𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu'alaikum. Malam tambayana anan shine: Nine
nakeda budurwa muna tare har yakai ga mukayi zalunci (ma'ana muka sadu da juna
har ta samu juna biyu daga karshe taje ta cire) gashi ni kuma ban taɓa yin zina ba. Daga nan hankalina ya
tashi! tun daga wannan lokaci nakasa samun kwanciyar hankali sabida muninsa.
Hatta lokacin da abin ya auku nayi nafila da istigfari ina me zubar da hawaye
da nadaman abin da ya faru. Tunda nake ban taɓa yin abin da nayi nadama kamar wannan ba.
Aman malam tun daga nan ban sake ba, na tuba inata neman gafaran ubangiji.
Malam hakan ALLAH ze yafe min duk da abin da ya faru na cire cikin?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Duk da cewa waɗannan laifukan da kuka aikata suna daga
cikin mafiya girman laifukan da Allah ya haramta, Kuma ya gargadi bayinsa
akansu, to amma wannan ba yana nufin cewa Allah ba zai gafarta muku bane.
Mutukar kunyi tuba irin tubar da Allah yake so, to
tabbas Allah zai gafarta muku waɗannan
laifukan. Allah Madaukakin Sarki ya gaya ma Annabinsa (sallal Lahu alaihi wa
aalihi wa sallam) cewa:
قُلْ يَا عِبَادِيَ الَّذِينَ أَسْرَفُوا عَلَىٰ أَنْفُسِهِمْ لَا تَقْنَطُوا مِنْ رَحْمَةِ اللَّهِ ۚ إِنَّ اللَّهَ يَغْفِرُ الذُّنُوبَ جَمِيعًا ۚ إِنَّهُ هُوَ الْغَفُورُ الرَّحِيمُ ٣٥
Ka ce: (Allah Ya ce): "Yã bãyĩNa waɗanda suka yi ɓarna a kan rãyukansu! Kada ku yanke ƙauna
daga rahamar Allah. Lalle Allah na gãfarta zunubai gabã ɗaya. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai gãfara, Mai jin
ƙai." (Suratuz Zumar ayah ta 53).
Imamu Ahmad ya ruwaito wani hadisi acikin Musnadu
nasa (Juzu'i na 4 shafi na 385) daga Sayyiduna Amru bn 'Abisah (rta) ya ce :
"Wani mutum yazo wajen Manzon Allah ﷺ tsoho ne Tukuf, yana dogarawa da sandansa. ya ce
: "Ya Rasulallahi hakika ni ina da wasu Laifukan yaudara da kuma Fajirci
waɗanda na aikata. Shin za
a gafarta min kuwa?".
Sai Manzon Allah ﷺ ya tambayeshi "Shin baka shaida cewa
babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah ba?".
Sai mutumin ya ce "Eh, Kuma na shaida cewa
Kai Manzon Allah ne".
Sai Manzon Allah ﷺ ya ce masa "An riga an gafarta maka
laifukanka na yaudara da kuma fajirci".
Al Imam Ibnu Katheer ya ce duk waɗannan ayoyin da hadisan Manufarsu ita ce a
fahimci cewa Allah yana gafarta dukkan Zunubai amma bisa sharadin tuba. Kuma
kada wani bawa ya yanke tsammani daga samun rahamar Allah. Domin rahamar Allah
mayalwaciya ce.
Bisa waɗannan Hujjoji nake Qara jan kunnenka da cewa ka
yawaita tuba tare da cikakkiyar nadama. Kuma ka nisanci dukkan wasu ayyukan saɓon Allah. Kuma ka yawaita istighfari da
ayyukan alkhairi ko yaushe. Da sannu waɗannan ɗin zasu zama dalilin kankare wadancan kusakuren
naka._
Kuma ina baka shawarar cewa kayi kokari kayi aure
domin kiyaye mutuncinka da addininka. Kamar yadda Annabi ﷺ yayi umurni kuma ya kwaɗaitar da al'ummarsa.
Allah ta'ala ya tsare maba imanimmu
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.