Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Yin Fitsari A Tsaye Ga Mace Ko Namiji

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakaatuhu, Don Allah malam menene hukuncin yin fitsari a tsaye ga mace ko namiji a Musulunci?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Ya halatta ga namiji ya yi fitsari a tsaye, saboda hadisin da Bukhari ya rawaito cewa: "Annabi ya je jujin wasu mutane sai ya yı fitsari a tsaye" kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi na 222...

Tare da cewa duk hukuncin da ya zo dağa Annabi yana haɗa mace da namiji, in ba'a samu abin da ya keɓance shi ba, Tabbas fitsarin mace a tsaye zai jawo matsala wajan cikar tsarkinta, saboda yanayin halittar da Allah ya yı mata.

Yana daga cikin Ka'idojin sharia gabatar da wajibi akan abin da aka halatta, yin fitsari a tsaye ya halatta ga mace, saidai zai kai ga kunci wajan tabbatar da Dhahara, wacce sallah ba ta ingantuwa saida ita.

Duk hadisan da suka zo cewa Annabi ya hana yin fitsari a tsaye ba su inganta ba, sai hadisin Nana A'isha wanda Hakim ya inganta, in da take cewa: "Duk wanda ya ce muku Annabi ya yi fitsari a tsaye kar ku gaskata shi" kamar yadda Nasa'i ya rawaito a hadisi mai lamba ta: 29.

Malamai suna cewa: za'a dau maganarta akan tana bada labari ne, akan abin da ta gani, wannan ba ya kore a samu wani abin daban wanda ba ta sani ba, tun da ba koyaushe take zama tare da shi ba, yana daga cikin Ka'idoji a wajan malaman Usulul-fiqhi:

Duk wanda ya tabbatar da abu za'a gabatar da maganarsa akan wanda ya kore, saboda wanda ya tabbatar yana da Karin ilimi na musamman wanda ya buya ga wanda ya kore.

Don neman Karin bayani duba: Sharhu Assuyudy ala Sunani Annasa'i 1\26.

Allah ne mafi sani.

Amsawa:-Dr. Jamilu Zarewa.

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

 HUKUNCIN MACEN TA TAKE YIN FITSARI A TSAYE DON GUDUN KAMUWA DA CUTUTTUKAN SANYI (INFECTION):

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum malam Barka da safiya ya dalubai malam dan Allah tambaya nake mene ne hukuncin macen da take yin fistari a tsaye idan ta shiga banɗaki marar tsafta dan gudun kamuwa da cututtukan sanyi amma in tagama za ta wanke jikinta da ruwa sosai.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikis Salaam:- Toh Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam wata Rana Yana cikin tafiya shi da Sahabin sa ta Gefen wani Makabarta, sai wannan Sahabin ya ga Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wa Sallam ya Ciro wani ita cen Debino Danye wadda yake ɗauke da Ganye, sai ya zo ya kafa wannan Danyen ita ce debino ɗin akan Qabarin wasu, sai Sahabin ya Tambayi Annabi me ya sa ya yi hakan? Sai Manzon Allah ya ce masa ai wannan mutumin da ya ga kafa masa ita ce akan Qabarin sa, ya Kasance idan Yana Fitsari yana barin Fitsarin sa nna watsuwa akan Kafafun sa, toh wannan Dalilin ne ya sa ake Yi Masa Azaba a Cikin Qabarin sa, amma wannan ita cen da na kafa masa, ya ce toh zai samu ɗan Sauki wato Rahmar Ubangijin sa, amma ita cen tana Bushewa Azabar zai dawo. Toh Kin ji Hadisi. Don Haka akwai illa sosai ga mai yin haka duk Wadda Fitsarin sa yake watsuwa zuwa Kafafun sa toh Akwai Azabar Qabari na jiran sa.

Wadda Kuma Bai yarda Fitsarin yana taɓa jikin sa ko Kafafun sa ba, toh a Ranar Alkiyama Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam Ya ce Wutar Jahamnama ba za ta ci Kafafun sa da Fuskar sa da Hannayen sa ba, Dalilin Alwalar da yake Yi idan zai Yi Sallah.

Sabida haka Mata a kiyaye dokokin Allah domin wai ke a naki tunanin kina gudun Ɗaukar Infection a toilet ɗin mutane ki tsaya a Tsaye wai kina Fitsari duk Fitsarin ki ya watsuwa a kafafun ki, tana iya yiyuwa ma idan kin tashi wankewa iya wadda kika gani shi za ki wanke sauran kuma kin bar shi Kenan, ki je kiyi Alwala kiyi Sallah da Najasa a tare da ke Sallar ki bai yi ba.

Wajibi ne gare ku ki kiyaye wannan Mace kwata kwata ma bai dace ba ace kin tsaya wai kina Fitsari a Tsaye ba, ko da a ce Namiji ne wannan Kuskure ne balle a ce ga ke Mace, Hadisan da ake kawo akan cewa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya yi fitsari a tsaya wannan Hadisan ba su inganta ba, Darajar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya wuce ya kwatanta shi da irin wannan Siffar, don haka wajibi ne gareki ki kiyaye, na Farko ibadar ki yana cikin Hatsari, na biyu Azabar cikin qabarin ki zai same shi, to me kika yi kenan? a ji tsoron Allah Mata.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/Cnf26Q8MPqz9yUYU1nzqRq

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments