Ticker

6/recent/ticker-posts

Shin Ya Halatta Musulmi Ya Yi Musafaha Da Kafiri?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Shin Ya Halatta Musulmi Ya Yi Musafaha Da Kafiri?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

الحمد لله العلي الكبير.

Dalilai Ingantattu sun tabbatar da hani dangane da fara yiwa kafiri sallama, bayahudene ko kirista, Kamar yanda Muslim yaruwaito a cikin Sahihin littafinsa (2167) Daka Abu huraira Allah yakara masa yarda Manzan Allah Sallallahu Alaihi wasallam ya ce: ( Kada kufara yiwa bayahude ko kirista sallama) .

Haka dalilai Ingantattu sun nuna za a Amsawa kafiri Sallama idan yayiwa Musulmi sallama.

Bukhari yaruwaito hadisi (6257) da Muslim (2164) daka Abdullahi Bin Umar Allah yakara masa yarda Manzan Allah Sallallahu Alaihi waslam ya ce: ( Idan bayahude ya yi muku sallama, yana cewa( Assalamu Alaikum, kace dashi: wa'alaika).

Haka wajan yin musafaha kada kafara baiwa kafiri hannunka dan kuyi musafaha, Idan yamiko maka hannu dankuyi musafaha saika mika masa.

Ibnul Ƙayyeem ya ce: Idan wannan sababin yakau, kirista ya ce: Maka Assalamu Alaikum Adalci shi ne kamayar masa irin Abun da ya yi maka Sallama dashi.

" Ahkamu Ahlul Zimmah".

"Sama" Abun da take nufi shi ne mutuwa.

Da Sallama da Musafaha ba'aso Musulmi yafara yiwa kafiri, Amma idan kafiri yayima yanada cikin Kyautatawa kamiƙa masa hannu kugaisa, kakuma Amsa Masa Sallama.

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/JLojawdOWYsEOeSHZMNdjf

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments