Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Wacce Janaba Ya Same Ta Tana Cikin Haila

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamualaikum warahmatullah wabarakatuhu malam ya kokari Allah ubangiji ya saka da Alkhairi Ameen. Malam idan mace tana cikin haila setayi mafarki namiji na saduwa da ita to idan ta tashi zatayi wanka sakamakon mafarkin datayi kokuwa za ta bari har seta samu tsarki wato idan tagama haila.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salamu, ƴar uwa idan abubuwa guda biyu masu wajabta wanka suka haɗu a lokaci ɗaya, kamar janaba da haila, ya halasta a yi niyyarsu duka da wanka ɗaya, wato a yi wanka ɗaya da niyyarsu duka. Wannan shi ne fahimtar mafi yawan ma'bota ilimi da suka haɗa da Aɗá'u da Abuz Zinad da Rabee'a, da Malik da Sháfi'iy da Ishaƙ da As'háburra'ayi. Duba Almugniy na Ibn Ƙudama 1/162.

Amma idan janaba ya sami mai haila za ta iya yin wanka da nufin gusar da janaba, tare da cewa hailarta tana nan, saboda ta sami damar karanta Alƙur'ani, domin janaba tana hana taɓan Alƙur'ani da karanta shi, ita ko haila tana hana taɓan Alƙur'ani ne kawai ba tare da hana karanta shi ba, saboda haka za ta iya yin wankan janaba don ta fa'idantu da karanta Alƙur'ani, ba tare da ta taɓa shi ba.

Shi wankan yana gusar mata da janaba ne kaɗai ban da haila ɗin, kamar yadda Ibnu Ƙudama ya faɗa.

Duba Almugniy 1/154.

Allah ne mafi sani.

Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.🏻

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/BXjuXb1WxX99NV3OsXPnLV

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments