Ticker

6/recent/ticker-posts

Tasirin Addinin Musulunci A Kan Sunayen Hausawa Na Gargajiya

Takarda da aka gabatar a taron ƙara wa juna ilimi na ɗalibai masu karatun Digiri na Uku (PhD) a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato, Satumba, 04-09, 2023.

UMAR MUHAMMAD

+234 806 057 0930

Tsakure

Maƙasudin rubuta wannan takarda shi ne gano irin wainar da ake toyawa a kan tasirin addinin Musulunci kan sunayen Hausawa na gargajiya, kasancewar addinin Musulunci ya ratsa dukkanin ɗangarorin rayuwar ɗan Adam baki ɗaya. Domin cimma nasarar wannan takarda, bayan gabatarwa an yi ƙoƙarin gano su wane ne Hausawa? Kuma a ina suka fito? Sai kuma mu ɗan yi ratse game da ma’anar addini da sunayen Hausawa na gargajiya na Bahaushe da kuma bayani kan addinin Musulunci, uwa-uba sai bakandamiyar aiki da ke nuna tasirin addinin Musulunci ga sunayen Hausawa na gargajiya kuma da ita ce aka naɗe wannan aikin.

1.0 Gabatarwa

Kasancewar addinin Musulunci shi ne addini na Allah Maɗaukakin Sarki mai kowa da komai da ya aiko Annabin rahama. Annabi Muhammad (S.A.W.) da shi ga dukkanin al’ummun duniya baki ɗaya domin ya zama shiryarwa ga mutane bisa ga kyakkyawar hanyar bauta masa da gaskiya.

Bisa ga wannan haƙƙin ne al’ummar Hausawa suka rungumi kiran nasa sau da ƙafa har ya yi tasiri ta kowace irin rayuwa ta Bahaushe, kamar yadda ya yi tasiri ga sauran al’umma baki ɗaya.

Bisa wannan dalilin ne wannan bincike zai mai da hankali kan tasirin addinin Musulunci a kan sunayen Hausawa na gargajiya ta yadda wannan tasirin na addinin Musulunci ya fitowa Bahaushe da sunaye kyawawa nagartattu da suka ƙara fitowa da ƙima da darajar Bahaushe a matsayin mai addinin da Allah ya aiko Manzonsa Annabi Muhammad (S.A.W.) don musanya Bahaushe da sunansa na ƙwarai “Bahaushe” ba “Bamaguje” ba.

2.0 Ƙasar Hausa Cikin Tarihi A Taƙaice

Masana da manazarta sun tofa albarkacin bakinsu dangane da muhallin da ake kira ƙasar Hausa, amma zan taƙaita kan wasu daga cikinsu.

Habib da wasu (1980:iv) sun ruwaito Adamu ya ce, ƙasar Hausa ta asali ta faro ne daga Lalle Asadu can Arewa-maso-Gabas da Agadas daga nan ne Gobirawa suka taso da kaɗan-kaɗan har suka iso inda suke a yau Nijeriya, a yanzu kuma Hausa tana yaɗuwa ne tana ƙoƙarin komawa har zuwa gidanta na jiya. Ƙarshen iyakar ƙasar Hausa a Kudu shi ne Yauri da Zaria da inda Bauchi ta yi iyaka da Kano.

Garun Gabas (wato Birom) ita ce iyakar ƙasar Hausa daga Gabas. A Yamma kuma Filinge, ya kuma ƙara da cewa, ƙasar Hausa ita ce inda ba a buƙatar naɗa Sarkin Hausawa. Wato, wannan bayani ya ware duk wasu zango-zango inda ake Magana da Hausa. Dangane da yanayin ƙasar Hausa kuwa, galibinta shimfiɗaɗɗiya ce, mai yawan sarari, akwai ta da tsaunuka da tuddai jifa-jifa kuma duk yawan wannan ƙasa manyan koguna biyu suka ratsa a cikinta da Kogin Rima da Kogin Haɗeja, Kogin Kwara ya zama kamar iyaka daga Yammacin ƙasa, Kogin Rima shi ne ya ratso daga ƙasar Zamfara ya gangara ya yi Arewa zuwa Nijar sannan ya karkata Kudu ya bi ta Yamma da Sakkwato ya je ya faɗa cikin Kogin Kwara. Shi ma Kogin Haɗeja ya fara ne a ƙasar kano daga nan ya gangara Gabas ya bi ta  Gashuwa da Gaidam ya je ya haɗe a Tafkin Chadi. Ƙasar Hausa tana da dazuzzuka iri biyu Sahel daga ɗangaren Arewa, sai kuma Kudu akwai dajin Sabana. Haka kuma, yanayin shekara a ƙasar iri biyu ne lokacin damina da rani, wato hunturu da zafi.

2.1  Su Wane Ne Hausawa?

Masana ilimin kimiyyar harshe da tarihi da adabi da al’ada sun tofa albarkacin bakinsu kan asalin su wane ne Hausawa?

A ra’ayin wani masani, ya bayyana cewa Hausawa su ne waɗanda suke zaune a ƙasar Hausa tuntuni, kuma suna magana da harshen Hausa a matsayin harshen uwa (Ibrahim, 1992:2). Wani masani kuma yana ganin Hausawa sun haɗa da mutanen nan waɗanda saboda ƙaura da magabatansu suka yi daga ƙasar Hausa zuwa wasu sassa da ke maƙwabtaka ta kusa ko ta nesa da ƙasar Hausa, ko da kuwa ba sa magana da harshen Hausa ko yin al’adu ko abubuwan Hausawa, sun ɗauke su Hausawa ne. Misali: Abakwariga da kuma wasu waɗanda suke iƙirarin su Hausawa ne da suke zaune shekaru da daɗewa da suka gabata a ƙasashen Cote de Voire da Burkina Fasa da Mali (Adamu, 1978:3).

Akwai kuma waɗanda saboda zama cikin ƙasar Hausa sun manta da harshensu da al’adunsu na asali, sun ɗauki na Hausa a taƙaice. Sun koma Hausawa a harshe da al’ada da adabi. Misali: Kambarin Barebari da Barebarin Katsina da Buzaye (Sallau, 2007:71).

Magaji (1986:33) ya bayyana Hausawa don su ne mutane waɗanda harshensu shi ne Hausa, sannan dukkan al’adunsu da tadodinsu na Hausawa ne. haka kuma, addinin Musulunci ya yi cikakken tasiri a kansu. Hausawa dai su ne mazauna ƙasar Hausa tun asali, masu Magana da harshen Hausa, kuma ba su da wani harshe in ba Hausa ba. Idan suka saɗa haka, to barbarar yanyawa ne. (Bunza, 1990:12).

A nawa ra’ayi, Hausawa su ne waɗanda Hausa ita ce harshensu na asali, ba su da wata ƙasa in ba ƙasar Hausa ba.

3.0 Ma’anar Addini

Safana (2010) ya fassara addini da cewa hanyar bautawa wani abu wanda mutum yake tsammani shi ne zai biya masa buƙatun rayuwar yau da kullum. Addinin farko da mutanen ƙasar Hausa shi ne addinin gargajiya, wato tsafi, ta hanyar bautar Iskoki ko mutanen ɗoye sai kuma takwarorinsa Bori da camfi. Irin wannan addini ya faru ne ta bin wasu hanyoyi da mutane suka ƙago wa kansu na bautar waɗansu abubuwa don cimma biyan buƙatunsu na rayuwa. Wannan hanyar bauta, ta daɗe ƙwarai da gaske a duk sassan duniya ba ƙasar Hausa kawai ba, har ma da sauran ƙasashen duniya baki ɗaya. (Safana, 2010).

3.1  Addinin Hausawa Na Gargajiya Kafin Zuwan Musulunci Ƙasar Hausa

Mafarin addinin gargajiya shi ne bautar gumaka, wato addinin gargajiya ya wanzu ne ta bin wasu hanyoyi da mutane suka ƙago wa kansu ta bautar waɗansu abubuwa don cimma biyan buƙatunsu. Irin wannan hanyar bauta ta daɗe ƙwarai a duniya. Mutane da suka fara zama a duniya su suka ƙago ta, daga nan kuma abin ya zama al’ada ga sauran ƙabilun da suka biyo bayansu. Da haka abin yana tafiya har ya zo kan Hausawa. Sai dai irin wannan addinin yawanci idan Allah Maɗaukakin Sarki ya aiko wani Annabinsa zuwa ga ƙabilar da aka aiko shi, bayan an sha gwagwarmaya, sai ka ga ya yi sauƙi, amma da wuya a bar shi gaba ɗaya ba tare da tasirinsa ya dinga bin wannan ƙabilar ba (Muhammad, 1982).

Al’ummar Hausawa na addininsu na gargajiya ne ta hanyoyi guda uku, tsafi, bori, camfi. Amma tsafi shi ne babban jigo kuma yana cikin hanyoyin bauta a cikin addinin gargajiya na Hausawa. Sai dai irin wannan bauta ba wani gunki ake sassaƙawa ana bauta masa ba. Amma da yake yanzu yawancin Hausawa duk sun shiga cikin addinin Musulunci, rayuwar waɗanda ba su shiga ba su ake kira Maguzawa, kuma su ne har yanzu suke bin wannan addini. Ta hanyar tsafi Maguzawa sukan bauta wa wani aljani, wanda yawanci sukan ce yana zaune a kan wani dutse ko a kogon wata bishiya, tsamiya ko kuka. Haka kuma, kowane tsafi a kan sami wani mutum wanda yakan zama mai kula da shi. A taƙaice dai, addinin gargajiya kafin shigowar Musulunci shi ne ya shafi tsafi, bori da kuma camfi (Muhammad, 1982).

3.2 Sunayen Hausawa Na Gargajiya Kafin Zuwan Musulunci

Wannan ɗangaren zan ɗan waiga baya ne kawai mu ga sunayen Hausawa na gargajiya a al’adar Bahaushe kafin zuwan Musulunci. Hausawa a gargajiyance, yawanci sukan dubi lokacin da aka yi haihuwa ko halin da aka yi haihuwa ko yanayi su samo sunan, daga nan su sanya wa abin haihuwa.

Haka kuma, yawancin Hausawa sukan sami sunaye iri biyu: sunan yanka da na kakanni, amma kusan dukkaninsu iri ɗaya ne kuma ta hanya ɗaya ake samunsu. Ga kaɗan daga cikin sunayen Hausawa (Maguzawa) kamar haka:

1.      Sammako – yaron da aka haifa da sassafe

2.      Ranau – yaron da aka haifa da rana idan mace ce ta-rana

3.      Na-hantsi – yaron da aka haifa da hantsi

4.      Dare ko Ɗandare – yaron da aka haifa da dare

5.      Shuka/Shukkau – yaron da aka haifa lokacin shuka

6.      Nomau – yaron da aka haifa ana noma

7.      Damina/Damana – yaron da aka haifa da damina

8.      Malka – yaron da aka haifa lokacin tsululin ruwa

9.      Anaruwa – yaron da aka haifa lokacin tsululin ruwa

10.   Ci-gero/Maigero – yaron da aka haifa lokacin cin sabon gero

11.   Ci-wake/Roro – yaron da aka haifa lokacin cin wake

12.   Ƙosau – yaron da aka haifa lokacin ƙoshi

13.   Wadata – yaron da aka haifa lokacin wadata

14.   Ɗari/Taɗari – yaro ko yarinyar da aka haifa lokacin ɗari

15.   Kaka/Ɗankaka – yaron da aka haifa lokacin kaka

16.   Maidamma – yaron da aka haifa ana ɗaura damman hatsi

17.   Ajuji/Ayas/Ayashe – yaro ko yarinyar da aka haifa bayan an yi ta haihuwa suna mutuwa (ana wabi).

18.   Mairiga – yarinyar da aka haifa da rigar haihuwa (ta fito cikin yanar rigar haihuwa).

19.   Shekarau – yaron da ya shekara a cikin ciki

20.   Tanko/Namata/Mati – yaron da aka haifa bayan haihuwar mata

21.   Magawata – yaron da aka haifa bayan wata ya tsaya

22.   Gagarau – yaron da aka haifa bayan an yi ƙoƙarin zubar da cikinsa abu ya gagara.

23.   Mantau – yaron da ya daɗe a ciki kafin a haife shi

24.   Cindo//Mai Cindo – yaron da aka haifa da yatsu shida

25.   Cibi/Maicibi – yaron da aka haifa da cibi

26.   Kanta – yaron da aka haifa tare da mace

27.   Auta – yaro ko yarinyar da aka haifa a ƙarshen haihuwa

28.   Maigiya – yaro ko yarinyar da aka haifa ana dafa giya

29.  Malka – yarinyar da aka ana tsuga ruwa

30.   Kande/Dela/Deluwa/Barauki/Ige – yarinyar da aka haifa bayan an haifi maza da yawa.

31.   Kumatu – yarinyar da aka haifa da kaurin kumatu

Kaɗan ke nan daga cikin sunayen Hausawa na gargajiya da suke ambaton ‘ya’yansu kafin Musulunci. Hausawa sun ci gaba da amfani da waɗannan sunaye ko bayan shigowar Musulunci domin kuwa kusan dukkanin sunayen ba su da wata alaƙa da Musulunci.

4.0 Addinin Musulunci

A wannan gaɗa, ya kamata a yi ɗan bayani a taƙaice dangane da ma’anar Musulunci.

Gusau (1999: 1) ya ce, “Addinin Musulunci shi ne addinin da Allah mai girma da ɗaukaka ya aiko Annabi Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da shi domin ya shiryar da mutane zuwa ga kyakkyawanr hanyar bauta Masa. Da wannan, mun tabbatar cewa shi Musulunci addini ne da ya zo daga Allah kuma ya wanzu ta hanyar Annabi Muhammad (S.A.W.). Haka kuma, shi addini bai nuna wata wariya a cikin al’umma ba, wai ko don kana shugaba, amma ya yi tanadi a yi wa shugaba ɗa’a gwargwadon hali, in dai bai kauce wa shari’ar  Musulunci ba.

Gusau (1991:2) ya ƙara da cewa Musulunci shi ne gaskatawa da miƙa wuya zuwa ga abin da Manzon Allah (S.A.W.) ya zo da shi daga wurin Allah Subhanahu wata ala, sannan da aiki da shi.

4.1  Tasirin Addinin Musulunci Ga Sunayen Hausawa Na Gargajiya

Kafin mu tsunduma ga wannan bakandamiyar aiki wato tasirin addinin Musulunci ga sunayen Hausawa na gargajiya, kamata ya yi mu san kalmar ‘tasiri’ ita kanta.

Tahar (1990) ya bayyana tasiri da cewa karɗuwa da amincewa kuma da mamaye kowace irin harka da ta shafi rayuwar wasu jama’a, Wasagu (2002) ya fassara kalmar tasiri da nufin sauyin da ake samu a cikin wani abu dalilin wani abu.

Bayan addinin Musulunci ya shigo ƙasar Hausa ya yi ƙarfi da tasiri ga kowane ɗangaren rayuwar Bahaushe, sai ya zama sunayen da Bahaushe yake amfani da su a gargajiyance idan an yi masa haihuwa suka ƙara yawa, har suka sauya zuwa ga sunayen Musulunci.

Ga dai sunayen manyan bayin Allah kamar Annabawa da Sahabbai da mutanen kirki (waliyyai) da ma matansu da na ‘ya’yansu. Ga kuma sunayen Mala’iku da suke sa wa yaransu. Duk waɗannan sunayen suna sa musu ne don neman albarka. Ban da waɗannan kuma, Hausawa sun ci gaba da amfani da sunayen gargajiya irin na asali don yi wa yaro laƙabi. Wato, a taƙaice dai, idan an haifi yaro a ranar suna za a sa masa suna wanda zai zama ko sunan Annabi ko na Sahabi ko na mutanen kirki (waliyyai) ko na Mala’iku ko kuma in  mace ce, a sanya mata sunan matar wani Annabi ko ‘yarsa ko matar Sahabi ko ‘yarsa, to bayan wannan suna kuma, sai a sami sunan gargajiya wanda yawanci kakanni ko waɗanda ba za  su faɗi  sunan ba, saboda kunya irin ta al’adar Hausawa za su sa wa yaro ko yarinya shi. Ga misalan sunayen yanka na Hausawa kamar haka:

Muhammadu, amma saboda suna son sunansa da yawa, mutum ɗaya yakan iya sa wa ‘ya’yansa maza goma (10) duk sunan “Muhammadu” sai dai zai bambanta a cikin Larabci ya ce Muhammadu na ɗaya ko na biyu ko na uku har zuwa na goma (10). Misali:

1.      Muhammadu Auwalu

2.      Muhammadu Sani

3.      Muhammadu Salisu

4.      Muhammadu Rabi’u

5.      Muhammadu Hamisu

6.      Muhammadu Sadisu

7.      Muhammadu Sabi’u

8.      Muhammadu Saminu

9.      Muhammadu Tasi’u

10.  Muhammadu Ashiru

Sauran sunayen Annabawa da Hausawa kan sa wa ‘ya’yansu su ne:

1.      Adamu

2.      Nuhu

3.      Idrisu

4.      Salihu

5.      Hudu

6.      Ibrahim

7.      Yakubu

8.      Isma’ila

9.      Yusuf

10.   Yusha’u

11.   Iliyasu

12.   Yahaya

13.   Zakariya’u

14.   Dawuda

15.   Suleiman

16.   Musa

17.   Isa da sauransu.

Sannan sukan sanya sunayen Sahabbai kamar:

1.      Abubakar

2.      Umaru

3.      Usmanu

4.      Aliyu

5.      Abbas

6.      Zubairu

7.      Sa’adu

8.      Abdullahi

9.      Abdurarrahman da sauransu.

A cikin sunayen Waliyyai kuma, sun fi sa sunayen:

1.      Abdulƙadir

2.      Ahmadu Tijjani (ruwayar ‘yan ɗariƙa ce)

3.      Ahmadu Rufa’i

4.      Usmanu da sauransu.

A cikin mata kuma, sukan sa:

1.      Aminatu

2.      Faɗimatu

3.      Maryamu

4.      Ummul Kulsumi

5.      Zainabu

6.      Ruƙayyatu

7.      Hindu

8.      Hindatu

9.      Habibatu

10.   Maimunatu

11.   Halimatu da sauransu.

A cikin Mala’iku kuma sukan sa:

1.      Jibrilu

2.      Mika’ilu

3.      Ridwanu

4.      Maliki

Daga cikin waɗannan sunaye akwai waɗanda Hausawa suke faɗarsu daidai, kamar yadda suke a cikin littafi, akwai kuma waɗanda suke jirkitawa. Misalin waɗanda suke faɗa daidai su ne:

1.      Hudu

2.      Nuhu

3.      Musa

4.      Isah

5.      Hindu

6.      Asama’u

Misalin sunayen da suke jirkitawa su ne:

1.      Adamu – Ado

2.      Idrisu – idi

3.      Salihu – Sale

4.      Ibrahim – Iro, Ibran, Buraima, Ibro, Ibra

5.      Zakariya’u – Zakari, Ya’u

6.      Abubakar – Abu, Habu

7.      Abdullahi – Audu, Abdu

Abdurrahman da sauransu

8.      Zainabu – Abu

9.      Hadijatu – Dije, Dija, Dijama

10.   Maimunatu –  Maimuna, Munari, Muna

11.   Rukayya – Rakiya, Ruke

Haka kuma har wa yau, bayan zuwan Musulnci, an sami sunayen da ake sa wa ‘yan tagwaye (’yan biyu) kamar haka:

Al-Hassan – Na littafi

Alasan  – sunan ɗan tagwayen da aka fara haihuwa namiji

Hassan – yadda Hausawa kan faɗa

Al-Hussaini – na littafi

Usaifi – na Hausa

Alhassanatu – na littafi

Hasana – na Hausa

Alhasanatu  – na littafi

Usaina – ‘yar tagwayen da aka haifa daga ɗangaren mace.

Dangane da sunayen gargajiya kuma Hausawa sun ci gaba da amfani da sunaye na da, amma ban da irinsu Maigiya da Shagiya da Ramau da Taroro, waɗannan sai Maguzawa kawai suke amfani da su. Haka kuma, Musulunci ya sa Hausawa sun ƙara ƙago waɗansu sababbin sunaye irin na gargajiya. Ga misalin irin sunayen da Hausawa suke amfani da su bayan Musulunci a matsayin sunayen kakanni, ko sunayen rana kamar haka:

1.      Dogara (Na dogara ga Allah)

2.      Alabura (Allah ya bari)

3.      Nabara (Na bar wa Allah)

4.      Dangana (Na dangana ga Allah)

5.      Bawa (Bawan Allah)

6.      Barmini (Allah ya bar mini)

Sunayen yara maza da aka haifa bayan an yi ta haihuwa suna mutuwa (‘yan wabi).

1.      Sadau     – yaron ko yarinya da aka haifa bayan mace ta koma ɗakin mijinta.

2.      Sodangi – Yaro ko yarinyar da aka haifa bayan iyayensa sun dawo cikin dangi, ko a lokacin da dangi suka taru don yin wani sha’ani.

3.      Korau   – yaron da aka sa wa sunan wani mutum, amma ba a daɗe ba sai mutumin ya mutu.

4.      Wada/Dawada/Maiwada/Ɗanyalwa – yaron da aka haife shi lokacin wadata ko kuma wanda iyayensa suka sami wadata bayan haihuwarsa.

5.      Tawada/Yalwa/goshi – yarinyar da aka haifa lokacin wadata ko kuma aka sami wadata bayan haihuwarta.

6.      Maikuɗi – yaro ko yarinyar da iyaye suka sami kuɗi ranar haihuwarta, ko kuma waɗanda aka haifa ranar Talata.

7.      Sallau/Nasalla/Maisalla/Tasalla/Tasalluwa – yarinya ko yaron da aka haifa lokacin salla.

8.      Labaran/Ɗanazumi/Azumi – yarinyar da aka haifa a watan azumin watan Ramalana.

9.      Ladan/Maisalla/Mai salati – yaron da aka haifa lokacin da ladan yake kiran salla.

10.   Gambo – yaro ko yarinyar da aka haifa bayan haihuwar ‘yan tagwaye.

11.   Kadarko – yaro ko yarinyar da aka haifa a tsakanin haihuwar ‘yan tagwaye.

12.   Gwamma (Gwamma ita da babu) Hakama (Haka ma ina so) – yarinyar da aka haifa bayan an sa ran haihuwar namiji.

13.   Bakuso –  yaro ko yarinyar da aka haifa bayan an saki uwarsa ko uwarta.

14.  Yawale – yaron da aka haifa a hanyar zuwa Makka.

15.   Yabi – yarinyar da aka haifa a hanyar zuwa Makka.

16.   Talle – (Tallafin marayun Allah) – yaro ko yarinyar da uwarsa ta mutu a wurin haihuwarsa ko bayan haihuwarsa kaɗan.

17.   Alhaji/Baita – yaron da aka haife shi a lokacin shagalin salla babba.

18.   Hajiya/Kyauta (kyautar Allah) – yaro ko yarinyar da aka haifa bayan uwarsa ko ubansa sun fitar da rai da samun haihuwa.

19.   Tunau/Ɗantune – yaron da aka haifa bayan uwarsa ko ubansa sun fitar da rai za su kuma samu haihuwa.

20.   Tune – yarinyar da aka haifa bayan uwarsa ko ubanta sun fitar da rai za su kuma samun haihuwa.

21.   Makwashi – yaron da bora ta haifa.

22.   Kilishi – yaro ko yarinyar da aka haifa bayan an ci sarauta.

23.   Dawai – yaron da aka haifa bayan kome (mace ta dawo ɗakin mijinta).

24.   Dawo – yarinyar da aka haifa bayan kome.

25.   Sharubutu – yaro ko yarinyar da uwarsa ta sha rubutu da yawa kafin ta haife shi.

26.   Sutura/Mairiga – yarinyar da aka haifa da rigar haihuwa.

Sunayen Ranakun Mako

Kafin zuwan Musulunci kusan in ban da su “yau, gobe, jibi, citta, jiya da shekaranjiya Hausawa basu da sunayen ranaku, sai dai su kira kowace rana da sunan garin da kasuwarsa take ci a wannan rana. Misali, ranar Ɗanbatta, ranar Ma’aduwa, ranar Bakori, ranar Maƙarfi da sauransu. Da Musulunci ya zo, sai ya kawo musu sunayen ranakun mako kamar:

1.      Assibit  – Asabar

2.      Al-Ahd  – Lahadi

3.      Al-thnain  – Litinin

4.      Al-thulatha’a – Talata

5.      Al-Arba’a   – Laraba

6.      Al-Khamis   – Alhamis

7.      Al-juma’at – Juma’a

Daga waɗannan sunaye ne Hausawa suka ƙago sunayen da za su sa wa yaron da aka haifa a waɗannan ranaku kamar haka:

1.      Ɗanasabe/Ɗan’asibi – yaron da aka haifa ranar Asabar.

2.      Ɗanladi/Lado/Nalado – sunayen yara maza da aka haifa ranar Lahadi.

3.      Ladi/Ladidi/Ladingo/Ladigo – sunayen yara mata da aka haifa ranar Lahadi.

4.      Ɗanliti/Ɗantani/Liti – sunayen yara maza da aka haifa ranar Linitin.

5.      Tanin/Liti – sunayen yara mata da aka haifa ranar Linitin.

6.       Ɗantala/Ɗantata/tatu/Maitala/Maitalata – sunayen yara maza da aka haifa ranar Talata.

7.      Talatuwa/Talatu/Tatu/Lantu – sunayen yara mata da aka haifa ranar Talata.

8.      Bala/Balarabe/Ɗanbala/Ɗanlarai – sunayen yara maza da aka haifa ranar Laraba.

9.      Larai/Balaraba/Laraba/Balarabiya/Tabawa – sunayen yara mata da aka haifa ranar Laraba.

10.   Ɗanlami/Na Lami – sunayen yara maza da aka haifa ranar Alhamis.

11.  Lami/Laminde/Lamisuwa – sunayen yara mata da aka haifa ranar Alhamis.

12.   Jume/Jumare/Wajume/Ɗanjuma/Ɗanjimmai/Na-Jimmai – sunayen yara maza da aka haifa ranar Jumu’a.

13.   Juma/Jummai/Aljumma – sunayen yara mata da aka haifa ranar Jumu’a.

Gwargwadon hali, waɗannan su ne misalan sunayen da ake kiran Hausawa da su bayan shigowar addinin Musulunci ƙasar Hausa da suka danganci ranakun mako.

5.0 Naɗewa

Tun kafin bayyanar addinin Musulunci a ƙasar Hausa. Al’ummar Hausawa suna da sunayen da suke sanyawa ‘ya’yansu ta hanyar dubin lokaci da yanayi ko halin da aka yi haihuwar ko dai wani dalili na daban, su sanya wa abin haihuwar suna. Da addinin Musulunci ya shigo ƙasar Hausa, sai ya sauya waɗannan sunayen na Maguzanci zuwa na Musulunci ta hanyar inganta su da ƙara masu yawa kan tsarin koyarwarsa. Kan haka, wannan bincike mai taken “Tasirin Addinin Musulunci Kan Sunayen Hausawa na Gargajiya” ya cimma burinsa gwargwado, ya yi ƙoƙarin sanin al’ummar Hausawa da ƙasarsu, sai kuma taƙaita bayani kan addinin Hausawa na gargajiya, da na Musulunci da kuma kawo sunayen Hausawa na gargajiya gwargwadon hali. Sai kuma uwa-uba hasashen aikin da ya shafi tasirin addinin Musulunci kan sunayen Hausawa na gargajiya inda binciken ya zayyana su dalla-dalla tare da misalai ingantattu.

Sakamakon Bincike

Bayan gabatar da ƙumshiyar wannan bincike a taƙaice, ba zan naɗe wannan ‘yar takarda ba, sai na ɗan yi tsokaci kan wasu abubuwa da wannan binciken ya gano kamar haka:

1.      Binciken ya yi ƙoƙarin gano tasirin addinin Musulunci kan sunayen Hausawa na gargajiya ta fuskoki da dama.

2.      Binciken ya kuma yi ƙoƙarin gano dangantakar al’ummar Hausawa da Larabawa da ma sauran maƙwabta malamai wanda dalilin su ne Bahaushe ya karɗi Musulunci har ya sauya suna daga “Bamaguje” zuwa “Bahaushe”.

3.      Haka kuma, dalilin addinin Musulunci ya sauya sunayen Bahaushe na haihuwa ta la’akari da lokaci da yanayi da rana, ya ba shi sunayen Musulunci ta ɗangarori daban-daban.

4.      Binciken ya waiwayi sunayen Bahaushe na gargajiya ya kwatanta su da na shi, ya ɗebe tsaki da tsakuwa ya fitar da gari don ya gyara wasu sunaye ya daidaita su da na shi, ya zubar da na zubar wa irin sunan “Shagiya” da “Kumatu” da sauransu.

Manazarta

Alti, K.M. (2012). “Wasu Dabarun Gargajiya na Kawar da Talauci A Birnin Katsina. Kundin Digiri na Biyu (M.A. Hausa). Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Amfani, A.H. (2011). “Hausa da Hausawa da Kuma Ƙasar Hausa Jiya Da Yau”Takardar Da Aka Gabatar a Taron Ƙara wa Juna Sani, Assembly Hall Ahmadu Bello University, Main Campus Zaria, Kaduna State.

Aliyu, A.Y. (1973). “Asalin Hausa” A Cikin Littafin Makon Hausa. Kano: Jami’ar Bayero.

Augie, A.R. Da Wasu (1991). Nazari a Kan Tarihin Al’ummar Ƙasar Zuru Gabanin Kafa Mulkin Mallaka Na Turawa. Ƙungiyar Raya Ci Gaban Ƙasar Zuru (ZED).

Bunza, A.M. (1990). “Hayaƙi Fidda Na Kogo: Nazarin Siddabaru Da Sihirin Hausawa”. Kundin Digiri na Biyu (M.A. Hausa) Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.

Bunza, A.M. (2008). “Gadon Feɗe Al’ada”. Jerin Littafan Cibiyar Nazarin Al’adun Hausawa, Lagos: Tiwal.

Bunza, A.M. (1995). “Magungunan Hausa a Rubuce: Nazarin Ayyukan Malamin Tsibbu”. Kundin Digiri na Uku (Ph.D Hausa) Juzu’i na Ɗaya. Kano: Jami’ar Bayero.

Gobir, Y.A. (2002). “Iskoki a Idon ‘yan Bori da Masu Ruƙiyya”. Kundin Digiri na Biyu (M.A.Hausa) Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Gobir, Y.A. (2013). Tasirin Iskoki Ga Cutuka da Magungunan Hausawa. Kundin Digiri na Uku (Ph.D Hausa) Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Gobir, Y.A. (2023). Laccar Kwas Hau: 933 Mai Taken. “Hausa Culture and Islam” Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Ibrahim, Y.Y. da Wasu (1986). “Jagoran Nazarin Hausa”. Northern Nigeria Publishin Company Zaria.

Magaji, A. (1989). “Gudummuwa a Kan Ƙoƙarin da Ake Yi Na Samar Da Cikakken Tarihin Hausawa da Harshensu” Maƙala, Kano: Takardar da Aka Gabatar a Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Magaji, A. (2002). “Wasu Al’adun Hausawa da Yanaye-Yanayensu a Ƙasar Hausa”. Kundin Digiri na Uku (Ph.D Hausa) Tsangayar Fasaha da Addinin Musulunci. Kano: Jami’ar Bayero.

Nafisa, M.G. (2014). “Kutsen Baƙin Al’adu Cikin Hidimar Aure a Sakkwato” (M.A. Hausa) Kundin Digri na Biyu. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Sama’ila, A.K. (2019). “Al’adun da Addinin Musulunci ya hana Aikatawa, Kuma Ake yi a Wasu Masarautun Ƙasar Hausa”, Takardar da Aka Gabatar a Taron Ƙara wa Juna Sani, Kwalejin Share Fage da Karatu Mai Zurfi Yelwa-Yauri.

Safana, B.Y. (2001). Maguzawa Lezumawan (Babban kada) Gudummuwar Safana a Jihar Katsina. Kundin Digiri na Farko (B.A. Hausa) Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Sallau, B.A.S. (2009). “Sana’ar Wanzanci da Sauye-Sauyen Zamani Jiya da Yau”. Kundin Digiri na Uku (Ph.D Hausa) Sashen Harsunan Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.

Tahar, M.A. (1990). “Siddabaru a Ƙasar Hausa Yadda Yake da Yadda Ake Yin Sa”. Kundin Digiri na Biyu. (M.A. Hausa). Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.

Tukur, A. (2015). “Sana’ar Saƙa a Ƙasar Hausa”. Kundin Digiri na Farko. Sashen Harsunan Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.

Umar, M. (2015). “Zumuntar Tsafe-Tsafen Hausawa da Dakarkari (M.A. Hausa). Sashen Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Umar, M. (2017). “Tasirin Zuwan Turawa ƙasar Hausa”. Takardar Da Aka Gabatar a Taron Ƙara wa Juna Ilimi. Kwalejin Share Fade Da Ilimi Mai Zurfi Yelwa-Yauri.

Wushishi, B.J. (1998). “Dangantakar Magani Da Wasu Sana’o’in Hausawa Na Gargajiya”. Kundin Digiri na Biyu. Sashen Harsunan Nijeriya, Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Waziri, M. (2013). “Tasirin Sarautun Hausawa a kan Ƙabilar Kare-Kare da Sayawa”. Kundin Digiri na Biyu (M.A. Hausa). Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Zaruma, (1983). A Culture Magazine of Sokoto State.

Post a Comment

0 Comments