𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum Malam Khamis ga tambayata, meye
hukuncin matar data yiwa mijinta sihirin mallaka a addinin musulunci.?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam warahmatullahi Wabarkatuh
Hakika Sihiri Yana Daga Cikin Laifuka Masu Girma,
Kuma Yana Ɗaya Daga Cikin Nau'ikan Kafirci, Sannan Yana Daga Cikin Abin da Ake
Jarabtan Mutane da shi Tun Shekaru Dubban Daruruwa da Suka Wuce Har Zuwa Wannan
Lokacin. Anayinsa Lokacin Jahiliyya Kuma Wannan Al'ummar ma Ba'a Barta a Baya
Ba Wajen Aikata Wannan Mugun Aiki. Jahilci Yana Daga Cikin Abin da Ke Sabbaba
Yin Sihiri da Kuma Karancin Imani.
Duk matar da tayiwa mijinta sihiri Ta aikata
Haramun. Kuma duk abin da ya aikata ba a saninsa ba wanda idan da Ace yana sane
ya aikata wannan abin za'ayi masa azaba akai, to ita Allah zai kama da
kwatankwacin wannan azabar.
Hakika Sihiri Kafirci ne Mai Yinsa da Wanda Yasa
Akayi Dukkansu Sun Kafirta Saboda Nassi Karara da Ubangiji Ya Kafirta Wadanda
Sukeyin Wannan Aikin, Inda Yake Cewa:
ﻭَﺍﺗَّﺒَﻌُﻮﺍ ﻣَﺎ ﺗَﺘْﻠُﻮ ﺍﻟﺸَّﻴَﺎﻃِﻴﻦُ ﻋَﻠَﻰ ﻣُﻠْﻚِ ﺳُﻠَﻴْﻤَﺎﻥَ ﻭَﻣَﺎ ﻛَﻔَﺮَ ﺳُﻠَﻴْﻤَﺎﻥُ ﻭَﻟَﻜِﻦَّ ﺍﻟﺸَّﻴَﺎﻃِﻴﻦَ ﻛَﻔَﺮُﻭﺍ ﻳُﻌَﻠِّﻤُﻮﻥَ ﺍﻟﻨَّﺎﺱَ ﺍﻟﺴِّﺤْﺮَ
“Sai Sukabi Abin da Shaiɗanu Suka Karanta Game da Mulkin Sulaiman,
Sulaiman Be Kafirta ba Sai dai Shaiɗanu ne Suka Kafirta Suna Koyawa Mutane Sihiri”.
Sai Allah Madaukakin sarki Ya Bada Labari Game
Kafircinsu Na Koyawa Mutane Sihiri. Duba da Wannan Ayar Zamu Fahimci Kafircin
Yin Sihiri Kai tsaye.
Duk Yanda Mai Sihiri Yakai ga Iya Yin Sihiri,
Shirinsa Bazai Taɓa Yin
Tasiri ba Sai da Izinin Ubangiji. Idan Allah Yaso Ya Jarabci Bawa Sai Ya Kaddara Sihirin Yayi Tasiri Akansa.
Allah Yana Cewa:
ﻭَﻣَﺎ ﻫُﻢْ ﺑِﻀَﺎﺭِّﻳﻦَ ﺑِﻪِ ﻣِﻦْ ﺃَﺣَﺪٍ ﺇِﻻ ﺑِﺈِﺫْﻥِ ﺍﻟﻠَّﻪِ
“Kuma Su Bazasu Iya Cutar
da Wani da shi (Sihirin) ba Sai da Izinin Allah”.
Hadisi Ya tabbata daga Sayyiduna Imrana bn Husayn
(rta) ya ce Manzon Allah ﷺ ya ce
: "BA YA TARE DAMU DUK WANDA YAYI CHAMFI KO AKAYI MASA CHAMFI DOMINSA. KO
KUMA YAYI BOKANCI KO AKAYI MASA BOKANCI DOMINSA, KO YAYI SIHIRI KO AKAYI MASA
SIHIRIN DOMINSA. WANDA YAJE WAJEN BOKA KUMA YA GASKATASHI CIKIN ABIN DA YAKE FAƊA, TO
HAKIKA YA KAFIRCE MA ABIN DA ANNABI MUHAMMADU ﷺ YAZO DASHI". (Imamul Bazzar ne ya
ruwaitoshi).
Mata kuji tsoron Allah, ku fahimci cewa samun
mallakar zuciyar miji ta hanyar amfani da layoyi ko kulle-kullen tsafi ba samun
yardar Allah bane. Hasali ma hanya ce ta kafirci da gushewar imani. Kuji tsoron
Allah ku tsaya bisa abin da yake na halal. Wato addu'a da kuma neman mafita
awajen Allah. Tare da Qaurace ma bin miyagun shawarwari irin na bokanci.
Babu wata hanya mallake miji kamar ladabi da
biyayya da girmama miji, da kyautata masa, tare da gyaran jiki, da kiyaye hakkokinsa da suke kanki, da
sauransu... In shã Allãhu Zaki mallaki zuciyarsa ba tare da bin waccan hanyar
bokayen ba.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Du5LNx31U9hDi6RQbbrzgW
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.