𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Mlm tambayata ita ce: Idan miji
ya yi amfani da matarsa ta cinyoyinta da matse-matsinta amma bai shiga cikin
gabanta ba. Shi ya gamsu ta hakan amma ita babu abin da ta ji, kuma ba ta fitar
da maniyyi ba, to wanka ya wajaba a kanta?
Allaah ya saka wa malam da alhairi.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Al-Imaam Muslim ya fitar da Hadisi cewa: Lokacin
da aka saukar da wannan ayar:
وَيَسْأَلُونَكَ عَنِ الْمَحِيضِ قُلْ هُوَ أَذًى ، فَاعْتَزِلُوا النِّسَاءَ فِي الْمَحِيضِ
Kuma suna tambayarka game da haila, ka ce: Shi ƙazanta
ne! Sai ku nisanci mata a wurin haila (Surah Al-Baƙarah: 222).
Sai Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa
Sallam) ya ce:
اصْنَعُوا كُلَّ شَىْءٍ إِلاَّ النِّكَاح
Ku aikata dukkan komai, sai dai aure (saduwar
jima’i) kawai.
Kuma Al-Bukhaariy da Muslim sun fitar da Hadisi daga
Maimunah Bint Al-Haarith (Radiyal Laahu Anhaa) ta ce: 'Duk lokacin da Annabi
(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) yake buƙatar wani abu daga
matarsa a halin tana haila, sai ya umurce ta ta ɗaura gyautonta (kamar sikel ko wandonta),
sannan ya aikata duk abin da yake buƙata.’
Malamai sun yarda cewa: Janaba tana samuwa ce ta
hanyoyi uku, kamar haka:
1. Fitowar maniyyi ta hanyar saduwa a tsakanin
namiji da mace.
2. Fitowar maniyyi a cikin barci ko a farke, kamar
ta hanyar yin wasa da al’aura (istimnaa’i), ko amfani da ‘budurwar roba’.
3. Nutsewar kan al’aurar namiji a cikin na-mace a
wurin saduwa, ko da kuwa maniyyi bai fita ba.
Don haka, idan miji ya yi amfani da wani sashen
jikin matarsa, ba cikin farjinta ko duburarta ba, kuma idan har ya yi maniyyi
da hakan, to ya yi janaba kuma sai ya yi wanka saboda haka.
Amma ita matar babu abin da ya same ta, matuƙar dai
ba ta fitar da maniyyi ba.
WALLAHU
A'ALAM
Sheikh Muhammad Abdullah Assalafiy
Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/GUƙ2GCCzlcdL6nknƙLYYox
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.