Ticker

6/recent/ticker-posts

Mu Guji Yada Sakon Da Bai Inganta Ba

TAMBAYA (03):

Assalamualaikum warahmatullah. Fatan muntashi lfy yakokari. Allah yayimn jagora ameen.

Dan Allah malam me menene gaskiyar wannan (👇)

FROM DR ISAH ALI PANTAMI.

IYAYENMU MATA GA WATA FATWA, DON ALLAH ADAURE AYI

1.Idan ki katashi da asuba kafin ki yi wa kowa magana sai ki dafa kan yaro koda yana barci sai ki karanta.

(Ihdina ssiradal mustakim ) 41 ki kwana 7 ban da fashi, to koda yaro ya fara rashin ji Wallahi zai daina, wannan mujarrabi ne kada a yi sakaci, ku yi wa yaran ku za ku ga natsuwa ta mamaki a tare da su

2. Idan yaranmu suna cikin barci a tofa musu inna anzalnahu kafa daya a gabansu da kirjinsu kafa dai daya bazasu tafa kusantar wani da miji ba inba mijinsu ba haka maza ma

3.Uwa takaranta Suratul Fatiha daga farko zuwa karshe kafa arba'in da daya 41 tsakanin magariba da Isha. Allah zai shiryarmata yaranta  su zama masu hankali masu ladabi da biyayya da tausayin iyaye

3.Idan yaranmu zasu kwanta suyi barci sai a tofa musu Bismillah a midigarsu kafa bakwai Yana Buda kwakwalwa

4.Don Allah ki turawa kowa kada ki manta da mutum ko da daya, Rabbi gifirli minkulli zambin wa'atubu ilallahi idan kika turawa kawarki  wannan, Allah zai yaye miki kowacce irin matsala idan kika dogara da Allah.

Allah Ya datar da mu, domin QudurarSa.

AMSA:

USMANNOOR: Wannan karya ce kawai aka yiwa Malam. Sunan wannan laifin "Plagiarism" ma'ana neman suna da sunan wani wanda ya shahara kuma babban laifine ko a hukumance ballantana kuma a addinance

Akwai wadanda kawai suke zama su tsara rubuce rubuce marasa tushe irin wadannan kuma su danganta hakan ga Malaman addini

Karya suke masa kuma indai basu nemi yafiyar malamba to tabbas Allah ba ya yafe laifin wani akan na wani

A iya sauraren karatuttukana da kuma binciken da nake ban taba jin makamanciyar wannan addu'ar ba daga bakin malaman Ahlus Sunnah wal jama'a

Kara karanta addu'o'in zaki fahimci da akwai kuskure dayawa da kuma karancin ilimi. Kamar abin da marubucin ya ce wai idan katashi kafin kayiwa kowa magana (To wanene ya ce idan addu'a zata amsu saidai sharadin hakan yazamo ba wanda zakayiwa magana da asubar fari ?)

Wai a kwana 7 banda fashi, kenan idan aka kwana 6 sai wani uzurin yasa akai fashi a kwana na 7 shikenan addu'ar bazata amsu ba kenan (Inaga ko marubucin bai karanta hadisin "Innamal a'amali binniyyati" ba) la'akarida duk niyyar da uwar yaron tayi baza'a amsaba sai an jera kwanaki 7 cir. Wannan ma bidi'a ne a addini

Da ya ce ko da yaron ya fara rashin ji wallahi zai daina, to a wanne hadisin ya dauko wannan addu'ar, na tabbata dai marigayi Shaikh Sa'id Alqataani bai kawota ba a cikin Hisnul Muslim. Idan kuma marubucin yana da hujja to kice wadanda sukai miki sharing rubutun su tambayesa ya kawo hujjar (Ballantana ma bazai samu hujjar ba a cikin sahihan hadisai)

Na 2 ya ce a tofa Suratul Qadr, to ina marubucin yabaro karanta Surorin Mu'awwidathayn (Falaqi da Nasi) da qarin Suratul Ikhlas (kamar yanda Shaykh Pantami ya kawo hujjarsa a cikin Sahihul Bukhari hadisi mai lambata 5748) a tofawa yara don nema musu kariya daga mutum da aljan ? Ina ya baro sahihin hadisin da Ma'aiki SAW ya ce: Duk wanda ya kwanta da alwala kafin yayi bacci, Allah SWT zai sa Mala'iku 2 suyi gadin mutum har gari ya waye ?

Na 3, naji marubucin ya ce uwa ta karanta Fatiha sau 41, a ina aka iyakance adadin Fatiha sannan kuma tunda Ma'aiki SAW aka saukarwa da Qur'aninnan sai mu tambayi marubucin shin Ma'aiki SAW ya taba karanta Suratul Fatiha sau 41 ga yar sa Nana Fatima ko ga dansa Ibrahim ?

Shin Annabi SAW da sahabbai su suka fimu fahimtar Qur'ani sai suka manta basu koyarda falalar hakan ga yayansu ba ko kuma shi marubucinne yayi qiyasi ya gano hakan, har ya sha'afa bai kawo mana hujja ba ?

A tofa musu Bismillah kafa 7 a madiga, wanene ya koyar da hakan ? Ma'aiki SAW, sahabbai, tabi'ai ko kuma tabi'uttabi'un ?

Na 4 menene hujjar marubucin na tabbatar da cewar Allah zai yaye damuwar duk wanda yayi sharing saqonnasa ? Da ya ce a turawa kowa kada a manta da ko mutum daya, (indai har ya tabbata rubutun haka yake daga asalin wanda ya rubuto) to tabbas marubucin yana fama da cutar jahilci domin kuwa Annabawa da Manzanni ne kawai sukeda tabbacin ga abin da zai faru ga wane shima sai Allah ya sanardasu domin kuwa babu masanin gaibu sai Allah SWT. Kuma sanin kanmune Annabta ta kare daga kan Ma'aiki SAW kamar yanda ya fada a sahihin hadisi

Don haka irin wadannan yaye-yayen rubuce-rubucen sunanan sunata yawo a media platforms kuma marasa ilimi ne suke yadasu don wata manufa tasu suna dilmiyar da wasu a rashin sani. Allah yasa su gano kuskurennasu tukunna domin kuwa saima sun gane mistake din sannan zasu tuba

A karshe kuma zanso na nusar dake irin addu'ar da Annabi SAW yake yiwa jikokinsa wato Hassan da Hussaini bin Ali (Allah ya kara musu yarda baki daya) wadda ta tabbata a cikin sahihan hadisai, kamar yanda Shaikh Sa'id Alqataani (Rahimahullah) ya kawo a cikin littafinsa na Hisnul Muslim (Asaka mawallafin littafin a addu'a domin kuwa a satinnan ya koma ga MahaliccinSa)

Inda ya ce: Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance yana nema wa Hassan da Husain tsari da wannan addu'ar (Harma ya ce babanku {Annabi Ibrahim AS} yana yiwa yayansa {Annabi Ismail da Ishaq} ga addu'ar kamar haka:

أُعِيذُكُمَا بِكَلِمَاتِ اللهِ التَّامَّة، مِنْ كُلِّ شَيْطَانٍ وَهَامَّةٍ، وَمِنْ كُلِّ عَيْنٍ لاَمَّةٍ.

"O'eezukuma bikalimatil-lahit-tammah, min kulli shaytanin wahammah, wamin kulli 'aynin lammah"

Bi ma'ana: "Ina neman muku tsari da kalmomin Allah cikakku daga dukkan shaidan da wata dabba mai dafi, da kuma dukkan wani mai kambun baka, mai cutarwa"

(Shaykh Pantami yakawo hujjarta a cikin Sahihul Bukhari hadisi mai lambata 3371)

Sannan kuma tun ran gini tun ran zance, akan yi tuya a manta da albasa ma'ana mutane sukan manta da addu'ar da Annabi SAW ya koyar kafin tarawa da iyali, wadda rashin yinta kan iya kawo yiwuwar a haifi yaro kangararre yazo ya dameku ya dami al'umma da shaidanci domin kuwa sakacin rashin neman tsarin Allah ne daman yasa shaidan kan shafi abin da Allah ya azurta ma'aurata tunma kafin a haifi yaron, addu'ar itace kamar haka:

بِسْمِ اللهِ اللّهُمَّ جَنِّبْنَا الشَّيْطَانَ، وَجَنِّبِ الشَّيْطَانَ مَا رَزَقْتَنَا.

"Bismil-lah, allahumma jannibnash-shaytan, wajannibish-shaytana ma razaqtana"

Ma'anarta: "Da sunan Allah. Ya Allah! Ka nisantar da shaidan daga garemu, kuma ka nisantar da shaidan daga abin da Ka azurta mu da shi"

Sannan kuma shima Prof. Pantami yakawo wannan addu'ar harma ya kafa hujja da cewar tana cikin Sahihul Bukhari tareda Fathi 4/181, harma ya ce ba abin mamaki bane idan kaga shaidanin yaro a wannan zamanin, kana bin salsala zakagano iyayensa basuyi waccan addu'ar bane

Don haka wadannan sune wasu daga cikin sahihan addu'u'o'in da suka inganta daga Ma'aiki SAW, batun wadancan kuma a barsu a inda suke. Muna roqon Allah ya bamu ikon fahimtar addini dakuma aiwatar dashi, ya Allah ka tabbatardamu bisa tafarkin magabata na qwarai (Salafus salih)

Wallahu ta'ala aalam

Subhanakallahumma, wabi hamdika, ash-hadu anla'ilaha illa anta, astaghfiruka, wa'atubi ilayk

Amsawa:

Usman Danliti Mato, Usmannoor_Assalafy

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

WHATSAPP👇

https://chat.whatsapp.com/Fc3hX6HoDt65aKhhKOiDpX

https:///

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments