𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalaamu Alaikum Wa Rahmatul Laah. Surukarsa ce
ta yi mafarkin wai wani abu mummuna zai same shi, don haka maganin hakan shi ne
ta umurce shi da yin yanka da sadaka. Shi ne shi kuma yake tambayar matsayin
hakan a shari’a?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laahi Wa
Barakaatuh.
Hadisi ya tabbata a cikin Sahih Al-Bukhaariy
(7044) da Sahih Muslim (6040) daga Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa
Sallam) cewa shi ya ce:
« الرُّؤْيَا الصَّالِحَةُ مِنَ اللَّهِ فَإِذَا رَأَى أَحَدُكُمْ مَا يُحِبُّ فَلاَ يُحَدِّثُ بِهَا إِلاَّ مَنْ يُحِبُّ وَإِنْ رَأَى مَا يَكْرَهُ فَلْيَتْفِلْ عَنْ يَسَارِهِ ثَلاَثًا وَلْيَتَعَوَّذْ بِاللَّهِ مِنْ شَرِّ الشَّيْطَانِ وَشَرِّهَا وَلاَ يُحَدِّثْ بِهَا أَحَدًا فَإِنَّهَا لَنْ تَضُرَّهُ ».
Kyakkyawan mafarki daga Allaah ne. Don haka idan ɗayanku ya ga wani abin da ya yi masa daɗi kar ya gaya wa kowa sai wanda ya ke so.
Idan kuma ya ga wani abin da bai masa daɗi ba, to ya yi tofi a gefen hagunsa sau uku, kuma
ya nemi Allaah ya tsare shi daga sharrin sheɗan kuma da sharrin abin da ya gani, kuma kar ya bai wa kowa labari.
Idan ya yi hakan ba zai cutar da shi ba.
Haka kuma ya tabbata a cikin Al-Jaami’u (2449) na
Al-Imaam At-Tirmiziy cewa, Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya
ce:
« الرُّؤْيَا ثَلاَثٌ فَرُؤْيَا حَقٌّ وَرُؤْيَا يُحَدِّثُ بِهَا الرَّجُلُ نَفْسَهُ وَرُؤْيَا تَحْزِينٌ مِنَ الشَّيْطَانِ فَمَنْ رَأَى مَا يَكْرَهُ فَلْيَقُمْ فَلْيُصَلِّ ».
Mafarki iri uku ne: Akwai mafarki na gaskiya, kuma
da mafarkin da yake labarin zuciyar mutum ne, sai kuma mafarkin da sheɗan ne yake cusa wa mutum baƙin
ciki da damuwa. To, duk wanda ya ga abin da yake ƙyama sai ya tashi ya yi
sallah.
Daga tattaruwan waɗannan irin riwayoyin ne malamai suka samo
cewa:
Mafarki iri uku ne ta fuskar yadda ya ke a
asalinsa: Mafarki daga Allaah, da labarin zuciyar mutum, da kuma sharri da
makircin sheɗan.
Ta fuskar yadda yake shafar mutum mafarkin iri
biyu ne: Ko dai mai kyau mai daɗi, ko
kuma mummuna mara daɗi.
Ayyuka uku ake nema daga wanda ya yi kyakkyawan
mafarki: Godiya ga Allaah, murna da jin daɗi da hakan, ya sanar da wanda yake ƙauna
kaɗai.
Idan kuma mummunan mafarki ne ya yi, to ayyukan
suna da yawa, kamar haka:
1. Addu’ar neman Allaah ya tsare shi daga sharrin
sheɗan da
sharrin abin da ya gani.
2. Ya yi tofi sau uku ta gefen hagu a lokacin da
ya farka.
3. Kar ya gaya wa kowa labarin mafarkin.
4. Ya juya daga sashen jikin da yake kwance zuwa
wani sashen.
5. Ya tashi ya yi sallar nafila.
Amma game hanyoyin kare kai daga sharrorin sheɗanu da ƙulle-ƙullen
maƙiya da mahassada da sauran masharranta, matakai ne kamar haka:
1. Kyautata imani da tsoron Allaah da biyayya ga
dokokinsa a ɓoye da
bayyane.
2. Nisantar saɓo da dukkan nau’ukan zunubi manya da ƙanana
a ɓoye da fili.
3. Yawaita zikirori da addu’o’in neman tsari da
kariya daga Allaah, kamar na lokacin kwanciyan barci da na farkawa, da na
yammaci da wayewar gari, kamar wannan zikirin
« لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ، وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ، يُحْيِى وَيُمِيتُ، وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَىْءٍ قَدِيرٌ »
Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya
ce: Duk wanda ya maimaita shi sau goma a bayan sallamar sallar Asubah tun kafin
ya warware ƙafafunsa, za a rubuta masa lada goma, a goge masa
zunubai goma, a daga masa darajoji goma, kuma a cikin wannan yinin yana cikin
tsaro daga dukkan wani abin ƙyama, kuma yana cikin samun kariya daga sheɗan, kuma babu wani zunubin da zai iya
riskarsa a wannan yinin sai dai idan tarayya da Allaah ne. Haka ma idan a bayan
Maghriba ce ya karanta. (As-Saheehah: 113-114).
WALLAHU A'ALAM.
Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/J1hm5Tw12uYBqfaiPwf28l
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.