𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum. Dafatan Allah ya yi mawa wannan group albarka tare da karin ilmi ga malamin mu. Tambayata itace meye hukunchin mutumin da yake soyayya da wata mace bayan ya mata alkawarin aure kuma sai iyayensa suka zabar masa wata macen daban don ya aure ta?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumasalam warahmatullahi wabarakatuh.
Alhamdulillahi rabbil alamin wassalatu
wassalamu ala rasulillah.
Da farko dai kulla alaƙa ta soyayya da wata
mace irin wanda akeyi a wannan
lokaci bai halatta ba ko da kuwa da
niyyar aure ne, dalilan kuwa sune; Hakan
yana haifar da kalamai masu mattuƙar gaggauta faruwar ɓarna ta hanyan magana ta waya, chatting,
sakon katta kwana sms, kallo, taɓa
jikin juna wasu lokuta har da zina ko kuma mafi karanchi yaudaran juna.
Wannan bai hallata bah idan mutum ya yi haka
batare da neman iznin auren ta ba, yin
hakan wata irin salo ce ta yaudaran abokin alaƙa.
Idan muka ɗauka bisa ga kaddarawa shi wannan saurayi ya barta
neh saboda yin biyayya ga iyayensa to mai yasa ya yi mata alkawarin aure tunda
ya san cewa ba shi yake da cikakken iko da kansa ba game da al'amarin samar ma
da kansa matar da zai aura?
Hukunchi wannan mutumin hakika ya faɗa cikin kananan alamu na munafinci, saboda
ya nuna dabi'a irin ta ƙarya, karya alkawari, tare da yaudara, waɗannan duka kananan alamune na munafinci
kamar yadda yazo a cikin hadisin manzon Allah ﷺ: An karbo daga abu hurairah " manzon
Allah tsira da aminchin Allah su tabbata a gareshi yace ayoyin munafiki guda
uku neh idan zaiyi magana zaiyi karya, idan ya yi alkawari sai ya karya, idan
aka yarda da shi sai ya ci amana"
A karshe yakamata ya ma iyayensa bayani a buɗe cewan ya yi wa wata macen alkawarin
aure, idan sun amince Alhamdulillahi, idan kuma basu amince ba sai ya auresu
duka biyu. Idan ko bahaka ba Allah mai girma da daukaka zai iya yimasa hukunci
ta hanya da bai taɓa zato
ba.
Allah shine mafi sani.
Amsawa
Malam Aliyu Masanawa
Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/JoWs3feDfdyGE9yBsa1RSC
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.