Ticker

6/recent/ticker-posts

Shin Akwai Tambayar Ƙabari Ga Wanda Ya Rasu A Daren Jumma’a ?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Ko akwai tambayar ƙabari ga wanda ya rasu a daren Jummaa amma ba a rufe shi ba sai ranar Lahadi? Tun da an ce babu tambayar ƙabari ga wanda ya rasu a ranar Jummaa?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.

Al-Imaam Ahmad da At-Tirmiziy sun riwaito hadisi daga Abdullaah Bn Amr (Radiyal Laahu Anhumaa) wanda Al-Albaaniy ya ce: Hasan ne ko sahihi lura da tattaruwar hanyoyinsa da wasu shawaaheed da yake da su daga riwayar Anas da Jaabir (Radiyal Laahu Anhumaa) cewa: Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

 « مَا مِنْ مُسْلِمٍ يَمُوتُ يَوْمَ الْجُمُعَةِ أَوْ لَيْلَةَ الْجُمُعَةِ ، إِلاَّ وَقَاهُ اللَّهُ فِتْنَةَ الْقَبْرِ »

 Babu wani musulmi da zai mutu a ranar Jumma’a ko daren Jumma’a face kuwa Allaah ya kare shi daga fitinar ƙabari.

Watau wannan hadisin yana magana ne a kan cewa: Mutuwa a ranar Jumma’a tana kare shi daga Fitinar Ƙabarin ce, amma ba magana yake yi a kan: Tambayar Ƙabari ba.

Sannan kuma samun ni’ima ko azabar ƙabari waɗanda suke biyo bayan tambayar ƙabari ba su da alaƙa da rufewa ko rashin rufewa a cikin ƙabari, kamar yadda malamai suka ce:

 ‘Wanda namun daji suka cinye jikinsa, ko jikinsa ya tarwatse ya lalace, ko wanda aka ƙone gawarsa aka waste tokarsa a cikin iskar tudu da teku, ko wanda aka ajiye shi a cikin macuware na tsawon lokaci, ko wanda aka nutsar da shi a cikin ruwa, ko aka gicciye shi, da dukkan wanda ba a rufe gawarsa a cikin ƙabari ba saboda wani dalili daga cikin dalilai, duk da haka dai Azabar Ƙabari ko Niimarta za ta shafe shi. Kuma zai rayu rayuwa irin ta barzakhu har zuwa Ranar Al-Qiyamah _. (Diraasaatun Aqadiyyah Fil Hayaatil Barzakhiyyah, shafi: 348, kamar yadda As-Sallabiy ya kawo a cikin littafinsa: Al-Imaanu Bil Yaumil Akhiri, shafi: 60-61)._

Allaah ya ƙara mana fahimta a cikin addininmu.

WALLAHU A'ALAM

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments