𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalaamu Alaikum, Malam,
tambaya ce gare ni: Mutum mai mata biyu, wai me ya halatta a tsakaninsa da
matar da ba a ɗakinta ya ke ba? Za su iya riƙe hannu ko sumbanta ko runguman juna?
SHIN YA HALLATA GA MIJI YA
SHIGA ƊAKIN
MATAR DA BA KWANANTA BA?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa
Rahmatul Laah.
A’ishah Ummul-Mu’mineen (Radiyal
Laahu Anhaa) ta ce:
كَانَ رَسُولُ اللَّهِ - صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ - لاَ يُفَضِّلُ بَعْضَنَا عَلَى بَعْضٍ فِى الْقَسْمِ ، مِنْ مُكْثِهِ عِنْدَنَا ، وَكَانَ قَلَّ يَوْمٌ إِلاَّ وَهُوَ يَطُوفُ عَلَيْنَا جَمِيعًا ، فَيَدْنُو مِنْ كُلِّ امْرَأَةٍ مِنْ غَيْرِ مَسِيسٍ ، حَتَّى يَبْلُغَ إِلَى الَّتِى هُوَ يَوْمُهَا ، فَيَبِيتُ عِنْدَهَا
Manzon Allaah (Sallal Laahu
Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya kasance ba ya fifita sashenmu a kan sashe wajen
rabon-kwana, a iya zamansa a cikinmu; kuma da ƙyar
wani yini guda ke wucewa face kuwa ya kewaya mu gaba-ɗaya,
kuma ya kusanci kowace mace amma ba tare da saduwa ba, har sai ya kai ga mai
girki a ranar, sai ya kwana a wurinta. (Abu-Daawud: 2137 ya riwaito shi).
A cikin riwayar Al-Bukhaariy
(5268) da Muslim (1474) ya ce: Idan ya yi sallar La’asar sai ya kewaya matan
aurensa… Kuma a cikin riwaiyar Ahmad ya ce: Sai ya kusance ta: Ya shafe ta amma
ba tare da saduwa ba.
A ƙarƙashin
wannan hadisin da makamantansa malamai suka gano cewa:
1. Haƙƙin miji ne ya yi adalci a
tsakanin matan aurensa a wurin rabon-kwana da ciyarwa da shayarwa da tufatarwa
da sauran abubuwan da suke a fili, kar ya fifita wata a kan wata.
2. Haƙƙin mata ne ta san cewa, miji
ba zai iya yin adalci a tsakanin matan aurensa ba a cikin abubuwan da suke a ɓoye,
kamar soyayyar zuciya da sha’awar saduwa da sauransu.
3. Haƙƙin miji ne kar ya shiga gida
ko ɗakin
matar da ba kwananta ba da dare, sai in akwai larura mai ƙarfi, kamar rashin lafiyarta da makantan
haka.
4. Haƙƙin miji ne kar ya shiga ya
kwanta, ko kuma ya yi barcin dare sai a ɗakin
matar da ya ke kwananta ne kawai.
5. Haƙƙin miji ne kar ya sadu da
wata daga cikin matansa sai wacce ita ce ke da kwana, ko kuma idan akwai
amincewa da yarda daga wacce ta ke da kwanan.
6. Haƙƙin mata ne kar ta yarda
mijinta ya sadu da ita idan dai ba kwananta ba ne, ko in ba da izinin wadda ta
ke da kwanan ba.
7. Haƙƙin miji ne ya shiga ɗakin
wadda ba kwananta ba da rana, kuma ya kusance ta da dukkan komai, in dai ba
saduwa ba.
8. Haƙƙin mata ne kar ta hana
mijinta yin komai na soyayya tare da ita a lokacin da ba kwananta ba, matuƙar dai hakan ba zai kai ga saduwa ba.
9. Haƙƙin mata ne kar ta goya wa
mijinta baya wurin wuce-iyaka har a kai ga saduwa a lokacin da ta san ba
kwananta ba ne.
10. Haƙƙin mata ne ta yarda idan
miji ya shiga ɗakin wacce ba kwananta ba, ko da kuwa ya
yi wasa da ita, in dai bai kai ga saduwa ba.
(Dubi Ta’leeƙ na
As-Shaikh Sameer Az-Zuhairiy ga Buluugh Al-Maraam, shafi: 324).
WALLAHU A'ALAM
Sheikh Muhammad Abdullaahi
Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.