𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakaatuhu,
Don Allah malam menene hukuncin yin fitsari a tsaye ga mace ko namiji a Musulunci?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Ya halatta ga namiji ya yi fitsari a tsaye, saboda
hadisin da Bukhari ya rawaito cewa: "Annabi ﷺ ya je jujin wasu mutane sai ya yı fitsari
a tsaye" kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi na 222...
Tare da cewa duk hukuncin da ya zo dağa Annabi ﷺ yana haɗa mace da namiji, in ba'a samu abin da ya
keɓance shi ba, Tabbas
fitsarin mace a tsaye zai jawo matsala wajan cikar tsarkinta, saboda yanayin
halittar da Allah ya yı mata.
Yana daga cikin Ka'idojin sharia gabatar da wajibi
akan abin da aka halatta, yin fitsari a tsaye ya halatta ga mace, saidai zai
kai ga kunci wajan tabbatar da Dhahara, wacce sallah ba ta ingantuwa saida ita.
Duk hadisan da suka zo cewa Annabi ya hana yin
fitsari a tsaye ba su inganta ba, sai hadisin Nana A'isha wanda Hakim ya
inganta, in da take cewa: "Duk wanda ya ce muku Annabi ﷺ ya yi fitsari a tsaye kar ku gaskata
shi" kamar yadda Nasa'i ya rawaito a hadisi mai lamba ta: 29.
Malamai suna cewa: za'a dau maganarta akan tana
bada labari ne, akan abin da ta gani, wannan ba ya kore a samu wani abin daban
wanda ba ta sani ba, tun da ba koyaushe take zama tare da shi ba, yana daga
cikin Ka'idoji a wajan malaman Usulul-fiqhi:
Duk wanda ya tabbatar da abu za'a gabatar da
maganarsa akan wanda ya kore, saboda wanda ya tabbatar yana da Karin ilimi na
musamman wanda ya buya ga wanda ya kore.
Don neman Karin bayani duba: Sharhu Assuyudy ala
Sunani Annasa'i 1\26.
Allah ne mafi sani.
Amsawa:-Dr. Jamilu Zarewa.
Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
HUKUNCIN MACEN TA TAKE YIN FITSARI A TSAYE DON
GUDUN KAMUWA DA CUTUTTUKAN SANYI (INFECTION):
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu
Alaikum malam Barka da safiya ya dalubai malam dan Allah tambaya nake mene ne
hukuncin macen da take yin fistari a tsaye idan ta shiga banɗaki marar tsafta
dan gudun kamuwa da cututtukan sanyi amma in tagama za ta wanke jikinta da ruwa
sosai.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikis
Salaam:- Toh Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam wata Rana Yana cikin
tafiya shi da Sahabin sa ta Gefen wani Makabarta, sai wannan Sahabin ya ga
Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wa Sallam ya Ciro wani ita cen Debino Danye
wadda yake ɗauke da Ganye, sai ya zo ya kafa wannan Danyen ita ce
debino ɗin akan Qabarin
wasu, sai Sahabin ya Tambayi Annabi me ya sa ya yi hakan? Sai Manzon Allah ya
ce masa ai wannan mutumin da ya ga kafa masa ita ce akan Qabarin sa, ya Kasance
idan Yana Fitsari yana barin Fitsarin sa nna watsuwa akan Kafafun sa, toh
wannan Dalilin ne ya sa ake Yi Masa Azaba a Cikin Qabarin sa, amma wannan ita
cen da na kafa masa, ya ce toh zai samu ɗan Sauki wato Rahmar Ubangijin sa, amma ita cen tana
Bushewa Azabar zai dawo. Toh Kin ji Hadisi. Don Haka akwai illa sosai ga mai
yin haka duk Wadda Fitsarin sa yake watsuwa zuwa Kafafun sa toh Akwai Azabar
Qabari na jiran sa.
Wadda Kuma
Bai yarda Fitsarin yana taɓa jikin sa ko Kafafun sa ba, toh a Ranar Alkiyama Annabi
Sallallahu Alaihi Wasallam Ya ce Wutar Jahamnama ba za ta ci Kafafun sa da
Fuskar sa da Hannayen sa ba, Dalilin Alwalar da yake Yi idan zai Yi Sallah.
Sabida haka
Mata a kiyaye dokokin Allah domin wai ke a naki tunanin kina gudun Ɗaukar Infection a toilet ɗin mutane ki tsaya
a Tsaye wai kina Fitsari duk Fitsarin ki ya watsuwa a kafafun ki, tana iya
yiyuwa ma idan kin tashi wankewa iya wadda kika gani shi za ki wanke sauran
kuma kin bar shi Kenan, ki je kiyi Alwala kiyi Sallah da Najasa a tare da ke
Sallar ki bai yi ba.
Wajibi ne
gare ku ki kiyaye wannan Mace kwata kwata ma bai dace ba ace kin tsaya wai kina
Fitsari a Tsaye ba, ko da a ce Namiji ne wannan Kuskure ne balle a ce ga ke
Mace, Hadisan da ake kawo akan cewa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya yi fitsari
a tsaya wannan Hadisan ba su inganta ba, Darajar Manzon Allah Sallallahu Alaihi
Wasallam ya wuce ya kwatanta shi da irin wannan Siffar, don haka wajibi ne
gareki ki kiyaye, na Farko ibadar ki yana cikin Hatsari, na biyu Azabar cikin
qabarin ki zai same shi, to me kika yi kenan? a ji tsoron Allah Mata.
WALLAHU
A'ALAM
Zauren Fatawoyi
Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Cnf26Q8MPqz9yUYU1nzqRq
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.