Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Shafa A Kan Khuffi Da Safa

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum. Dan Allah ina son in san hukunci game da shafa a kan huffi ko safa, idan mutum ya yi alwala kuma ya saka safa to idan har fitsari ya kama shi, shin idan ya je ya yi, shin idan har zai yi alwala sai ya sake cire safar ko kuma zai yi shafa a kanta? Na gode.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Shafa a kan khuffi ko safa sunnah ce ba farilla ba. Ya halasta idan mutum ya saka khuffinsa ko safarsa a lokacin da yake da tsarki, yayin da ya zo yin alwala ba sai ya cire khuffin ko safar ba, kawai sai ya yi shafa a kansu.

Haka nan idan alwalar mutum ta karye akwai khuffi ko safa a ƙafarsa, idan ya yi nufin sake yin alwala ba dole sai ya cire su ba, kawai sai ya yi shafa a kansu, dalilai da yawa sun zo a kan haka a hadisan Annabi ingantattu, daga ciki akwai hadisin da Sahabin Annabi Almugeeratu ɗan Shu'uba Allah ya ƙara masa yarda ya ruwaito, a inda yake cewa:

Na kasance tare da Annabi a halin tafiya, sai na yi nufin in cire masa khuffinsa, sai Annabi ya ce mini "KA BAR SU, DOMIN NI NA SA SU SUNA DA TSARKI", Annabi da ya gama alwala sai ya yi shafa a kansu”.

Bukhari 203, Muslim 274.

Baya ga wannan akwai hadisai da dama da Sahabbai suka ruwaito cewa Annabi idan ya saka khuffi a halin tsarki, yayin da zai sake yin alwala ba ya cire su don wanke ƙafa, barin su kawai yake yi, sai ya yi shafa a kansu.

A'immatul fuƙaha'i sun haɗu a kan halascin yin shafa a kan khuffi ko safa a lokacin alwala matuƙar lokacin da aka sa su an sa su ne a halin tsarki. Inda kawai suka yi saɓani shi ne adadin kwanakin da mutum zai iya yi yana shafa a kan khuffi ko safar.

Allah S.W.T ne mafi sani.

Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/Du5LNx31U9hDi6RƘbbrzgW

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments