𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum warahamatullahi wabarakatuhu.
Malam tambayata ita ce: Idan aka kira sallah, shin mu mata wai bai hallata ba
mu yi sallah sai liman ya idar za mu yi?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam warahmatullahi Wabarkatuh
Da zarar mukutarin lokacin sallah ya shiga, mace
za ta iya yin sallarta ba sai ta jira har sai masallaci sun idar sannan ta yi
tata ba, saboda sallar mace sallah ce mustaqilla (mai cin gashin kanta) kamar
yadda sallar liman da mamu take mustaqilla. Kawai abin da mace ya kamata ta
kiyaye shi ne ta tabbatar lokacin sallah ya shiga kafin ta yi tata, ko liman ya
idar ko bai idar ba.
Amma idan mace a gida ba ta iya gane cewa lokacin
sallah ya shiga, to a nan ya fi kamata ta jira har sai ta ji liman ya idar,
sannan ta yi tata.
Allah ne mafi sani.
Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.
Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance
Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/FmJ5Ojsns1KFolTP8qu9GT
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.