Ticker

6/recent/ticker-posts

Mutuwa A Cikin Watan Azumi

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Malam tambaya ce a kan wanda bai yi Azumin Ramadan ba saboda larurar rashin lafiya, har kuma ya rasu. Yaya za a yi?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Malamai sun saɓa a kan wannan mas’alar:

1. Waɗansu sun ɗauki cewa babu komai a kan magadansa.

2. Waɗansu kuma sun zaɓi cewa sai magadansa su rama masa, ko da kuwa Azumi Ramadan ne, ko kuma Azumin Bakance ne, ba bambanci.

3. Waɗansu malaman kuwa rarabewa suka yi, suka ce: Idan Azumin na Bakance ne, shi ne magadansa za su rama masa. Amma idan Azumin na Ramadan ne, to sai dai su biya masa da ciyar da abinci ga talakawa. Watau sai a lissafe adadin kwanakin da bai yi azumin a cikinsu ba a ciyar da abinci ga daidai wannan adadin na talakawa.

Wannan maganar ta ƙarshe kuwa ita ta fi bayyana a gare mu. Domin da haka ne manyan Sahabbai guda biyu: Aishah da Ibn Abbaas (Radiyal Laahu Anhum) suka bayar da fatawa, kamar yadda Ibn Hazm ya riwaito daga gare su da isnadi ingantacce a cikin littafinsa Al-Muhallaa .

Kuma wannan shi ne abin da suka fahimta daga maganar Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) da ya ce:

مَنَ مَاتَ وَعَلَيْهِ صَوْمٌ صَامَ عَنْهُ وَلِيُّهُ

Wanda ya rasu alhali ana bin sa Azumi, sai waliyinsa ya yi masa Azumin.

 Al-Bukhaariy (1952) da Muslim (1148) suka riwaito shi .

Musamman ma dayake su suka riwaito shi. Mai riwaya kuwa shi ya fi kowa sanin ma’anar abin da ya riwaito, kamar yadda Malamai suka faɗi.

Abin lura: Wannan maganar tana kan mara lafiyar da ya warke ko ya samu sauƙi ne, har ya samu damar ramawa amma bai raman ba!

Amma shi wanda rashin lafiyarsa ya doge masa har zuwa rasuwarsa, a kan wannan Malamai sun ce: Babu komai na laifi a kansa: Ba za a rama masa komai ba, kuma ba za a ciyar masa da komai ba, kamar yadda shi ma ba za a kama shi da laifin komai ba saboda hakan. (Tamaamul Minnah: 2/174).

WALLAHU A'ALAM

Sheikh Muhammad Abdullaahi Assalafiy

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/EbkKRXdFzNu4F8aQZbZ1Vx

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments