𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
malan ina da tambaya mijina kullum idan muka yi faɗa saiya dinga duka na, koyaya na
batamai rai sai duka, yamai Dani jaka sai idan dare yayi sai yace Yana bukatata
sabida ya kasance me bukata malan menene hukuncin wannan auran. Nagayama
iyayena sunce yadena duka Amma dukda haka bai bari ba Malan menene mafita Dan
Allah, Wlh malan komai kankantar laifi sai duka zagi yayitamun masifa mutane
naji. Dan Allah menene mafita?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Tabdi! Duk Macen da ta tsinci kanta a gidan namiji
mai duka tofa sai tayi hakuri kan hakuri. Domin wani ya mai da kumatun matarsa
kamar kumatun wani kato, sai dai kawai kaji ya falleta da mari, ya tadiyeta
yayi ta dukanta kamar baiwarsa shi ko kunya ma ba ya ji.
Yazo a Hadisi Annabi Yace ﷺ "Shin dayanku baya jin kunya ya duke matarsa
kamar yana dukan baiwa, zai duketa da rana sannan ya nemi saduwa da ita a
karshen dare shin baku jin kunya". Don haka ba komai bane matar ka za ta
yi maka kayi ta dukanta, kayi mata targade ka kumbura mata jiki wata ma har
tana zuban jini saboda mugun dukan mijinta. Ba'a kwana biyu ba tare da ya
lallasa matarsa ba.
Allah Maɗaukakin Sarki ke cewa:
...
وَاللَّاتِي تَخَافُونَ نُشُوزَهُنَّ فَعِظُوهُنَّ وَاهْجُرُوهُنَّ فِي الْمَضَاجِعِ وَاضْرِبُوهُنَّ ۖ فَإِنْ أَطَعْنَكُمْ فَلَا تَبْغُوا عَلَيْهِنَّ سَبِيلًا ۗ إِنَّ اللَّهَ كَانَ عَلِيًّا كَبِيرًا
"Matayen da kuke tsoron saɓawarsu, to ku yi masu wa'azi, ku qaurace
masu a shimfa, ku dake su, amma idan suka yi maku biyayya kada ku nemi hanyar
cutar da su, lallai Allah Ya kasance Mai ɗaukaka ne Mai girma. (Suratun Nisá'i aya ta 34.)
Malaman Tafsiri sun nuna cewa waɗannan matakai guda uku su ne miji zai bi
wurin mu'amala da matarsa a lokacin da ta saɓa wa umurninsa ko umurnin Allah, wato da
farko zai fara yi mata wa'azi da nasihohi ne, ba sau ɗaya ba, a lokuta mabambanta, idan ba ta
gyara ba sai ya qaurace mata a shimfiɗa, wato ya daina kwanciya da ita, idan duk ta qi
gyara halinta bayan waɗannan
matakai guda biyu, to yana iya dukanta amma ba duka mai cutarwa ba, kamar yadda
malamai suka bayyana a Tafsirai. Amma wasu malaman sun ce barin dukan ya fi,
duk da kasancewar addini ya ba da damar a yi.
Kaɗan
daga cikin Shawarar da zan baki a nan 'yar'uwa shi ne, Fushi da zafin zuciya da
ɓacin rai shi yake jawo
namiji ya daki matarsa, don haka idan yace wance kibar kaza kiyi kokari ki
bari, idan yace wance ayi mun kaza yi sauri ki tashi kiyi masa. Ki ɗaure wurin kaucewa abin da zai jawo ya
duke ki.
Sannan wani lokaci kace nace shi yake janyo namiji
ya kaiwa mace duka, don haka idan yazo yana fada yana zagye zagye kice wane
nasan abin da nayi ban kyauta I'm sorry, Allah ya huci zuciyar ka, daga nan
kiyi shiru yayi ta fadansa, domin kada yazo garin tanka masa ya faffaleki da
mari.
Sannan iya magana, idan mijin ki bahagon namiji ne
tofa sai kin iya magana ta yadda da yazo yana fadan nan sai ki kalallame shi da
sanyayan kalmomi, kiyi taushi kiyi sanyi ki zama kamar kankara. To idan mai
tausayine sai kaga yayi shiru ya daina fadan. Don wasu kwata kwata basu iyawa
namiji mai zafi sanyayan kalamai ba.
Sannan ki dage da addu'a, domin gaskiya rayuwar
auren ba zai rinka yi miki daɗi ba, tun
da wanda ya kamata yasa kiji daɗin shi
ne kuma yake kilarki. Ina rokon Allah ya gyara tsakanin ko wacce mace da mijinta
mai irin wannan halin.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/G5NSbo2TyHMD6bcoEfds5E
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.