𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Malam mene ne hukuncin auren kashe-wuta a shari'ance??
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wato dai Abin da ake ƙira da suna Auren-Kashe-Wuta shi ne,
Mutum yasaki Matarsa har Saki (3), kuma daga baya sai ya ji yanason yadawo
da'ita to kuma babu damar yin hakan a Shari'ance, to shi ne sai Mijin su haɗa
baki da wani abokinsa akan cewa abokin ya aureta daga baya kuma yasake sai
takoma gidan tsohon Mijinta, wato dai anufinsu shi ne kamar sun yiwa Shari'ar
Aℓℓαн (ﷻ)
wayo kenan, Ko-Shakka-Babu cewa auren Kashe-Wuta haramunne bai halattaba, kamar
yadda ya zo a cikin Hadisi Mαɳzσɳ Aʅʅαԋ (Sallallahu Alaihi Wasallam) Yana cewa:
" ﻟﻌﻦ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﻤﺤﻠﻞ ﻭﺍﻟﻤﺤﻠﻞ ﻟﻪ
" (ﺭﻭﺍﻩ ﺃﺑﻮ ﺩﺍﻭﺩ)
MA'ANA: Aℓℓαн (ﷻ) Ya
tsirewa Mai Halattawa (mai Auren Kashe-Wuta) da kuma wanda za a Halattawa (tsohon
mijin kenan).
Danhaka kenan idan Mutum
yasaki Matarsa har Saki (3) to bai Halatta yadawo da'itaba dole sai ta auri
wani Mijin kuma ingantaccen aure, kuma bawai ya aureta ba ne da nufin nangaba
yasake ta dan takoma wajen tsohon Mijintaba, Sannan kuma Sharaɗine ya
kasance Mijinda ta aura ɗin yataɓa
Jima'i da'ita aƙalla
ko da sau ɗayane, to idan Mijin ya rasu ko kuma yasake
ta dan raɗin kansa, to ya halatta takoma wajen
tsohon Mijhnta ya aureta, amma idan yazamana cewa Sabon Mijin da ta aura baitaɓayin
Jima'i da'itaba har suka rabu da shi, to haryanzu batazama halal ga tsohon
Mijintaba dole sai tasake wani auren kenan.
Amma idan ya kasance Mijin
dayasaki Matar saki uku, dama sunhaɗa
bakine da shi da wani abokinsa da kuma ita Matar akancewa shi abokinnasa ya
Aureta inyaso daga baya sai yasake ta ta dawo wajen tsohon Mijinta, to ko
shakka babu cewa wannan haramunne kuma Kaba'irace daga manyan zunubai, Sannan
kuma shi wanda ya aureta ɗin danufin haka aurensu
da'itaɗin Ɓataccene a Shari'a, idanma yasadu da'ita
to Zina kawai sukayi, hakanan kuma ko da ya sake ta to bai halattaba takoma
wajen Mijinta nafarkonba, idankuma har takoma yasake aurenta to sutabbata cewa
zaman Daduro (zina) sukeyi.
Amma idan shi wanda ya
aureta ɗin
babu wani haɗin baki dasukayi da tsohon Mijinnata
wataƙilama shi tsohon Mijinnata baisanma cewa
wannan ɗin
zai auretaba, amma shi kuma wanda zai aureta ɗin
dama azuciyarsa yanaso kawai ya aureta dan yasake ta taƙara komawa wajen tsohon Mijinta, to shi
ma aurensa da Matar Ɓataccen
aurene sakamakon mummunar niyyarsa kuma shi ma in yasadu da'ita to zina kawai
sukayi, danhaka shi ma ko da yasake ta to baihalatta takoma wajen Mijinta
nafarkoba.
Amma idan ya kasance ita
Matar dama azuciyarta tanasone ta auri wani danufin cewa idan suntare daga baya
zatanemi yasake ta ko kuma ta yi ta munana masa haryagaji yasake ta, to anan sai
Malamai sukayi Saɓani, Mazhabin HANABILA da
kuma wasu daga cikin Malamai kamar irin su: Hasanul-Basriy, Ibrahimun-Nakh'iy,
Shaikhul-Islam Ibn-Taimiyya, Suka ce shi ma wannan nau'ine na auren Kashe-Wuta,
danhaka shi ma bai halattaba sakamakon mummunar niyyarta, Sannan suka ce idan ɗaya
daga cikin su ukun (wato mijin ko matar ko kuma shi wanda zai aura) ya yi nufin
a yi auren kuma daga baya asake ta takoma wajen nafarko, suka ce duk hukuncinsu
ɗayane
auren baiyiba.
Sai dai Mazhabin MALIKIYYA da
kuma wani sashe na HANABILA suka ce idan har yasake ta to ya halatta takoma
wajen tsohon Mijinta suka ce niyyarta na auren Kashe-Wuta ba ta da wani tasirin
da za ta ɓata aurensu, Sai dai wasu daga cikin
Ma'abota Ilimi suka ce Maganar farko tafi ƙarfi,
tun da asali bai halatta takomaba harsai ta yi ingantaccen aure, amma yanzu
taje tayine da nufin nangaba takashe auren awani lokaci sananne suka ce bai
halattaba, domin yazama kamar ta yi auren Mut'ane kenan, Sannan kuma gashi ta
yaudari Mijin, ta cutar da shi, ta munana masa, dankawai yasake ta.
Sai dai Mafi yawa daga cikin
Malamai suka ce idan harMijinta nabiyun yasake ta to yahalatta takoma wajen
Mijinta nafarko, suka ce duk wanda igiyar aure ba ahannunsa takeba to niyyarsa
ta rabuwa ba ta da wani tasiri, domin ba ta da'ikon ta'iya sakin kanta dakanta
dole sai ansake ta, Sai dai abin da tayiwa Mijin na yaudara da munanawa suka ce
ananne takeda laifi, da kamata ya yi a ce ta yi amfani da hanya maikyau wacce
Mijin bazai cutu sosaiba, wato ta lallabashi har ya yarda su yi Khul'i ta mayar
masa da Sadaƙinsa, hakan shiyafi
dacewa.
ﻭَﺍﻟـﻠَّـﻪُ ﺳُـﺒْـﺤَـﺎﻧَـﻪُ ﻭَﺗـَﻌَــﺎﻟـَﻲٰ ﺃَﻋْـﻠَـﻢُ
Doмυn nЄMan Ƙarin bayani sai aduba waɗannan
Լitattafai kaMar Ӈaka:↓↓↓
" ﺷﺮﺡ ﻣﺴﻠﻢ
" (3/10
)
" ﺍﻟﻔﺘﺎﻭﻱ ﺍﻟﻜﺒﺮﻱ
" (6/298
)
" ﺍﻟﻤﻐﻨﻲ ﻹﺑﻦ ﻗﺪﺍﻣﺔ
" (7/138)
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Cnf26Ƙ8MPƙz9yUYU1nxƙRƙ
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
HUKUNCIN AUREN KASHE-WUTA
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mene ne hukuncin auren wanda yasaki matarsa saki uku, sannan ya sa wani ya aure ta yasaketa domin yasake aurenta tadawo gidansa?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد لله والصلاة والسلام على أشراف الخلق الله.
Idan mutum yasaki matarsa saki uku, ba za ta sake zama halal agareshi ba harsai wani ya aure ta, Aure na kwadayi bawai Auren kashe wutaba, Sannan suka rabu da ita, saboda fadin Allah madaukakin Sarki a cikin Suratul Baƙara ayata (230):
فَإِنْ طَلَّقَهَا فَلَا تَحِلُّ لَهُ مِنْ بَعْدُ حَتَّىٰ تَنْكِحَ زَوْجًا غَيْرَهُ ۗ فَإِنْ طَلَّقَهَا فَلَا جُنَاحَ عَلَيْهِمَا أَنْ يَتَرَاجَعَا إِنْ ظَنَّا أَنْ يُقِيمَا حُدُودَ اللَّهِ ۗ وَتِلْكَ حُدُودُ اللَّهِ يُبَيِّنُهَا لِقَوْمٍ يَعْلَمُونَ
Sa´anan idan ya sake ta (na uku), to, bã ta halatta a gare shi, daga bãya, sai tã yi jima´i da wani miji waninsa. Sa´anan idan (sãbon mijin, watau na biyu) ya sake ta, to, bãbu laifi a kansu ga su kõma wa (auren) jũna, idan sun (mijin farko da matar) yi zaton cewa zã su tsayar da iyãkõkin Allah, kuma waɗancan dõkõkin Allah ne Yana bayyana su ga mutãne waɗanda suke sani.
Abu dauda yaruwaito hadisi (2076) Annabi Sallallahu Aaihi wasallam ( ya tsinewa mai Auren kashe wuta, dawanda ya aura danta halatta gawanda yasaketa).
Albani Ya Ingantashi A cikin sahihu Sunan Abu dauda.\
Haramunne da mijin farko suka hada baki banda sanin daya mijin, ko matar da mijinne suka hada baki banda sanin ita matar, Malamai Sunyi Saɓani Amma ingantacciyar magana shi ne kota wacce hanya akayishi haramunne.
Shaikul Islam Ibnu taimiyyah ya ce: " Hasan da Naka'iy suka ce: idan daya daka cikin ukun yabada himma to Auren kashe wutane, mijin farko dana biyun da ita matar, An ruwaito haka daka Ibnul Musayyeeb, lafazin Ibrahimun naka'iy: idan niyyar daya daka cikin Su ukun ( Mijin farko, kona Biyu, ko matar) Auren kashe wutane, wannan nakarshen bataccene ba za ta halatta ga mijin farkon ba....
Fatawa Kubra na Shaikul Islam ( 6/298)
Domin Samun cikakkun bayanai a kan hakan duba " Madalibu Ulin nahayi (5/127) da Al-Mugny " (7/139 " da " Kashshaaful Ƙina'i" (5/96) da " Hashiyatu Dasuƙy " (2/258), Da I'lamul muwaƙƙe'iynah (4/36)
Saboda haka wannan Aurene batacce kuma bata halatta ga mijinta nafarko ba, kuma kaba'irane cikin manyan zunubai.
Zata halatta agareshi ne kaɗai idan miji nabiyu abisa radin kansa yanemi Aurenta, harsai yadan-dani dadinta ta dan-dani dadinsa sunzauna sosai, randa Allah yakawo musu rabuwa suka rabu, idan mijin farko yaga haryau yanada Bukata a kanta saiya aure ta tadawo wajansa.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.