Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Wanda Yayi Zina Da Wacce Ba Musulma Ba

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum. Malam mun gode Allah saka da alheri da abunda kake mana. Mallam nine nayi NYSC na a Jos plateau state Mallam sai na haɗu da wata yer christan mallam sai Shaiɗan ya shiga tsakaninmu har mukayi zina sai tazo tayi aure mallam da tayi aure sai muka sake saduwa har muka kwana agidana amma kafun na kwana da ita bayan aurentan sai abokina ya ce mun tunda ita christan ce ba komi zayyu na kwana da ita sai na sadu da ita da aurenta mallam yanzu mene hukunci na mallam. ina cikin matsala ayi hakuri agaya mun naji hukunci na nagode ALLAH saka da alheri.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumus salam.

Hukuncinka daidai yake da na kowanne mazinaci.  Da farko dai kaci amanar kanka Kuma kaci mutuncin addininka amatsayinka na Musulmi. Sannan kaci amanar hukumar Qasarka wacce ta turaka domin yin bautar Qasa acikin al'ummar wani yankin da ba naka ba, tunda ka aikata irin wannan laifin.

Zinar da ka aikata da ita kafin aurenta da bayan aurenta duk laifin yana nan akanka. Shi abokin naka da ya baka wannan gurguwar fatawar, shin mecece hujjarsa acikin shari'ar musulunci?. Kaima kasan bashi da hujjah. Ka biye ma fatawarsa ne bisa son rai. Kuma tabbas Allah zai tambayeku dakai dashi.

Ta hanyar aikata zina ka fitar da kanka daga layin muminan kirki awajen Allah. Domin kuwa ita zina saboda girman laifinta awajen Allah, yana ha'data waje guda ne tare da shirka da kisan kai. Sune laifuka uku mafiya girma a Musulunci.

Allah yana magana acikin Alqur'ani game da siffar bayinsa na kwarai, ya ce :

وَالَّذِينَ لَا يَدْعُونَ مَعَ اللَّهِ إِلَٰهًا آخَرَ وَلَا يَقْتُلُونَ النَّفْسَ الَّتِي حَرَّمَ اللَّهُ إِلَّا بِالْحَقِّ وَلَا يَزْنُونَ ۚ وَمَنْ يَفْعَلْ ذَٰلِكَ يَلْقَ أَثَامًا

Kuma waɗanda bã su kiran wani ubangiji tãre da Allah, kuma bã su kashe rai wanda Allah Ya haramta fãce da hakki kuma bã su yin zina. Kuma wanda ya aikata wancan, zai gamu da laifuffuka. (Suratul Furqan 68)

يُضَاعَفْ لَهُ الْعَذَابُ يَوْمَ الْقِيَامَةِ وَيَخْلُدْ فِيهِ مُهَانًا

A riɓanya masa azãba a Rãnar Ƙiyãma. Kuma ya tabbata a cikinta yanã wulakantacce. (Suratul Furqan 69)

إِلَّا مَنْ تَابَ وَآمَنَ وَعَمِلَ عَمَلًا صَالِحًا فَأُولَٰئِكَ يُبَدِّلُ اللَّهُ سَيِّئَاتِهِمْ حَسَنَاتٍ ۗ وَكَانَ اللَّهُ غَفُورًا رَحِيمًا

Sai wanda ya tũba, kuma ya yi ĩmãni, kuma ya aikata aiki na ƙwarai to, waɗancan Allah Yanã musanya miyãgun ayyukansu da mãsu kyau. Allah Ya kasance Mai gãfara Mai jin ƙai. (Suratul Furqan 70)

Malamai irin su Ikrimah sun ce acikin Jahannama akwai wasu ramuka guda biyu masu suna "Gayyu da Atham" acikinsu ake jefa mazinata da sauran masu biye wa sha'awa anan duniya.

Ibnu Abid dunya ya ruwaito wani hadisi ta hanyar Haitham bn Malik Atta'eey (Allah ya yarda dashi) ya ce Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ya ce : "BAYAN SHIRKA BABU WANI ZUNUBI MAFI GIRMA AWAJEN ALLAH FIYE DA MANIYYIN DA MUTUM YA SANYA ACIKIN MAHAIFAR DA BATA HALATTA GARESHI BA".

Don Qarin bayani aduba tafseerin Ibnu Katheer, Suratul Furqan ayah ta 68-70.

Ga kuma hadisin da Bukhary da Muslim ta Tirmidhiy suka ruwaito ta hanyar Sahabbai daban daban, wanda Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ya ce "MAZINACI BA ZAIYI ZINA ALHALI YANA MUMINI BA" (WATO YAYIN DA MAZINACI YAZO ZAI YI ZINA, ANA CIRE MASA IMANI NE DAGA ZUCIYARSA).

Idan laifin zina ya tabbata akan saurayi musulmi, ko kuma yayi furuci da kansa cewa yayi zina, to hukuncinsa shine bulala ɗari kamar yadda ayar cikin suratun Nur ta bayyana.

Don haka nake yi maka nasihar cewa kaji tsoron Allah ka tuba zuwa gareshi. Shi Allah mai karɓar tuban bayinsa ne. Ka nisanci zina da duk abin da ya shafeta. Kaje kayi aure ka runtse idanuwanka daga kallon haram ko aikata haram. Domin akwai ranar da Allah zai tambayi kowacce ga'bar jikinka akan dukkan aikin da ka aikata da ita.

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/K7RkQRMf2b57l3UENoJ1Or

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments