𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Wani ne suka yi soyayya da wata yarinya, hasali
baidai Yi Zina da ita ba Amma sun rinka soyayya wadda ta saɓa ma shari'a, Karshe sun rabu, Shi ya Zama
bawan Allah nagari, salihi, Amma ita daganan ta cigaba sosai yanzu haka
yarinyar tazama karuwar gida, Shin ya zaiyi, shi ne ya Zama sanadiyyar fadawar
ta ga hakan.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Bābu wani mutum da zai yi wa wani nuni zuwa ga
wani aiki face sai ya samu kamasho na sakamakon wannan aiki duk lokacin da aka
aikata.
Wanda ya lalata mace ya ɗora ta a hanyar fasiqanci, har ya kasance
ta saba da abin, to zai cigaba da samun kamasho a duk lokacin da ta yi
fasiqanci da wani, koda kuwa bayan ya mutu, domin shi ne ya yi sanadiya ko ya
fara jefa ta a cikin wannan hali.
Zina tana da wahalar bari ga wanda ta ratsa
ruhinsa. Shiyasa Aʟʟαн(ﷻ) Ya ce:
وَلَا تَقۡرَبُوا۟ ٱلزِّنَىٰۤۖ إِنَّهُۥ كَانَ فَـٰحِشَةࣰ وَسَاۤءَ سَبِیلࣰا ٢٣
Kuma kar ku kusanci zina. Haƙiƙa! Ita alfasha ce, kuma
mummunar hanya ce. (Surah Al-Israa’i: 32)
Allah Mai ilimine a kan komai, Ya san cewa idan
mun kusanci zina za mu iya afka mata, kuma barinta ya fi fara ta wahala.
Duk da cewa shi be aikata zina da ita ba, amma ai
shi ne ya ɗora ta
a hanya, shi ya kusanto da ita zuwa ga zunubin, don haka ba zai tsira daga
zunubin da take samu ba.
Tunda shi yanzu ya tuba ya gyara ayyukansa,
wajibine ya same ta ya yi mata wa'azi. Kamar yadda be ji kunyar saɓa wa Allah tare da yarinyar ba, kada ya ji
kunyar zuwa ya yi mata nasiha. Ya yi iya bakin 'kokarinsa wajen fahimtar da ita
hatsarin abin da take aikatawa tare da azabar da Ubangiji Ya tanadar wa
mazinata.
Idan ta ji tsoron Allah ta daina, to madalla. Idan
kuma ba ta daina ba, Allah Ya ga zuciyarsa, sai ya cigaba da istigfari da
yawaita ayyukan alkhairai, tare da yin ayyuka masu gudana da za su amfanar da
shi har bayan mutuwarsa. Tabbas Allah Mai yawan gafara ne.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/GUq2GCCzlcdL6nknqLYYox
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.