Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Wacce Ta Bar Ibadah Da Gangan

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu akaikum Malam Dan Allah ina tambaya. Wata ce take gaya min abunda ta aikata abaya yanzu kuma ta shiryu take san taji yadda zatayi akan abin da tayi abaya. Wani lokacin da ya wuce bata azumi kuma bata sallah ko ance taje tayi sallah sai tace tayi, Kuma azumi koda ta dauka sai ta karya  babu wanda yasani. To yanzu kuma ta dage tana yi, shine tace yaya zatayi da waccen ta baya? Malam muna san karin bayani.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Akwai fatawoyi guda biyu akan wannan mas'alar. Wasu maluman suna ganin wajibcin ramukon dukkan salloli da azumin da kika barsu a baya koda sun kai na shekaru 20 ko 30 ko fiye da haka, saboda kasancewar sallah ita ce aiki mafi girma acikin rukunan musulunci. Shi kuma azumi yana daga cikin manyan ibadun dake bin bayan sallar.

Amma wasu Maluman suna ganin cewa ba sai kin ramasu ba. Sun dogara da hujjar cewa ai duk wanda yabar sallah da gangan ya riga ya kafirta. Koda kwaya ɗaya ce, kuma koda ya yarda da farlancinta akansa, ya riga ya kafirta. Shi kuwa kafiri babu wajibcin yin azumi ko zakkah ko sauran ayyukan musulunci akansa.

Yanzu kuma da kika tuba, to kin dawo musulunci kenan. Shi kuwa musulunci yana rushe duk wani laifin da mutum ya aikata acikin kafirci kamar yadda Manzon Allah ya fada acikin hadisi "MUSULUNCI YANA RUSHE ABIN DA KE KAFINSA".

Don haka yanzu sai kici gaba da kula da sallolinki na farillah, ki yawaita nafilfili, kuma ki yawaita yin azumin nafilah da sadaqoqi domin samun kusanci da Mahaliccinki.

Kada ki sake yin wasa da sallah domin ita ce marabar musulmi da kafiri. Kuma Manzon Allah ya ce "Abin da ke Tsakanin mutum da kafirci shine barin yin sallah".

Da kuma cewarsa "Sallah ita ce ginshikin addini. Wanda ya tsayar da ita hakika ya tsayar da addini. Wanda kuwa ya rusheta to ya rushe addini".

WALLAHU TA'AALA A'ALAM.

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments