tana
turo bakin ta gaba.
''
Shiko Yarima
Samad bude kofar ya yi yana kallon Faruk da yanayin sa ya sauya.
Cikin damuwa ya ce Yarima Samad muryan Rahama
mukai ta ji tana surutai hankalin mu ya tashi sossai ''
Ajiyar zuciya
ya sauke ya ce bafa wani abu bane ta tsorata ne a bandakin kar ka damu.
Ka san mata basuda hakuri insukaga abun tsoro.
Aminu ne yakaraso wajen ya ce amma duk da haka
akwai Ayar tambaya anan wajen kamata ya yi ka tambayeta abun da tagani asan
mafita fa.
Yakarashe
zancen yana yarfe hannayen sa.
Faruk ya ce wannan gaskiya ne.
Yarima Samad kallon su yake ya ce to yanzu ya
kuke so nayi da ita ka san ba gayamin komi za ta yi ba.
Faruk ya ce ai wannan ma zancen banza kake yi
yaza ai kaida matar ka kace bazata saurareka ba.
Su fa mata ba a musu sarauta agida dan sune
keda linzamin juyawa Ko wani da namiji dan haka muna rokon ka.
Kaje kabincika da kyau yanda Yarinyar nan ke
kara gsk ruwa baya tsami banza.
SAMAD shiru ya yi kamar yana tunanin wani abu ya
ce to zan duba mugani yana kokarin komawa dakin..
Yaji muryan ta
tana fadin dan matsa zan fita.
ba ta hanya ya yi hakan ya sa ta yi tozali
dasu Faruk dasuke jero mata sannu.
Kallon su take cikin siririyar muryan ta wanda
ke kashe garkuwan jikin Samad ta ce wani abu ya faru ne tana kokarin sauka Daga
kan matakalan step din.
Aminu ya ce
ihun ki mukaji shi ya sa muka zo.
Cak ta tsaya Daga kan matakalan step din.
Taso waigowa
saita fasa.
Ta ce nima ban
san hakan tafaru ba tana mai cigaba da tafiyar ta.
Yarima Samad da su Faruk kallon juna suka yi.
***********************
🇧🇯
Kwatano
Bokan baban
Maryam ne duk Zufa ya keto masa ta Ko ina sakamakon Aljanun da ya tura sun dawo
suka yi masa bulala hamsin shima Yaji kadan Daga cikin azabar da suka sha.
Da ƙyar yasha a hannun su
Daukar wayar
sa ya yi yakira baban Maryam ciki fada ya ce ni wannan aikin da kaban bankara
tura Aljanuna ku hakura kawai tazo garin zefi yakin da ya kamata kayi kenan.
Daga can ɓangaren
ya ce haba boka hakuri zakai amma na maka Alkawari zamu sa tazo garin kwatano
dan cika Burin mu baza a wuce sati ba InshAllah.
Boka ya ce kar ka kara fadin kalmarka ta
karshe ya daka masa tsawa tare da katse wayar.....
Dan Yaji
haushin InshAllah daya furta.
Baban maryam zaune a dakin sa Maryam tana
zaune kusa da shi duk abun da ake fade a gaban ta ne.
Kuka ta saki ta ce yanzu baba wannan matar ta
yi nasara kenan.
A'a batayi nasara ba cewar baban Maryam..
Maman Maryam ta shigo falon hannun ta dauke da
flask din abinci.
Kallon Maryam da baban ta ta yi ta ce ya ake
cikine naga kunyi jugum..
Neman wuri ta yi tazauna suna face din juna da
maryam..
Baban Maryam ya ce wannan karan aikin naki ne tun
da kin isa da Yarima Samad kibashi umarni yazo da matar shi inhar zezo shari'a
da ze kawo shi...... Yazo da ita kawai shi ne magana.
Maman Maryam ta
ce zankirashi yanzu ɗana
shiga daki na.
************************
Hajiya Hassana
cikin unguwar zongo Cotonou ta sauka hôtel royal wani kayataccen hôtel royal
nan ta sauka.
A garin batasan kowa ba tana ta tunanin ta
inda zata fara tambayar Masarautar Gheuzo.
Ta fito wajen hôtel din tana sanye cikin
habaya bleu ba ƙaramin kyau ta yi da shigar ba..
Kallon titunan take masu mashina dake ta wuce
wa..
Suna sanye da uniforme din su.
Gefen ta ta hango wani babban restaurant ana
gashin kaji awajen.
Ka santuwa ba
ta ganin kaza tabari.
ya sa ta nufi wajen cikin nutsuwa take tafiya
Idanun dauke de glass..
Daidai wajen
mai gashin naman ta tsaya.
Barka dazuwa hajiya na nawa za a sako miki cewar
me saida naman.
Yawwa barkadai
ta ba shi amsa cikin fara'ar ta har hakoran makkah suka bayyana.
Kallon kajin take ta ce aban guda biyu.
OK to ya shiga yin abun da tasashi.
.
Wani kyakywan matashi tagani ya paka motar sa.
Awajen tare da
nufar wani babban super market dake wajen.
Me naman rike da baki ya ce Wata Sabon gani.
Yariman Gheuzo ne a unguwar tamu.
Hassana cikin mamaki ta ce dan Allah ka san
shi ne ?
Wani Yariman ne ta jefo m'asa tambaya.
Mai saida nama ya ce aikuwa nasan shi dan
Sarki jikan Sarki ne.
Ahmad salihu Turaki.
Zare idanu ta yi cikin kidima ta ce me
kace.......
Ta ku har
kullum kyauta Daga Allah
.4️⃣5️⃣
Ta ce me kace
bawan Allah sake da baki '' cikin sakin fuska ya ce amma hajiya ke bakuwa ce Ko
?
Gyada masa kai ta yi alamun haka ne.
Mai saida nama yana cigaba da yanka naman ya
ce uhmm ai hajiya wannan a yanzu jikin Sarki ne.
Hajiya Hassana ta ce shin zan iya ganin Ahmad
din.
Kallon ta yake yana kokarin zuba mata naman
cikin teakaway ya ce hajiya beda girman kai amma inbukatar Kudi Ko taimako
yayan sa zaki nema dan wannan ƙaramin zaki ne.
Hajiya Hassana ta Murmusa ta ce kaiko inbanda
abunka ai ƙaramin
zakin sai ya zama babba.
Mika mata naman ya yi ta amsa.
Ganin Ahmad ya fito mutane sun biyo shi harda
yan mata.
Sai yauki suke sunga handsome gay jinin
sarauta.
ka ga ajiye mun naman nan ina zuwa tana Mika
masa ta nufo wajen motar tashi.
Kwankwas glass din motar ta yi dan yana
kokarin tada motar.
Da mamaki yake
kallon ta tare da sauke glass motar kallon take tare da hada fuska ya ce hajiya
lafiya kuwa yana mata nuni da hannu.
Murmushi ta yi tare da gyara Tsayuwar ta ta ce.
Ta ce ina son ka kai ni masarautar gheuzo dan
girman Allah Saboda...
Dakatar da ita
ya yi da hannu ya ce Saboda kiyi maula Ko me tsaki ya yi tare da rufe glashin
motar sa yabar wajen tare da tada mata kura.
Waɗanda
suka zo rakiyan Nasa kallon ta suke suka ce Keko hajiya Daga ganinki baki cikin
wahala meye na damun kanki a kan gidan sarauta in taimako kike nema ki
masarautar ki nemi aha daki da jakadiya in Allah ya sa kinada rabo zata saurare
ki.
Hajiya Hassana uhmm ta ce taya za a rakani
masarautar gheuzo dan ina bukatar taimako ta marairace fuska.
Kallon ta yake ya ce duk mai mashin din da
kika tara kikace masa masarautar gheuzo za a kaiki ba boyayyen waje ba ne...
Godiya tayiwa mai naman tare da komawa hôtel
din.
Reception ta
nufa ta nuna tanason layi na kasar.
Zabi suka ba ta akwai.
Layin MTN da MOOV.
Batayi wata wata ba ta ce ita MTN za a bata.
Tare da ba dan aiken kudi takoma dakin nata
tana jiran akawo layin.
Wani tafasassen daki na gani gado da kujeru
mai taushi da laushi ga TV plasma a jikin bangon.
Banda sanyi Ac babu abun da ke kadawa a dakin.
Zuwa ta yi ta dan kwanta tana tunanin mafita
'' ciza labban ta ta yi ta ce uhmm wannan Salihu na dauko wa kaina babban Aiki
mamakin kanta take da har ta damu da lamarin sa....
***********************
Ahmad Horn ya
yi mai gadi ya bude masa gate.
Yana shigowa parking space cikin hanzari ya
nufi cikin gida kai tsaye sashin fulani ya nufa dan ya yi mata wani magana Ko
me yatuna sai ya dawo baya Jin murya na tashi Daga cikin dakin kamar muryan
Maman Maryam yake ji abun ya yi matukar daure masa kai.
Kasa wuce wa ya yi yana kokarin bude dakin
yaci karo da Abban Marwan dake kallon sa azabure.
Dariyar yake yake masa cikin muryan sa dake
nuna fargaba ya ce Au Ahmadu kaine yana mai sutsa keyar kansa.
Ahmad ya ce eh ni ne Mama fulani na ciki kuwa.
Saurin katse
shi ya yi ta hanyar fadin ai babu kowa ciki.
Ahmad ya ce kamar muryan Maman Maryam na ji a
dakin nan.
Zare idanu baban Marwan ya yi ya ce Maman
Maryam kuma to meze kawo ta gidan nan.
Ahmad ya yi shiru kamar me nazari ya ce haka
ne kuma ainasan da tazo dakin Mamy zan ganta.
Barin wajen ya yi yana tafiya yana tunanin
anya kuwa ga kunnen sa beji masa daidai ba...
Da Sallama bakin sa yashigo sashin Mamy iske
Khadija kwance kanta nakan kafafun Mamy rike da waya tana chattin da kawayen
ta.
Mamy kallon sa take yanda duk yanayin sa ya
canza lokaci daya.
Zama ya yi kusa da ita yana kallon yanda Mamy
ke shafa kan Khadija ita Ko lumshe idanu take abun da Mamy ke mata ba ƙaramin
dadi yake mata ba.
Gyaran murya ya yi ya ce Mamy Maman Maryam
tazo gidan nan ne ?
Kallon shi take cikin mamaki take kallon sa ta
ce aida tazo da ka ganta ahmadu ya akai ne tana mai tsareshi da idanu.
Numfashi ya fesar ya ce kawai de nazo wucewa
ta wajen dakin Mama fulani na ji murya kamar nata.
Mama fulani kuma Mamy ta maimaita ta ce A'a
badai Maman maryam ba to me ze kawo ta gidan nan ba ta shigo sashi na in banda
abunka tafada cike da rudani.
Ahmad ya ce uhmm yana iya zama banji daidai ba
'' Mamy wai yaushe Samad zezo da Amarya tasa ne.
Khadija ta yi caraf ta karbi zancen ta ce wlh
Haba Mamy ace ya yi aure amma haryanzu ba zai dawo kasar shi ba yo me yake yi acen
din tafada tana me turo baki gaba.
Mamy ta ce to iyayena kun gama mun fada rike
kunnen ta ta yi ta ce korafi be karbu ba.
Naga dai duk kunada lambar wayar sa amma kun
tasani agaba da magana inba tsoro ba kirashi mana kai Ahmad.
Dariya ya yi saida kuncin sa ya lotsa ya ce
Mamy kin san zan iya gayamai kawai dai amsar daze ba ni shi nake tsoro.
Oho ni kuka raina kenan cewar Mamy tana
kokarin tashi dan shiga kitchen.
Khadija ta ce
Mamy wlh banson ki tashi inhar kina mun tausa...
Mamy Murmushi ta yi ta ce uhmm yar auta ai
tashi zaki yi mu shiga kitchen tare..
Ahmad ya ce Mamy mu je in tayaki mana tun da
ita ta kasa tashi gaba ya yi Mamy na dariya ita Ko sai zumbure zumbure take yi.
.
Ahmad ne ke feran doya dan yau Mamy ta ce doya
da miya zasuci da miyar kaza....
Yanka doyan har doyan yankewa yake hade da
bawon.
Mamy dake juya naman ta a kan wuta ta juyo
tana kallon yanda Ahmad ke ta dawaniya da doya.
Rike da baki ta ce yau naga ikon Allah aka ake
feran doya.
Da Yarima ne habawa tuni anwuce wajen..
Khadija da yanzu ta shigo kitchen din banda
dariya babu abun da take '' dago kai ya yi suka hada Idanu.
ta yi masa gwalo sossai ya ciza bakin sa ya ce
dani kike ta ce eh din kai fa.
Aiko bin ta ya yi aguje.
Mamy rike da baki
ta ce yau naga shashanci kullum ba sa girma ne.
Shiko Ahmad
har daki yaki bita tana kokarin shiga bandaki ya j'awo daman be wanke hannun sa
ba aikuwa ya shafa mata kaikayi wani uban tsalle khadija ta doka aguje tafada
bandaki tsutsa jikin ta tashiga yi..
Banda dariya
babu abun da yake yi harda rike ciki yabar dakin.
Abunka da farar mace nan da nan fatar ta ya yi
jajir ruwa take ta sakar wa kanta tana ayyana aranta wlh saita rama...
************************
Drever Samad
ne ke ta zarya a compound din gidan Karima yake jira.
Jin takun ta
ya sa yakoma da baya baya suka koma parking space..
Cikin kasa da murya ta ce Ali drever yaya
kasamu wani labari a kan su Abban Marwan kuwa.
Gaskiya bansamu ba yabata Amsa cikin yanayin
damuwa amma sainake ganin kamar sun fi mu wayau fa.
Karima ta ce kamar ya..
Numfasawa ya
yi ya ce duk sanda zanbi bayan su wuri daya kullum suke zuwa su dawo.
Cikin yanayin damuwa Karima ta ce to amma inda
suke tsayawa ka san inane.
Kada kai ya yi Alamun A'a.
Karima ta ce nex time ka tafi dani akwai abun
da zan duba.
OK karki damu yabata amsa cikin yin kasa da
murya ya ce ke ga Marwan cen zuwa maza kibi ta baya..
Babu ba ta lokaci tabar wajen cikin hanzarin
ta kallon ta yake Harta ba ce masa da gani.
Marwan ne yakaraso wajen yana kallon sa cikin
tuhuma ya ce Ali me kake yi anan kai kadai.
Murmushin dole
ya yi ya ce au daman aikena Mamy ta yi shi ne natsaya duba motar da zan fita
dashi.
Wani kallo
Sama sama yake jifan Ali da shi yana yatsine fuska.
Ya ce kai ai Mamy bakowa ba ce a gidan nan ba
ce matar barawo..
Firgit ya yajuyo yana nanata kalaman sa.
Bangane Matar
barawo ba ya ba shi amsa.
Marwan ya ce za ka gane ne inhar aka kore su
Daga masarautar nan kujira kuga abun da zebiyo baya.
Wuce shi ya yi
yana huci.
Ali cikin tsananin damuwa ya ce za su bar
Masarautar to su koma ina kenan wa'iyazubillah..
Dole ya san
abun yi.
Yafada tare da neman layin Samad be same shi
ba...
🇬🇦
Gabon
Baba Salihu
zaune shikadai a dakin sa yana tunanin yanda ze gana da yarima Samad.
Wata zuciyar ta ce inkai haka aika tonawa
kanka asiri kazauna dai matsayin da kake ciki shize fiye maka..
Karar wayar sa yadawo da shi cikin hayyacin
sa.
Yana Daga wayar ya yi sallama.
Daga can ɓangaren
ya ce ya shugaba gaskiya abubuwa suna tabarbarewa fa.
Cikin kaduwa ya ce banfahimta cikin tsoro da
fargaba yake magana Daga can ɓangaren
ya ce gaskiyar magana dole ne.
Yarima Samad
yakoma kwatano da zama.
Yawon da yake
yi dan neman ka ya isa haka.
Sannan akwai
wani zanen hoton wata Yarinya daya zana suna yanayi da Rahama har yanzu ya kasa
gane cewar wannan zanen ita ce matar da yake aure..
Idanun sa sun
rufe ya shugaba NA.
Baba Salihu cikin damuwa ya ce wai haryanzu
Yarima na yana bibiyan wannan hoton mafarki nasan shi ne yahanashi aure.
Daga can ɓangaren
ya ce aibe hakura ba rannan matar shi muka bar asibiti muka shiga gari da
wannan zanen hoton ka kadai ne beda shi shima dan Mamy tahana ne.
Baba salihu ya
numfasa ya ce turomin hoton zanen ingani.
Sannan dole
yakoma gida aikin sa na kano Ko babu shi komai ze tafi daidai InshAllah..
Daga haka suka
yi Salama..
Baba Salihu
cikin yanayin damuwa yake tuno Mamy ya ce baiwar Allah na cutar dake shekara
biyar.
Kuka yake
sossai tare da durkushe a kasa.
************************
🇳🇬
Kano.
Salma sossai
ta ji sauki har aka basu Sallama.
Bayan sun dawo
gida akai ta shigowa gaishe ta da jiki harda iyayen Al'amin.
Shiko Al'amin
Ko gezau bezo ba.
Sheik zaune
kusa da Salma ya ce mata sannu ta gyada m'asa kai.
Kallon ta yake
ya ce MashaAllah yanzu tun da kin dawo gida banda yawo kin san aure na kanki..
Wayar sa ce tafara ring yana dubawa yaga
nombar Rahama ne.
Cikin Jin dadi ta ce Abba ygida ya jikin
Salma.
Amsa mata ya
yi ta ji sauki.
Shiru ne ya
ratsa tsakanin su.
Sheik ya ce Rahama ta
Ta ce naam
Abby.
Yana ga kinyi
shiru gayamin mêke faruwa ne.
Salma Jin
furucin Abba dadi ta ji tana tunanin Ko itama duka tasha gun mijin nata.
Jin sheik na
salati ya ce Rahama garin yaya kika bari iska ke damun ki agidan auren ki.
Ke ce fa
kikewa mata ruƙiya yau shi ne ƙaramin abu ze gagareki maza ki farka in
barci kike ki yaki da kanki.
Daga jin labarin nan shaidanun Aljanune...
Sossai Rahama
ke Zufa ta ce Abby ka kara turomin wasu adu'oi masu karfi..
Abba ya ce
yanzu kuwa aikina WhatsApp da layin nan ta ce eh inayi Abba..
Daga haka suka
yi Sallama.
Ran Salma
inyayi dubu ya tashi ta ce chab ashe ma baduka tasha ba....
********
*************************
Yarima Samad Daga shi sai Rahama kadai ne
agidan.
Kallon ta yake ta gefen idanu yanda taketa kai
kawo a kitchen...
Uhmm taita
yawo da katon hijabi acikin gida saikace matar mamaci.
Ita Ko Rahama a
Nutse tagama girkin nata.
Ta gyara
kitchen tsaf..
Abinci ta jera
kan dinner table kamshin Abinci ba ƙaramin tadawa Yarima Samad hankali ya yi ba
Yana son ya yi
magana ya kasa.
Kallon ta yake
da mamaki bayan zumbulelen hijab dake sharan kasa da tasa.
Har nikaf taje
dakin nata ta dauko tasa ta ce azuciyar ta za ka ga karyan, wulakanci dani kake
zancen..
Kokarin daukan remote yake yi dan canza tasha
yaga tadawo falon ta zauna banda bakin kwayar Idanun ta babu abun da yake gani.
Cikin kidima ya
ce keee ina zaki je?
Kallon shi
take tacikin nikaf din ta ce hanyar waje ka ga nayi ?
Maida kallon
ta a kan TV tayi.
Sake da baki ya ce bayan katuwar hijab din
nikaf kika sako.
Ta ce kwarai
kuwa kaine ka koyamin in akwai namiji awaje in suturce jikina.
Kaman ce
rannan a daki cemin kayi indai na yawo tsirara inda namiji a daki yo meye
laifina takarashe zancen tare da maida kallon ta kan TV.
Tashi Daga zaune ya yi yana cijje labban sa
cikin tsawa ya ce ciremin hijabin nan tare da nufota ta gadan gadan cikin
zafin....
Ta ku har
kullum kyauta Daga Allah4️⃣6️⃣
Gadan Gadan
cikin zafin nama zafin nama yake kokarin cire mata hijab itakuwa gam tarike
tana fadin please ka sake hijab din wuya wayyo anty zecire mun wuya..
Jin karar
knocking Daga waje ya sa ya cika ta tare da komawa kan kujerar sa ya ce waye ne
cikin bacin rai.
Aminu ya ce dan iska to mune harda kulle mu a
waje.
Tashi ya yi yana tafiya yana tsaki murda
handle din kofar ya yi ya bude kofar.
Faruk da Aminu kallon shi suke yanda yake ta
cika yana batsewa shikadai.
Kusan a tare suka shigo falon '' Faruk ya ce
Madam ke ce anan kallo kike ne ya jefo mata tambaya yana kokarin hawa kan
matakalan step shida Aminu.
Zazzakar muryan ta yaji tana fadin eh kallo
nake sannun ku da zuwa ya gajiya tana magana hankalin ta nakan TV.
Aminu ya ce kalau muka dawo Madam Samad.
Yarima Samad tsaye yake kasa zaune danna wayar
sa yake yi.
Wayar sa ya fara ring ganin Maman Maryam ya sa
ya ɗaga babu ba ta lokaci.
Cike da nutsuwa yake yake gaishe ta ya ce ummy
kina araina ya kike ya mutan gida ina Abban maryam yake da makawfta duk ya jero
mata tambaya.
Daga can ɓangaren Murmushi ta yi tana
zaune kan kujerar mulki ta ce kowa na lafiya lau Abdul Samad amma ba ka tambayi
Maryam ba.
Ransa ne yabaci sai ya dake ya ce kash
narigaki a zuci kin rigani abaki.
Aidole in tambayi yar ƙanwata mana.
Dafatan tana
lafiya Ko tare da neman guri yazauna kan kujera 1str hankalin sa nakan TV.
Maman Maryam ta ce tana lafiya lau saide ba ta
gida taje unguwa inta dawo zan hadaku waya.
OK toh yabata amsa dan abar zancen.
Maman Maryam ta ce Ɗana.
Naam ya ba ta Amsa tare da maida hankalin sa
kan wayar dasuke yi.
Maman Maryam cikin iya bariki ta ce daman
sonake ince maka ina Matar taka take ka hadani da ita mugaisa mana wai ita ba
ta tambayar ɗangin
mijin ta ne koko feleke ta iya.
Murmushi ya yi saida kucin sa ya lotsa ya ce
kiyi hakuri zata San ku ne wataran.
Daga can ɓangaren
maman maryam ta ce Samad bangane zata san mu wataran ba ina matsayin uwar mijin
ta.
Shi ya sa auren yayan Malamai wallahi matsala
ne kardai ta shanye maka kurwa.
Samad Murmushi kwance a kan fuskar shi ya ce
babu kodaya ummy na InshAllah zan gyara kokarin katse hiran yake dan shi kwata
kwata beson korafi.
Uhmmm Ummy na inba za ki damu ba anjima
zankiraki yanzu fita zanyi ne yana kallon agogon hannun sa.
Maman Maryam ta hada rai sossai kamar yana
gaban ta ta yi tsaki amma beji ba.
Ta ce daman sonake kazo da Matar taka mu ganta
tun da rowar ta kake mana Ko hoton ta bamudashi.
SAMAD YA CE Ummy na ina me baki hakuri ba zan
zo da ita kwatano ba.
Saboda auren nan dai Auren biyayya ne ''.
Kallon Rahama
yake wanda shi take kallo itama tana jinjina kalaman auren biyayya daya
furta...
.
Cigaba da
magana ya yi kinga ba zan kawo ta cen kasar mu ba..
Harsai ta Mallaki hankalin kan ta.
Maman Maryam cikin fushi ta ce wani mallakan
hankalin kai daya wuce auren ka da tayi.
Ai tasan komai kaine kake mata kallon yarinya.
Ni dai ka taimaka inzaka zo shari'ar da za ai
nan da kwana shidda kuzo tare tun da ance befi kayi sati ba ka juya saiku juya
tare dan Allah narokeka.
Tagama kashe masa jiki cikin Sanyi murya ya ce
InshAllah zanzo da ita.
Sai dai ba zan barta a kasar ba.
Cikin Jin dadi Maman Maryam ta ce eh kan ya yi
ka ga zamu kulla zumunci.
Daga haka suka yi Sallama.
Ita Ko Maman Maryam suna gama waya da Samad
rawan murna take ta yi yar aikin ta ta fito tana dariya ta ce maman mu abun
farin ciki ne ya samu.
Cikin Jin Dadi ta ce eh wallahi kedai ɗana ne ze zo da Matar sa
kinga dole in taka.
Yar aikin ta ce mama nima ina tayaki murna
Daga hk tashige daki dan goge goge da mopin.
*************************
Yarima Samad
yana gama wayar da Maman Maryam dakin sa ya nufa kai tsaye dan shiryawa za su
je yawon neman baban sa dakuma hoton Mafarkin sa.
Wanka ya fito yana daure da towel iya kugun
sa....
Gaban miroir yatafi yana kallon kansa a madubi
tare da daukan mayukan sa masu dankaren kamshi ahankali yake shafawa a jikin
sa.
Kallon jikin sa yake yanda Ko ina da gashi ne
kwance luf luf gwanin ban sha'awa.
Sumar kansa yake kokarin tajewa dan yana dan
tara su kadan.
Kallon kansa yake ta cikin madubi ya ce
Uhmmm..
Bara in yi sauri na fita Ko Allah ya sa mudace
a yau dinnan.
Kayan da zai saka suna a gefen sa..
Wando Jean ne da riga maroon.
Saka kayan ya yi ba ƙaramin kyau ya yi ba.
Shi kansa ya san ya yi kyau hakan ya sa ya yi wa
kansa selfie.
Yana daukar hoto yaji sallamar Rahama ta shigo
dakin.
Ko kallon inda take beyi ba yaci gaba da
daukar hoton sa.
Cikin hanzari ya zura takalmin sa komboss
tafiya yake cike da izza da takama.
Haryakai bakin kofa yaji muryan ta.
Tana fadin Abba
na ya ce in gayamaka ba a ga hoton nan ba amma ya ce da zaran angani za a turo
Abdul Jalil da sako.
Jimm ya yi kamar me nazarin wani Abu..
Be ba ta Amsa ba ya sakai ya fi ce Daga dakin.
Itakuwa hakan be dame ta ganin yanda ya ba ta dakin
dan shigowan da ya yi ta ce ikon Allah badai ba ta waje ba.
Jibi yanda ya
hargitsa dakin nan kayan da yacire yanda ya watsar dasu a dakin take kallo da
mamaki.
Cikin hanzarin ta tashi ta gyara tare da maida
komai a muhallin sa...
Nan da nan
tagyara dakin har bandakin tashiga ta wanke shi tass..
Jin karar wayar ta ya sa ta fito cikin sauri
domin Dagawa.
Tana amsa kiran ta ce wacece ne.
Daga can ɓangaren
ta ce eh lallai na yarda kin aure Rahama murya ta kika mance..
Murmushi ta yi saida kuncin ta ya lotsa hijab
din dake jikin ta ta cire tare da nikaf din..
Ta ce Haba Asiya wace ni inmace dake kawar
Arziki.
Asiya ta ce ainagani kin canza layi baki
nemeni ba amma nida na damu dake har gida naje gun anty tabani takarashen
zancen cikin Jin dadi..
Rahama ta ce kiyi hakuri inada niyar in kiraki
natuba kawata..
Asiya ta ce yawuce ya mijin naki yake ne ?
Rahama ta ce kalau yake yafita ma.
Wai yaushe zaki zone nayi miss dinki.
Asiya ajiyar zuciya tasauke tana Lure da
Rahama duk sanda ta yi mata maganar mijin ta basar da zancen take tahanyar
dauko wani firan.
InshAllah Zanzo cikin Satin nan aikina
WhatsApp da layin nan Ko ?
Rahama ta ce eh da shi nake yi mu koma kan
whsap kawai Daga haka suka yi Sallama.
Itako Rahama kayan ta take hadawa zata koma
dasu dayan dakin dan tagaji da kwana kasa babu kwakwaran dalili bawai rasa
wajen kwanan akayi ba mulki dai ake nuna mata..
************************
Yarima Samad
yana saukowa kasa samun su Faruk ya yi har sun shirya.
Kallon Faruk
ya yi ya ce inafatan ka fito da wannan zanen hoton.
Faruk ya ce ya
za ai in manta da ranka yana Murmushi..
Aminu ya ce ina fatan yau bazamu dade ba Ko.
Kan wannan hoton wlh saikaita ba mu bakar
wahala kai wallahi mafarkin ka munafuki ne taya ze nuna maka mace a kano be
nuna maka gidan su ba..
Faruk ya ce kuma fa haka ne wlh sai dai ya yi ta
ba mu dan banzar wahala haba.
Samad da duk suka cika mai kunne da hayaniya
sunsan abun da yatsana kenan surutu.
Dakatar dasu ya yi da hannun cikin halin Ko in
kula da zancen nasu.
Ya ce akwai
wanda na daure acikin ku ne.
Duk wanda yaga be iya zuwa ya koma dakin sa
yazauna.
Mikawa Faruk
hannun ya yi Alamun ya ba shi zanen.
Faruk ya ce dan Allah malam mu tafi in mun
barka ka tafi kai kadai ba cewa zakai arasa gane inda kashiga..
Gaba suka yi
Faruk da Aminu.
Kallon su yake yana ciza yatsa lallai suncika
yan rainin wayau...
Binsu ya yi abaya
cike da dan saurin sa
************************
Rahama tana
kai kayan ta dayan dakin Idanun ta ya sauka a kan lefen da Samad yadauko Daga
gidan su Adamsy wanda tun da ya ajiye mata su.
ba ta bi takan su ba..
Kallon akwatunan take tsadaddu akwatina ne
wanda Daga ganin su za su kai a kalla dubu dari biyar...
Bude babban akwatin ta yi taga uban kaya
turame guda dari na Atamfofi ikon Allah tafada yayin da taga wasu a ciki an
dinkasu daidai size din ta.
Saita tuna
lokacin da Adamsy yazo yadauke ta yakai ta gun tela da su auna size dinta.
Murmushi ta yi me kama da ciwo ta ce Uhmmm
haryanzu Adamu bandaina sonka ba..
Bakin cikin rabuwa da Adamu take ta ce wayyo
ni Rahama Allah kai ka san daidaii ina rokon ka a kan falalar ka kasama
zuciyata hakuri da dangana..
Jiki Asanyaye tabude sauran akwatunan.
Su lesss da
materiel.
Hartakai kan ƙaramin
akwati da gold ne zalla a cikin su.
Mamaki ne yacika ta ta ce me zanyi da uban
kayan nan harda kayan darirukan milyoyi.
Wayar tadauka tare
da dannawa Anty kira.
Daga can ɓangaren ta ce my Rahama
dafatan kina lfy.
Rahama ta ce
kalau nake uwata ta kaina..
Murmushi anti ta yi duk sanda ta ji Rahama ta
ce mata haka to akwai magana mai muhimmanci da za ta yi mata.
Rahama ta ce antina akwatuna lefe ne aka ajiye
mun a dakina wanda Adamsy ya hada ne shi ne Abban Adamsy ya ba shi yakawo nan
gidan da sunan nawa.
Anty ta ce wa
'akaba.
Rahama ta yi shiru
batasan yanda zata fadi sunan sa ba..
Anty ta ce haba yata yimun bayani wa' aka ba
nace.
Cikin yin kasa da Murya ta ce me nan gidan.
Murmushi Anty
ta yi ta ce Haba Rahama ki maida hankalin ki waje daya nasan kinada tarbiyya
kokarin da kikai na zama gidan miji bakowa bane ze iya ace Daga wajen daurin
aure a canza a ba ka wani daban kinyi namijin kokari Rahama ta.
Abun da nakeso
dake ki dauki komai ba komai bane kamar yanda naga mijin naki yana da saukin
kai ga girmama na gaba da shi ki kalle shi da kyau Rahama duk inda ake son
namiji yakai kyakywa mai Addini ga nutsuwa.
Hamdala
zakiyiwa ubangiji ki..
Kema kam duk abun
da na lissafa a kan sa Allah yabaki '' cancantar kune ya sa Allah ya hada auren
naku '' uhmm Rahama ki kama mijin ki dakyau ni uwa ce ba ni ce zan koyar dake
yanda ake kama miji ba.
Amma InshAllah
zanturo da Asiya suna dan saki ahanya koda ta whsap ne inyakama suje gidan ki
za su je.
Kinga Asiya
kawar ki ce ina tabbacin bazata ci Amanar ki ba itama Ƙanwata haka.
Cike da
nutsuwa ta rinƙa Jan hankalin Rahama...
Ta ce su
wayannan kayan da suke a dakin naki wanda Adamu ya hada zan gayawa baban ki.
Muji abun da ze
ce akai..
Rahama ta ce Anty
nagode sossai samun uwa irinki sai Antona.
Cikin Jin dadi
da Begen juna suka yi Sallama....
Rahama maida kayan gefe daya ta yi tare da
gyara dakin dan ya yi kura ka santuwa ba a kwana ciki..
***********************
Yarima Samad
wani unguwa sukaje rijiyar lemu daidai wani babban Massalacin yan Darika ya
paka motar sa..
Faruk bude murfin motar ya yi yana kallon
yanayin unguwar.
Aminu shima fitowa ya yi ya ce ka ga la'asar
takusa.
Kallon Samad suka yi da Alamun jira yake su
bude masa kofa.
Faruk y abude
masa ya ce maza kafito inrufe motar.
Ka san yanzu za
a tada Sallah.
Samad ya ce to l'imam munji tare da yin gaba
dan ɗauro Alwala.
Ciki sauri sauri suka yi Alwala suna shiga
Massalacin aka tada Sallah.
Bayan sun idar ne suka dan zauna yin Azkarai..
Aminu duk
yarigasu fitowa Daga Masallacin..
Suna fitowa
suka same shi atsaye yana jiran su...
Samad kokarin
bude murfin motar yake yaji sautin muryan mace Daga bayan sa.
Firgita ya yi dan Jin muryan ya yi Daga sama.
Nan da nan ya tsuke fuskar sa babu digon
Mutunci ya fuskance ta..
Ya ce keee...
Wai meyasa ku
yaran matan yanzu Sam bakuda kamun kai ne..
Kin tsaya mun
a ka.
Fadawa zaki yi
a jikina ne
Kallon banza
yabita da shi tare da bude murfin motar yashiga.
Su Faruk da
Mamaki suke kallon Yarinyar dan sunga ba ta da makusa amma matar shi tafita
kyau.
Kwabe baki suka
yi ganin yanda boss ke ta zuba ruwan masifa.
Wata
matashiyar yarinya ce wacce ta dade tana kallon hoton Samad a labaran duniya
kuma ta dade da fadawa kogin son sa har gidan su kallon zautaciyya ake mata
fadi suke yi duk arzikin uban ki bekai na yarima Samad ba.
Yan uwan ta da
iyayen ba ta shawara suka yi data hakura da shi dan ba Ganin shi za ta yi ba
har Abada ba....
Hawaye sun cika Idanun ta dan ko tun da ya
tsare ta da ruwan masifa bakin ta mutuwa ya yi Daga ta ce Assalam alaikum shi
ke nan cibi yazama kari..
Ganin har sun
shige mota ne suna kokarin barin unguwar.
ta yi saurin tarar me napep ta ce dan Allah bi
bayan bakar motar cen mercendez...
Tayi mai nuni
da hannun ta.
Inna ce zan
tsaya daukar mota ta za su ba ce mun da gani tafada cike da damuwa a kan fuskar
ta.
cikin Jin tsoron kada tarasashi lokaci daya..
Me nepep juya
akalar keken nasa ya yi yabi bayan su.
Bama nisa suka yi ba daidai gidan Alh umar mai
salula suka yi parking din motar tasu..
Cikin sauri Faruk yabude wa Samad kofa.
Kokarin dauko zanen Daga cikin motar yake
Idanun sa ya yi har ba da yarinyar tana kokarin fitowa Daga napep din..
😳😳
Tana kokarin
fitowa Daga napep din...
Tsaki ya yi yana
maganar zuci.
Dauko zanen ya
yi suka nufi jama'ar dake wajen bakin su dauke da sallama Farruk ya ce dan
Allah tambaya nake.
Cikin su wani ya ce Allah ya sa mun sani.
Dan Allah muna neman Alhaji Salihu Turaki.
Cikin mutanen da suka iske zaune ya ce gaskiya
bana tunanin a wannan unguwar yake.
Yarinya da ta biyo karasowa ta yi tana
fuskantar Faruk ta ce wa kuke nema ?
Farruk ya ce ke yar unguwar nan ce ?.
Ta ce eh mana
tana me kallon Samad daya juya mata baya yana magana da wasu.
Faruk ya ce Alhaji Salihu Turaki muke nema.
Yarinyar mai suna Samira ta ce ayya ban san
wannan sunan a unguwar nan ba.
Amma sunan
yamin kama da sunan wani Sarki a kwatano.
Muna gani a
jaridu.
Faruk ya ce eh
to bashi bane.
Zanen hoton ya
nuna mata kota San me kama da wannan..
Samira ta ce eh tabbas nasan nataba ganin
fuskar nan a rijiyar zaki.
Makarantar ɗana
bari ne..
Sunan yarinyar
nan na mance gaskiya.
Faruk ya ce dagaske kike dan Allah bamusan
wasa fa.
Ta ce wlh
dagaske nake maka yar uwar ku ce.
Cikin zumudi Faruk ya samu Yarima Samad da
yaketa tambayar sunan mahaifin sa da zanen hannun sa.
Ya ce kai dan Sarki Albishirin ka yau burinka
daya ze cika saura daya.
Da sauri Samad yabar wajen da yake ya ce musu
ya gode.
Dawowa ya yi wajen Faruk ya ce ba ni insha
mana.
Faruk ya nuna Samira ya ce ka ga wannan
yarinyar ta ce tasan zanen nan a rijiyar zaki....
Samad kallon rashin yarda yake mata yana
kallon zancen ta amatsayin karya ne dan tasamu suyi magana ne ta yi hakan..
Kallon ta yake
yana nazartan ta cikin yin kasa da murya ya ce kin tabbatar da kintaba ganin
wannan zanen..
Eh nataba gani nasan ta munyi makaranta daya.
Aminu ya ce
tana nan batayi aure bane Ko ta yi ?
Samira ta ce
gaskiya ban san wannan ba saide naje na bincika..
Numfashi Samad ya fesar yana kallon ta ya ce
wlh inkikai wasa da hankalina zaki sani kalleni da kyau banson araina mun
wayau.
Fuskar sa a
murtuke.
Faruk ya ce haba Samad tun da ta ce ta santa
ai baza ta yi karya ba...
Samira tagama lura yanzu duk abun da ta ce ze
mata dan yana son yaga wacce yake nema da Jan ido.
Cikin Jan aji itama ta ce na tafi naga sai bin
ku nake kuna dizgani gaban mutane.
Aminu ne yasha gabanta ya ce haba wane mu ''
yanzu ki ba mu nombar wayar ki.
Tare da mika
masa wayar cikin Jin dadi ta karba tasa masa nombar wayar ta.
Samad be bar abun
da yakawo su ba yacigaba da tambayar Salihu Turaki kowa sai ya ce besan shi ba.
Dawowa ya yi wajen su Aminu ganin yarinyar ta
tafi ajiyar zuciya ya sauke.
Ya ce yww
Faruk wancen yarinyar ka ga tafiyar ta Ko ?
Dan kada ta
sake biyo mu.
Farruk ya ce
eh ta tafi amma na karbi nombar ta nabata nawa tun da ta ce tasan ta.
Make kafada Samad ya yi ya ce oh wannan
matsalar kuce wlh kar ka sakoni koda wasa kar ka nuna mata gidana wlh.
Maganar zanen
hoton.
Inka shirya ta raka ka inta kaika kai kuma saika
kaini inaga haka ze fi.
Aminu ya ce kwarai kuwa hakan ya yi Yarima.
Maganar neman
baban ka Samad Ko zamu canza kasa ce.
Samad kallon sa yake ya ce meyasa kace haka
Aminu.
Numfashi ya fesar ya ce jikina yana ba ni yana
raye kuma baya cikin Nigeria.
Wahalar da
kanmu a banza muke nifa a ganina.
Faruk ya ce gaskiya ne wlh adai duba lamarin
nan.
Kokuma musa
rokon Allah a kan a duk inda yake Allah ya bayyana shi.
Samad ya ce na fahimce ku hakan ma mafita ce
babba.
Aminu gyara Tsayuwar sa ya yi ya ce to me ze
hana kasa matar ka Rahama ta rinƙa tashin ɗare
tana rokon ubangiji ya yi gaggawa bayyana inda yake a tunanina.
Kuma surukin ka mahaifin ta babban malamin ne
koshi mu nema ya sa mu a adua mana duniya fa da fadi cewar Faruk taya zamu
gansa cikin dumbu jama'a bayan ba mu San inda yake ba..
Sossai Samad ya yi Amanna da bayanan su.
Ya ce to mu je
kai tsaye gidan sheik imam basai ankoma gida ba..
Cikin gamsuwa
da bayanan sa suka bude masa murfin motar baya..
Shiga ya yi
Suma suka
shige motar. suna Dagawa jama'ar wajen hannu Alamun godiya da kulawar da suka
basu.
*************************
Al'amin tun da
Salma tabar gidan sa sai yau ya samu yazo gidan nasu.
Sheik ya yi masa
fada sossai da waazi da illan cin Amanar iyaye hakuri ya ba shi ya ce yarufa masa
Asiri kar jama'a gari suji.
Sheik ya ce uhmm Al'amin kenan kai kana
tunanin ban san halin da kake ciki bane ka san Allah gafurum rahim ne ba a
shiga tsakanin bawa da mahallincin sa.
Zancen Salma
ta koma bema taso ba.
Duk yanda Al'amin ya yi sheik ya ce babu
wannan zancen fur yakiya akarshe ya ce to kana iya zuwa kasamu Salma inta
amince saiku koma inkuma taki sai dai kabarta zuwa nan gaba.
Jiki babu
kwari Al'amin ya shiga Daga ciki.
Dan ganawa da
Salma.
Mama na ganin
sa habawa tarufe sa da masifa dan iska shege la'ananne yanda ka cutar mun da yata
InshAllah kaima za ka wulakanta.
Sossai Al'amin
yaji haushin mugayen duar da take tamasa cikin rashin kunyar sa ya ce Mama
karki sake zagina fa dan kina tunanin kinban jakar yar ki aini wallahi diyar kishiyar
ki Rahama na so abani dan ba ta samu tarbiyya ba..
Anty cikin sauri takaraso wajen tana kallon
yanda Al'amin ke zazzaga wa Mama ruwan jaraba.
Anty ta ce habawa Al'amin rashin kunyar ka
haryakai ka zagi uwar matar ka.
Sunne kai ya yi ya ce kiyi hakuri maman Rahama
wlh matar nan ba ta da mutunci ne.
Kuka Mama ta
saka iya karfin wiwi ta ce Abubakar kana ina ne.
Yau ga dan
iskan surikin zamani.
Abdul jalil
dake shigowa cikin gidan ya ce ai bayanan yafita lafiya kuwa ganin Al'amin
yanda yake cika yana batsewa..
Mama ta ce
wannan dan rainin wayon ne mana yazo waishi ze tafi da Salma.
Abdul jalil ya mikawa Al'amin hannu suka yi
musabaha kallon Al'amin yake ya ce kayi hakuri antina bazataba koma yanzu ba.
Salma ce ta fito Daga dakin ta sanye take
cikin doguwar hijab har kasa..
Karasowa wajen
nasa ta yi tana masa kallon tara saura kwata..
Bismillah ta
ce masa suka yi zauren gidan nasu.
Gyara
Tsayuwarta ta yi tana kallon sa Daga kasa har sama.
Tana kar kada
kafa.
Amma wlh kacika dan rainin wayau Al'amin
harkai kana tunanin zankoma wannan kazamin gidan naka kurkuku wanda a agidan
namu Ko me gadi yafishi mukami..
Wlh ka yanka
mun takardan Saki wawa lusarin namiji.
Al'amin banda
tsuma babu abun da jikin sa yake yi ya ce nine lusarin lallai zan tabbatar miki
da hakan.
Zancen saki
kuma ai babu shi tsakanin mu dansai na wulakanta ki kamar yanda kika mun..
Murmushi ya yi
me kama da ciwo ya ce eh daman nasan ke jarabbabiya ce shi ne nazo indaukeki mu
je in rage zafi karuwar gida kawai..
Salma zata Daga hannu ta mare sa Abdul jalil
ya rike mata hannu'.
Girgiza kai yake
yi ya ce antina kada kiyi haka komai lalacewar sa mijin ki ne iname baki hakuri
ki shanye koma mene ne ya yi miki.
Kallon sa
yamaida kan Al'amin ya ce kaikuma kaine shugaban ta intayi kuskure ka gyara
mata ta hanyar nasiha yakarashe zancen tare da fita Daga gidan yabar su nan..
Kallon shi
suke har ya ba ce musu da gani.
Salma ta ce ni
zanshige wataran zamu hade ai.
Tana hararan
sa tabar wajen sai wani yauki take yau gâta isassa.
Kallon takun
tafiyar yake ya ce ai Salma ban dandani zumar ki ba har yanzu sonake ki shigo
hannun na.
Zan canza miki
gida fita Daga gidan ya yi yana tunanin yanda wasan ze kaya tsakanin su..
Salma na
komawa gida Anty ta tareta ta ce karki damu da Abun da ya yi tashin balaga ne
ke kuma kisan matsayin sa.
Ki girmama
shi.
Mijin ki ne
Aljannar ki na tafin kafar sa.
Hannun tayiwa Anty
Alamun ya isa haka tana kunkuni ta ce ainasan da haka Rahama ce ba ta sani ba
tana cen gidan da ba a son ta..
Fuuuuu tawuce cikin
dakin su..
Anty da mamaki
take kallon ta ta ce wai ita wannan yaushe za ta yi hankali ne.
Uhmm Allah
yashirye ki tafurta tare da barin wajen...
**********************
Sheik zaune
kofar gidan sa shida Aminin sa Isa.
Suna tattauna
tafiyar da zasuyi zuwa kasar Gabon.
Gwanati ta gayya
ce shi zuwa taron walimar daurin auren diyar shugaban kasar Gabon.
Parkin din
motar da akai daidai kofar gidan nasa..
Murmushi Sheik
ya yi ganin anrubuta Samad a jikin motar.
Aminin sa ya
ce kamar surukin ka kobashi bane yana kallon Samad dake kokarin fitowa Daga
motar.
Sheik ya ce eh shi ne ashe ka gane shi.
Eh mana dole
in gane shi ka san wajen daurin auren nan jinai yana fadiwa mai martaba wani
Samad din za a daura wa aure..
Sheik ya yi Murmushi
ya ce au Ko ni ne hakan zancen daga zuwa daurin aure sai ta juye dani..
Fuskar su
dauke da Murmushi suna kallon Samad dake tunkaro su
Shida abokan
sa..
Cike da
nutsuwa suka karaso kan su akasa suka durkuse kasa cikin ladabi suka gaida
sheik da Aminin sa.
Sossai suka
amsa musu cike da fara'a.
Sheik. Ya ce
kace munada manyan baki.
Muje Daga ciki
Ko.
Tashi suka yi tare
da Aminin sa.
Suka yi ciki
Samad da abokan sa suna bayan su.
Direct dakin
baki yakaisu tare da ajiye musu ruwa da lemu a gaban su..
.
Yarima Samad ya
ce sheik imam mungode sossai da karramawa..
Sheik. Ya ce
anzama daya ya Rahama take ?.
Cikin Jin
kunya ya ce tana lafiya lau.
Aminu ne ya yi gyaran murya yasoma yiwa sheik
bayanin dalilin zuwan nasu...
Sossai sheik
da Aminin sa suka jinjina Al'amarin
Sheik ya ce yanzu
kimanin wata nawa baku ganshi ba.
Yarima Samad cikin yin kasa da murya ya ce
shekaru biyar kenan har muna neman na shidda..
Kada kai sheik
ya yi ya ce eh lallai andade Allah ya bayyana shi.
Dukan su da
Ameen suka amsa.
Kallon Samad
ya yi ya ce kar ka damu zamu tayaka da adua.
Kaima ka dage
har tashin ɗare kar kayi
wasa dashi.
Samad ya ce
InshAllah.
Adu'oi
yarubuta masa masu muhimmancin
Jikin wata
farar paper.
Masu karatu in
kuna bukata zan turo muku very important wlh..
Mika masa ya
yi ya ce sadaka kada kayi wasa da shi ɗana
za ka ga haske.
Sannan kasa
Rahama ta tayaka nasan ba ta da sanya wajen sallah ɗare.
InshAllah za a mata magana Daga haka suka
tashi har wajen mota suka yi masu rakiya shida Aminin sa.
saida motar tasu
tabar unguwar Sannan suka juya shida Aminin sa..
Suna yaba hankali
da nutsuwa irin ta jinin saurata basusan dawan garin ba..
*************************
🇧🇯
Hajiya Hassana
daidai kofar masarautar mai mashin ya ajiye ta....
Ta sallame shi
tare da nufo kofar masarautar gheuzo.
Kallon yanayin
tsarin gine ginen su take yi yanda aka kawata wajen sossai..
Gwanin ban
sha'awa.
Kwankwasa
kofar ta yi ya yi daidai da ana kokarin budewa Yarima Ahmad kofa zefi ta yana
cikin motar sa.
Sauke glashin
motar ya yi yana zare idanu ganin hajiya hassana da ya yi cikin hanzari ya fara......
Ta ku har
kullum kyauta Daga Allah4️⃣8️⃣
Cikin hanzari ya
fara kiciniyar bude kofar motar sa '' cikin azama yataho gaban ta kallon ta
yake tare da sauke fask mask dake fuskar sa.
Baiwar Allah me kike nema ne wai dan Allah.
Meyasa ku mutane bakwa gane maula ba sana'a ba
ce yakarashe zancen yana nuna mata hanya data wuce Daga nan..
Hajiya Hassana
cikin dan ba ta rai yaro ƙarami na gayamata kalamai daya zo bakin sa, ta ce uhmm kai
Ahmad ashe haka kake maganar mutane gaskiya ne kenan..
Kallon rashin fahimtar inda zancen nata ya
dosa ya fara ya ce bangane zancen mutane ba wani abu akace miki nayi..
Gyara Tsayuwar
ta yi ta ce, kwarai Kuwa an gayamin kana da girman kai sabanin yayan naka.
Kuma ni ba maula nazo yi kai kanka ka san nafi
karfin haka..
Kallon ta yake yanda ta hada rai take gayamai
maganganu.
Daga kasar Ghana nake.......
Aiki nake nema
kuma a gidan sarauta nakeso dagaske nake maka ba maula nazo ba ka yarda dani
Wani kallo
yake bin ta da shi masu tarin ma'anoni ''
Kinga dan
Allah ba na son shishigi
Bama bukatar
ma'aikata a masarautar.
Tun da angaya
miki inada girman kai meye na tsaida ni yakarashe zancen tare da komawa wajen
motar sa.
Kallon banza
yake ta bin ta dashi.
yana shiga motar yakara gaba
kallon sa take harya fita layin.
Karasawa wajen
kofar shiga masarautar ta yi taci Sa'a khadija ta fito yiwa kawar ta rakiya.
Inawuni ta ce musu kallon ta suke suke..
suka amsa mata da lafiya lau ne.
Tare da wuce
ta.
Kawar khadija ta
ce wannan matar kuma Daga ina tana kwabe baki.
Khadija ta ce
ina zan sani nima hk nagan ta..
Ciki gaba da
tafiyar suka yi inda suka tsaida me napep.
Kawar khadija na
hawa napep
Khadija ta
juyo da nufin komawa ciki.
Hajiya Hassana
ta tareta cikin damuwa kwance a fuskar ta ta ce dan Allah baiwar Allah ki
taimaka mun inshiga masarauta aiki nake nema kudina ne suka kare Daga nazo
neman mahaifina gashi ina son komawa kasar mu Gabon kudin jirgin da gindin sa
yazauna hôtel din ɗana
sauka yau kudina zekare ban san ya zanyi ba insuka koreni ba..
Khadija ta ce
subuhannalah wayyo baiwar Allah kinban tausayi.
Kin buga gidan
ne ba a bude miki ba ?
A'a ina dai
kokarin bugawa naga wani matashin saurayi ya fito a mota kin saurarena ya yi inaga
sauri yake.
Khadija ta ce
Ayya haka yake kiyi hakuri nasan yaya Ahmed ne, zan taimaka miki InshAllah bara
inshiga ingayawa Mamy intaban izini zanshigo dake takarashe zancen tare da
barin wajen...
Hajiya Hassana
ta ce uhmm Allah ya sa ta amince dan wannan bukata ta shi ne farkon nasara ta
InshAllah..
Khadija na isa
sashin Mamy ta iske ta ta yi uban tagumi batayi wata, wata ta ce Mamy na wai
haryanzu ba za ki rage damuwa ba.
Kinga wata
bakuwa awaje ta ba ta labarin yanda suka yi ta ce kuma fa Ahmad kin sauraren ta
ya yi yawuce.
Mamy ta ce gaskiya
be kyauta ba ki je ki shigo da ita muji me tazo dashi.
Cikin Jin dadi
ta tafita wajen
Dan ta shigo
da hajiya hassana.
*************************
Fulani da
Abban Marwan zaune suke fuskokin su dauke da damuwa.
Marwan cikin
bacin rai ya ce wlh Mamy kashe Yarima ya kamata muyi da matar sa.
Kokuma a raba su.
Idan anje miki
ya kusance ta karkiyi Gardama wallahi.
Cikin takaici
Abban Marwan ke ta huci SAMA YA CE AI INSHALLAH ba zai kusance ta ba dan
haryanzu beda karfin sha'awa a jikin sa.
Fulani ta ce
injiwa ya gayamaka haka bakada labari ne.
Bokan daji
cewa ya yi wallahi rannan kadan yarage be kusance ta saida suka sauya mata
halittar ta zuwa na kunama shi ne dalilin dayasa be aikata abun da ya yi niya
ba.
Dankali Abban
Marwan ya furta nan take wani Zufa ya keto masa duk sassar jikin sa..
Kiyi hakuri
Fulani in Allah in Allah ya yarda da matar tasa zezo..
Ai kinga
kwanaki da Samad zeje kano Mai martaba ya yi na'am da tafiyar sa yanzu kuma ya
fara Jin haushin haka har yana mummunar furuci a kan Yaya Salihu..
Wlh koda mai
Martaba kadai da ita shegiyar matar Samad zamu iya rusa su gabadaya.
Nifa har Mamys
sonake tabar masarautar nan to zaman me take yi ne yafada cikin Daga murya...
Fulani ta ɗara ta ce kai ai Mamy da
kake gani muguwar icce ce bakar munafuka ce ai yanda mijin ta yabar Masarautar
nan InshAllah itama tana ji tana gani zata barshi bari har surukarta tazo ni
Fulani wlh saina nasa sun zama abun tausayi acikin masarautar nan....
Dariya Marwan
ya yi ya ce nima dai yanzu na ji bugu.
Har labari
yazo mun wai Mai martaba yana son ya Nada Yarima Samad a matsayin Sarki kiji
fa.
Yana kallon
uwar sa.
Dafashi suka
yi shida Fulani suna bubbuga bayan sa Alamun rarrashi.
Kwantar da
hankalin ka Marwan InshAllah Burin su ba zai cika ba...
**********************
Da sallama
bakin su suka shigo Sashin Mamy khadija na gaba Hajiya Hassana nabiye da ita
abaya....
Mamy dake
zaune tana canza channel ajiye remote din hannun ta ta yi fuskar ta dauke da
Murmushi ta yi sannun ki da zuwa ga waje nan ki zauna.
Hajiya Hassana
neman waje ta yi a kasa ta zauna cike da ladabi take gaishe da Mamy..
Mamy ta ce dan
Allah tashi ki koma kan kujera.
dan Allah kiyi hakuri a kan abun da Yarima
Ahmad ya yi miki..
Hajiya Hassana
Murmushi ta yi ta ce haba ai yaro da nakowa ne wlh bakomai bane '' Inkika duba
wani ɓangaren yana da
gaskiya yanzu mutum ba abun yarda bane..
Kuma zama ka
san ya yi min dadi kada ki damu nagode da kulawa.
Mamy ta ce haka
ne kuma Amma kasa kyakyawan niya InshAllah baza a ci galaba a kan ka ba...
**************************
Gabon 🇬🇦
Cikin tashin
hankali baba Salihu yake kallon computer dakin nasa..
Ganin hassana
hankalin sa ya yi mugun tashi ya ce wannan matar me take nufi ne wai haukar
taje tafadawa mata ta Ko sotake ta tona mun asiri asan inda nake..
Wata zuciyar ta
ce tome abun damuwa kawai kabar kasar..
Ya ce A'a
kozan ban kasar nan sai nayi yanda za a yi wannan matar ta dawo Gabon InshAllah
Ransa a
matukar ba ce yakira me bashi labari.
Bugu daya ya
Daga..
Daga can ɓangaren ya ce ya shugaba na
ji muryan ka sai a hankali..
Baba Salihu ya
yi masa bayanin matsalar daya kunno kai
.
Jinjina
Al'amarin ya yi ya ce ka san dai ina kano Ko amma akwai wanda nayarda da shi anan
kwatano kuma amintaccen yarima Ahmad ne zansashi ya sa idanu a kan ta.
Ba tare da ya
san dalilin yin haka ba.
Cikin. Gamsuwa
da bayanan sa baba Salihu ya ce pls ka taimaka mun dan banson duk shirina
yatashi a banza ta dalilin ta..
Daga haka. Suka
yi sallama.
Kasa zaune ya
yi yanata safa da marwa a dakin nasa..
*************************
🇳🇬
KANO
Horn suka yi
mai gadi ya wangale masu gate....
Parking space
suka ajiye motar..
Faruk ya
zagayo dan budewa Samad mota
Sai gani ya yi
ya bude amma be fito ba.
Ya saura
acikin motar be fito ba
Aminu ya ce, wannan
lafiya kuwa shibe fito ba.
Faruk ya ce ka
kyaleshi Sarauta ce ta motsa naga dai yanzu yagama waya.
Zomu shige
ciki inya gama ya fito dan kansa.
Barin sa wajen
suka yi..
Tare da shiga
cikin gidan.
Rahma zaune
take duk hankalin ta yatashi sossai Saboda mummunar mafarkin da tayi.
Ganin su Faruk
sun shigo Daga cikin gidan '' cikin sauri sauri ta nufo su.
Fuskar ta babu
walwala ta ce sannu ku da dawowa
Yawwa suka
amsa mata.
baza idanu take yi inda zata ga Yarima Samad
ya bullo sai gani ta yi shiru ne..
Kallon ta
tamaida a kan su Faruk dasuke kokarin hawa kan matakalan step..
Da kakkausar
murya ta ce ku daka ta nace Ko ?
Da mamaki suka
juyo suke kallon yanda Idanun ta suka kada lokaci daya.
Faruk ya ce
Madam Samad lfy kuwa ?
Ta ce ina fa
lafiya kunshigo gida babu bayanin da kuka mun.
Ina Mijina
yake kuka dawo ku kadai bayan tare kuka fita kallon agogo ta yi ta ce karfe
goma ɗa rabi na ɗare..
Ina magana
kunyi shiru.
Aminu ya ce
yana cikin mota zaune muka barshi.
Be gama rufe
bakin sa.
Tayi hanyar
wajen aguje..
Har buge kafar
ta ta yi dan sauri.
Wajen motar
tasa ta nufa mutuwar tsaye ta yi ganin..
Taku har
kullum kyauta Daga Allah4️⃣9️⃣
Mutuwar tsaye
ta yi ganin Yarima Samad hancin shi na fitar da jini ya jingina kansa jikin
kujerar mota numfashin sa nata fisga sama_sama harya fara fita hayyacin sa.
Sossai
hankalin ta ya tashi batasan lokacin data shiga taba jikin sa ba, jikin ta na
rawa aguje takoma gidan gudu take ba ta ganin inda take jefa kafafun ta.
Faruk takira
sunan sa da karfi har gidan ya amsa da sautin muryan ta.
Faruk dake kokarin canza kayan jikin sa.
Jin muryan
Rahama ya sa suka fito cikin hanzari shida Aminu.
Da sauri sauri
suke saukowa Daga kan matakalan Step.
Rahama na
ganin sunfito.
Cikin fita
hayyacin ta datayi ta ce Dan Allah kuzo mu je bakin ta na rawa '' ku taimaka
mun mijina ba ta jira cewar su ba ta yi wajen a guje.
Cikin hanzari
suka take mata baya kokan su Iso
Har tana
kokarin fiddo shi Daga motar da iya karfin ta.
Faruk a razane
ya ce Abdul Samad cikin tsananin tashin hankali suka tara hannu shida Aminu
wajen ciccibar sa zuwa daki...
Daga shi suka
yi cikin tashin hankali Rahama ta ce ina zaku kaishi ne.
Ku dawo da shi
mu je asibiti ta fada cikin raunin murya.
Faruk ya ce
kibari a dai fara du bashi mugani suna cigaba da shiga ciki dashi.
Kan kujerar
3str din falon suka ajiye shi..
Aminu ya ce
yanzu wani likita ne zamu kira ya duba shi.
Rahama dake
arude shafa fuskar Samad ta yi ta ce akwai docto family house din mu zan kira
Abbana ya turo mana shi..
Cikin hanzari
tadauko wayar ta tare da dannawa sheik kira.
Wayar sa ta yi
ring har ta katse ba a Daga ba.
Tallafo kansa
ta yi tana ta masa fifita.
Ganin Zufa
yake ta yi duk karfin Ac dake dakin.
Aminu ya ce
basu Daga bane yana tambayar ta.
Eh be Daga ba
kila ya kwanta ne amma bari inkara mama ta.
Takarashe
zancen tana mai dannawa anty kira.
Bugu daya anty
ta Daga.
Cikin
sheshekar kuka ta ce anty dafatan kuna lfy dan Allah nombar docto ishaq zaki ba
mu nakira Abba na be Daga ba.
Anty cikin
kidima ta ce subuhannalah daughter meyake samun ki ne bakida lfy ne wayyo
gayamin kinyi shiru cikin gigita take magana duk tabi ta rude.
Rahama cikin
sassauta murya ta ce ba ni ba ce.
Shi ne beda
lafiya.
Idanun ta na
Shiru ta yi Jin
yana motsa hannun sa na dama.
Jefar da wayar
ta yi ta nufesa hannun ta Daga cikin kuka ta ce Faruk dan Allah kabani ruwan
zam_zam in akwai agidan nan in babu kaban ruwa pls tafada cike da bukatuwa..
Faruk cikin
hanzari yatafi dan cika umarnin ta.
Anty sai hello
hello take ta fadi amma shiru take ji sai tashin maganar da suke yi a falon
take ji.
Hakan ya sa ta
kasa kunnen ta..
Ganin Rahama
ta ma mance da ita hakan ya sa ta katse wayar tare da lalubar lambar docto
ishaq.....
Faruk hannun
sa dauke da ruwan zam zam ahannu cikin hanzari yakaraso falon yana mai kokarin
mika mata..
Bata karba
Daga hannun sa cikin sanyin murya ta ce dan juye mun a kofi.
Adu'oi take ta
karantowa tana tofah masa a ilah'irin jikin sa..
Samad Idanun sa a lumshe.
Ajiyar zuciya ya soma saukewa ahankali yake
kokarin Daga hannayen sa.
Ganin haka ya sa Rahama ta yi saurin Daga shi tare
da daura kansa kan cinyar ta.
Faruk miko
mata ruwan ya yi ta karba cikin sauri.
Nan m'a ta
shiga karanto adu'a sossai take yi wanda saida ta dauki minti shabiyar.
Sannan ta dan
dan Daga shi da taimakon Farruk.
Cikin sanyi
murya ta ce Amjad ga ruwa na kawo maka kasha dan Allah..
Ahankali yake
bude Idanun sa yana kallon yanda duk tabi ta susu ce.
Hannun ya yi mata Alamun ta ba shi dan shi
kansa kishi yake ji sossai..
Mika masa
ruwan adu'ar ta yi tana kallon yanda hannun sa ke rawa ya kasa rike kofin cikin
hanzari tasa hannayen ta cikin nashi tare da kai masa kofin abaki.
Shanye shi ya
yi tass.
Yunkurin Amai
yasoma cikin hanzari ta ce Aminu dan ba mu roba a bandaki.
Ganin Aminu ze
ba ta mata lokaci hakan ya sa ta tashi aguje ta tafi tadauko tana kokarin tara
masa agaban sa daidai da saukan Aman.
Amai yake yi
ba kakkauta har Idanun sa sunjuye.
Wani ciwon
ciki mai uban Azaba ya turnuke shi tun daga kan mara zuwa cikin izuwa kirjin sa
Nishi Nishi
mai wahala yake fitar wa.
Rahama na
kokarin tashi taje ta zubar da Aman wani riko ya yi mata yanda Ka san mace tana
nakuda irin haihuwa tazo Gadan Gadan.
Sabon yunkurin
Amai ne yataso masa.
Yanayin Aman
'hankalin su ya yi mummunar tashi ganin bakaken zare da Allurori hade da
bakaken kyankyasai ya amayo.
Nan da nan.
Ya fara sauke
Ajiyar zuciya akai akai.
Rahama da su
Faruk kallon abun da ya amayo suke da mamaki.
Faruk ya ce
innaliahi wa'inna il rajun.
Samad me
wannan kuma nashiga uku ni Umar wayyo Allah na
Aminu cikin
tashin hankali ya ce wannan abun sai mun dauki hoton sa dan wlh ba mu yarda ba.
Nida ataba
Samad wllh gwamma ni aka taba.
Daukar wayar
sa ya yi yadau hoto.
Rahama
gabadaya bakin ta yamutu Idanun ta sun kada jajir '' kallon Samad take saita ji
yabata tausayi.
Cikin aro jarumta ta ce Faruk ku taimaka mun
inshigar da shi daki ya yi wanka yakwanta kai kuma Faruk Zam _zam za ka karo
mun su.
An gama Ranki
ya dade yafada daukar roban Aman Samad ya yi tare da fita da shi Daga falon
zuwa bandaki na baki
Dan ya zubar
ya tsafta ce falon..
Aminu ya
taimaka mata wajen shigar da shi daki.
Duk abun da
ake Samad yana Jin su saide babu wani kuzari a tattare da shi bare ya taimaka
wa kansa..
Kallon Aminu ta yi cikin sanyi murya ta ce
kana iya fita dan ya samu ya yi wanka.
Aminu ya ce
babu damuwa inda abun da kike bukata ki sanar muna.
Kallon shi
take harya fice Daga dakin
Tunani take
taya zata taimaka masa ya yi wanka.
Cikin tausayin
sa daya darar mata lokaci daya tasoma kiciniyar cire masa riga '' lafaffen
cikin sa take kallo yanda gashi ya kwanta luf a jikin sa...
Tunani take to
taya zata cire masa duka kayan jikin sa.
Wata zuciyar ta
ce anya zaki iya yiwa wannan wanka kedai akwai sa kai rigima..
Barin wani
Tunani ta yi cikin hanzari tasoma kokarin tadashi.
Duk ya sake mata
nauyin shi kallon ta yake yanda yanayin ta ya canza sossai..
Tana kaishi
bandaki taimaka masa ta yi wajen cire dogon wandon nasa.
Ƙaramin
wando dake jikin sa tabar masa.
Ahakan m'a ta
kasa jure kallon sa..
Ganin banda
kallon ta babu abun da yake yi kuma ya kasa yin komai.
Uhmm Allah mai
iko wannan wankan ma ba zaiyi ba saina masa...
Barin wani
tunanin ta yi tare da yi masa wanka.
Babu ba ta lokaci
tadawo da shi cikin daki.
Kaya masu dan
nauyi tasaka masa Saboda tsabar sanyin da ake yi.
Kwantar da shi
ta yi cikin muryan rarrashi ta ce inhada maka coffe ne kasha.
Shiru babu
Amsa sai kallon ta da yake yi.
Hakann ya sa
tafita tare da zuwa kitchen ta daura ruwan zafi coffe ta hada masa.
Tana kokarin
kai masa a daki taci karo da Faruk da Aminu.
Ganin Docto
Ishaq a gefen su zaune..
Cikin yanayin
damuwa ya ce Rahama yakike ya mai jiki Alhmdulilah ta ba shi amsa dasauki. ta
ce Docto a tsohon daren nan kazo.
Mun saka ka
aiki nasan kila kana hutawa ne anty takira ka tafada cike da kulawa.
Docto Ishaq ya
ce karki damu ai ɗare
beyi ba sossai ina pection din yake.
Ganin Abdul
jalil na kokarin shigowa da mamaki take kallon sa ta ce kaikuma daga ina..
Murmushi ya yi mata ya ce antina aini na rako Docto na tsaya Daga waje ne ina
waya.
Rahma ta ce
kash nade taso ku babu shiri my kani sannu da zuwa.
Kallon Docto
ta yi ta ce mu je ta yi gaba suka take mata baya dukan su.
Dakin tashiga
bakin ta dauke da sallama ganin har ya yi barci.
Ta karaso
wajen gadon ahankali take shafa fuskar sa wanda ya sa ya bude Idanun sa..
Yasauke su a
kan ta yana kallon coffe dake hannun ta yana turiri..
Shigowar su
Farruk da Docto ya sa tafara kokarin mika masa coffe..
Babu musu
yakarba ahankali yake sha.
Yana lumshe
Idanun sa Alamun yaji dadin sa dan cikin sa ya yi dumi sossai.
Kokarin ajiye
kofin yake hakan ya sa Rahama ta yi sauri karba Daga hannun sa sannu take ta
jero masa akai akai cikin tsananin damuwa.
Docto Ishaq
matsowa ya yi kusa da shi tare da duba sa cike da kulawa.
Kallon Docto
suke yanda yake ta abu daya tun dazu.
Faruk cikin
Kosawa ya ce Docto ka gano matsalar dake ɗamun
sa ne har Amai ya yi hade da mugun abu acikin sa
salati Docto ya
fara ya ce subuhannalah acikin nasa..
Aminu ya ce
kwarai kuwa tare da kunna masa hoton daya dauka..
Cikin tashin
hankali Docto ke kallon hoton cikin damuwa ya ce ni dai gaskiya a iya fahimta
ta wannan ciwon bana asibiti bane..
Zan masa
allurar daze ya samu barci sossai yatashi da karfin jikin sa.
Magunguna ya
fiddo Daga jakar sa.
Ya mikawa
Rahma...
Hannun biyu
biyu ta karba..
Wayar ta ne
yasoma ring tana dubawa taga Abba ne..
Cikin hanzari
ta Daga wayar tare da karawa a kunne cikin sanyi murya tagaishe shi Daga can ɓangaren ya ce kin kira
harna kwanta barci yau da wuri na kwanta..
Sa'adatu ta ce
Mijin ki babu lafiya har Abdul jalil yaraka docto gidan naku..
Rahama ta ce
eh Abba sunzo jikin ma dasauki tana son ta yi wa Abba bayani ganin mutane a
dakin ya sa tafasa...
Abba ya ce
Allah yakara lafiya ku kula da shi dan Allah kinji yata.
InshAllah ta
furta tare da yin sallama ta ajiye wayar.
Docto da Abdul
jalil sallama suka yi masu a kan za su koma..
Rahama godiya
ta yi musu '' su Faruk da Aminu rakiya suka yi masu.
Kudi Faruk
yadauko da niyar sallamar docto amma fur yaki ya ce ai yiwa kaine karsu
damu.....
Rahama gyarawa
Samad kwanciya ta yi tare da rufa masa blanket a jikin sa..
Zaune takoma
ta yi tagumi tuna abun da ke gabanta ya sa ta tashi tare da dauro Alwala ta yi shafa'i
da wutri..
Alkur'an mai
girma ta dauko ta bude tafara karanta shi cike da nutsuwa muryan ta na tashi
tana karatun tana kallon Samad dake motsawa a gadon sa.
Faruk da Aminu
sake dawo wa cikin dakin suka yi ganin Rahama na karatu shikuma barci yake
hakan ya sa suka juya dan zuwa nasu dakin..
Aminu ya ce ka
ga ikon Allah Ko badan yarinyar nan ba ya zamuyi da shi wlh iyaka mukai shi
Asibiti ayi ta magani daban cuta daban..
Faruk ya ce ka
san kwanakin baya sanda ba ka gari wlh ya yi ciwo sossai dan har nacire rai a
kan ze tashi.
Ba ɗare ba rana haka muke kuka
nida Mamy da kannen sa.....
Aminu ya ce
subuhannalah andade ana ruwa kasa na shanyewa kenan.
Yakamata mu
kira Mamy a sanar mata da abun da ke faruwa cewar Aminu..
Faruk ya ce haka
ne kuma tare da lalubo wayar sa ya dannawa Mamy cikin sa'a kuwa ta Daga hakanan
ta ji ba ta da nutsuwa banda bugawa babu abun da zuciyar ta take yi.
Cikin rawar
murya ta ce Faruk ina fatan dai lafiya Ko.
Farruk yabata
labarin abun da ke faruwa cikin tsananin tashin hankali tafara kuka ta ce shi
ke nan ɗana ze mutu.
Hawaye shar a
Idanun ta.
Farruk ya ce
Mamy hakuri zakiyi ai ya samu kulawa sossai gun matar tasa kinga ita ce silar
fitar mugun ajiyar dake cikin cikin sa.
Mamy ta ce ina
matar tashi take 'Faruk ya ce tana dakin su inkai mata wayar ne ?
Eh kai mata
wayar nan dan Allah.
Cikin sauri
sauri ya nufi dakin iske Rahama ya yi zaune inda yabarta karatu take yi hartayi
nisa tsitt kake Jin dakin banda sautin muryan ta da kamshi turare babu abun da
ke tashi a dakin...
Cike da kulawa
ya ce Madam Samad mamy za ta yi miki magana yafada yana me mika mata wayar.
Amsa ta yi tare
da ajiye Alkur'an a gefen ta cike da girmamawa ta gaida Mamy ta amsa da lafiya
lau ya me jiki.
Ta ce yaji
sauki Alhmdulilah.
Mamy shiru ta
yi tana nazarin tayanda zata bullo mata..
Cikin sassaita
murya ta ce diyata Rahama ta amsa da naam tana me maida hankalin ta a kan abun
da take shirin fade.
Mamy ta ce dan
Allah kisa idanu sossai a kan sa '' ki taimakeni yanda Allah yataimake ki
Rahama.
Dan Allah
karki ringa nesa ɗashi
indai yana gida Ko baya gida ki ringa bin diddigin sa.
Rahama cikin
sanyin jiki ta ce InshAllah Mamy zan kula.
Cikin Jin
dadin Amsar ta Mamy ta ce Allah ya yi miki Albarka nasan dai ya yi barci Ko
Rahama da
Idanun ta na a kan sa ta ce eh ya samu barci sossai ma.
To dan Allah karki kiyi nisa da shi koda cikin
ɗare ne.
Maganar Mamy ba
ƙaramin
tada mata hankali ya yi ba ita da take shirin ta shimfida bargon ta akasa tun
da yau kwana ya kamata a dakin sa..
Mamy ta ce
dafatan dai kingane abun da nake nufi..
Rahama ta yi shiru
ba ta bata Amsa ba..
Mamy tsab ta
lura Rahama tana Jin kunyar ta sossai Daga haka suka yi sallama.
Ajiye wayar ta
yi gefen gado ganin Faruk yafice..
Cikin sanyin
jiki taje ta murzawa dakin key tare da dawowa cikin dakin.
Samad da yanzu
yafarka amma be bude Idanun sa ba. Kallon ta yake yanda take ta safa da marwa
acikin dakin.
Zam Zam na
hannun ta wanda ta juye a kofi yaga sai adu'oi take yi ba kakkautawa tana
gamawa ganin ta nufo inda yake lumshe Idanun sa ya yi kamar me barci.
Yana Jin yanda
take shafa masa ruwan adua a jikin sa har zuwa fuskar.
Taci gaba da
shafa masa har zuwa wajen marar sa daidai hannun ta na kokarin..............
Ta ku har
kullum kyauta Daga AllahUhmm masu fitar da novel.
Masu jiran na
sata ayi ku sha zaman Jiraa dakyau fa.
😏
5️⃣0️⃣
Hannun ta na
kokarin taba Samad din ta yi saurin zame hannun cikin Jin tsoro Kallon ta yake
jiyayi kamar su shekara ahaka dan duk da ciwon da yake ji hakan be hana shi Jin
felin na taso masa.
Kallon ta yake
yanda take kokarin ajiye ruwan hannun ta.
Blanket ta
rufa masa.
Kallon fuskar
sa take taga eh lallai barci yake..
Uhmm ka ga
mutum dan beda lafiya duk ya saki jikin sa saikace ƙaramin yaro '' komai sai
an yi masa ni yanzu inama zan kwanta ne tafada afili kallon bakin gadon ta yi ta
ce uhmm bara indan kwanta anan kafun ya tashi
na farka karya ganni tana me kokarin sauka
Daga kan gadon ta yi dan canza kayan jikin ta zuwa na barci.
Kayan barcin
ta dauka direct bandaki tashiga dan saka su.
Murmushi ya yi
ganin ta tafi bandakin yana cikin tunanin maganar yarinya nan da suka hadu a
rijiyar lemu yake
so yake ya
tambayi Faruk a kan tabbacin zancen nata
Wata zuciyar ta
ce masa tokai Samad idan ka ga zanen hoton ka da ka dade kana nema ya zakai da
Rahama.
Murmushi ya yi
azuciyar fadi yake ita Rahma *KYAUTA DAGA ALLAH* CE.
Wancen muradin
raina ce.
Ahaka har
barci barawo yai gaba dashi..
Tana fitowa
Daga bandaki cikin sauri sauri taje tasamu wajen cen karshen gadon takwanta.
Tunanin mafita
take yi so take ta ji tarihin Yarima Samad '' kasa kwance ta yi tare da zama ta
zabga uban tagumi lallai abun da tagani ba ƙaramin tada mata hankali ya yi ba.
Koma wanene
tana tabbacin asiri akai masa.
Oh lissafi ya
kwace mata so take tasan tasan komi game da Yarima Samad wa zan tunkara kenan
take tambayar kanta.
Wata zuciyar ta
ce haba Rahama ke kuwa kike da waɗanda
za su baki labari tiryan tiryan.
Khadija ce ta
fado mata arai Girgiza kafafun ta take yi lallai ba shakka badan ɗare ya yi tabbas da na kira
khadija dan in ji Ko tasan wani abu game da yayan nata.
Ahaka barci
barawo yai awon gaba da ita..
***********************
Alarme din
wayar sa ne yasoma kara '' ahankali ya bude Idanun sa tare da sauke su a kan ta
barci take amma da ka kalle ta sai kayi zaton Idanun ta biyu.
Harda gajiya
suka dirar mata lokaci daya...
Sauka Daga kan
gadon ya yi yana tafiya babu kuzari a tattare da shi amma tabbas yaji sauki
sossai a kan jiya..
Jin karar bude
kofar bandaki ne ya sa arazane ta farka.
Cikin hanzari
ta nufo sa.
Cikin muryan
barci ta ce ina za ka je ne tana murza Idanun ta.
Kallon ta yake
cikin yin kasa da murya ya ce bakiga time din Sallah ya yi bane ba tare da
yajira cewar ta ba ya shige.
Ta kai minti
biyar tsaye inda yabar ta kallon kofar bandakin take.
Ko me ta tuna
tajuya zuwa dakin nata.
Acen ta yi sallah
tana idarwa ta tazauna yin azkar saida haske ya fito Sannan ta fada bandaki ta
yi wanka da ruwa mai zafi dan sanyi ake yi ba kadan ba..
Shiko Samad
yau a dakin nasa ya yi sallah anan kan darduma barci ya yi awon gaba dashi.
Faruk da Aminu
sanye suke cikin farar jallabiya hannayen su cikin Aljihun rigar su.
Daga massalaci
suke.
Aminu ya ce
anya Samad ya tashi kuwa.
Yakamata mu
kyaleshi zuwa anjima tun da matar sa tana nan.
Takun tafiyar
Rahama ya sa hankalin su yadawo a kan ta.
Ina kwana ta
ce musu a mutunce suka amsa mata da lafiya lau.
Faruk ya ce ya
me jiki.
Amsa masa ta
yi da yaji sauki har ma ya yi sallah yakoma yakwanta kokarin wuce wa kitchen
take cikin dan saurin ta.
Kayan break
take kokarin hada musu '' ruwan zafi ta dafa hade da citta da kanumfari' ganyen
shayi da lipton sai dan lemun tsami data matsa kadan ya yi '' ruwan na tafasa
ta ta ce shi hade da juye shi a flask.
Cikin hanzarin
ta soya musu kawai duk ta zuba a babban kula ka sancewa abincin da sukafiso
suyi break da shi kenan '' kan dîner table ta jera komai a natse take aikin ta
cike da nutsuwa..
Na Yarima
Samad gèfe daya ta ajiye kallon kofar dakin nasu take tana tunanin takai masa
koko taje ta fito da shi dan ya yi break..
Wata zuciyar ta
ce je ki kai masa kawai.
Cike da wannan
tunanin ta tafi da su har cikin dakin nasu.
Iske shi ta yi
ya fito Daga bandaki Alamun wanka ya fito.
Ajiye kayan
hannun ta cike da ladabi kanta akasa ta ce ina kwana ya jikin naka ?
Kallon ta yake
yana son gano wani abu amma abun ya ba ce masa.
Lafiya lau
yabata amsa.
Zama ya yi bakin
gadon nasa.
Kallon ta yake
ta ja tebur tare da daura kan brek din.
Kokarin hada
masa shayin take har ta suga tadauko madara zata zuba ta ji ya riko hannun nata
yana kallon kwayar Idanun ta cikin kasala.
Ya ce kin san
bana son madara a shayi.
Yi hakuri na
mance ne ta fada tare da miko masa shayin.
Kwai data soya
ta matso da shi gaban sa.
Kallon kwan
yake ya ce ah ni ba zanci ba.
Dago kai ta yi
kamar za ta yi kuka ta ce dan Allah kaci koda kadan ne pls...
Kallon yanda
take magiya ya sa shi cewa stop zanci amma a baki zaki ba ni Inkin yarda.
Kalamin nasa
Jin sa ta yi a bazataba shiru ta yi kamar me nazari kalaman anty dana Mamy sune
suke yawo mata akai.
Cikin yi kasa
da kanta ta ce na ji zan ba ka dan gyara zaman naka.
Kallon ta yake
ya ce kidan cire hijab din ki kada ya barar mun da shayi yafada cike da
bukatuwan haka.
Kamar bazata
cire ba
to tanason yaci hakan ya sa ta cire hijab din
ta.
Durkushen da
ta yi ya fito da saman boob din ta..
Mika masa
shayin take amma shi hankalin sa baya kan abun da take miko masa.
Amsar shayin
ya yi Daga hannun nata yana sha Idanun sa nakan boob din ta.
Har ya shanye
shayin ba tare da ya sani ba be ajiye kofin shayin ba...
Kokarin tashi
dan bashi kwan abaki take.
Cikin takura ta
ce yawwa dan bude bakin naka inbaka tafada cike da kunya.
Shikuwa
bemasan me take fadi ba ya yi nisa baya Jin kira a kallon Boob din ta..
Kallon shi
take ta ce lafiya kuwa shiru kake ji banda sautin numfashi sa babu abun da take
ji.
Batai aune ba
sai jiya ta yi ya saka hannun kai tsaye cikin boob din ta..
Za ta yi
magana ya ce mâta shiiiiiii.
Shiru ta yi cike
da tsoro da Fargaba ta ce am zanje indan sawa Faruk da Aminu break.
Kallon ta yake
ya ce Faruk da Aminu kuma meye hadin ki dasu badai kin ajiye ba sun zuba da kan
su..
Ina nufin basu
San na ajiye ba zan sanar dasu ne.
Kallon ta yake
ya ce ni kibari inna fita zan sanar dasu.
Taso nace
umarni nabaki inkinaso Albarkan aure..
Jikin ta na
rawa ta hau gadon ta zauna ganin ya ture tebur din shayin gefe hankalin ta ya
yi mugun tashi.
Innaliahi take
ta m'aimaitawa.
Shiko kashe
mata idanu ya ce Rahma yau nakeson in tabbatar dake cikakkiyar mace dan haka
kishiga bandaki kiyi wanka ki ɗauro
Alwala.
Tashi ya yi tare
da nufar kofar dakin nashi yarufe tare da cire key din..
Hannun ta
yakama ya je mu je muyi wanka muyi Alwala Ko.
Kin san kazar
nan na kawo shi tun ranar da kika tare inwani kike bukata to..
Zansiya sai
bayan komai yatafi yanda nakeso..
Kukan zuci
take tana tunanin ya za ta yi babu mafita Samad yau soyake sai ya cimma Burin
nasa..
.....
************************
Baba salihu
zaune cikin dakin nasa kamar yanda ya saba kallon camera yake ya yi dan kwata
kwata tun da yaga hassana a masarautar su beda sukuni......
Waya yake yi
dame bashi labarai ya ce ya ce ya'akai ne kasamo mun dalilin ta na zuwa cen..
Me bashi
labarai ya ce ya shugaba NA ance aiki taje nema kuma Mamy ce ta dauke ta aiki.
Cikin tsoro da
Fargaba baba salihu ya ce yanzu wace hanya zanbi in gana da ita.
Me ba da labarai
ya ce eh to inka san gidan nasu kaje kabar musu sako Ko kuma kazo da kanka a
sirrince nasan inkazo to matsala yazo karshe kenan.
Baba salihu ya
ce zan duba maganar taka intayi daidai zan dauka Daga haka suka yi sallama.....
*****************,
******
Sheik da
Aminin sa Isa suna ta hada kayayyakin amfanin su na tafiyar da za su yi zuwa
Gabon..
Aminin sheik ya
ce Allah ya yi tafiyar tamu gobe ce..
Sheik ya ce
haka daman rayuwa take duk abun da akasawa rana tabbatas.
Sai yazo.
Salma ce tazo
cikin kyakkyawa shiga tana sanye da habaya Pink sossai ta yi kyau tana ta baza
kamshi.
Durkusa ta yi ta
ce Abba zanje gidan Rahama ne..
Kallon ta yake
cikin Sakin fuska ya ce kin san gidan ne..
Eh anty tamun
Kwatance zangane.
Kingayawa
mijin naki ya jefo mata tambaya.
Kallon shi
take cikin yin kasa da murya ta ce na gaya masa ya ce inje.
.
MashaAllah tun
da ya amince Allah yatsare napep zaki hau ne.
Eh napep zan
hau Abba.
Kudi yaciro
Daga Aljihun sa ya Mika mata.
Ko godiya
batayi ba ta tashi ta wuce.
Aminin sheik ya
ce Allah yabaka yaya kyakkyawa wlh amma. Halayen sun banban ta.
Sheik ya ce ai
Salma sai du'ai..
Allah dai
yashirya.
Ameen suka.
Furta tare...
.
************, *************
Samad yana
rufe kofan dawowa dakin ya yi ganin yanda jikin ta yadau rawa.
Sossai..
Kamo hannun ta
ya yi ya ce Rahama rabo ya rantse hakuri zakiyi babu abun da zakiyi ni yau
Samad ba zan iya kyaleki ba wlh..
Amma in komai
ya tabbata na miki Alkawari zanbarki ki sarara..
Cikin kuka ta
ce kayi hakuri ka fadi duk abun da kake so zan maka dan Allah wlh jikina ciwo yake...
Kallon ta yake
yanda take kuka da gaskiyar ta..
Uhmm Rahama
kenan.
Kinada
masaniya a kan me kikazo yi gidan miji..
Ko kin dauki
auren ne azo azauna ayi ta safa da marwa acikin gida.
Kada kai ta yi
Alamun A'a.
OK tashi mu je
muyi wankan tare.
Cikin yin kasa
da murya ta ce kai kaje kayi wanka danni nayi nawa.
. Ba na son
musu Ko Rahama ta
Yana kallon ta
yana kokarin kusanto inda take.
Hannun ta
yakama ya hade da nashi.
Bara incire
miki kayan tun da kin kasa cirewa.
A'a kabarshi
zan iya.
Rufe Idanun ta
Jin harya fara cire..............
Ta ku har
kullum kyauta Daga Allah
Ankai rabin
littafin..
Zanje hutu
sati daya InshAllah ina dawowa hutu babu ba ta lokaci za a ci gaba...
Sai munhadu a ƙanwata
book 2ƘANWATA.
Barkan mu da
dawowa Daga hutu.
5️⃣1️⃣
... Jin har ya
fara cire mata riga ya sa cikin tashin hankali ta ce dan Allah Amsad ka bari
wlh tsoro nake ji cikin tsananin tashin hankali jikin ta ya ɗau rawa sosai kamar mazari,
kallon ta yake cikin yin kasa da murya
ya ce
"haba Rahma wai me kike so in yi miki ne so kike in zuba idanu ina kallon
ki?
ba na son na shiga hakkin ki ya ƙarashe
zancen tare zagaye hannayensa wajen kugun ta yana
ƙara
matsowa da ita kusa da dashi.
Sumbata yake
kokarin kai mata tana zame wa sai girgiza kai take ta san sarai abun da take yi
ba dai-dai bane amma haka kurum baza taba yarda wanda besan darajan auren ta
ba.
Da wannan
tunanin ta fara kiciniyar kwacewa daga hannunsa ina sai dai karfin ba daya ba
ne dan ya gama gano lagon ta so take ta bijire masa.
Cikin niya da
kudiri ya fara aika mata da zafafan sakonni motsa sha'awa wanda hakan ya sa ta
yi sanyi har ta fara mance niyar ta.
kokarin sa yake yaga ya rabata da kayan dake
jikinta wanda ita a halin da suke ciki yanayin wasanni da yake mata ba ƙaramin
tafiya da tunanin ta ya yi ba.
Kwantar da ita
da ya yi yana kokarin mata rumfa yaji karar buga kofa da karfi,
kallon kofar yake da cike da jin haushin haka
amma a hannunsa yana cikin boob din ta yana wasa dasu.
Tsaki ya ja
yana kallon Rahama yanda mood din ta ya canza,
Idanunta a
lumshe yake sam ta mance gaban Yarima take.
Soma bubbuga
gadon ya yi firgit ta dawo hankalin ta cike da mamaki take kallon kan ta babu
kaya cikin razana ta ce ina kayana suke ne?
Saurin rufe
mata baki ya yi da hannunsa ya ce mata "shhii"
Tare da nuna
mata kofa da hannun sa a'lamun akwai wani a wajen kofar.
Cikin zazzare
idanu da kunya da ya cikata ta sauko hade da zanin gadon kasa dan kada ya ganta
ta manta ya gama kallota mai dauka ne kawai beyi ba.
Cikin hanzari ta maida kayan jikinta.
Shiko sai
tsaki yake ta jerowa akai akai jallabiyar sa dake gefen sa ya ɗauko tare da zira ta.
Jin Ankara
buga kofar da karfin tsiya ransa ya ba ce yanufo kofar cikin da bacin rai ya
bude.
Sakaka yake
kallon Salma dake tsaye bakin kofar Idanun ta dauke da glass taci abaya.
Cikin hada
fuska "ya ce baiwar Allah Daga ina hk kuma wa ya baki izinin shigo min
gida har kina kokarin ballamin kofa? Ya ƙarashe zancen yana mai nuna mata hanyar
sauka daga kan matakalan (steps) ɗin.
Da mamaki take
kallon sa da ita ba fadan da ya keyi ya dame ta bakin sa take kallo ji take
kamar taje ta l'ashe dan ba ƙaramin Jan hankalinta ya yi ba.
Tsawar daya
daka ta mata ya jawo hankalin Rahama dasu Faruk da Aminu dake kasa.
Cikin hanzari
suka karaso saman ya yi daidai da fitowar Rahama Daga dakin,
cikin sakin
Fuska Rahama "ta ce my kanwaty kece?
Cikin hanzari
ta rungume ta
Faruk ya ce
wai kai har kaji sauki ne da ka ke ihu ba ka san zai taba lafiyar ka ba,
Meye ya hada
ka da kanwar matar ka?
Yarima Samad da
ransa yake aba ce ya ce kanwar matar tawa ita dabba ce,
kokuwa
mahaukaciya ce ?
Dan ba ta da
tarbiyya an bata, ta zubar a titi ya za ai tazo ta ringa buga mun kofa ina
barci ta tashe ni ita ba ta Jira ne?
Rahama mutuwar
tsaye ta yi ganin yanda ya rufe Idanun sa yana zazzaga ruwan masifa dan sosai
yaji haushin ta inda ze iya Zane ta tabbas daya Zane ta.
Cikin rawar
murya Salma ta yi kasa da kanta a duke ta ce dan Allah kayi hakuri ban san kana
barci ba.
Kallon banza ya watsa mata tare da yin tsaki.
Yabar wajen a
zuciye tare da komawa dakin nasa zuciyar sa na tafasa.
Faruk da Aminu
kallon Rahama suka yi Amma basu ga a'lamun bacin rai a tattare da ita ba wannan
yana Daga cikin dabi'ar ta ba ka gane fushin ta sai inhar ta bude baki ta yi lafazin
da zai sa a gane Ranta ya baci ba.
Faruk ya ce"
Madam Samad kiba kanwar ki hakuri muma mun dauka yana farke ne shi ya sa da ta
ce ba ta iya jira muka nuna mata dakin naku.
Salma ba ƙaramin
bakin cikin wulakancin da Samad ya yi mata takeji ba.
Rahama cikin
cool voice din ta ta ce "My kanwaty am sorry bai san ki bane shi ya sa
amma zan mai bayani"
Kusan a tare
suka sauka Daga kan matakalan( Steps) ɗin.
Farruk ya ja
Aminu suka fita compound din gidan dukansu wayoyin su na hannun a rike sukabar
falon.
Itakuwa Rahama
zama ta yi cikin muryan rarrashi ta ce haba ƙanwata kiyi hakuri na kin hade rai tun
dazu.
Salma kallon
Rahama take tana jin mugun tsanar ta a cikin rain ta ayyana a ranta dole saita
raba Rahama da Samad daman cikin wannan daulan take jibi fa dakin sa ta fito
Girgiza kai tashiga yi.
Rahama dake
kallon ta ta ce haba Salma har yanzu baki huce bane?
Murmushin yake
ta yi cikin salo na bariki ta ce ayya karki damu ai yana da ikon yamin fada
yayana ne shima.
Rahama
murmusawa ta yi tare da tashi zuwa gaban TV ta kunna mata kallo.
Remote ta miƙawa
Salma ta ce gashi ki canza tashar da kike so bara inje kitchen in daura mana
girki Ko Salma ta ce Tom maza ki je tana yatsine fuska.
Kallon Rahama
take yanda take tafiya cikin saurin ta.
Harara tabita
da shi ta ce wahalalliya mai bakin hali irin na Anty sai kinyi kuka wlh
InshaaAllah ba dai ni ba ce zaki sani ne.....
Samad yana
komawa cikin dakin zaune ya yi bakin gado rike da kansa dake Sara masa hade da
wani zazzabi banda haushin Salma ba abun da yake ji tabbas ita ce silan wargaza
mishi cikar Burin shi.
Agogon dake
makale jikin bangon dakin ya kalla ganin time yatafi ya sa cikin kasala ya
shiga bandaki rage kayan jikin sa ya yi ya sakar wa kansa shaya wannan ruwan
dake sauka bisa kansa izuwa gangar jikin sa ba ƙaramin tasiri suka yi ba wajen rage masa
abun yake ji ba.
Lumshe Idanun
sa ya yi abun da ya faru tsakanin da Rahama ne ya fara dawo masa ji yake kamar
ya yi tariya ya koma baya cike da takaicin Salma ya fito daga bandaki tare da
sane jikin sa da towel.
Gaban miror ya
je yana kallon kansa ta cikin madubi Murmushi ya yi cikin maganar zuci ya ce ya
Allah kanuna mun cikar burina na tabbatar inna same ta zata kula dani yanda ya
kamata,
tsaki ya yi a
ransa ya ce to ya'akai ne duk aji na amma gaban wannan yarinyar sai in kasa
rike shi?
Barin wanan
tunanin ya yi tare da dauko mayukan sa ya fara bin jikin sa dashi,
wasu tsadaddun
kayan sa ya dauko Daga wadrobe ɗin
sa kallon kayan yake yana tunanin Ko ya canza su ne wata zuciyar ta ce tun da
ba ka taba saka su ''l
sa abunka kila
rabo ya yi yau ka hadu da zanen hoton ka.
Da wannan
tunanin ya yi maza ya saka wannan babban shaddar daya haddaden dinki Daga gun
kwararen tela sossai rigar ta zauna masa a jiki,
ka sancewa
bleu ne shaddar hula bleu ya saka ya dauko wanda ya yi macin sosai da kayan
jikin sa.
Cikin dan
hanzari ya zura agogo tare da saka takalmin sa half cover.
Sosai shigar
ta yi masa kyau kara koma gaban miror ya yi yana kallon kansa tare da dauko
turaren one love ya feshe jikin sa dashi.
wayar sa dake
ajiye kan miror ya dauka tare da yiwa kansa hoto.
Kallon kayan
break din Da Rahama ta kawo masa ya yi wanda ga sunan ba ta kwasheba kwabe baki
ya yi ya ce uhmm badai an hadani da aiki ba,
In ba haka ina
ni ina aure garin kano kuma a kanon ma wacce ban taba mafarkin samun ta ba.
Rahama dawowa
falon ta yi ganin Salma ta daura kafa daya kan tebur din tsakiyar falo Kuma tasan
Yarima in yagani to sai ya yi magana musamman da yake jin haushin su.
Su Faruk ma
baya barin su daura kafar su akai ce musu yake suje su nemo nasu wannan nashi
ne.
Cikin sanyi
murya da dabara ta ce uhmm Salma zo mu danje kitchen ki tayani aiki mana?
Salma cikin
hada rai ta ce au har wani aiki zan tayaki inzo gidan naki ni dai ki dafa kiba
ni.
Kalamin Salma
caraf a kunnen Samad dake saukowa kan matakalan (steps)din Jin karar tafiyar sa
ya sa Salma da Rahama kallon sa.
Salma
tabarakallah Masha Allah take ta furtawa ji take kamar taje ta rungume shi
wanda haddaden gayen shi ne mijin Rahama ah lallai tana girgiza kai.
Rahama kasa da
kai ta yi ganin ya karaso falon.
Fuskar sa a
hade babu ya hada rai kallon Salma yake yanda kafafun ta ke yawo a kan wannan
tebur din nashi.
Karasowa wajen
ya yi yana kallon ta cikin idanu ya ce keee!
Da kakkausar
murya yake magana wanda ya sa gaga Rahama har Salma tsorata.
Cikin bacin
rai yake magana ya ce "ke waya baki damar ki daura kafafun ki anan?
Rike da kugun
sa ya fara zazzaga mata ruwan masifa
wanda ya jawo
hankalin su Faruk da daki suka fito dan Jin ba asi.
Cikin sauri
Salma ta sauke kafafun ta.
Ta boye bayan
Rahama dan gani take kamar bugun ta zeyi.
Faruk ya ce" Yarima wai me yake damun ka
ne?
Tun da ka
kwanta ciwon nan shi ke nan sai ka fara dawo da halin ka na baya"
"Wannan
fa kanwar matar ka Rahama ce ba ka ga suna kama bane haba dan Allah ka sassauta
mata"
Yarima Samad
da yakai wuya wajen bacin rai ya fuskanci Faruk cikin muryan sa dake nuna
zallan bakin ciki ya ce.
"Ina
ruwana da ita wacece Ko da tare suka zo duniya da Rahama karshe kenan ba abun
da ya dameni a kan me zata zo mun gida irin wannan lokacin kuma tazo da hauka
ace ba zan magana ba"
Kallon Rahama
ya yi wacce ta yi kasa da kan ta.
Ya ce ki bude
kunnen ki da kyau ki saurareni,
Wannan
yarinyar in har tazo gidan nan ki ringa sauke ta a dakin ki Ko dakin baki ba na
son in yi tozali da ita"
Rahama cikin
kasa da murya dan yanzu ya fara ba ta tsoro ta ce" Insha Allah zan
kiyaye"
Kallon sa ya
maida a kan su Faruk ya ce kuzo mu je aina ga ku shirya Ko?
Aminu ya ce ai
dole kace haka jibi yanda ka kure adaka shi ne za ka ja mu kamar wasu raguna
babu kyaun gani.
Samad gaba ya
yi ya ce to ina compund din gidan da kun gama ku same ni bai san me ya sa
kwata-kwata baya son zaman falon tun da yaga Salma inda khadija ce daya zane ta
wannan abun haushin ka.
Niko nace
Yarima ya da daukan zafi haka daga ta buga maka kofa shi ke nan sai ka sa ta a
gaba.
Kallona ya yi
ya ce ke kuma Daga ina haka cikin yin kasa da Murya nace suna na *kyauta Daga
Allah* wani kallo yabini da masu tarin ma'anoni ya ce suwaye ba na Allah ba?
Ganin kansa na
hayaki ya sa na wuce sadaf sadaf ba tare da ya ganni ba na boye wani lungu dan
cigaba da kawo maku labari.
Kallon agogon
hannunsa yake ya na buga uban tsaki
Har ya zangaya
ze shige motar ya sa Su Aminu har, sun fito suna ta buga uban sauri suma.
Samad ya ce
yawwa Faruk wannan yarinya nan ya ma sunanta ?
Faruk ya ce
Samira kenan kake nufi?
Eh ita ya
bashi amsa a takaice.
"Dan kira
ta ka tambaye ta yaushe zata raka ka?
Faruk zaro
wayar sa Daga cikin Aljihun sa ya yi tare da dannawa Samira kira.
Wayar ta yi ring
har ta yanke ba ta Daga ba.
Aminu ya ce"
tun da ba ta ɗaga ba
muna iya tafiya unguwar da ta ce"
"Amma fa
kamar unguwa sheik Imam ne"
Samad ya ce
"au haba unguwar ce aikuwa tazo gidan sauki"
Samad ya ce, "
kamar ya kenan?
Aminu ya ce, "akwai
wata kawar Rahama mai suna Asiya unguwa take inada nombar ta sai intura mata
zanen ta whsap zata bincika mana basai mun;sha wahala saka yarinyar nan agaba
ba"
Ajiyar zuciya
Samad ya sauke" ya ce to dan gwada tura mata"
Bude datar shi
Aminu ya yi ganin kamar Asiya ba ta online yau kwana hudu kenan.
Samad da Faruk
da suka tsaresa da idanu suka ce ya ne katura mata.?
Aminu ya ce
"eh natura mata saide ta kwana biyu ba ta hau ba"
Faruk ya ce kar
ka damu da ta hau zata gani.
Samad shiga motar
ya yi yana kokarin shiga mazaunin drever.
Faruk ya
tareshi cikin hada fuska a wasa ya ce tabe tabe ya da haka ne
Wai?
Da mamaki
Samad yake kallon sa ya ce waye tabe_tabe ne wai rannan na ji kuna fadi kuma
yanzu naga kuna yawan fadin haka.
Aminu ne ya
tuntsire da dariya ya ce" haba Samad dani yake fa wai ni ne tabe tabe.
Samad dake
masu kallon rashin yarda da zancen Aminu ya ce "ku gaya min Ma'anar tabe
tabe nace tare da hade fuska tamau.
Faruk kokarin
shiga mota yake Samad ya jawo shi ya dawo da baya suna face din juna.
Murmushi Faruk
ya yi ya ce ka basar wani film ne muka kalla nida Aminu sosai wannan shirin ya
kayatar damu kuma sunan film din tabe tabe shi ya sa nasawa Aminu sunan ya
karashe zancen yana Murmushi tare da bude mota yashige.
Samad tsaye ya
yi yana nazarin wani Daga bisani shima shiga motar ya yi shida Aminu suka bar
unguwar cikin gidan.
************************
🇧🇯
Mamy zaune
falo Ahmad na kusa da ita.
Cikin Fada
take magana ta ce "haba Ahmad meye hujjar ka na fadin kai ba ka yarda da
wannan matar ba?
Ahmad
fuskantar Mamy ya yi cikin yin kasa da murya ya ce
"Mamy wannan matar fa na hadu da ita a
zongo rannan dan ta ji ance Daga gidan sarauta nake shi ne fa ta biyo ni har da
cemin in kai ta gidan mu"
Mamy tsarkan
dake wuyar ta gold ce Hatta agogon hannun ta na gold ne kallo daya nayi mata
tsab nagane bawai taimako take nema akwai wata manufa akasa"
Sossai Mamy ta
gamsu da bayanan sa.
Kara matsowa
ta yi kusa da shi tare da kama hannun sa cikin nata tana murzasu, kallon shi
take ta ce maganar ka gaskiya ce wani lokacin tunanin ka sai ya fi nawa zurfi.
Amma kuma
matar nan bana tunanin tana da wani mugun nufi amma zan sa idanu sosai a kan ta
kai kuma karage tsanar da kake nuna mata pls"
Ka ringa
gaishe ta kaji my son?
Murmushi ya yi
wanda ya bayyana zallan kyawun sa ya ce "InshAllah Mamy zan kiyaye"
Tashi ya yi ya
ce "to ni dai zan fita"
Fatan Alkhairi
Mamy ta yi masa.
Tana kallon sa
har ya bar dakin Girgiza kai ta ke yi ta ce "uhmm ko shi Samad ya
zamantakewar sa da iyalin sa?
Daukar waya ta
yi ta kira Samad.
Cikin hanzari
ya ɗaga yana zaune kan
kujerar office din sa a'lamun tarin aiki gaban sa.
Mamy ta ce ɗana ya kake ya gida.?
Lafiya lau ya
ba ta amsa still dai hannun sa dauke da biro wayar hans free ya sata tare da
ajiye ta kan tebur yana rubuce rubucen sa.
Mamy ta ce
"ina diyata Rahama?
Kalau take ya
ba ta amsa.
Mamy cikin
zakuwa ta ce Samad wai ME maman maryam ta ce maka ne?
Cikin raba
hankalin sa gida biyu ya ce" Mamy cewa ta yi inzo da Rahama dan su
ganta"
Gaban Mamy ya
yi mugun faduwa ta ce "tokai amsar me kabata ne?
Samad ajiye
biron hannun sa ya yi tare da daukar wayar yacire hans free ya kara ta a kunne.
Ya ce nace
mata zamu zo tare in har zan zo zaman kotu Inshaa Allah.
Nifa mamy na
kusa komawa kwatanon da lokaci kadan yarage..
Mamy da gaban
ta ya tsanan ta bugawa ta ce "bangane ka kusa dawowa ba?
Ajiyar zuciya
ya sauke ya na mai shafa sajen shi da suka kwanta lub lub a fuskar sa ya ce
"Mamy naga ai har yanzu Burina be cika ba dole zamu cigaba da adu'ar Allah
ya bayyana shi"
.
Barin kanon ba
zai tsaida kamfanin ɗana
bude ba komai zecigaba InshAllah dan zan ringa zuwa duba abubuwa kuma inacen ma
ina tafiyar da komai kar ki damu..
Ajiyar zuciya
Mamy ta sauke ta ce Allah ya taimaka ya kuma kawo ku lafiya ka gaidamun Rahama"
Cikin Jin dadi
ya ce" za ta ji mamy Daga haka suka yi Sallama"
Sai karfe hudu
suka baro kamfanin Samad.
Kai tsaye
babban super market Aljazeera suka nufa,
Suna parking
din motar nasu ya yi dai-dai da wata bakar mota ta paka.
Wanda ke cikin
motar ta cikin madubin motar take kallon Samad.
Samad kokarin
shiga wannan Super market din ya yi Idanun sa ya yi masa tozali da wannan matar
da take kokarin boye kan ta a cikin motar.
Mutuwar tsaye
ya yi ya kasa tafiya cikin zafin nama ya juyo.........
5️⃣2️⃣
Cikin zafin
nama yajuyo zeyi wajen wannan bakar motar '' hango Yarima Samad ya sa wannan
dattijuwar fisgan motar ta aguje cikin sauri tabar wajen, aguje ya karaso amma
ina har tana kokarin hawa titi.
Cikin ihu yake
kiran Faruk da Aminu wanda tuni sun shige super market din..
Ba tare da
yajira fitowar su yashiga motar a 360 ya fisgi motar ya take mata baya '' yana
tuki cikin zakuwa daya cimma ta...
Wannan
dattijuwar lura da yana bayan ta ya sa ta canza hanya wacce bana gidan su ba ''
kwana ta rinƙa
bi da shi har ta yi sa'ar ba ce masa da gani.
Su Faruk da
Aminu aguje suka yi waje 'ikon Allah Faruk ya furta ya ce" Yakira mu Ko
ina yatafi ne?
Aminu zaro
wayar sa Daga Aljihun rigar sa ya danna Yarima kira.
Samad da ransa
yake ɓace ya daga
cikin Kosawa ya ce ku jirani gani nan tafe tare da katse kiran...
Aminu rike da
baki ya ce" ka ga nine nakira shi amma beban daman magana ba, amma yafadi
nashi ya katse..
Faruk ya ce meya
ce maka ne? Yatsare shi da idanu...
Cewa ya yi mu Jira sa yana yarfe hannayen sa
cikin takaici..
Isowar Yarima ya sa suka yi gunsa tun kan
yagama parking din motar.
Daga zaune
cikin motar ne ya leko kansa waje cikin dan ɓacin
rai ya ce" Kungama ne kufito da kayan Muje.
Faruk ya ce"
Inafa muka gama nagadai kaine kayi ihun kiran mu.
Dafa kai Samad
ya yi ya ce" Oh My god babu ba ta lokaci ya fito cikin motar gaba ya yi suka
take masa baya har cikin super market din..
*************************
Salma kallon a
gogo ta yi bayan ta idar da sallah tana me kara bin gidan da kallo '' kowa ina
tsaf yake cikin kwabe baki ta ce" Wai Anty Rahama kinada Y'ar aiki agidan
nan ne?..
Kallon Rashin
fahimta Rahama ta bita da shi tana kokarin kwashe kwanukan da suka ci Abinci..
Salma numfasawa ta yi ta ce eh naga gidan nan
yamiki girma sossai ya kike yi wajen aikin gidan nan ke kadai? Nasan ba za ki
iya ba ko kinada masu yi ne?..
Murmushi Rahama ta yi ta ce" kanwaty ai
ba wani aiki bane agidan nan me wahala.
Kwabe baki Salma ta yi tana taunan chiugum
karas karas a bakin ta.
Yayi dai-dai da
shigowar Samad da su Aminu cikin dan sauri sauri Yake tafiya. '' Caraf Idanun
sa ya tsarke ɗana
Salma tsuke fuska ya yi tare da barin wajen cikin dan hanzari.
Salma kallon
shi take tana Ayyana to laifin me taimishi ya tsaneta..
Faruk da Aminu falon suka karaso cikin sakin
Fuska suke kallon Rahama da Salma tare da yi musu sannu,
Suma sashin su suka nufa ba ɓata lokaci.
Salma dake kallon ikon Allah ta ce uhmm kedai Anty
Rahama kinada aiki babba Wallahi.
Rahama ta ce name kenan? Cikin son Jin abun da
zata ce..
Ai dole ince haka gida duk katti ke kadai ce
Mace a cikin su '' Sannan da dukan Alama Mijin nan naki dan bakin rai ne
Wallahi, jibi tun da nazo yanda yake ta Jin haushina....
Hadiye sauran
maganar ta yi Jin takun saukowa Daga kan matakalan step.
Gaban ta ya shiga dukan uku uku ganin Yarima
azuciye ya sauko kasa yana kokarin kaiwa Salma mari, Aminu ya yi caraf ya kama
hannun.
Hannun Yarima
rawa rawa yake Saboda tsabar bakin cikin bekaiwa Salma mari ba.
Aminu cikin
kasa da murya ya ce" Waime Yarinyar nan ta yi maka ne haka?.
Cikin ɓacin
rai ya kalli Salma bakin sa na rawa ya ce suwaye Katti agidan nan?
Faruk shima zare idanu ya yi ya ce katti kuma
? Yana kallon Yarima.
Samad ya ce" Wannan Yarinyar ba ta da
mutunci wai mune katti acikin gida...
Bakin Rahama
na rawa ta ce" Yi hakuri ba da kai take ba wani firan muke.
Samad Beko bi takan Rahama ba dan ita kanta
haushi take basa.
Direct kitchen yazarce.
Rike da kugun
sa yana kallon yanda aka gyara wajen tsaf kamar ba ai aiki cikin ta gaba.
Frij ya bude yadauko lemun champagne, 🥂
kwalba guda, ya karaso falon iske Salma ya yi har ta fice Rahma zata bi ta dan
rakiya, '' muryan shi ta ji yana Fadin Inkika kuskura kafarki tabar falon nan
da sunan Rakiya uhmm sauran basai na fada ba..
Cak Rahama ta tsaya Idanun ta cike da kwalla
tadawo itako Salma Jin furucin sa ya sa tabar gidan cikin saurin ta..
Tana buga uban sauri wanda ya ja hankalin mai
gadi, kokarin bude mata gâte yake amma koda ta Iso bankade shi ta yi yana
kokarin faduwa.
Subhanallahi
ya furta, wannan Mahaukaciya kuma Daga ina? Tsuke bakin sa ya yi kada aji shi tare
da zama kan kujerar sa yana Girgiza kai...
Salma tarar me napep ta yi Unguwar Malam isa
ta yi masa Kwatance.
Babu ba ta lokaci akai Unguwar da ita, yana
sauke ta ta sallame shi tare da fadawa kai tsaye Gidan malam isa.
Sa'a taci Malam isa ya fito zeje Unguwa, yana
Ganin Salma ya gane ta ya ce" Amarya bakwa laifi mu shiga Daga ciki..
Suna shiga dakin malam isa ya zauna itama
zaman ta yi dirshan Idanun ta cike da kwalla.
Kallon ta yake ya ce" Nasan mèke tafe
dake.
Cikin mamaki ta
ce" Ina ga ba muyi maganar damuwa ta da kai ba yanzu nashigo...
Malam isa bushewa da dariya ya yi wanda saida
dakin ya amsa ya ce" Tun jiya nasan da zuwan ki a yau
Kuma matsalar ki daya ne kina son mijin yayar
ki.
Kinje gidan yaita miki wulakancin Ko ba haka
bane?
Haka ne ta furta cewa Salma..
Malam isa yabuga kasar dake gaban sa ya ce"
Ke Salma wannan auren ba zamu iya raba shi ba kamar yanda muka raba wancen ba.
Cikin rashin fahimta Salma ke kallon shi ya za
ai kace bazamu iya ba malam?
Cikin kuka take magana ta ce" Malam ba ka
san radadin danakeji ba inna bude idanuna naga wai yaya ta ce take auren wannan
balaraben sai in ji kamar in kashe kaina malam..
Kallon ta yake yanda take zaro zancen ya san
har cikin zuciyar ta take fiddo zance..
Salma yakira sunan ta atausashe !!
Na'am ta ba
shi amsa tare da dago kai suna kallon juna.
Hanya biyu ce
inma zaki kashe yayar ki ta hanyar sa mata guba a abinci, Ko kuma ayi amfani da
Mijin nata wajen dauke hankalin sa a kan Yayar ki, amma fa ba zai sake ta ba
duk rintsi kuma akwai haihuwa tsakanin su.
Firgit Salma ta zare Idanun ta ta ce"
haihuwa fa kace ya za ai a toshe wannan hanyar, Wallahi banson ta hada shimfida
da shi inma ta hada banson taci gaba.
Malam isa ya ce" Keko Salma ai kinga
munyi nasaran hana wancen auren to wannan ya fi karfin mu domin shi kansa
bibiyar ransa ake Daga cen ɓangaren
dangin sa.
Salma bibiyar
ransa kuma koda yake ai kyaun dan maciji ne beda mutunci.
Malam isa ya ɗara ya ce" Au kyaun
dan maciji ne ni dai kam banga haka ba amma yana da zafin rai bayason takura da
raini duk na gani dana buga kasa.
Salma ta ce uhmm kaide asamu mafita Wallahi
dan dagaske na kamu da son sa, kuma so na hakika wancen na baya kudin sa nakeso
wannan Ko beda kudin zan iya zama dashi, pls ka taimaka mun harda matso guntun
hawayen ta.
Malam isa tashi tsaye ya yi yana kallon agogon
hannun sa.
Kinga Salma
akwai Inda zanje na lura bakya fahimtar abun da ake fadi haba tun dazu muyi ta
maimaita zance daya, nagayamiki mafita ki je kiyi shawara wacce kika ga ze miki
sauki ki dawo ki fadamun" Ya ƙarashe zancen tare da barin dakin cikin
sauri.
Ita Ko bayan sa takebi da kallo tare da tashi
jiki asanyaye ta fito, dakin lissafi ya fara kunce mata wanne za ta yi a ciki
ne dan gaskiya bazata yarda ta rasa Samad ba..
Al'amin ne yafado mata wata zuciyar ta ce
Kekuwa Salma kiyi yanda zakiyi ya sake ki Sannan Burin naki ze cika...
**********************************************
Gabon
Baba Salihu
zaune kamar yanda saba gaban computer yana kallon abun da ke faruwa a agidan
Samad.
Rike da baki
yake kallo yana cizza labban sa yaga dai Salma tambayar kansa yake to laifin me
tayiwa Samad, yanda yake kallon Samad na yarfe hannayen sa ya tabbatar faɗa yake musamman daya kalli
yanda fuskar sa take.
Rufe ɓangaren
Samad ya yi yana Girgiza kai yakoma ɓangaren
Masarauta.
Nan m'a kallo yake yanda hassana ke manne da
Mamy, ɗâfe kansa ya yi
cikin takaicin wannan Matar tambayar kansa yake wai ana so dole wai in banda
hauka ma ya za ai taje wajen Matar shi duk da besan har yanzu meya kaita ba, amma
ya tabbata wani ne yabata labarin sa harya ba ta adireshin sa tunani yake kodai
canza kasa zeyi dan bayason kwata kwata abun da zai sa yadawo Masarautar duk da
Mahaifin sa yana cikin waɗanda
suka goyi bayan karya a kan sa..
Kuma yahana yatafi da iyalin sa '' kukan zuci
yake ya ce" Mamy ancutar dake baiwar Allah zuciyar sa tana kuna.
Tashi ya yi Daga zaunen yakashe computer.
Kiran me bashi
labari ya yi bugu daya ya Daga.
Me bashi labari ya ce" Ya shugaba na har
yanzu ina nan inasa idanu a kan Samad Yarinyar nan babu abun da ya taba shiga
tsakanin Su na mu'amala.
Nan yaba baba
Salihu labarin zuwan Salma gidan da abun da ya faru.
Baba Salihu ya
ce Ayya wai yaushe Samad ze rage zafin rai ne.
Me bashi rahoto ya ce" Inafa ya shugaba
na sai dai Addu'a amma dai haryanzu fulani na bayan Samad da kanin ka.
Sossai ran sa
ya sosu cikin kuka ya ce" Allah yakawo karshen wannan bala'in.
Ameen ya amsa
yana kokarin katsewa ya ce" ya shugaba na akwai wani motar, wata dattijuwa
da Samad yabi amma be gayamana wacece ba.
Baba Salihu rike da habarsa ya ce" To
kayi kokarin ya gayamaka abun da ya gani koma wacece ina sauraren ka.
Daga haka suka
yi Sallama.
***********************
Salma jiki a
sanyaye tadawo gida dai-dai mashigar gidan taci karo da Al'amin tsaye sai
kallon agogon hannun sa yake yana Girgiza kai.
Gaban ta ne yafadi ganin sa shima stil ita dai
yake kallo, ya kura mata idanu ganin yanda ta yi masa kyau ta yi wani haske da
kiba fatar ta ta yi fresh 'cikin sassauta murya ya ce" daga ina kike ?
Bakin ta na rawa ta ce gidan Rahama naje.
Kallon ta yake
yana nazartan kalaman ta.
Amma kin san
inada hakkin ki gayamin duk inda zaki je Ko ?
Bakomai na
rufa miki asiri wajen Mahaifin ki.
Dana nuna masa
nasan da fitan ki '' tun da tafiya zeyi gobe ki tattara gobe kema ki dawo gidan
naki, na canza miki gida zuwa cikin gari kuma kusa da gidan antyn ki na kama
haya yana shu'umin Murmushi.
Salma Zare idanu ta yi ta ce" Da gaske
kake koda wasa?.
Dagaske nake ai nayi maki surprise ne dan haka
gobe ki shirya zanzo indauke ki..
Cikin Jin dadi ta ce" Ai babu matsala
zanbika bara in shiga in gayawa su Mama.
No pls ki tsaya ina son mu je koda hôtel ne indai
rage zafi dake kingane Ko.
Wani kallo take binshi da shi na rainin
hankali cikin kwabe baki ta ce" Amma kai Al'amin kai badahume ne kana
tunanin zankara yarda kamin abun da kamun wancen lokacin ne? Ka cutar dani a
banza dan kasamu Mahaifina mutum ne mai hakuri da kawaici, da wallahi ba za ka
sha ba.
Wallahi inma dan wannan ne kake son in koma
toka canza tunani dan ba yanzu ba Wallahi kaji na gayamaka.
Tun da tafara magana bakin ta kawai yake bi da
kallo yana ayyana aransa irin rashin mutuncin daze shuka mata kafun ya sake ta.
Wata zuciyar ta ce kaiko ai Salma ba irin
Matar da za ka aura ka saka bane kaci gaba da kwasar ganiman ka har ta yi expire
kafun nan kayi waje da ita.
Dawo da hankalin sa ya yi a kan ta ya ce"
Haba Salma taya za ai kice haka Inkin ce bakiso ni ba zan miki dole ba, aike
nake so ba jikin ki Ko kin manta ni ne Al'amin din ki ne.
Murmushi ta yi ta ce" To na ji zankoma
din.
Hannun ya sa Aljihun sa ya zaro dubu daya yana
kokarin mika mata.
Kallon kudin take da rainin wayau tadawo da
kallon ta a kan sa tana yatsine fuska wannan kudin na mene ne ?
Kudin kashewa ne nabaki Ko mata ta.
Tsaki ta yi ta ce" Allah ya kiyaye aiko
Ubana ba zai ban wannan ba..
Dazun ma dazanje gidan antina dubu biyar
yaban.
Al'amin ya ware idanu ya ce" Dubu biyar
fa kudin mota napep dinne ?dubu biyar ai Wallahi in'nine ba zan iyaba ina laifi
dari biyar..
Ganin ze ba ta mata rai wuce shi ta yi tabar
shi tsaye rike da kudin sa ahannu.
Maida kudin ya yi a jikin sa yana Girgiza kai tare
da sa kai yafice.
Anty zaune kofar dakin ta tana waya da Asiya
cikin damuwa ta ce" Asiya.
Daga can ɓangaren ta ce" Na'am
maman Rahama.
Ina son ki je gidan Rahama dan Allah kin san
Rahama ba ta da wayewa sossai a kan rayuwar aure, duk da zamani ya canza amma
tana bukatar mai daurata a kan hanya.
Cike da damuwa
take magana.
Asiya ta ce"
Maman Rahama karki damu Insh Allah zanje har gidan nata naji, Abokin Mijin nata
yana cemin wai za su tafi garin kwatano tare da da Rahama za su je.
Anty ta ce" tare da Rahama kuma amma ta
sani kuwa ?
Asiya ta ce"
bana tunanin tasani dan bamuyi hiran da ita ba.
Anty cikin ba da umarni Sam haka nan ta ji ba
ta da nutsuwa, a kan zaman Rahama gidan Mijin nata '' ta ce kizo gida Asiya
yanzu in ba abun da kike yi.
Asiya ta ce"
Zan shigo InshAllah.
Tana katse
wayar direct dakin Sheik ta nufa iske Mama ta yi a dakin zaune.
Da sallama
bakin ta tashiga dakin.
Tare da neman waje ta zauna cikin sakin fuska ta
ce" Maman Salma ashe kina nan ?
Mama ta ce"
eh ina nan cikin Kosawa da maganar ba ƙaramin haushin ganin ta ta yi ba..
Sheik dake kokarin kulle ƙaramin
a kwatin sa dago kai ya yi yana kallon anty cikin sakin fuska, ya ce"
Sa'adatu ya jikin naki?
Anty ta ce lafiya lau alhmdulilah.
Yawwa gwamma
da kuka taru Anan gobe ne tafiya ta nida Aminina, dan Allah ku tsare gida da
mutunci.
Har Allah ya
dawo dani.
Ke kuma Anty
yakamata ki je asibiti su dauraki a kan magani kin san mata irin ki na bukatar
hakan.
Insha Allah zanje anty ta furta ta ce"
daman nazo muyi magana a kan Rahama.
Jin ta Ambaci
Rahama ya sashi maida hankalin sa a kan ta..
Mama dake kallon su Ranta yakai kololuwa wajen
baci.
Anty cike da nutsuwa take ba sheik labarin
lefen da ke gidan Rahama.
Sheik ya ce" To ai inhar Saboda ita aka
kai tana iya amfani dasu tun da dai ba ita ta nema ba, Iyayen Adamu ne suka
aiko.
Maganar gold dasuke cikin akwatunan ta tazuba
a wadrope din.
Anty ta ce saura daya.
Murmushi ya yi
ya ce" fadi inajin ki.
Cikin yin kasa da murya ta ce" Gidan
Rahama nake son zuwa Insha Allah Ko nan da jibi ne.
Sheik ya ce" Masha Allah zaki je dubo
Y'ar taki Allah yakaimu, inzaki je kisa drever yakaiki yadawo dake..
Cikin gamsuwa da bayannan sa ta ce to.
Sheik kallon
Mama ya yi da kiris yarage ta fashe ya ce" ki gayawa Salma ta rike mutunci
auren ta tazauna waje daya banda yawo da auren wani a kan ta..
Mama cikin
bacin rai ta ce kullum ba ka kyawawan zato a kan Salma, wai me ta tsare maka ne
haba ai wannan tsana ce, Ko ince kiyayya ce.
Tun da take
zazzaga ruwan masifa sheik ya mike tsaye yana kallon Anty, ya ce" Sa'adatu
yau dakin wa nake acikin ku..
Anty ta ce
dakin ta yake OK to saina dawo yafice a dakin dan kwata kwata beson biye mata.
Ita Ko Anty fuskantar mama ta yi ta ce haba
Aishatu kina ban mamaki Wallahi Rahama diyar ki ce ta cikin ki amma kike nuna
mata rashin kauna..
Me laifina dan Rahama tana Y'ar daki na?
Wallahi duk abun
da zakiyi saide kiyi Wallahi ba zan taba Jin ina tsanar Rahama ba, koda kuwa
ita Rahama ta nuna ba ta yi Uban ta ya damka mun Amanar ta karkiyi tunanin
kinayin haka ne dan na ji haushi, Ko yau Allah yabarni ban haihu ba ba zanyi
bakin ciki ba tun da ina da Rahama...
Tsaya kiji dakyau Wallahi tallahi rantsuwar
musulmi nafison Rahama a kan Abdul jalil kinko san da cikina na haife shi..
Wallahi zakiyi kuka da idanun ki kirubuta ki
ajiye.
Tun zuwana gidan nan nakebin ki da lalama
burina mu zauna lafiya.
Sheik dai yana
mutunta ki sossai dan na lura ya fi sonki akaina hakan be taba batamin rai ba
Saboda nasan tare naganku, amma kuma mutuntuwa fa ya fi ganin mutuncina a kan naki,
Saboda kin zubar da girman ki antake shi.
Kinba Y'ar ki mummunar Tarbiyya Wallahi da
hannuna Salma ta zauna nasan Allah shi ne mai shiryawa da Wallahi ansamu saukin
tabarar da take yi " Ta ƙarashe zancen tana kokarin barin dakin.
Mama ce ta dakatar da ita cikin isa ta ƙaraso
gaban ta ta ce" ke Sa'adatu kike Ko tsiya.
Ai ke baki isa kice banda Tarbiyya ba shi ya
sa Yata Salma ba ta da shi ba.
Mu bama bin bokaye da malamai ba dole sheik ya
mutuntaki ba
Kuma....
Sallamar Salma da Abubakar ne ya sa Mama yin
shiru.. Cikin ɓacin
rai taga Abubakar tasan wa'azi ze tsaya musu barin wajen ta yi kamar zata
bangaje Anty....
Salma banda
harara babu abun da take jifan Anty dashi.
Har zata juya
Abubakar cikin tsawa ya ce Salma zo nan.Jiki babu kwarai tazo cikin tsoro..
Kallon banza yake binta da shi ya ce"
Wannan ba Uwar Ki ba ce kike hararen ta, Matar da duk wata matsalar ki tazo ita
ce kan gaba ita ce me nuna jajircewa a kan ki, duk da rashin hankalin da kike
nuna mata.
Maza ki duka
ki ba ta hakuri Ko in yi kasa kasa dake.
Anty Murmushi ta yi ta ce" Haba Abubakar
Yarinya ce fa haryanzu ka kyaleta kar ka damu Ko taki taso ni uwar ta ce.
Cikin zumbure zumbure baki ta dur kusa cikin
muryan takura ta ce" Anty kiyi hakuri Daga haka ta Mike ta yi sashin Uwar
ta..
Abubakar hakuri yake ta ba Anty ya ce" ta
yi hakuri shibesan irin Mama ba.
Amma wataran
zata gane gaskiya.
Anty ta ce"
kar ka damu ɗana Allah
yadada shiryamu dukan mu..
Da ameen suka
amsa dukan su....
************************
Samad kwance
yake kan kujerar falo 3str Idanun sa a lumshe zakai tunanin kallo yake, amma
Sam ya yi zurfi a tunani har barci ya fara daukan sa nan take wajen ya yi barci.
Cikin barcin ya
fara mafarkin wannan zanen tashi daya zana.
Tafiya yake
cikin ciyayi inda wajen zagaye yake da fulawowi masu ban sha'awa gwanin
burgewa.
Sai fadi yake
ina kike ne hasken zuciya ta yau raina a ɓace
yake, pls dan fito mana kidaina boye mun wannan kyawawan fuskar taki kullum
cikin nikaf kike, amma bankasa kazo zanen naki a nikaf din ba.
Dariyar yaji wanda ya sa shi juyowa yana
kallon ta tana tahowa cikin wani irin tafiya mai daukar hankalin, tasha ado
kamar Matar basarake stil dai wannan nikaf din na fuskar ta..
Fuskar ta dauke da Murmushi ta ce........
5️⃣3️⃣
Ta ce yakai
Amjad din zuciya madubin dubawa ta hasken idaniya ta.
Tabbas ni ta kace
kuma uwar yayan ka haryanzu ba ka gamsu bane tana Murmushi mai kayyatar da
masoyin ta.
Samad cikin shakuwa yake nuna mata ta kalli
sama kusan a tare suka Daga kai suna kallo.
Ya ce kinga
yanda sararin samaniyar nan ke haskawa haka kaunar ki take karuwa acikin zuciya
ta '' pls Abar sona ki gayamin gidan naku Ko ince inda zan same ki.
Kinmin
Alkawari zaki tsaya mun a kan komai na rayuwa ta.
Kwabe fuska ta yi cikin wasa ta ce kai Amjad
dîna ka san dani kaje kayi aure.
Kallon yake cikin kasa da murya ya ce nayi
aure kisani ba ta da gurbi acikin zuciyata kece muradina ita Zabin iyayena ce
ki fahimce ni.
Kallon shi take kallo mai daukan hankali Kallo
mai nutsar da zuciyar ma'abota soyayya.
Wacce ka aura ba zan iya zaman kishi da ita
ba.
Yarinya mai kamala ma'abociya addini ce saurin
katse ta ya yi da fadin kamarke haka take !!
Ki faɗa
min sunan ki da unguwar kinada ga cikin dalilin zuwa na kano.
Kince innazo
zanga mahaifina nazo Amma shiru ne bangan shi ba..
Kallon shi take tana nazarin kalaman sa.
Ahankali take motsa labban ta ta ce kaine kake
ganin bakaga mahaifin ka ba.
amma shi ya san
da inda kake kuma yana da labarin ka.
Alkawari daya
za ka min duk rintsi kar ka wulakan ta matar ka.
Koda kuwa
bakason ta.
Ba na son ka
aikata aikin ɗana sani
InshAllah nakusa bude maka wannan kyawawan fuskar da kake ambata kana son
gani..
Tashi ta yi zata fice.
Da sauri Samad
yasha gaban ta ya ce yau ba zamuyi yawo cikin jejin nan bane.
Girgiza kai ta yi Alamun A'a.
Ganin tana ta
zuba uban sauri yana ihu dan dakata mana.
Faruk tsaye a kan sa rike da kugun sa hannun
ya sa yasoma bugun kafar sa firgit ya farka Idanun sa ya sauka a kan Faruk..
Faruk ya ce haba yaushe rabon da kayi mafarkin
nan tun kan kayi aure.
Shi ke nan mun
shiga uku mafarkin yadawo wlh Samad harda Aljanu ke damun ka..
Tashi Samad ya
yi Daga kwance yana mika hade da hamma cikin muryan barci ya ce nifa ba na son
sa'idanu ina ruwan ka da mafarkin inbanda gulma na cinka.
Faruk rike da baki ya ce wallahi matarka saida
ta toshe kunnen ta yanda kake ta ihu kana fadin ki tsaya karki tafi dan iska
tashi kabita mana amma ba anan za ka baje mana kana kashe mana kunnuwa ba.....
Aminu ne
yakaraso falon ya ce Faruk dafatan dai ya farka Ko caraf Idanun sa suka tsarke
cikin juna shida Samad dake hararan sa yana tsaki.
Barin su ya yi
cikin sauri yake hawa kan matakalan step direct dakin sa ya nufa...
Faruk da Aminu kallon shi suke harya shige
dakin.
Faruk ya ce gaskiya mu nemo masa magani karya
Aljana ta aure shi..
Aminu ya ce
kuma haka ne amma dole ne mu nema mishi magani....
Samad na shiga dakin kan gadon sa yafada yana
mika hade da kara rufa lausasan bargon sa ajiki..
Adu'oi kariya ya fara karantowa yana gama
adu'a ya tofe jikin sa..
Kallon inda
Rahama ke kwanciya ya yi ganin wayam babu ma kayan ta awajen Abun da ya faru
dazun ne ya fara dawo masa cikin kan sa.
Jikin sa a mace ya furta ya Salam wai me damun
sa ne meyasa yaci zarafin wannan kanwar Rahama wata zuciyar ta ce yarinyar ce ba
ta da hankali '' amma duk da haka yana ganin kamar ya yi kuskure hana Rahama
rakiya cike da tunani barci ya yi awon gaba dashi...
Itakuwa Rahama zaune kan dadduma tana waya da
Asiya cikin Jin dadi ta ce kice gobe ina manyan baki.
Asiya ta ce
kwarai kuwa gayamin me zaki dafa mun me dankaren dadi.
Rahama jujjuya
Idanun ta ta yi wanda ya bayyana cikar Idanun ta ta ce uhmm ke ai nidake babu
shamaki tsakanin mu duk abun da kike so zan dafa miki ko ki dafa da kan ki..
Asiya ta ce ke dai Allah yakaimu Aminiyata.
Da ameen ta
amsa mata.
Asiya ta ce
Rahama wai meyasa bakya yawan hawa online ne Ko mijin naki beso ne ?
Rahama ta ce ni
dai ce banda lokaci Asiya ga karatu ga aikin gida '' be zama lallai inba whsap
lokaci na ba.
Amma in ina
free Tabbas zan hau ayi hira..
Asiya ta ce haka
ne kuma Allah ya samu adanshin ku.
Ameen tabata amsa cikin muryan dake nuna
kasala ta ce Asiya ni zan kwanta Daga haka suka yi Sallama.
Kokarin hayewa
gado take ta ji ring din wayar ta hakan ya sa ta saurin dubawa ganin nombar
Sheik ne ke yawo kan screen din wayar..
Cikin hanzari
ta Daga.
Bakin dauke da
sallama.
Sheik cikin
Jin dadin Jin muryan ta ya ce diya ta dafatan dai kina lafiya.
Lafiya lau ta
ba shi amsa.
Abby nayi miss
dinka ina son inzo gida inkawo maku ziyara.
Murmushi ya yi
ya ce Rahama ta basai kinzo ba kisha zaman ki ni gobe ma tafiya zanyi nida
Amini na..
Rahama ta ce
Abby tafiya kuma ina za ka je tafada cikin yanayin damuwa.
Sheik ya ce
walimar aure ne a kasar Gabon kedai kiyi muna adua dalilin kiran naki kenan..
Rahama numfashi ta fesar ta ce Allah ubangiji
yakaiku lafiya yadawo daku lafiya..
Ameen summa
Ameen suka amsa...
Daga haka
sukaci gaba da hiran su yana kara mata haske kan abubuwan da suka shige mata
duhu......
Kashe Gari.
Bayan ta idar
da Sallah Asuba zaune takoma kan sallayar ta tana azkarai.
Alkur'an
tadauko zata fara karatun ta ta ji karar buga kofa..
Hakan ya sa ta
ajiye a kan dardumar ta tare da nufar kofar dakin a hankali ta murda handle din
kofar.
Tare da budewa
kallon shi take yana sanye cikin farar jallabiya da hula a kan sa.
Tsintar murya
ta yi yana Fadin lokacin Sallah haryawuce na mance ban tashe ki ba.
Cikin sanyi murya ta ce ai nayi sallah.
Durkusawa kayi ta yi cikin ladabi ta ce ina
kwana ya karfin jiki..
Ciki ciki ya amsa mata da lafiya lau.
Kokarin rufe dakin take ya zuba mata zararan
Idanun sa masu kashe garkuwan jikin yan mata..
Ya ce ina tsaye bakin kofar zaki rufe ?
Yi hakuri na zata za ka wuce ne kara bude
kofar ta yi tana nuna masa hanya ya shiga.
Shiga dakin ya yi sai bin dakin da kallo yake
har Idanun sa suka sauka kan wannan akwatunan lefen..
Kallon su yake
yana ciza labban sa.
Cikin isa da
izza ya ce wannan kayan kinfara Amfani dasu ne ?
Girgiza masa
kai ta yi Alamun A'a.
To karki kuskura kiyi Amfani da nasan kina jin
dadin zaki saka kayan da wani kato yasiya to ni agida na ba a wannan tsarin ina
fatan kin fahimce ni.
Gyada masa kai tayi.
Ya ce wannan
kayan zan adauke su Aba mabukata.
Su kuma gold
din saida su zanyi inkai kudin gidan marayu.
Rau Rau take
kallon sa a zuciyar sai fadi take to saime daman akwatunan basu dameni ba.
Kallon ta yake
ya ce kina magana ne ?
Naga labban ki
na motsawa...
Girgiza kai ta yi Alamun A'a gaskiya ba abun
da nace..
Good ya furta kindaiji abun da nace lefe da
kaina zan hado miki kwanan nan ki shirya anjima mu je super market ki duba
kayyayakin da kike so..
Daga nan mu je
kasuwa insaimiki atamfofi da lace material.
Kin san zamu
ta yi Ko.
Tafiya ta maimaita a fili.
Tana mai
kallon sa..
Daga mata gira
ya yi Alamun haka ne.
Shiru ta yi tana tunanin to ina za su je ne
wai Allah batason barin garin su...
Dawo da ita
cikin tunanin ta ya yi ta hanyar fadi zamuje garin kwatano dake ki shirya nan
da kwana uku masu zuwa..
Kallon reaction
din yake yanda yaga zallan damuwa..
Cikin yin kasa da murya ta ce Allah yakaimu.
Ameen ya amsa mata cen ciki tare da baro dakin
nata.
Itako Rahama
tunani tashiga meyasa sai yau ze gayamata zasuyi tafiya ''
Tafiyar mai ba ta kusa ba oh Allah yazanyi
rayuwa garin da ba nawa ba ban taɓa
fita kasar nan ba.
Iyaka ta
Lagos.
Yau gashi anzo
mun da bakon Al'amari.
Daukar wayar ta ta yi tare da kiran anty ta
sanar mata anty nuna mata ta yi bama tasan da zancen ba ta ce kwatano kuma
zakije Rahma kiyi hakuri aure ne babu inda bekai ya mace amma InshAllah gobe da
kaina zanzo karki wahalar da kanki kice zakizo gida nafison sai kin shekara
Sannan kizo kinji Ko daughter.
Gyada kai ta
yi cikin gamsuwa da bayanan anty sallama suka yi.
Inda Anty ta
ajiye wayar Domin zuwa hadawa sheik break da dawuri za su tashi...
Bayan kowa ya
karya agidan sheik ya tara s'u ya ce to Allah ya yi zan tafi dan Allah azauna
lfy da juna.
Kallon Salma
ya yi ya ce ke banson yawo inbada izinin mijin ki ba.
Abubakar ya ce Abba kaide gayamata fa dan naga
tafita wlh zan gyara ta sai dai in mijin nata ne yabata damar fita yakarashe
zancen yana mai daukar jakar sheik ze fice waje.
Mama ta ce
amma dai Abubakar bakada kunya kenan ni ka daukeni uwar banza kenan kana nufin
zanbar Salma ta yi abun da taga dama ne kaine me hankali kaika iya magana Ko ?
Rike da baki
Abubakar ke kallon uwar sa ya ce haba Mama wai ina ruwan ki da sha'anina da
kannena ne naga dai bake kadai ba ce agidan nan akwai anty ita bataji zafi ba
saike.
Mama ta ce
taya za ai ta ji zafi tasan zafin haihuwar ya mace ne akasa ta tsinta.
Sheik yaji haushin kalamin ta hakan ya sa ya
fi ce Daga gidan.
Bin bayan shi Anty
da Abdul jalil suka yi suka bar Mama da Salma.
Kofar gida sheik ya ce to sa'adatu mun tafi
Allah ya kaddara saduwar mu
Adu'a ta fara
masa cikin sanyi murya ta ce Allah yakaika lafiya yadawo da kai lfy yatsare ka.
Ameen suka
amsa tashi yayin da drever ya bude masa mota ya shiga...
Abubakar da
Abdul jalil shiga motar suka yi suma.
Anty na tsaye
tana kallon su har motar yabar unguwar tana ta Daga musu hannu.
Komawa Daga
cikin gidan tayi.
Nan inda tabar
mama da Salma nan ta same su mama na ganin ta takara sautin muryan ta.
Ta ce ke Salma
ki abun da ranki yake so tun da baya nan duk inda kike so ki je wlh banga uban
da ze hana ba kuma wata munafukar taje ta gayamasa zata fuskanci hukunci Daga
gareni.
Salma shewa ta
yi tana taba hannun ta ta ce yawwa mama shi ya sa nake sonki.
Kada kai Anty ta yi tare da barin wajen cikin
hanzarin ta...
Cen airport
Aminin Sheik zaune yana jiran sa ganin karasowar ya sa ya nufi inda su sheik
suke.
Babu ba ta lokaci
aka fara kiran suna hakan ya sa sheik bin bayan Aminin sa cikin sauri.
Abdul jalil da
Abubakar kallon su suke suna Daga musu hannu har suka shige jirgin....
Kasar Gabon.
Yau tun safe
baba salihu yake ta faman hada kayan sa.
Ze bar kasar
zuwa kasar Nigeria kano..
Duka wata daya
zeyi yakoma Gabon..
Sai kiran su
yake airport din suna kara jaddada masa jirgin kano besauka ba.
Data sauka za
a sanar masa yazauna cikin shiri..
*************************
Masarautar
gheuzo.
Mai Martaba
zaune cikin shigar sa na sarakuna gefen sa waziri ne.
A damar sa
Abban Marwan ne zaune dirshan cikin muryan roko ya ce Allah ya taimaki Sarki
ataimaka ayiwa Marwan aure yaga wacce yake so..
Mai Martaba
kallon sa yake cikin dattako ya ce Marwan ne za ai wa aure yaron da Ko aikin yi
beda shi.
Abban Marwan ya yi kasa da murya ya ce cikin
tsoron mahaifin sa ya ce mai martaba aiyasamu aiki Samad compagny a kano tare
suke aiki nan ze koma yaci gaba da aiki.
Mai martaba ya
ce A'a ya je ya nemi aikin kansa ya yi inda gaske ne meyasa Abdul Samad be faɗa min ba.
Abban marwan ya
ce kila ya Manta ne amma tabbas tare suke aikin da shi aka bude kamfanin.
Mai martaba ya
ce na ji zanyi magana da Samad in ji kanun labarai.
Ba ƙaramin
haushi Abban Marwan yaji ba yafadi magana amma ace masa sai anbincika cikin dan
bacin rai ya ce nina tafi mai martaba saina jika.
Daga haka ya
fi ce cikin Jin haushin su..
Mai martaba
kallon waziri ya yi ya ce ina son afara tarawa gidan nan Saboda ayi shela domin
sanarwa jama'ar masarautar nan gangarumin taron da za a hada na tarban Matar
Samad 'sashin da zata zauna ita da mijin nata agyara musu a canza furniture
komi na dakin.
Sannan lefen
da masarautar ta hada akwatuna 24 su zama ready.
Zamuyi taron
bikin namu na musamman nan da sati biyu InshAllah kafun nan ɓangaren mamy zata zauna.
Waziri cikin bangirma ya ce ya shugaban Adalai
InshAllah yanda kace haka za ai.
Jakadiya ce ta
shigo cikin bangirma ta ce ya shugaba Mama karama tana neman ai mata iso wajen
ka.
Allah ya
taimakeka Sarki mai ran karfe.
Kallon ta
yake.
Waziri ya yi caraf
ya ce Jakadiya sarki yabada dama a shigo da ita.
Cikin rawar
jiki tabar fadan.
Kalllo bayi da
kunyagu take kowa na hidimar gaban sa sanye suke da uniforme din masarautar.
Ganin Jakadiya
ya sa suka fara gaishe ta.
Tare da rusuna
kai.
Hajiya Hassana
cin karo suka yi ita da Jakadiya.
Kallon kallo
suka Shiga yiwa juna.
Hassana da
Murmushi ta gaida jakadiya ta amsa mata cikin sakin fuska tana tambayar kan ta
Ko wannan ce bakuwar da Akace masarauta tayi..
Jakadiya ta ce
dan Allah Ko kece bakuwar gimbiya Mamy.
Murmushi ta yi
ta ce eh Nice, Sunana Hassana dafatan na sameku lafiya ina son abokiyar hira a
masarautar nan...
Jakadiya ta ce
ai indai wannan ne kinsamu zan ha daki da baiwar Samad Karima..
Hassana cikin
Jin dadi ta ce dan Allah hadani da karima.
Jakadiya ta
kalli cikin kunyagu dake kai kawo cikin masarautar ta ba da umarnin a rakata
gun Karima tare da yin gaba dan isar wa Mama karama sakon mai martaba...
Kunyaga takai
hassana har dakin Karima iske ta suka yi zaune Alamun wani muhimmin abu take
ganin su ya sa ta zabura.
Tafara in na
in na ciki yake ta ce ke Daga ina haka ai wannan bakuwar Mamy ce.
Hassana
Murmushi ta yi ta ce eh nina ce akawoni.
Kuyanga ta ce
jakadiya ta ce a kawo ta gun ki Daga haka tawuce.
Karima ta ce
bismillah tare da ba ta wuri ta zauna.
Shiru ne ya
ratsa dakin na wani lokaci.
Hassana ta ce
Karima ance ke baiwar Samad ne.
Eh 'ni baiwar
sa tabata amsa ataikaice tare da yin shiru na rashin sabo da ita..
Murmushi ta yi tana kallon Karima tana nazartan
yanayin ta.
Ta ce yawwa
Karima ina son in zama abokiyar hirar Ki inbabu matsala.
Karima ta ce
wannan me sauki ne.
Fita nake
shirin yi dan Shugaba na yakusa dawowa kuma tare da Matar sa Amaryar sa..
Hassana ta ce kina nufin daman Matar tasa ba
ta taba zuwa masarautar nan bane..
Karima gyara
zama ta yi tana fuskantar hassana.
Ta ce eh
betaba kawo ta ba Asalima wannan matar da ya aura gidan nan babu wanda ya san
ta sai Mamy da mai martaba da Abban Marwan..
Hassana rike da baki ta ce Ko zaki gayamin ya
haka ta ka sance kuwa da mamaki Yarima dan Sarki jikan ace ya yi aure ba tare
da duniya ta ji ba..
Karima ta ce
ai wannan karan duniya zata ji dan zuwan ta ba ƙaramin Girgiza masarautar nan zeyi ba....
Hassana ta ce
kamar ya kenan ?
Karima ta ce
zan miki bayani bakuwa ki bari anjima inna nutsu.
************************
Fulani ta
shiga babban tashi hankali bokan jeji ya tabbatar mata kada su bari Rahama ta
tako kafar ta cikin Masarautar nan yin haka ze wargaza komai sabanin da da ake
so tazo...
Yanzu kuma ya
lura zuwan ta ze ba ta komai ne ba gyara ba dan yarinyar tanada taurin kai.
**************************
Maman Maryam cikin tashin hankali take magana
da Abban Maryam dake fadi mata maza maza ta dakatar da Yarima tun da ita ce ta
ce yakawo ta.
Maman maryam
cikin zafin nama tadau wayar ta ta dannawa Samad kira...
Har wayar
takusa tsinkewa ya Daga.
Cikin bangirma
ya ce mommy na dafatan kina lafiya.
Lafiya lau ta
ba shi amsa atakaice.
Ta ce Samad
naam ya furta tare da gyara zama a kan kujerar 1str na falon sa yana sauraren
ta.
Ina son kafasa
zuwa da matar ka ?
Zumbur ya Mike
tsaye ya ce banji dan........
5️⃣4️⃣
ZUMBUR YA MIKE
TSAYE YA CE BANJI BA MOMMY KIKACE KADA INZO DA ITA.
MOMMY TA CE EH
HAKA NAKE NUFI YARIMA KA FAHIMCE NI.
Maryam ce take
kuka a kan son da take maka ta ce ba ka Daga wayar ta kwata kwata ina tsoron
kazo da matar ka Jinin ta yahau takarashe zancen tana kukan karya.
Samad dake sauraren ta lumshe Idanun sa ya yi
ya ce mommy naam ta amsa cikin tsai gaita kukan ta.
Ina son kisan
cewa na haramtawa kaina auren Maryam hakuri za ta yi Inde a kan Maryam ne ba
zan iya fasa zuwa da ita ba.
MOMMY kiyi
hakuri dan Allah nariga na gaya mata tare zamu tafi ba na son raini ya shiga
tsakanina da ita dan tana ba ni respect daidai yanda Allah ya ce.
MOMMY ta hada
rai kamar yana gaban ta '.
Ta ce yanzu
Samad duk kukan nan da nake yi dan yata Ashe ba za ki ji tausayin ta ba
Samad sassaita
muryan sa ya yi ya ce mommy ina me baki hakuri nariga nayi kudiri da niya kuma
har mai Martaba ya san da wannan batun.
Tun farko kece kika samun sha'awar zuwa da ita
sabanin da.
Da ban kawo
hakan araina ba..
MOMMY cikin
Jin haushin sa ta ce Samad kaban mamaki yanzu in Mamy ce za ka ce mata ta yi hakuri.
Cikin gyara
zaman sa ya ce kwarai kuwa har Mamy zan fadawa ta yi hakuri shari'a ba ta yarda
kaci zarafin iyayen ka ba.
Yi musu
biyayya abu ne mai kyau.
Amma Saboda ke
kadai ba zan ba ta ran mutane dayawa ba.
Yi hakuri
mommy Daga hk ya katse wayar ransa aba ce cikin Daga murya ya ce wai ita wannan
matar meye matsalar ta ne.
Murmushi ya yi
uhmm koda yake batasan kallon ta nake ba mu je zuwa.
Ita Ko maman
maryam tsine masa ta rinƙa yi ta ce shege dan akuya ni ze gayawa zancen banza.
Abban Maryam ya
ce Kinga matsalar yaron nan Ko ya zamuyi ne.
Maryam ce ta
fito Daga dakin ta sanye take da riga da wando cotton sossai yakama jikin ta
kowani sassa na jikin ta yana motsawa.
Cikin hanzari
takaraso Idanun ta cike da kwalla ta ce Mommy ya amince ba zai zo da ita ba Ko
?
Kallon Maryam
take ta ce inafa ya Amince dan iskan yaro.
Maryam ta ce
haba mommy kidaina ce masa dan iska agabana inajin ciwon haka.
Abban maryam ya
ce ke shasha ce duk wannan abun munayi dan ke ne.
Inkin ce kin
fasa baki son sa.
Zamu cire
hannu a kan lamarin sa '' kema kin san babu abun da matar sa ta tare muna Ko.
MOMMY TA CE gayamata shasha kawai.
Maryam cikin
kuka ta ce mommy ku yi hakuri wallahi ina son Samad duk abun da yadace ku yi.
Nabishi ta
lala m'a yaki kulani nazo ta kar kashin kasa nan m'a abu be canza ba..
Abba zama ya
yi kan kujera tare da zaunar da Maryam din.
Cikin muryan
rarrashi ya ce ki barta tazo din InshAllah Ko babu boka babu mallam akwai tugun
da zamu kulla mata wanda zai sa akore ta Daga masarautar gheuzo.
Cikin Jin dadi
takwanta jikin Abba ta ce wai dagaske kake Abba na..
Kwarai kuwa
Maryam dita.
Kisha kurumin
ki yata sai inda karfi na yakare InshAllah zaki zama uwar yayan Samad.
Murmushi ta yi
ta ce Abba nagode Allah yabaka sa'a.
Da Ameen mommy
da Abba suka Amsa.
Mommy ta ce
ina nan fa ina neman wani malami da akace mun yana aiki kamar yankan wuka.
Kawata keban
labari InshAllah zanje cen mugani..
Abban Maryam ya
ce wannan shi ne daidai in hagu taki a koma dama....
_________________________
Mamy cikin
dakin ta take tana dan gyara kayan wankin da suka bushe da tafiso ta gyara su
da kanta kafun tabayar ayi mata guga...
Shigowar
khadija yajawo hankalin ta a kan kallon ta take cikin sakin fuska ta ce
daughter har kin gama kallon ne ?
Cikin turo
baki gaba ta ce bashi bane ba.
Mamy ta ce wa
kenan ?
Sallamar
Yarima Ahmad ne ya sa ta fadin ke da shi ne kuke fada Ko.
Yarima Ahmad
zama ya yi kusa da Mamy tare da cire hulan kan sa ya ce wallahi Mamy yarinyar na
n taraina ni dayawa kiringa ba ni daman ina dan casa ta.
Mamy rike da
baki ta ce chabdi Amma ɗai
wuyan ka ya yi kauri duka da nawa ka girme ta.
Wai ma tukunna
ma laifin me ta yi maka ne..
Gyada kai
khadija ta yi ta ce atoh shi ne abun da ya kamata kiji.
Tana hararan
sa ta ka san idanu.
Shiko cikin
isa ya hada rai Alamun babu wasa cikin maganar sa.
Ya ce Mamy
koda tare muka zo duniya nida ita dole ne fa in gayamata mata gaskiya.
Wayar ta
nadauka wlh ba ta da kawaye sai zallan Arna.
Whasap din ta
nashiga bakiga irin fitsarrarun kawayen nata ba.
Cikin su harda
wata wai ita salomon shegiyar kafura wanda rabin nonon ta awaje hoton data
daura a kan Dp din ta..
Gasu nan
dayawa basai na fada.
Tashi ya yi Daga
zaune yana fuskan ta khadija cikin bacin rai ya ce wallahi Mamy wayar khadija ba
zan ba ta ba sai ta yi hankali.
Boko hauka ne
Ko wacce intazo da rashin kunyar ta sai ace ai yar Boko ce
Ni dai ba zan
zuba idanu ba Allah ya gani hakkina na ne inkula da ita.
Samari m'a
haka kowani kare yana da nombar ta.
Kai har m'a
kawayen ta musulman bakiga fitsarrarun da take hulda dasu ba.
Ni dai banaso
banaso banaso yakarashe zancen kamar ze take khadija da kafafun sa wanda haka
ya sa aguje ta Haye gadon....
Mamy cikin
sanyin jiki ta ce yi hakuri baba na kanada gaskiya kanwar kace kanada iko a kan
ta '' fuskantar khadija cikin bacin rai ta ce baki isa indaura a kan hanya
madaidaiciya ba wasu Arna da fitsarraun yaran musulmai susa ki kauce hanya ba..
Ki nutsu ki
maida hankalin ki a kan karatun ki.
Jiki magayi ba
zan kara hanashi ba inhar zebuge ki yana son ki bakowani dan uwa bane yake kula
da sa'idanu a kan dan uwan sa ba.
Wasu inkinga
sunyi magana sai ta baci.
Khadija kuka
take Daga zaunen.
Ahmad da kukan
ta yana kara hasala shi ya ce Mamy da kinbarni na dan gyara ta koda na minti
daya ne kinga ai ta yi kukan da hujja Ko..
Mamy ta ce A'a
kyaleta ai akwai gaba inhar ba ta gyara ba kayi mata yanda kaso.
Kara zama ya
yi kusa da Mamy ya ce yawwa Mamy Samad yakusa zuwa naga ana ta shirye shirye
har katuna aka buga na ganarumin taro da za ai na auren Samad.
Mamy Murmushi
ta yi ta ce to nacewa Mai martaba basai an yi ba tun da amma ya ce Sam ba
wannan zancen dole ne ya yi cewar shi jikan Fari abun soyuwar sa.
Ahmad ya ce
oho kenan in mune ba zai mana wannan gatan ba.
Mamy ta ce ina
zan sani kana iya zuwa fadar shi ka tambaye shi.
Ahmad Murmushi
ya yi ya ce ayi Samad ne kadai yake shiga fadar sa ba tare da an yi masa iso
ba.
Mune aka raina
Ko tonima auren nan zan nema gaskiya dan kada mu rasa gatan da ake yiwa masu
auren.
Jin muryan
khadija ya yi Daga bayan sa cen karshen gado ta ce uhmm wace mata ce zata aure
ka sai dai a rashin Sani.
Juyowa ya yi yana
kallon ta ya ce idan na kawo ta ki hanata zama yar rainin wayau ai Saboda ke
zan siye bulala na ajiye.
Tashi ya yi Jin
wayar sa na ring ya ce Mamy zanje indawo Daga haka yafice cikin tafiyar sa mai
daukan hankalin yan mata..
Yana fita Mamy
ta fuskanci khadija ta ce kinga ba na son kina masa rashin kunya kin san dan
yana ganina ne yake shanye wani abun ''badai kin rainasa ba ai ga uban gayyan
nan zuwa zamu ga yanda zaku kare da shi kin san halin sa babu sauki sai wajen
Allah..
Khadija ta ce
Mamy InshAllah zan canza kodan Mala'ikan mutuwa nan Yaya Samad..
Murmushi Mamy
ta yi ta ce Ko ke fa Dadina dake kina daukan shawara Allah Yayiwa Rayuwar ku
Albarka da Ameen suka amsa a tare.
______________________________
Karima a Nutse
ta yi aikin ta tagama tare da taimakon hassana sossai ta taya aiki suka yi
komai tare..
Hassana ta ce
woww gaskiya dakin shugaban ki yahadu sai kace ba a duniya ba Allah kasa ta
Aljanna tafi wannan haduwa.
Ameen Karima
ta amsa tana dariya ta ce ai Samad ne fa uban gidan nawa na daban ne antina..
Kusan âtare
suka dawo sashin Karima tare da zama ka san dakin dirshan.
Karima ta ce
antina zauna kan bakin gado mana.
Hassana ta ce
A'a nima ka san tafimin dadi.
Kallon Karima
take cikin zakuwa ta ce yawwa kin ce zakiban labarin Samad Ko yanzu tun da mun
gama kidan ba ni labari mana tana me gyara zaman ta..
Karima ta ce
kin san nama mance munyi haka dake bakida mantuwa.
Murmushi
hassana ta yi ta ce taya zan manta nida na zaku in ji labarin nan.
Karima gyara
zaman ta ta yi ta ce Samad da kike gani guguwa yake mai tada taro.
Hassana ta ce
inajin ki Karima ba ni Insha mana..
Karima numfashi
ta fesar ta ce uhmm ta ce wannan matar da Samad ya aura ai Daga gun daurin
auren wani dan abokin mai martaba ne aka fasa da wancen yaron aka ba Samad.
Hassana ta ce
kam buhu ya Samad din ya yi Ko ita yarinyar da Aka hadasu ba tare da sanin juna
ba.
Karima ta ce
ai yanzu bazamu San haka sai sunzo garin nan amma da dukan Alamu yana rike da
ita dakyau dan na lura da hakan beda wulakanta ɗan
Adam indai ba ya canza ba ne.
Hassana ta ce
wai mahaifin nasa yana ina ne ?
Karima cikin
tsoro wannan tambayar ta ce gaskiya nasan mahaifin sa baya garin nan..
Sai ta yi shiru
tana wasa da yan yasunta.
Hassana ta ce
kiban labari mana naga kinyi shiru Ko sirrine
Karima ta yi shiru
cikin yin kasa da murya ta ce antina gaskiya ba za kiji wannan labarin abaki na
ba..
Cikin razana
hassana ke kallon ta ya ce kamar ya kenan ?
Karima cikin
yin kasa da murya ta ce '' gaskiya na fada miki ba zan iya gayamiki komi a kan shugaban
adalai ba wannan sirrine tsakanina da ubangidana.
Amma meyasa
kike son sanin abun da be shafe ki ba ta jefo mata tambaya cikin tsareta da
idanu..
Hassana
Murmushi ta yi ta ce na de tambaya ne dan sainake ganin kamar mun zama daya tun
da nima gani a cikin masarautar gheuzo tun da kin ce haka babu matsala.
Karima ta ce
uhmm kedai bari Nina baduka nasani Ba a kan rashin zaman sa a masarautar ba
wannan sai jakadiya ita ce tasan komai sai Mamy da mai martaba da Samad wallahi
Ko Ahmad da khadija basu San komi ba dan an sirrin ta abunne duk da maganar ta
fita waje har duniya ta dauka.
Amma Daga baya
mai martaba ya dakatar da yaduwar wannan mummunar labarin.
Hassana cikin
yin kasa da murya ta ce Karima wani mummunar labari ne wannan da baki son naji.
Karima tashi
ta yi Daga tsaye tana kokarin shiga bandaki.
Hassana ta ce
haba Karima muna magana kin tashi ?
Cikin muryan
kuka Karima ta ce Alwala zanyi Daga hk tashige bandaki..
Hassana tashi
ta yi jiki asanyaye ta yi ɓangaren
Mamy tana Girgiza kan ta Alamun duk yanda ta dauki samun labari da sauki gashi
yana neman gagarar ta....
_________________________
Kano
Rahama cikin
rawar jiki ta ce ta rumgumi Asiya itama Asiya kara manne wa juna suka yi suna
kukan Farin cikin haduwar su.
Cikin zumudi
tasa ke tare da Jan ta suka iso falon kayan dake hannun Asiya take kallo tare
da sa hannu ta karba ta ajiye saman kujera..
Zama suka yi
cikin Jin dadi da Begen juna Asiya ta ce Rahama kinko ganki kuwa ?
Rahama ta ce
kamar ya kenan na rame Ko tana kwabe fuska.
Murmushi Asiya
ta yi tana gyara zaman ta a kan kujera ina fa Rama anan wajen ji yanda cika
ciko fa kinyi kiba sossai fa kirjin ki yacika komai hip din ki kardai kina
kashe bawan Allah nan Yarima da kayan kallo.
Rahama dariya
ta yi sossai da rabon ta da haka tun tana gida..
Ta ce kinga
Asiya har yanzu kina nan dai da halin ki Ko.
Kijimin zancen
banza tafada cikin cool voice din ta
Asiya ta ce
ina fa zancen banza anan wajen na tabbatar magana ta gaskiya ce..
Rahma kinyi
kyau kinyi fresh aure fa ya Amsheki kawata tashi Daga zaunen ta yi tare da zuwa
gaban Rahama ta manna mata kiss a goshi ta ce nayi miss din kamar in gudu dake
da kewa.
Rahama ta ce
ai basai kin fada ba kalaman ki da actin dinki sun nuna haka.
KADA in cika
ki da surutu bara in shiga ciki inhada inkawo miki abun sha.
Asiya ta ce
A'a ki barshi ba yanzu ba in ina bukata da kaina zanje indauka saikace bakuwa
muda gidan mu tana mata hararan wasa.
Rahama ta ce
au haka ne fa Sam namance tare da yin shiru suna fuskantar juna..
Shigowar Samad
ne yajawo hankalin su a kan sa.
Da sauri Asiya
ta sauke Idanun ta kasa dan ba ta fiya son kallon mazan mutane ba.
sanye yake
cikin farar shadda dinki zamani sossai shigar ta yi masa kyau.
Karasowa falon
ya yi yana kallon Asiya da mutuntaka tun lokacin daukan Amarrya ya yaba
hankalin ta.
Inawuni ta
furta ta ce yayin da take kallon le dan da Rahama ta ajiye kan kujerar.
Kamar ba zai
amsa ba.
Saita ji yana
fadin lafiya lau yau baki ne damu a gidan nan.
Asiya cikin
Jin dadin kalaman sa ta ce eh mune tun da bakwa neman mu ai ni nazo muku
ziyara..
Samad Murmushi
ya yi tare da zama kan kujera 1str yana kallon Asiya ya ce haba aminiyar mata
ta karki damu zamu zo miki ziyara dazaran mun dawo Daga kwatano yawwa inbabu
damuwa ina gayyatar ki rakiyar mu zuwa cen garin kwatanon..
Rahama da Asiya
kusan a tare suka kalli juna.
Samad dake kallon reaction ɗinsu ya ce Asiya ki fada
agidan naku dan Allah nasan dawuya su hana.
Rahama maganar
zuci take ta ce wannan mutumin inyaga mutane sai ya koma na Allah kamar duka
kenan Alhalin tsiya da wasali ne..
Asiya ta ce ni
me zanje in yi daga za ka je da matar ka saina biku.
Yarima ya ce
eh mana akwai wani taro da za ai acen ne kinga babu Kowa nata shi ya sa na zabe
ki..
Asiya ta ce
meze hana ku tafi da Salma.
Cikin dan ba
ta rai Rahama ta ce haba Asiya kina nufin Salma ita ce nawa yanda nake kusanci
dake banayi da Salma..
Samad ya ce
Rahama ki tashi ki je kitchen ki dauko mata abun tabawa kinbar bakuwa hakanan.
Cikin sauri
Rahama ta tashi dan cika umarni sa..
Ganin Rahama
ta tafi.
Fuskantar
Asiya ya yi cikin isar sa da kamalar sa ya ce Asiya ki taimaka ki je wannan
yarinya ce haryanzu kinfita sanin Rayuwa InshAllah Daga an yi taron nan zansa a
dawo dake koda mu ba mu tashi dawowaba
Asiya cikin
sanyin murya ta ce zanfada agidan mu insun amince zakaji Amsa abakin Rahama..
Dawowar Rahama
ne ya sa shi yin shiru yana kallon ta.
Ta kasar idanu
yanda durkushen da ta yi wajen siyaya wa Asiya lemu a kofi hakan ya sa rigar ta
sauka caraf Idanun sa a kan rabin boob din ta.
Tashi ya yi dan
be iya juran kallon wannan sakacin nata.
Sai Anjima ya
furta tare da fita compound din gidan.
Rahama zama ta
yi tana kokarin bude ledan da Asiya tazo dashi.
Yayin da Asiya
Kofin lemu na hannun ta a hankali take sha.
Samad sai.
Safa da marwa yake yi a compound din gidan yana tunanin wannan abun daya gani.
*******************...
Gabon
Baba Salihu a
filin airpot din shida dattijo suna zaman jiran waɗanda jirgi ya sauke su fita Sannan afara kiran
sunayen waɗanda za a
diba zuwa kanon..
Kallon jama'ar
dake sauka Daga cikin jirgin yake yana Murmushi ya ce ka ga kullum mutane cikin
yawan tafiye tafiye suke suzo suyi kasuwanci su koma yana murmushi.
Dattijo ya ce haka
ne ya shugaba na anjima za su sake dawowa daukan wasu.
Baba Salihu ze
bude baki ya yi magana...
Tashi ya yi Daga
zaune da yake yayin da yaga sheik yana kusanto inda yake shida Aminin sa
Cikin........
5️⃣5️⃣
Cikin sauri
yake kokarin barin wajen har yana neman tuntube Jin andafa bayan shi ya sashi
tsayawa cak ba tare da ya waigowa.
Sheik ya ce
bawan Allah lafiya kuwa kake buga uban saurin nan harkana tuntube kamanni naga
kana mun da wani bawan Allah.
Dan uwa na dan
juyo mana.
Aminin sheik ya
ce nima dai kamanni naga ya yi yawa ne shi ya sa nace mukaraso wajen mu
tabbatar da Idanun mu ne ke mana gizo koko dai shi dinne.
Baba Salihu
waigowa ya yi Idanun sa cike da kwalla.
Sheik da Aminin
sa kallon sa suke sake da baki.
Girgiza kai
sheik ya yi ya ce Ah Ah wannan ba baba salihu bane me ze kawo shi Gabon shida
yatafi gun iyalin nasa ba mu San abun da ya hana shi dawowa ba.
Aminin sheik ya
ce nima dai gaskiya ina tantama dan wannan Attajiri ne babban hamshaki.
Baba Salihu
kuma mai nema ne kamar mu.
Baba Salihu tun
da suke ta magana kallon su yake Idanun sa cike da hawaye.
Sheik ya ce yi
hakuri bawan Allah mun ba ta maka rai Ko wlh munyi zaton dan uwan mune.
Har sunsa kai
za su wuce.
Sheik yaji
ankira ainihin sunan sa
Abdurrazak
Abdurrazak Abdurrazak.
Waigowa ya yi yaga
wannan dai mutumin ne da suke kama da baba Salihu.
Sheik ya ce
Salihu Salihu kaine ?
Aguje ya je ya
rungume shi yana kuka sossai iya karfin sa.
Sheik ya ce
Salihu kai dinne dana sani koko kama ce.
Baba Salihu ya
ce Sheik nine mai gadin gidan ka.
Mutuwar tsaye
sheik ya yi kamar andauke wuta andawo dashi.
Aminin sheik
Malam Isa ya ce Salihu a Gabon bakin sa na rawa..
Sheik dasai a
yanzu yadawo hayyacin sa cikin bacin rai yakama hannun Aminin sa ya jashi cikin
sauri suke tafiya tare da nufar motocin da za su dauke su...
Baba Salihu
bin bayan su ya yi cikin Azama shida dattijo.
Koda suka iso
wajen nasu ganin Sheik suka yi anbude masa mota ze shiga.
Cikin masu
bude motar ya Kalli baba Salihu ya ce.
Ya shugaban
Adalai kaine nan da kanka ba za ka bari wani ya rakoka ba.
Sheik Sake da
baki yake maimai ta kalmar shugaban Adalai.
Baba Salihu
cikin yanayin damuwa yake kallon me masa magana ya ce.
Inka Kaisu ma
sauki kazo har gida ka dauke ni ka kaini gun su..
Sheik zeyi
magana ya ce A'a be yarda ba Aminin sa ya rufe masa baki da tafukan hannayen
sa.
Baba salihu na
tsaye motar tabar filin aiport din dasu Sheik.
Dattijo rike
da kugun sa ya ce ya shugaba na.
Wannan ai
shahararren Malamin Addinin nan ne muna kallon wa'azizunka sa
ka san shi
kenan da dukan Alamu..
Baba Salihu
kallon shi yake da rinannun Idanun sa da suka kada zuwa ja.
Ya ce eh nasan
shi mana shi ne wanda nake ba ka labarin sa nazauna gidan sa a kano.
Dattijo ya ce
gaskiya shugaba na dole ne yadau zafi duk da besan dalilin ka ba..
Baba Salihu ya
ce haka ne kana tunanin ze sauko ta ruwan sanyi ne.
Dattijo ya ce
kwarai kuwa inka hadashi da Allah da manzon sa ze saurare ka.
Murmushi Baba
Salihu ya yi ya ce nagode da shawara zo mu koma gida tafiya tasha ruwa..
Kai tsaye
wajen motar sa suka nufa.
Suna shiga
sukabar airport din..
****************************
Asiya kama
hannun Rahama ta yi suka je dakin nata rike da ledan da tazo dashi.
Rahama cikin
Jin dadi ta ce kinje super market ne kinsiyo mun biscuit ne kin san ina son cin
sa Ko.
Uhmm wanda ake
ajewa a gidan nan Sam bayamin dadi.
Asiya kallon
ta take tana Murmushi ta ce Rahama kenan kedai haryanzu kinki ki girma Ko.
Wai
intambayeki mana.
Rahma ta ce
inajin ki
In kika
kuskura kikamin tambayar banza zaki sani ne..ehee tana turo baki gaba.
Murmushi Asiya
ta yi ta ce na ji dai koma meye ai sai ki tsaya ki saurara Ko ?
Gyara zaman ta
Rahama ta yi tare da baza kunnuwa dan Jin abun da zata ce..
.
Asiya ta ce
Rahama nalura kamar babu shakuwa keda mijin nan naki kallo daya nayi muku na
fahimci hakan banson ki boye mun komai takarashe zancen tare da hada rai tamau
babu Alamun wasa..
Rahama ganin
Asiya ta daure ya sa ta daukan maganar ta serious.
Cikin yin kasa
da murya taba Asiya labarin komai tun zuwan ta gidan.
Asiye zare
Idanun waje ta yi da Rahma takai karshen labarin.
Ta ce yanzu
kina nufin tun zuwan ki gidan nan babu abun da ya taba shiga tsakanin ku keda
shi.
Rahama shiru
ta yi tarasa Amsar da zata bata..
Asiya tashi
Daga zaune ta yi tana ta buga hannayen ta..
Ta ce uhmm
Rahama kinban mamaki fa da karatun da sanin ki da komai amma kike take sani..
Rahma cikin
kunan rai ta ce Asiya eh da karatuna nasan abun da nake.
Taya zeringa
Fadin auren Sadaka ce kinkosan yanda kalamin nan yake min ciwo acikin zuciyata
kuwa banda wanda zan iya gayama abun da ke ba ta mun rai saike Asiya...
Da wannan
kalamin nasa na gwammace yabugeni zefimun sauki.
Sannan niban
hanashi kaina ba kin san banda karfin sa duk da ba ni so.
Shima kamar
yana zama dani dan dole ne.
Asiya Ki
fahimceni cewa ya yi auren biyayya ne banzo gidan nan ba dan in kuntata masa
ba.
Nadauki aure na
da shi Kaddara ce.
Asiya cikin
Jin tausayin Rahama ta zauna gefen ta rike da hannayen su cikin juna.
Ta ce Rahama
kema kin san Allah ya yi miki canji mafi Alkhairi shi ne ya mallaka miki
Yarima.
Wallahi
kundace kedashi duk wanda ya ganku.
Ki saki ranki
ga kayan gyaran jiki nan Anty ta hado miki dan batasan cewa har yanzu a leda
kike ba ba a bare ba.
Nasan dasai ta
kusa Zane matar Samad.
Rahama
Murmushi ta yi tana fiddo kayan dake cikin ledan.
Wani roban
Zuman yaji hadi sossai ta fiddo ta ce wannan Zuma ce.
Asiya ta ce
kisha kiji mana abu yana hannun ki amma kina tambaya ta..
Bude murfin
roban Rahama ta yi tare da da dan lakutowa da hannun takai bakin ta.
Lumshe Idanun
ta ta yi ta ce Asiya wannan Zuman badai dadi ba har wasu kwa kwa nake ji a
ciki...
Asiya ta ce uhmm
nasan ke uwar kwadayi ce saiki shanye tas yanzu amma fa kibi a hankali kisha
Rabi yanzu.
Sauran
kibarshi sai munje kwatano kinsha.
Rahama ta ce
haba wlh ni duka zan shanye ba zan iya bari sai munje cen ba.
Dariya Asiya
ta yi sossai harda rike ciki ta ce ina ruwana ki shanye mana Ai Samad yana gari
kika matsu ze rage zafi cikin ruwan Sanyi ba tare da yasha wahala ba...
Hararan wasa
Rahama tabita da shi kinga ba dakin mu daya ba nidashi ba.
Yana tashi ina
tawa.
Kidaina mun
mugun baki banaso.
Kafa roban
Zuman ta yi a bakin ta saida ta shanye shi tass ajiye roban.
Asiya rike da
baki ta ce wlh zaki gane bakida wayau au wannan ba simple din Zuma ba ce kema
kin sani Ko amma Saboda tsabar kwadayi kin shanye jiki magayi ina ruwana..
Rahama cikin
turo baki ta ce nafa gayamiki ba dakin mu daya ba.
Kuma ba zaimun
komai ba banson kina mun mugun baki fa..
Asiya ta ce
Tom nayi shiru yanzu dai kinga sauran kayan harda su gumba garurruka duk yanda
zaki sha su ga sunan anty ta rubuta a papper.
Rahama ta ce
uhmm nifa duk ba zan sha ba Zuman ce kadai ta mun dadi.
Asiya ta ce
wlh inbaki sha ba a gabana ba saina gayawa Anty wlh...
Asiya da kanta
tadauko madarar peak a frij din kitchen tazo ta hada mata magunguna tabata ta
shanye.
Sai yamutsa
fuska take kamar za ta yi Amai.
Asiya ta ce
kardai ki kuskura kiyi Amai kamar yanda kikai kafun bikin ki dan anbaki magani
saiki amayo
Rahama ta ce ni dai wlh magungunan nan sun
cika min cikina haka zan kwanta banci komai ba..
Nan da suka je
kitchen tare da da taimakon Asiya ta yi girki.
Tuwon semovita
da miyan ganye wai wannan girkin ba ƙaramin daukan ido yake ba abaki ma ba a cewa
komai.
Asiya ce ta
bude miyan dayaji kifi manya manya ta ce uhmm Rahama ni dai girki zaki koyamin
dan anan wajen ban kamo kafar ki ba.
Dibar miyan ta
yi takai bakin ta tare da lumshe Idanun ta wani dadi ne ya ratsata sossai.
Asiya ta ce
Rahama in babu damuwa ki koyawa fans din KYAUTA Daga Allah yanda kika hada
miyar nan dan wlh tahadu iya haduwa sai ma Yarima yaci ze baki note..
Rahama ta yi Murmushi
ta ce wai fans din KYAUTA Daga Allah insunce suna so zan fada musu meye aciki
ai karuwa ce..
Kusan a tare
suka fito da manyan Wamer flask cike da abinci suka jera komai a dîner table.
Faruk Da Aminu
cikin sauri suke saukowa Daga kan matakalan step din.
Aminu ya ce Ah
ashe manyan baki gare mu.
Asiya ta
murmusa tana kallon su cike da ladabi ta gaishe su.
Suka Amsa
cikin sakin fuska.
Faruk ya ce
Madam Samad wai ina Yarima yake ne ?
Rahama ta ce
uhmm yadai fita amma ban san inda ya yi ba...
Takun shigowar
sa ya sa ta yin shiru karasowa falon ya yi ya ce daman ina zaki San inda naje
yana kallon ta kauda kansa ya yi Daga kallon ta yadawo kallon Aminu da Faruk ya
ce sai yanzu kuka fito nasan yanzu ma yunwa ce ta sauko daku.
Faruk ya ce
wlh kuwa kamar ka sani amma naga ga abinci nan madam ta girka mana..
Dîner table
suka nufa Faruk da Aminu.
Shiko Samad
kallon su yake ganin Rahama da Asiya awajen ya kasa motsawa Daga inda yake..
Asiya daukar
abincin nasu suka yi suka yi dakin Rahama dan su basu waje.
Suna barin
wajen Samad ya isa kusa da su Faruk ya ce yan iska kawai waya hanaku ku yi
aure..
Faruk dayanzu
yakai loma daya a bakin sa ya ce wai wai kaji wani gardi da dadin abinci nan
kuwa.
Aminu ya ce tun
da nake ban taɓa cin
abinci me dadin wannan ba.
Samad dake
kallon su ya ce uhmm ku yi aure mana gwaurayen banza kawai.
Faruk ya ce ai
banbancin mu da kai daya ne.
Samad ya ce
bangane banbancin mu daya bane meye nufin ka.
Zama ya yi kan
kujerar yana kokarin zuba abincin a plate..
Faruk ya ce eh
mana Saboda kai da sunan kanada aure ne amma ba ka san Dadin auren ba..
Aminu ya ce
tabe tabe.
Faruk ya yi Murmushi
shima ya ce tabe tabe mana na gasken ma..
.
Samad ya ce ai
duk wani dan iska acikin ku kar nake kallon sa.
Nasan dani
kuke tabe tabe meye ma'anar haka ?
Aminu ya ce
zato zunubi ne koda ya ka sance gaskiya ne.
Kawai dai ka
tsargu ne tokai kana tabe taben ne.
Mun ce maka
film ne muka kalla kaki yarda Ko in kunna maka ne..
Samad ya ce
dan iska kunna mana mugani.
Murmushi Aminu
ya yi ya ce to bara ingama cin Abincin kar ka bari na kware.
Sossai suka ci
Abinci yayinda Samad yanaci yana lumshe idanu ji ya yi kamar taita girka masa
irin wannan abincin yanacin sa dan yanason irin abinci haka..
Kusan Magrib
Asiya tasauko da niyar tafiya gida.
Sossai Rahama
tashiga damuwa a kan tafiyar ta dan wunin da suka yi ji ta yi kamar su dawwama
tare.
Aminu da Faruk
zaune suna kallon Ball.
Asiya ta ce to
ni zan tafi ina angon Rahma yake ne ?
Daga can
zaunen kan dîner table yana chat yadago kai yana kallon ta.
Ya ce kice ina
Abdul Samad yake aini bankai matsayin ango ba..
Daga Asiya har
su Faruk darawa suka yi.
Ajiye wayar ya
yi ya iso wajen Asiya ya ce ki bari Farruk yakaiki har gida..
Aminu ya ce
kwarai kuwa bari mukai ki kinga mun samu mu nuna miki wani abu da muke nema a
unguwar ku.
Asiya ta ce
babu matsala Muje.
Gaba suka yi
ita da Rahama.
Samad ganin
Rahama na kokarin fita Daga Falon ya yi saurin fadin.
Ashe banhanaki
wuce iyakar falon nan ba inkikai baki ba indai ba ni ne nace ba
Cak ta tsaya cikin
Jin zafin haka tarasa dalilin sa.
Asiya ta juyo
tana kallon Rahama ta ce ki koma ai yana da gaskiya babu hijab zaki fito
haraban gidan..
Murmushi Samad
ya yi dan ya lura Asiya akwai ganuwa a fili ya ce.
Asiya kiyi
hakuri fa karki ga laifina..
Asiya ta ce ba
komai InshAllah zakaji amsa ta wajen Rahama..
Daga haka
tasakai tafita '' Faruk da Aminu suka bi bayan ta dan kaita gidan su..
Rahama dawowa
falon tayi.
Jin yanayin ta
yasoma canzawa saman kujera ta zauna 3str idanunta a lumshe wani bakon yanayine
yake ziyartan ta.
Mutsu Mutsu
tasoma Daga kwance wanda yajawo hankalin Samad dake kokarin hawa kan matakalan
step din..
Dawowa ya yi a
falon yana tsaye a kan ta kallon ta yake yanda Idanun ta arufe suke amma sai
nishi take fitarwa mai fidda sauti.
Hannu ya sa ya
taba jikin ta yaji jikin nata harya ɗau
zafi sossai.
Subuhannalah
ya furta yana kokarin.......
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.